Kwarata Littafi Na Ɗaya Complete Hausa Novel
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIR**GABATARWA:•* _Yabo da godiya da’iman wa abbadan na Allah ne. Salati da sallama su ne na fiyayyen halitta, shugaban annabawa kuma jagoran manzanni Annabi Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya._ *Shafin farko sadaukarwa ne ga kungiya mai albarka da marubutan cikinta, BRILLIANT WRITER’S ASSOCIATION Allah ya kara hadin kai.**Bazan manta da ku ba aminan albarka ina alfahari daku saina tunaku ko ina a bakin kura* 🐆*HALIMATU SADIYYA* _{{ My Leema }}_*HABIBA IDRIS* _{{ Hubbie }}_*HAUWA’U USMAN* _{{ Smasher }}_*MAIMUNA O . G* _Gaba daya littafin nan sadaukar ne gareku,_*ASMA’U ZAYYAN* _{{Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 1 ^^Shekaruna goma sha bakwai cas a duniya. Babana yana da mata hudu da “ya “ya hamsin da bakwai.^^ Mahaifina ya kasance dan auri saki ne, bakin abinda kunne na yaji mahaifina ya auri mata ashirin da takwas. Babana ya kasance talaka ne baya da wata sana’a wadda ta wuce “yan bige bige, ya gwanance wurin iya karya sannan kuma babu abinda kware dashi sai cin bashi………Talaka ne amma baya saka sutura irin tasu, idan kika gansa zaki rantse da Allah yana iya kyautar naira miliyan biyar, yasan dadin kudi sosai amma a sutura baya tausawa naira. ^^°Baya da gidan zama haka kuma baya da fili ko taki daya, munyi zama a anguwanni da dama sosai wanda duk anguwar da muka sauka suna mana lakabi da gidan inna ratata, ko kuma suce gidan yawa… Baya da aiki sai shaye shaye sannan kuma duk gidajen cacar dake garin katsina babu inda ba’asan shi ba, ya saka kansa caca wanda ake kira da nigerful, caca ce wacce take cinye tattalin arziki kuma ba kananan talakawa keyinta ba sai masu kudin gaske saboda idan har za’a buga wasan cacar mahaukatan kudine ake zubawa. Baya bayar da abinci haka kuma babu abinda ya damesa da rashin lafiyar “ya “yansa ko matansa, idan dai caca tayi masa dadi zai siyo kwanon shinkafa daya da kuma rabin doya,Da safe idan zai fita zai bayar da kudin kalaci ko wane daki naira talatin babu wani abinda ya damesa da yawanku. {}{{{}}} Wata rana can wurin wasan caccarsa aka cisa, amma baya da kudin da zai biya daga cikin abinda aka saka masa, dan haka suka cire masa sutura, tun daga inda ya buga wasan har zuwa gidanmu daga shi sai gajeran wando haka ya ratso mutane saboda tsabar shi tantirine har ya iso gida. Babu ruwansa da tarbiyar dan sa ko yar sa, shi yasa muka mayar da gidanmu kamar gidan karuwai, domin dai kowa abinda takeso shi takeyi dan babanmu yace sana’a itace tafi cancanta ga duk diyar daya haifa, ya daina biyan kudin haya yace mu zamu rika biya tunda kowa ya kawo karfi, dan haka duk yayuna suka tashi dan neman na kansu kowa ya kama sana’a amma banda ni, Abinda yasa kuwa shine, lura da irin kyawun da Allah yayi min, karkuyi tunanin kyawu na wasa ko ku lakaba abin da shirme ni nake gaya muku haka, bawai a gidanmu ba gaba daya zuri’armu babu yarinya mai kyau da daukar hankali kamar nawa…. Ina da kyau fiye da tunanin mai tunani, ina da diri daidai irin wanda maza ke so, ina da babban kugu sannan kuma Allah ya bani baiwar iya murzasa. Haka kuma ina da cikar kirji ina da manya idanuwa sannan ina da fari irin na fulanin asali, gaba daya zuri’armu babu mai haske na, idan na shigo taro mata sun gama wali haka kuma babu macen da zata kara tasiri harsai na bar wurin. Ni “yar gayu ce, na iya wanka kuma na iya shafa turare gaba daya bani da tsara idan na ziyarci wuri kamshina zaiyi ta kasancewa a wurin, haka kuma idan na barsa turarena zai dade bai daina tasiri ba, sannan duk gidanmu babu mai ilimin addini na wanda na samesa ta dalilin mahaifiyata saboda nayi sauka kuma bakin gwargwado nasan hadissai amma gaba daya zuri’armu babu mai barna irin tawa, ga sani ga barna dan duk yanda nake dakai a danginmu idan har na kwallafawa raina saina bata ka tou fa lallai saina bata maka rayuwa. Ku kasance dani a cikin littafin *KWARATA* domin jin wannan wane irin ubane ita kuma wace irin diya ce ? Kuma a cikin ita da uban waye yafi tantiranci ? Domin dai ni sana’ar da na zabawa kaina itace *KARUWANCI* danni a gani na itace sana’ar da tafi saurin kawo kudi. Babana mahaifi shine mutum na farko daya fara budemin lasisin karuwanci, domin dai a wurin wasan cacarsa yayi kyauta da budurcina, wannan dalili yasa na zabi sana’ar karuwanci, shine ya fara ni kuma naci gaba da kasancewa da wasan domin dai masu iya magana sunce so da yawa kana koyawa mutum abu amma saiya fika kwarewa. Ni babban kamfani ce kamar yanda ake sakawa a jikin kayan masarufi ace ingrediants to nima ina da nawa ingrediants in, kamar yanda company yake sarrafa abubuwa to nima company ce mai zaman kaina.Wannan labari a kiyayi juyashi ta ko wace siga domin yin hakan babban kuskure ne , ba kagoshi nayi ba a haka ta fadamin shi domin ina so ya zama izina ga matan aure, {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} Baba da Allah ka bamu naira goma zamu cika mu siyo magi, Ba tare daya kalleta ba yace me zakuyi da magi ? Cikin in ina tace dama kanzo ne zamu kwada,Naira biyar ya fiddo daga cikin aljihunsa, ya mika mata tare da cewa anshi idan kin samu kudin magin ki cika ki siyomin sigari…… Mahaifiyar ta dake tsaye tana daka kulin da za dasuci kwadon tace haba mai gida idan tana da kudin zata tambaye ka ? Itama bai kalleta ba yace wannan matsalarku ce keda ita, keni yi sauri ki kawomin sigarita jiranki nake ya fada tare da shashantar da maganar matar sa. Fa’iza mahaifiyarta ta kirata tare da cewa ina zaki samo kudin ? Bai bari Fa’izar ta bada amsa ba yace samarinta zasu bata ? Ke kike ganin bata da kudi duk yaran nan da kike kallo sun fiki kudi , ke ki hadomin da lemu mai sanyi kafin mai samomin abincin da zanci ta shigo. Fa’iza na kokarin fita daga gidan sukaci karo da Farida a bakin kofa, da yake gidan baya da zaure wanda ke wucewa ta waje ma zai iya hango na cikin gida, gidan kuma babu kaure sai labulen buhu da aka saka a jikin kofar, Babu sahihiyar katanga sai fasashshin buloluwa da aka jera, wanda ko yaro karami ya wuce zai hango na zaune. Fa’iza ganin Farida yasa ta tsaya tare da cewa, Farida da Allah ko kina da kudi ki rantamin na siyowa Baba sigari da lemu, anjima idan nayi awara zan baki, babu sauran kudi a hannuna duk na kasosu kasuwa canjin daya rage kuma nakai zubin adashe kinga lokacin biyan kudin haya ya kusa. Dan murmusawa Farida tayi tare da cewa ai tunda kika ganshi can ya mimmike kamar gawar sababi yau bashi da ko sisi, dan haka ma wallahi bazan shiga gidan ba komawa zanyi. Tun kafin Farida ta rufe bakinta ya fara kwarara mata kira amma tayi kunnen uwar shaggu dashi ta fice abunta. Rungume na fito da magena sanye cikin kayan islamiyata, nasha nikaf dina kayana sun dauki guga sai zabgaga kamshina nake da turarena dana siya na naira hamsin wurin masu siyar da turaren dure. Da sauri Baba ya tashi zaune tare da cewa Mamana barka da fitowa ? Murmushi nayi tare da cewa yawwa Babana barka da hutawa,Yawwa Mamana za’a tafi neman ilimin ? Eh Baba na fada a takaice, mikewa yayi tare da cewa muje in rakaki, wannan shine dabi’ar mahaifina duk inda zan tafi indai yana gida tou fa lallai shine zaiyi rakiya, A kofar gida muka hadu da Fa’iza sigarin ya ansa tare da cewa ki ajiye min lemun in dawo, shigewa tayi gida tare da cewa tom. A tafiye muke yana zukar sigarinsa hankali kwance, Baba wai har yanzu baka samu kudin da zaka siyamin keken ba ? Na tambayeshi, magen hannuna ya ansa tare da cewa machine zan siya miki uwa ta gari. Murmushin farin ciki nayi sannan nace Allah ya bada sa’a Babana , da amin ya ansa tare damin fatan alkairi dan mun iso bakin islamiya, magena na ansa na shige shi kuma yayi gaba. Yau inacikin farin ciki, domin dai idan har Babana yacemin zaimin abu tou fa ko zai mutu sai yayimin, yana min san da duk duniya bayayi wa kowa irinshi, yana kaunata fiye da yanda yake san kanshi, yana so ya ganni a cikin farin ciki saboda ina da sunan mahaifiyarsa. Yau ban wani yi karatu ba, hankalina ya tafi makarantar boko, na kagara gari ya waye dan injewa kawaye na da labari mai dadi zanyi sabon machine, nidai makarantar bokon haka nan nake zuwa dan ba abinda nake ganewa kaina fanko ne , a islamiya kadai Allah ya dafamin nake ganewa, amma a boko bana gane komai. Haka nan nake zuwa na dawo, Koda na dawo gida na kasa boye farin cikina, amma babu damar na fada, uban da ya kasa biyan kudin haya taya zan fada zai siyamin machine ? Dan haka naja bakina nayi shiru, saboda nasan idan suka ganni da machine in zasuyi tunanin kanin Mamana ne ya siya domin shine yake dauke da hidimata. Ina cire kayan islamiya ta na matsawa Inna sai ta bani kudi na siyowa magena kifi, bazan bayar ba shine amsar data bani , tare da hadamin da cewa itama kanta gari taci , saboda haka bataci kifi ba babu wanda zata siyama kifi. Gaskiya Inna bazan iya ba “yar madara gari taci ba, nice sheda saboda kin hana kanki kin cida magen banza, inna ta bani amsa, Tana fadar haka ta shige daki, na dade zaune a wurin ban samu mafita ba dan duk wanda ke gidanmu haushina yakeji kamar ya sakani wuta wannan dalilin yasa bana shiga sabgar kowa, Saida na gaji da zama na tashi a wurin ganin ban samu mafita ba, daki naje na kwantar da “yar jinjirar mage na nabar gidan dan samo mata abinda zataci, gidane babu kayan dadi daga gari sai kanzo inama amfanin talauci, shi kuma Baba ko tsoron Allah bayayi yazo gaban kowa yaci kaza dan zalinci, Amma duk wannan masifar Maman Fa’iza hada wani ciki ina tausayin dan nan da za’a haifa domin dai zai shigo rayuwar bala’e dama ya sani yayi zamansa baizo ba. Haka nayi ta galbaro a cikin anguwa babu tsiyar dana samo, dole na hakura na dawo gida dan lokacin sallar magrib yayi, Har bayan sallar isha’e Baba bai dawo gida ba, tunda naga ya wuce lokacin dawowarsa na sanyawa zuciyata salama tare da ba “yar madara hakuri, tunda ko mun tsaya jiransa bige zai dawo nasan yana can ya shawu iya shawuwa, mata hudu a gida amma yana neman matan waje. Tirrr da wannan hali. Tunani barkatai a zuciyata, ciki kuwa harda tunanin yanda zamu wayi gari ba tare da bango ya fado mana ba, dan gaba daya gidan nan ya rube ga wani irin hadari sai bakin rai yake, lallai wannan ruwan yau idan ya kwace gaskiya akwai matsala. Allah ka tsaremu da rayuwar talauci, rufe idona nayi domin inyi bacci addu’a nayi a fili cewa ya Allah ka tsare bayinka daga mutuwar katanga, kasa in kasance rayayya, in wayi gari cikin farin ciki, Allah ka shirya Babana ya daina abunda yakeyi, Inna ta ansamin da amin, tare da cewa Allah ya tsare gaba daya gidan, ban mata magana ba dan haushinta nakeji ta hanani kudin da zan siyowa mage na kifi, wani busashshen garinta can ta ajiyemin kuma banci ba, nasan idan naje makaranta gobe Amisty zata kawo mana shayi da biredi daga gidansu, shi yasa kafin kekena ya lalace nake saka “yar madara cikin kwandon gaban keken mu tafi tare itama ta maida miyanta. Da tunanin shayin gidansu Amisty nayi bacci, kuma dashi na tashi, tunda na farka naji yanayin garin da sanyi nasan jiya an kwana kwarara ruwa, dan haka tun kafin na sauko daga saman katifa nace Inna halan kin tara ruwan sama ? Na tara, ai jiya banyi bacci ba saida na tabbatar na cika komai nawa da ruwa, cikin damuwa na kara jan yagaggen zanin da nake rufa dashi tare da cewa wallahi bana san wanka da ruwan sama sai jikinka yayi ta wani sulbi kamar ka kama maciji, Banza tayi dani bata sake cemin komai ba, tsoki nayi tare da tashi ina mai mita cewa saidai kawai inyi sallah amma wallahi banyi wanka da ruwan sama, tsakar gida na fito rike da buta, ina maijin kyankyamin shiga bayinmu, Danni tunin duniya nayi sallama dayin fitsari daga tsugune, ko zanyi bayan gida makota nake shiga, wanka kuma dama tsakar gida nake wanke jikina baya da cikina kawai nake wanke wa a cikin bayin, ina watsa ma jikina ruwa tsikar jikina tana tashi. Dan gajeran tsoki nayi tare da daga labilen bayin na shiga, fitsari nayi na fito, a tsakar gida na wanke cinyoyina, nayi alwallah na dawo daki. Tun ina sallah Babana yake kirana tare da cewa uwar masu gida kiyi sauri mun makara naga har 7:30am, bana so Baba yana bina makarantar boko saboda duk kawata daya gani sai ya bita gidansu ni wannan abun yanamin ciwo. Tsaye na ganshi a kofar dakin mu yana daura agogo sai zuba kamshi yake yasha farar shadda sai daukar ido yake, murmushi nayi a zuciyata nace Baba kenan ko ba’aba ciki ba aba kaya, Katsemin zance zuci yayi da cewa maida hankali Mama mu tafi, mikewa nayi ba tare da nayi magana ba naci gaba da shiri, a gaggauce na shirya, tare da shafa “yar madara nace zan rago miki, Babana ya rikemin jakar makaranta muka fito daga gida……. _Gaba daya kaine sile, dan iska domin ni kai zan kira da kwarto, kaine silar rushewar rayuwata_ Cikin farin ciki muka fito daga gida, ina fadawa Babana yabi sannu karya bata jikinsa kasancewar ruwan daya kwanta saman kasa, Cikin jin dadi muke tafe muna fira, har mun kusa fita bakin titi ya sheko da gudu tuki na rainin hankali, tuki na gadara, tuki na wulakanci da rashin arziki, tukun da basa kaucewa mutane saidai mutane su kwauce masa, duk lokacin da zai shigo anguwar nan haka yake shigowa idan ya taka mutum ya taka banza, ko dabbobi gareka saidai ka daure abunka amma badai maganar ka sakesu ba. Tunda na hango motar nake cewa Baba dawo ta nan, amma kafin Baba ya hayo inda nake tuni yabi takan ruwan ya wuce shaddar baba ta koma brown, iya wuya raina ya baci kuma nayi alkawari ko zai kasheni tunda har ya tabomin Babana sai naci uwarshi a safiyar nan. Da gudu nabi motar ina watse hannuwa na yanda ake zagi dakkuwa, ina zaginsa, shima Baba biyoni yayi da gudu cikin tashin hankali, yana Mamana dawo, wanda yayi nisa bayajin kira, a kofar gidanshi da yake kiwon dokunan shi anan Baba ya sameni ya rikeni, shi kuma ya fito daga motar da bulala dorina irin wacce ake dukan dokuna da ita. Zagin dana taho inayi shi ya jawo hankalin mutane yasa duk mutane suka fito daga gidajen su, wanda ke waje suka iso wurin da muke dan ganin kwam, Rikeni sosai Babana yayi tare da rufemin baki saboda yasan ban iya zuciya ba, shima abokansa da sauri suka rikeshi tare da cewa *Dikko* karka daketa dan Allah yi hakuri, Babana kuma cewa yakeyi ranka ya dade kayi hakuri don Allah bata san kaine ba, Raina baci yayi ganin kamar mahaifina yana bawa yaron da haifa hakuri, dan haka na bambare hannun Babana daga bakina nace, nasan kaine kuma na zageka, ban kara maganar ba Babana ya wanka min mari. Tunda nake a duniya magana mai daci ko muni Baba baya fadamin ita, yana tattalin rayuwata yana kaunata amma yau saboda wani sakarai ni Babana ya daka,Ina cikin wannan bakin cikin Baba ya bashi hakuri da taimakon abokansa ya hakura suka ja banza suka shiga gidan da yake kiwon dokuna, A raina na dauka alkawari yanda Baba ya dakeni saboda Dikko saina rama dukana a wurinshi…… Hannuna Baba yaja muka taho yana bani hakurin marin da yayi min, wai yayi haka ne saboda Dikko kar yayimin wani abu, saida ya sakani napep sannan ya koma gida, Cikin bacin rai na tafi sch amma tabbas Dikko sai yaci kaniyarshi………{{{}}} {{{}}} 30/07/2019 Meelat Musa ce 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 2 Duk sanyi sanyin da akeyi saboda ruwan da aka kwana kwararawa a daren jiya hade da wani irin iska mai dadi amma Baba zufa yake kamar an tsare mai jegon da a saman gadon kara…… Cikin tashin hankali ya fara cire kayanshi yana dorawa a saman katanga, sai bakinshi dake motsawa babu wanda yakejin abinda yake fada saidai lokaci bayan lokaci yakan goge zufar data bulbulo daga jikinsa.. Ganinshi cikin wannan yanayi ya dagawa kowa hankali, gashi ya fita da farar shadda amma ya dawo da shadda kamar miyan goro, Idan yana cikin yanayin fushi baya so kowa yayi masa magana haka kuma bayasan ganin kowa kusa dashi, mata da “ya “ya suka gane haka shi yasa babu mai shiga sabgarshi, idan yana cikin yanayin damuwa Sultana kadai ke zuwa wurinshi ta bashi hakuri kuma ya sauka saboda soyayyar dake tsakaninshi da ita, Har na isa makaranta tunanin yi hakurin da Babana ya bawa jakin dana manta sunanshi nakeyi, sunanshi ya bacemin kwata kwata na manta sunan da aka kirashi dashi, nidai Allah yayi min jakar kwalwa, saboda ko “yan gidanmu ba dukansu nasan sunansu ba, amma na alakanta abun da yawan da muke dashi, yayin da wasu suke ganin rainin hankali ne……Ko a aji naso na bawa Amisty labari amma na manta sunan wanda zan fada mata, Amisty itace kadai abokiyata duk a ajinmu, abinda kuwa yasa na zabeta tana da kokari sosai kuma idan ana jarabawa tana bani satar amsa, Amisty irin yaran nan ne da idonsu ya waye tun suna cikin zanin jarintaka, bata da labari sai labarin maza, bata da aiki sai kallon B F, duk hotunan da zaka gani a cikin wayar Amisty hotunan tsiraici ne, walau nata walau na wasu, babu mai tarayya da ita saini kadai domin an dade da canfata cewar tana lesbian, nikam babu abinda ya dameni idan dai zata bani shayi nasha a tashi jarabawa ta bani satar amsa idan anyi rubutu nima tayimin a littafina shikenan banda wata damuwa. Lokacin dana shiga aji har malami ya shiga ya fita, ga rubutu nan a saman allo, bana gane sunan subject haka nan kawai na kalli allon nadan basar tare da cewa ashe malam harya fita. Da Eh kusan rabin ajin suka amsamin dan ina da masoya sosai, wasu saboda kyauna suke sona yayin da wasu kuma gashin kaina yake daukar musu hankali, okey shine abinda na fada kamar wata shegiyar baturiya dan itama okey din na dade ina koyonta a bakin Amisty dakel dai na samu ta zauna ram a cikin kaina, idan na fadi okey zakayi tunanin nasha turanci na koshi, amma babu abinda nake ganewa duk duniya sai sallolina biyar da Allah yasa na iyasu saboda nacin zuwa islamiya. Ina zuwa mazauni Amisty tace yau ina kika baro mana Baban namu ? Wata irin faduwar gaba naji dan nasan Babana shima ba karamin tantirin dan iska bane, kodai itama Amisty Baba ya zagaya ne ? Kinyi shiru, Amisty ta katsemin tunani na, maganata daukewa takeyi duk lokacin da ake tambayata abu, ina da nawar magana akan magana karama sai inja lokaci sosai, inayin in ina kadan wannan dalilin yasa ban cika yawan magana ba.Dan gajeren murmushi tayi tare da matsawa, zauna tacemin tare da maida hankalinta akan allo taci gaba da kwafar note. Zama nayi tare da cewa wane malami ne ya shigo ? Malama dai , wace malama ce ? Malamar English ! Me take koyawa na tambayi Amisty, turanci ta fadamin a takaice, murmushi nayi tare da cewa yarinya ai na gane dama dan inji idan zakiyi min karya. Kedai kika sani, ni ciro littafinki na rubuta miki idan kin gama rainin hankalin naki, Amisty ta fada…….. Bude jakata nayi sawon wani lokaci na kasa gano littafin da Amisty tacemin, tun ina dubawa a cikin jaka har na fito da duka littafan banga littafin turanci ba, dan gajeran tsoki nayi tare da cewa Amisty inajin nabar littafin a gida gaskiya. Daukar littafin tayi domin shine a sama, ajiyar zuciya nayi dan nima ta gane wata jar wuya ce , nace da yake jiya nayi karatu na dauka na barshi a gida ne, tou kawai tacemin bata sake magana ba, Haka malamai mata da maza sukaci gaba da shigowa har aka tashi daga makaranta, a bakin get din makaranta na tsaya ina jiran isowar Babana , tabbas nasan zaizo duk inda yake naji yana kusa dani yana zuwa bada jimawa ba. Banfi minti 2 ba Babana ya iso cikin wata irin kafirar mota yanzu ma yasha wanka ya murza wata irin dakekiyar shadda, sai kasaita yakeyi, murmushin jin dadi nayi domin dai Babana ya kankaro min mutunci na idan yayo wanka saboda dan gayu ne na koyi a idon duniya….. Cikin farin ciki na isa jikin motar na bude gidan gaba na wani kame abuna, zugar kawayena ne sukayo kanshi suna gaishe shi kamar yanda suka saba idan yazo daukata, Dan murmusawa kawai yakeyi tare da karkacewa cikin izza ya jawo wasu irin “yan dubu dubu wanda shi kanshi baisan ko nawa bane , Amisty ya mikamawa tare da cewa ku saka kati. Yana basu bai jira godiyar da suke mishi ba yaja mota muka tafi……, ba’a hana alkairi amma inajin bakin cikin abinda yakeyi, yabar gida da yunwa yazo waje yana alkairi, gida bai koshi ba yakai ma na waje banda gori da zagin iyayenmu babu abinda akeyi a cikin anguwa cewa Babanmu yana tsaye akanmu amma duk mu tsinannin Allah ne mu , haka zaisa ayi ta shiga da buhun na, na shinkafa gero masara katin katin na madara sugar da komai na sarrafawa idon duniya sun gani haka zai biyo dare ya kwashe abinshi yaje ya siyar wannan rayuwar zalinci ce, kuma bai sani ba kanshi kawai yake yaudara,Kasa hakuri nayi nace gaskiya Baba ni kadaina zuwa daukoni makaranta daga yau, ba tare daya kalli inda nake ba yace miyasa Mamana ? Kawai banajin dadin abinda kake ne , me nakeyi wanda bai miki dadi ba ? Wannan kudin da kake bayarwa dama gida kabawa su Inna sukaci abinci gidan kowa yunwa ta kamashi babu mai wani sahihin abinda zaici maganar daya ce kullum daga gari sai kanzo. Dariya yayi sosai tare da cewa Mamana kenan, aisu wannan mutane basa godiyar Allah, kima daina biye musu dan kona basu kudin cefane makalewa sukeyi, duk wanda kika gani a cikinsu daga mai tumaki goma sai mai shanaye babu adadi, idan na basu kudi boyewa sukeyi su hana ku abinci, suna can sun sayi dabbobi sunkai kauyika an boye musu, idan kuma kina magana akan abinda akayi ma wani kuma wannan halin shi ake kiran da hassada idan kikaga anyi ma mutum alkairi koya samu wani abu kikaji bakin ciki a zuciyarki shima hassada ne, kuma ita hassada tana cinye kyawawan ayyuka ne kamar yanda wuta takecin karmami, kuma yawan surutu yana sa mutum ya zama sakarai , ki daina hassada kuma bakinki shiru akan fadar wasu maganganu akaina idan kinki ji kuwa jahannama tsaye ko kina san ki shiga wuta ne uwar masu gida ? A , a Babana, amma zan fadawa su Inna gaskiya su daina irin abinda sukeyi zalinci ne, abun tausayi Baba kaji yaran nan suyi ta kukan yunwa wallahi ni har tausayinsu nakeji, kyalesu Mamana kina iya fada musu gaskiya suji haushinki barsu da halinsu…………….Maganarsa ta kare ne a daidai lokacin da muka tsaya wata majalissa. Fita muje, fitowa mukayi daga cikin motar muka tunkari taron dandazon mazan, kallo daya zakayi musu kasan cikakkin “yan tasha ne ko wannensu ya koshi da iskanci, Gaishe su nayi tare da matsawa daga gefe na zauna, kai bata abincin nan taci mu wuce, Babana yayi maganar a daidai lokacin da yake zama, Mikomin abinci akayi a cikin ci ka yada, { take away } gyara zamana nayi tare da juyawa inda babu mutane naci gaba da aiki, daga nan bansan abinda yaci gaba da faruwa ba, saidai naji hayani tayi yawa sosai anata bawa Babana hakuri ana rirrikeshi. Cikin tsananin bacin rai yake cewa da Allah ku sakeni wallahi saina kwakwale mashi idanuwa tunda nayi rantsuwa saina makantashi duk cikar garin katsina babu wanda ya isa ya hanani aikata abinda nayi niyya, da sauri na tashi nayi wurin Babana ina bashi hakuri, Abokin fadan Babana yake cewa, yo kai “ya “yan wasu nawa ka batawa rayuwa, saini kawai dan na kalli diyarka nace babban lambu zaka nunamin rashin kunya, cewa nayi zan shiga ciki ? Yabawa fa kawai nayi…. Sai kawai hankali ya tashi ? Sanin kanka ne duk kasuwar data burgeni saina ci ta hanyar shiga inyi siyayya a cikinta, duk gidan giyar daya burgeni idan na shiga saina sha kwalba biyar karanci kenan idan banda kudi, haka kuma idan naga gidan karuwai zan shiga ne inyi ta ciyayyar abinda ya sawwaka ba tare dana gajiya ba, Ka sani nima nasan haka, tunda saina gama nake ma gwanjon mata, banyi maka shamaki da matana ba haka diyana, kenan yanzu idan nace ka bani aron Sultana mu bata dare haka zakazo bakin kofa kayi tamin babatu ? Da sauri Babana ya rufe idanuwan shi tare da kauda kanshi gefe guda, tunda ni bansan abinda ya assasa fitinar ba, tou miye b’ata dare ? Kila shaye shayen su suke nufi, Jinjina kai Babana yayi tare da cewa kaci sa’a Mamana tana kusa amma zan maida ita gida na dawo na nuna maka karyar barikanci, yana fadar haka yaja hannuna mukayi gaba, har muka iso gida baiyi min magana ba, saida ya tabbatar na shiga gida sannan ya koma, Da sallama na daga buhun kofar gidanmu na shiga, gaba daya gidan suna tsakar gida uwaye da yara, yaran mazansu da matansu sun gurfana gaban wani dakekin mutum bakikkirin da cikinshi kamar ace Allah saukeshi lafiya, ni a tunani na assembly ake musu saida naga Inna na tuna ba makaranta bace. Saida nazo daidai inda suke nayi musu sallama kamar yanda na saba, ina kokarin wuce yace ke zonan, ban kalleshi ba kuma banzo ba haka kuma ban tsaya ba naci gaba da tafiyata na kusa shiga dakinmu naji yace waccan yarinyar ta raina mutane wallahi da nayi niyar yin hakuri amma na fasa sai kun tashi kunbarmin gidana. Hayani ta kwace bakajin maganar wani duk maganar ta koma iri daya yi hakuri , Allah ya taimake ka Allah ya kara arziki ka taimaka dan Allah karka tashemu, kaji hauka akan wannan rubabben gidan suke wani hadashi da Allah yayi hakuri, Allah ma yasa ya tashemu nayi addu’a ta a bayyane, Zainab ce ta tashi taje wurinshi tana wani irin karye karye, sai kace karyar gidan karuwa taga maza, magana tayi mishi babu wanda yaji abinda tace, saidai suka fita da mutumin, ganin tafiyarshi yasa kowa ya tashi yaci gaba da sabgar gabanshi, Babana da Zainab bansan yanda suka kare da mutanen su ba, haka Dikko bansan inda yake ba, dan an dauki wani lokaci banji labarin yazo anguwanmu ba, Kwanaki da dama sun shude, rayuwa tana tafiya babu abinda yayi gaba sai ci baya ake samu, amma ni na samu ci gaba na rayuwa domin dai Babana ya siyamin sabon machine kamar yanda yayi alkawari, a cikin matanshi kuwa maman fa’iza ta samu karuwa ta aihuwa, yanzu mun zama mu hamsin da takwas cas a gidanmu, Zaune nake a kofar dakinmu ina yanke farce na, “yar kyakkyawar magena tana shan madara, Baba ne ya siyomin madarar da yawa nake bata danni yanzu na daina tausayin “yan gidanmu tunda na gane duk munafikai ne, Kuma Babana ina gani duk safiya yana basu kudi amma bansan ko nawa bane, Kadangare ne ya fado daga saman bango fef, yana ganin mage ya ruga, ita kuma daina shan madarar tayi tabi kadangaren da gudu, nima binta nayi ina kiran “yar madara’ dan bana so tana cin kwarika, kadangare ya rugawa mage, ni kuma nabi magen haka muka fita a guje mu dukanmu muna gudu a tsakar santa…. Shima a guje ya shigo kamar yanda ya saba, ganin yanda mutane ke rike yaransu, masu tumaki na kamawa hakan ya tabbatar min dashi dinne ya sake dawowa, Nima kokarin kama “yar madara nakeyi, amma kafin in isa wurinta tuni dan iskan yabi ta kanta da mota ya wuce, jininta yayi tsartuwa a saman fuskata, yana wucewa na ruga na durkusa wurin magen, saida tayi miyau………. Sannan ta daina motsi, wata irin ashariya na babba tare da kurma wani irin ihu dan naji bakin cikin takata da mota da akayi. Cikin kuka na nufi inda yake, dama ina jiran zuwan shi saboda marin da Babana yayimin ta dalilinshi, shima din jirana yakeyi saboda zagin da nayi mashi waccan ranar, kowa yana jiran kowa, Bayan yayi parking ya fito ya zauna saman bayan mota, yauma bulalace a hannunshi yana wasa da ita, sai wani cin cingom yake sai kace karuwa… Abokan da yazo dasu waccan ranar yauma sune ya dawo dasu, mutum biyu tsaye a gefen damarshi biyu a haggunshi daya kuma tsaye ta gabanshi ya dade da bakin glashi, Lafiyayen kato ne mai kirar “yan dambe, singileti ce a jikinshi sai wani maski maski yakeyi kamar anyi mishi wanka da mai, dan nesa dasu na tsaya tare da cewa a cikinku waye yake tuka motar nan ? Na nuna motar da hannuna,Nine nan, mai kirar “yan dambe ya bani amsa, sannan yaci gaba da cewa ko wani abu ya faru ne ? Saida na kalleshi sama da kasa sannan nace da Allah mi yasa ka takamin mage ? Nayi maganar cikin sanyin murya, bashi ne ba nine na taka ta, kema idan kika tsaya a hanya gobe haka zanbi ta kanki in wuce kinji ko an mata, duk shi Dikko yayi maganar. Mai kirar “yan dambe ya anshi maganar cewa, ubangida na yanajin dadi yayi da yaga yana wulakanta talaka irinki, yana farin ciki idan ya zauna daga nan muka fara watso kayanku daga cikin kangon can, da nayi niyar murde miki wuya ki mutu , mutuwa irin ta beraye a ranar da kika wa mai gida rashin kunya, abu daya yasa ban kasheki ba kasancewar ke ba kowa bace, Murmushi yayi tare da cewa ta hanya mafi sauki za’ayi miki hukunci, juya kisha kallo, juyawa nayi a hankali dan inga abinda yake so na gani, babu gidanmu tuni wurin ya koma fili, lokacin da na juyo babu su Dikko babu alamarsu dan tuni sun jima da tafiya daga wurin. Salati nayi tare da tunkarar inda “yan gidanmu suke tsaye cirko cirko domin babu abinda aka bari suka fitar dashi komai an danneshi cikin kasa, sai motaci dake ta kwashe kasar wurin, Ina zuwa kusa da Inna da zumar tambayarta abinda ya faru ta rufeni da duka tare da cewa miya hadaki da Dikko kin dauko mana fitina kin jawo mana masifa Allah kadai yasan karshen wannan masifar. Cacai cacai kowa hayani yakemin a saman kai babu damar a dakeni Babana yaba mace rasid’i, ke kuma diyar gida kimin magana kijawa uwarki masifa, dan haka abinda kawai suke cewa miya hadani da *DIKKO ?* ……………. {{{}}} {{{}}} {{{}}}31/07/2019 Kubi sannu ku kasance da wannan labari, Taku a kullum Meelat Musa 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 3 Saida na gama kallesu daya bayan daya sannan nayi murmushin takaici da gefen bakina, kallon inda gawar “yar madara take na kalla wani makoko yazo ya tsamin a makoshi wanda ko yawun zan hadiye sai naji kamar lumfashi na zai dauke. Dikko………………….! Saida na jinjina sunan a zuciyata da kuma bakina, sannan na kalli dandazon taron ahalin gidanmu, nu na su nayi da dan yatsa manuni, sannan na dafa daidai kirjina da hannun haggu na , zanyi magana sai kuma maganar ta kasa fitowa dan bana iya magana a cikin yanayin bacin rai.. Wuri na samu na zauna ina ta sauke ajiyar zuciya, tsinuwa da zagi da Allah ya isa bansan iyakar adadin dozinan da suka saukemin ba, zagin ne dai kawai amma nasan bazan daku ba, Har yanzu babu wanda nayi ma magana kuma babu wanda na sake kallo, zama nayi na sauke kaina kasa, yayin da wasu suka gaji da tsayuwa suka durkusa wasu kuma suka bazama neman gida, dan su zasu nemo shi dan ko sun tsaya jiran Baba ko yazo bazaiyi wani abu ba, Bayan sun zauna ne sukaci gaba da tattauna maganar abinda Dikko yayi, ashe tun waccan ranar zagin da nayi masa ranar da zamu tafi makaranta tare da Babana bayan an bashi hakuri ashe baiyi hakuri ba. Da zai jira har na dawo daga makaranta ya takeni da mota ya wuce abinshi, tou bayan ya fito daga gidan da yake kiwon dokuna yaga Babana ya fito daga gidanmu,Shi Dikko mugune na gaskiya da gaskiya, duk duniya babu abinda ya raina yake kyankyami irin talaka, Dikko baya dariya haka kuma baya murmushi kullum fuskar nan tashi a hade take kamar hadarin tsakar dare, Bakya ganin dariyar shi kwata kwata, idan kuwa har Dikko yayi murmushi tou tabbas yaga cuta, idan kuma yayi dariya tou tabbas ku idan kuka ga abun sai kunyi kuka saboda tsabar tausayi. Danshi sai yaga mugunta yake dariya….. Bayan Babana ya wuce, Dikko ya kalli gidan ya sake masa kallo babu abinda baya gani na gidan daga nan waje inda yake tsaye, Kallon rainin hankali yayi ma gidan tare da bata fuska ya juyar da kai ya kalli daya daga cikin wanda suka zo tare sannan ya kalli agogon hannushi yace waye shi…. Ya nuna Babana da gidanmu… Bai tsaya yin magana ba ya bazama cikin anguwa, a cikin kankanin lokaci yaje ya samowa Dikko duk wasu bayanai daya kamata akanmu da rayuwarmu, Jinjina kai Dikko yayi bayan yaji komai tare da cewa karta mutu, amma barsu na jikatasu zata gane Dikko ba sa’ar ubanta bane daga wannan rana tsoron Dikko zai shiga zuciyarta maza a nemo min mai gidan daya basu hayar gidan, dan gajeren tsoki yayi tare da cewa talaka banza a banza, za’a nuna mata su kudi jigo ne masu nuna ishashshen iko. Daga wannan rana zata gane mai kudi ba’ayi masa hawan kasa, Cikin anguwa ya sake komawa dan binciken mai gidan da muke haya, aka fada musu anguwar da yake zama, da kuma wurin da yake zama dan kasuwancin shi, Bayan sun gama daukar duk bayanin da suke bukata, sukayi tafiyarsu, ashe Dikko gidan da muke haya yaje ya siya, kuma mai gidan da muke haya yace wa Dikko Babana baya biyan kudin haya tuni yayi niyar tashinmu sai wata yayata take biyanshi kudin haya daga cikin kaddarar rayuwarta, Tun wannan ranar Dikko ya biya kudin gidanmu, bayan ya biya tafiya ta kamashi, saida yayi wata biyu baya nan, shine fa yana dawowa babu notice kawai yasa aka rushe gidan…… Ajiyar zuciya na sauke bayan na gama jin duk bayanan su, yanzu ita Zainab zuwa takeyi anayin iskanci da ita kenan ? Amma ta bata wayanta, Yawwa an samo gida ku taso mu tafi, gaba daya sowar farin ciki suka dauka tare da mikewa suna cewa a ina gidan yake ? Gidan Alhaji Sabo ne yace mu zauna dan yaji abinda ya faru damu kuma ya tausaya mana sosai, amma duk watan duniya yace zamu rika biyan dubu goma, Eh hakan yayi babu wani damuwa, ku tashi mu tafi, yeay yara da manya sukayi ta shewa muka tafi dukanmu yayin da wasu ke cewa dan uwar Dikko yazo ya anshi wannan idan ya isa.Haka muka koma gidan Alhaji Sabo dake makotan gidanmu da Dikko ya siya, bamu da komai haka muka shiga gidan, kowa daga ita sai kayan jikinta, Nidai har yanzu banyi magana ba, abun duniya duk ya dameni kuma babu wanda yabi ta kaina ko Inna bata sake shiga sabgata ba sunyi ayari wuri daya ana ta shawarar yanda za’ayi a samo kudin Alhaji a bashi dan ya basu daga yau zuwa jibi su kawo mishi kudin shi. Har safiya basu samu mafita ba, haka kuma Babana bai kwana gida ba, bansan yanda akayi ba suka shiga suka fita suka bawa Alhaji kudin hayarshi ba, Kwanan mu hudu a sabon gida Baba yazo gidan, bai tambayi yanda akayi muka dawo ba haka kuma baibi takan kowa ba zance ya akayi aka biya kudin haya ba, haka kuma baiyi ma kowa magana ba saini daya, Uwar masu gida lafiyar ki qalau kuwa ? Lafiya qalau Baba na amsa masa, yace kwana biyu bakije makaranta ba har kawarki ta tambayeni ko lafiya ? Nace mata lafiya qalau gaskiya, kinsan nima bana nan naje Abuja, Allah sarki na fada, tou miya hanaki zuwa makaranta ne ? Ya sake tambaya na, saida na tattara bakina sannan nace Baba ai an rusa gidan, komai namu kuma an tattarashi an kwashe anje an zubar, banda kayan makaranta da littafai, Wayyo Allah Mamana, taso muje waje muyi magana, mikewa nayi nabi bayanshi, yana gaba ina binshi har muka fita kofar gida, Wuri muka samu muka zauna, muna zama Babana yace in fada masa dame dame nake bukata ? Nace masa ko kayan sakawa dukanmu gidan bamu da, kowa kala daya yake dashi, amma makota sun dan tattara mana kaya, murmushi yayi tare da cewa wallahi Uwar masu gida bata saka kwancen kaya, na dawo garin nan jiya da kudi fiye da tunaninki Mamana, Tunda naji abinda ya faru tsakanin shadda da yadi da boyal saida na siya kusan kala arba’in, takalmi da agoguna da hulana duk babu abinda ban siya ba, kayan suna can na kai dinki, Tsare Babana nayi da ido, a zuciyata kuma ina ganin rashin adalci irin na Baba, amma Baba bakada imani iyalinka na nan suna neman abinda zasuci karma ayi maganar wurin zama amma kai har lokacin siyan kaya kake yi Baba……? Duk a zuciyata nake wannan tunanin. Mamana, ya kira suna na, kallonshi nayi ba tare dana ansa ba, tunanin me kikeyi ? Bayan gani a duniya ! Idan har ina nan a raye baki da matsala nayi miki alkawari zan kula dake zan kange miki duk wani bakin ciki da damuwa, idan dan maganar kayan makaranta ne da littafai zan siyo miki komai ma ki daina damuwa, zan miki duk abinda kike so dan kiyi farin ciki Mamana , wallahi da ina da iko ko kuda da sauro da ban barsu sunzo wurinki ba, haka nake alfahari da aihuwarki farar mace lantarkin ciki gida, da nasan zan haifeki wallahi da ban tara wannan yame yamen “ya “yan ba, A ranar da aka aifeki a ranar naci makudan kudade a wurin wasan caca , tun daga ranar na gane ke mai sa’a ce, wannan dalilin yasa nasa miki sunan mahaifiyata ya karasa maganar yana murmushi, sannan yaci gaba da cewa zuwanki yasa talauci ya guji rayuwata, shi yasa na tattara miki buri da yawa domin nasan kedin mai arziki ce. Yana fadar haka yace tashi muje, tashi nayi nabishi, yauma cikin wata zakanyar mota muka shiga, ta gaji da haduwa sai sanyin A C ke tashi ga kamshi mai dadin shaka, Babana fa dan gayu ne gashi da wayewa kuma yana da kalar burgewa amma babu halin kirki. A daren nan saida Babana ya tabbatar duk abinda zan bukata ya siyamin, sannan muka wuce wurin dinki, tela ya aunani Baba ya biya kudi muka dawo gida, Tunda muka dawo matarshi Mariya ta tada hankali ta fara zagina tare da aibatani, bata san Babana yana tare dani ba da batamin ba, yana shigowa cikin gida yace mata ta tafi ya saketa, maimakon Mariya tayi farin cikin sakin kawai sai ta kama kuka, dani Babana ke aure ya sakeni wallahi sai nayi farin ciki sosai na rabu da rayuwar wahala, Amma Mariya saita durkushe tana bashi hakuri, wallahi ko sauraren ta baiyi ba, anyi an gama domin Babana idan ya saki mace ya gama da ita har abadan duniya baya maimaita mace idan har ya riga ya rabu da ita, dan yace ko sitira sawa daya yake mata mace kadai yake ma maimaici a rayuwar shi, shi yasa idan har ya saki yake mantawa da babinta a rayuwarshi. Fita yayi yabar gidan, Mariya kuwa kuka takeyi kamar zata mutu, wallahi ta bani tausayi sosai dandai ba hurumi na bane dana bashi hakuri kuma tabbas nasan zai hakura amma ba ruwana tunda ba hurumi na bane, kuma nasan tsakanin gobe da jibi tabbas saiya karo aure……. Zaune muke lafiya a gidanmu, rayuwar dai tana nan kamar kullum kowa shi yake cida kanshi, gaba gaba dai yayuna sun fara harkar barikancin su har a cikin anguwa, saboda Baba baya tsawa tawa dan yaga dama ma ya kwana biyar ko sati baya gida, Bayan sakin Mariya da sati daya Baba ya auro wata “yar fiririyar yarinya wacce zata tsaya iyakar sa’ata, kankanuwar yarinya itama mai zubin karuwai, wankan tarwada ce kallo daya zakayi mata kasan ta gaji da fekewa da bari… Idan kayi mata magana saita wani yamutsa fuska sannan zata daga idonta dakel tayi maka magana, kai nidai sam tsarinta bai burgeni ba haka kuma bata wani shiga raina ba, dan bata da kunya ko ta misali, caccakakkar “yar iska ce , tasha iskanci ta koshi, amma anyaBaba auro yarinyar nan yayi kuwa ? Rayuwata nakeyi cikin farin ciki, bani da wata damuwa shi yasa bana gane abinda kowa yake ciki a gidanmu, idan na fito daga dakinmu sai dare nake komawa saboda Innata bata san gani na, dan kishiyoyi sun tisota a gaba da habaici saboda ni, Babana yana kula dani sosai baya barina shiga damuwa, ina zuwa makarantar boko da islamiya , amma boko gugar kaya kawai nake inje, islamiya kadai nake da fahimta. Tafiye nake a cikin nikaf ina, sauri kawai nake na isa gida saboda hadarin daya taso, sai wani irin iska akeyi mai hade da kasa, walkiya da cidar hadari duk sun karade sararin samani, tunda na biyo santar nan banci karo da kowa ba har na iso inda nake tunanin nan ne gidanmu, Kamar yanda nayi hasashe haka na yanki hanya domin shiga gida dan bana ganin gabana saboda kasar data shigar min ido, na daga kafata in taka sumintin kofar gidan naji wayam, kara mika kafata nayi dan a tunani na ban tako daidai ba, kamar yanda naji daga farko yanzu ma haka naji, Da sauri na bude idona dan inga lafiya ? Filin wurin kawai na gani kamar ba’a taba gini a wurin ba, salati nayi na sanar da ubangijina to ina “yan gidanmu suka tafi ? Makota na shiga na tambayi inda “yan gidanmu suke, aka cemin Alhaji Sabo ya canza mana gida kafin wata ya kare mu tashi, tambayar dalilin tashin da rusa gidan da akayi nayi amsar da aka bani itace, *Dikko* ne ya siyi gidan amma wannan karon anyi ma kowa uziri ya fita da kayanshi. Bance komai ba saidai na sake tambayarta ina gidan yake ? Kwatanci tamin gida na like da gidan da aka rushe nan muka koma, ban sake cewa uffan ba na nufi gidan. Daki daya ne tak a gidan saboda haka kowa yana zaune cikin barandar dake tsakar gidan, sallama nayi amma babu wanda ya ansa min sallamar har Innarmu, nima ban sake sallamar ba na samu wuri na zauna tare da jan bakina na kameshi, Dukanmu a tsakar gida muka kwana yayin da wasu suka kwana a zaure, babban gida ne sosai amma daki daya ne ya gina shima ajiye ajiye yake a cikinsa, gari na wayewa na shirya na tafi makarantar boko, Baba bayanan sun tafi gasar caca, dan bai fadawa kowa sunan garin daya tafi ba, ni kadai yayiwa bankwana. A makaranta Amisty ta lura ina cikin damuwa, dan haka ta tambayeni abinda ya dameni, ban fada mata ba, saidai nace mata da Allah waye Dikko a garin nan ? Hmm su Amisty idon duniya saida tayi masa wani irin kirari sannan tace miya hadaki dashi ne ? Nace mata kawai dai labarinsa nakeji shi yasa nake san sanin koshi din waye. Abinda Amisty tacemin shine, yanda kike takama Babanki yana masifar sanki da kaunarki dan dole wannan misalin da kanki zanyi shi idan ba haka nayi miki ba tou fa lallai nasan baza ki gane ba, Dikko d’a daya tak a wurin mahaifin shi, yana da yayu mata sosai saboda suna da yawa gidansu suma, amma basu kai gidanku yawa ba, abinda yasa kuwa aka tara yawa a gidansu saboda san haihuwar d’a namiji da basu samu ba, Akan Dikko ya samu namiji daga shi kuma har zuwa yau din nan ba’a sake haihuwar namiji ba, Dikko gaskiya yana da kirki kuma shi ba dan iska bane amma gaskiya baya san raini,Yana da alkairi sosai amma shi baya dariya haka kuma baya murmushi, ni bayan wannan bansan komai ba haka dai kawai naji ana fada a gari, Gyara zama nayi tare da tambayarta shi kuma waye ubanshi ? Murmushi Amisty tayi sannan tace da Allah karki dauki ne wake da shinkafa mana, Dikkon ne a katsina baki san waye ubanshi ba ? Wallahi ban sani ba, na bata amsa, tashi tayi ta barni a wurin dan ita a tunanin na sani jan zance ne. Har muka tashi makaranta Amisty bata fadamin ko waye uban Dikko ba, ni kuma ana tashi makaranta ban tsaya komai ba na nufi gida tunda nasan Babana baya nan, Tunda napep ta ijiyeni, na hango kofar gidanmu daddabe da mutane, Dikko yana zaune a saman gaban mota ya kwantar da bayanshi saman gilas din motar kafarshi daya saman daya, ya tallabo kanshi da hannayen shi, kamar kullum yauma cingom yake ci, kananan kayane jikinshi ya dode da gilashi mai saukin duhu. “Yan gidanmu sun daddabe shi suna bashi hakuri amma ko inda suke bai kalla ba bare su sa a ransu zaiyi magana, sai waso mana kaya akeyi daga cikin gida, yayin da “yan zaginshi ke cewa ai tunda har kuka tabo mai gida a garin nan sai kun rasa gidan zama, wannan dinma ya siyeshi idan kunyi zuciya ku gina naku talakawan banza kuna jayayya da masu katsinar gaba daya, Inda jakar islamiyata take naje na duka na dauka, na koma gefe nayi tsayuwata tunda ko nayi magana babu wanda zaimin magana kowa haushi nake bashi, Wani dattijo ne shima makoci ne , yace ni inje in bawa Dikko hakuri duk saboda abinda nayi masa yake ta wannan saye sayen gidanje, dan gajeren murmushi nayi tare da cewa Baba kenan aini wancan dan iska nafi karfinshi wallahi baikai matsayin da zan kalleshi ba bare har na bawa banza hakuri, idan kuma har ka tilasta naje to lallai ina zuwa zan jawo dan iska ya fado kasa, Lallashi na dattijon nan ya farayi akan lallai sai naje na bawa Dikko hakuri, a lokacin har an gama fito da komai namu an fara rushe gidan.01/08/2019 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 4 Ya uzura min sosai akan naje na bawa Dikko hakuri dan haka na tunkari wurin kai tsaye zuciyana tana min tsake tsaken mugunta iri daban daban. Cike da bacin rai na isa wurin, kamar yanda na fadawa tsohon nan zanyi haka kuwa nayi, dan ina zuwa na kamo kafar Dikko da zumar na fadar dashi kasa ya karya kashin baya, Amma ina, dan ina riko kafar shi daya, ya tattakura yakai min halbi da dayan kafar da ban rike ba, hanci baya raina duka lokaci guda jini ya ballemin kamar an yanka kosashshiyar kaza, Yana halbina ya diro daga saman motar shima ashe yayo dagon muguntar shi yana neman inda zan sauketa ya huta, ganin jini yana bimin baki har yana digowa kasa yasa hankalina ya tashi, Sosai nayo kan Dikko, yaranshi suna kokarin rikeni yace su barni yanzu zai koyamin hankali yanda idan na ganshi da gudu zan canja hanya. Daga nesa mutane suka fara bashi hakuri dan babu wanda ya isa yazo kusa dashi, babu wanda ya kalla bare kayi tunanin ko zai saurare ka, kusa dani ya matso sosai, yasa hannuwan sa biyu ya riko min fuska, sai yanzu nakejin halbin da yayi min yake ratsa duk ilahirin cikin kokon kaina, gaba daya jikina ya saki ya koma kamar ba nawa ba, Sama sama nake ganin Dikko har yanzu bai daina cin cingom in da yakeci ba, saida yayi min kyakkyawan riko sannan ya cire gilashin dake fuskarshi ya kalleni ido cikin ido sannan yayi dan kyakkyawan murmushi, wanda ke nuni da mugunta ta tashi… Sai mun sake had’ewa an mata…yana fadin haka ya k’uma min kanshi da nawa wuri daya wanda haka yayi sanadiyyar daukewar gani na gaba, amma har zuwa wani lokaci goshina da nashi yana hade wuri daya, Bai sakeni ba saida ya tabbatar na tafi suma, dan tabe baki yayi tare da dage girarsa ta dama sannan ya sakeni ya zura hannuwansa cikin aljihu ya nufi motarsa dashi da tawagarsa suka bar anguwarmu. Ni kuma na fadi kasa somammiya, Allah sarki dan uwa mai dadi duk “yan gidanmu basu ji dadin abinda Dikko yayi min ba, sun tausayamin iyakar tausayi gashi babu mai kwandalar da za’a kaini asibiti, saidai aka samo kankara aka rika dandan na min a goshina tunda habo ne nayi, Abokin Babanmu shi yaji labarin abinda ya faru damu, yana da wani gida na Alhaji Sabo da aka saka a caca ya ciwo gidan, shine ya bada makullin gidan aka kawo mana yace mu bude mu shiga, Daukata sukayi suka shiga hadani tare da bani kulawa ta musamman, amma duk abinnan saida nayi sati daya kafin na dawk daidai,Babana har yanzu bai dawo ba kuma bamuji labarinsa ba ko ta waya, kuma har yanzu ban yadda na sake fita ba koda zaure saboda zuwa wannan lokacin bana san ganin Dikko ko inuwarsa, Gaba daya na jingine islamiya da wata bokon banza, daga tsakar gida sai daki, idan ina tsakar gida naji karar mota ma daki nake komawa, Satinmu ukku a gidan abokin Babanmu Baba baizo ba, kuma baiyo aike ba, shima kuma wannan gida da muke ciki Dikko ya siyeshi, ba’a gidan kadai ya tsaya ba duk gidan da yasan na hayane a anguwar saida Dikko ya sayeshi duk sun zama mallakinsa, tashin hankali da damuwa kowa ya shiga, Saida abokin Baba yazo yake fada mana cewa an kama Babanmu yana can an kulleshi saboda ya ranci miliyan biyar din wani abokinsu bai bashi kudin ba, shine ya kaishi wurin hukuma suka tsareshi,Kowa ya jinjina miliyan biyar saboda babu wanda yasan abinda Baba yayi da kudin nan, shiba gida ba, ba mota ba ba fili ba, haka kawai ya saka kanshi rikicin duniya. Inna na kalla data zabga tagumi tana d’igar da hawaye, cikin yanayin tausayi nace Inna wai da zaki auri Babana bakuyi binciken halinsa ba kafin auren ku? Banza Inna tayi dani bata bani amsa ba, tsoki nayi tare daci gaba da cewa muma mata muna da matsala yayin da muka hangi tilin dukiya da babbar mota hankalinmu, ganinmu da kuma tunanin mu sukan b’ace , idan aka samu kwadayayyar zuciya sai kuma takai mutum ta baroshi, kamar dai ku duk zuciyoyi ne da kwadayin duniya suka kawo ku nan suka barku, kiyi ta addu’a kema Allah sa ya sakeki ki huta. Kunga mutum da arziki bakusan taya yai ya samu abinsa ba, Inna dai bata tankamin ba, muka fito domin “yan gidanmu sunce muzo mu tafi wata primary school dake bayan gidanmu mu kwana tunda dare yayi kafin mu samu gidan zama, duk muna tsaye a tsakar gida dan Dikko yace wallahi idan muka kara cikakkun mintina biyar saiya kunna mana wuta, Cikin kyarmar jiki nacewa Maman Fa’iza “yan uwan Babanmu basu da kirki kowa ya zura masa ido dashi da iyalanshi sai wuta mukesha babu mai roka mana sassabci a rayuwarmu, ansa daya ta bani itace, ai babu ubanda yasa shi aure auren kuma basune suka sa duk yayi cikunnan ku aka haifo ku duniyar ba. Haka tayi ta surutai marasa dadi na bad’ala da rashin kamun kai har muka fita gidan muka tafi makarantar, koda muka fito motoci sunkai biyar masu zafi tsadaddu masu burgewa da daukar hankali, an haska fitilinsu duka, amma yau babu Dikko dan naji suna magana cewa mai gidansu yayi tafiya baya k’asa amma ya umurcesu da su tabbatar bamu kwana gidan nan ba, idan mun fita mun huta idan bamu fita ba a kunnawa gidan wuta, wannan shine sakon da Dikko ya aiko dashi, A makarantar mukaci gaba da zama cikin azuzuwa, { Classes } idan dalibai sunzo zamu fita waje idan sun gama suka tafi zamu koma mu zauna, ni na gaji na fadawa matan Babana waisu basu da gidan iyayensu ne ? Wannan wulakanci ai ya isa haka, kowa ta tafi gidan ubanta ta huta mana, ai fa yak’ai yak’ai kamar zamu cinyeni d’anyata saboda tsabar masifa, dole naja d’an bawan Allahna nayi shiru. Satinmu daya kullum sai an koremu kamar karnuka kuma kullum bama tafiya sai mun dawo, da safe kuma su tura yaransu su shiga bara cikin gari, rayuwa dai wulakantattar rayuwa mafi muni da k’ask’anci, Babana baya da adalci kuma baya da imani hakika zai tadda Allah, domin wannan zalincin yayi yawa. Ranar da muka cika kwana takwas aka koremu da karfin bala’e mukabar makarantar malaman suka kara da cewa gwamnati bamu ta ginawa makarantar nan ba muje can musan inda zamu zauna amma ba makaranta ba, suka kara jaddada mana idan suka sake ganin wata wallahi sai sun kaita an kulleta wurin “yan sanda, Nanfa Allah ya bamu sa’a cikin malaman wani ya ji kanmu ya bamu kyautar fili dan mun fada musu matsalar mu, shi kuma ya tausaya mana, saifa suka fara yahani akan fili yayin da kowa ke cewa saidai a siyar da filin a raba kudin aba kowa, Yayin da wasu ke cewa ayi hakuri a zauna, masu cewa ayi hakuri a zauna sun rinjayi wanda keso asiyar, dan haka dole suka hakura, muka dinguma zuwa fili, bayan munje akayi tamalmala ta malmala aka siyo buhunna dasu aka zagaye gidan , Wannan fili dai bazai ansu a wurin Dikko ba, nima ganin mun samu mazauni hankalina ya komawa tunanin Babana, {{{}}} {{{}}} Bayan wasu kwanaki, Rayuwata nakeyi cikin jin dadi, nidai Allah ya taimakeni bana bara saboda kanin inna yana kawo mana dauki da abinci, kunsan idan mace ta koshi tou fa lallai bata da aiki sai iskanci da rashin kunya, toni dana koshi nawa iskancin Dikko kadai yake nema ido rufe, kullum ina bisa hanyar zuwa tsohuwar anguwar mu, haka zan hau napep kamar duka kenan saina tabbatar mun kusa zuwa sai in dire abuna, wasu basajin fita ta wasu kuma suna gani idan suka bini basu kamoni ba saidai suyi min Allah ya isa, nima na fara dauko kadan daga cikin dabi’un Babana. Yauma direwa nayi, da gudu nasha lungu na shige wani gida, zaure na tsaya saida na huta sannan na tattaro natsuwa na shiga ciki da sallama, Cikin sakin fuska matar ta ansa min, wuri na samu kasa na zauna ina gaisheta, ta ansa lafiya lau, shiru nayi zuwa wani lokaci nace mata hajiya dan Allah kin iya rubutun wasika ? Murmushi tayi sannan tace niko na iya rubutun wasika, nace tou don Allah kitaima min mijin Yayata ne suka rabu shine yayi mata shegen duka ya raba mata kai da tab’arya tana can asibiti rai hannun Allah, kuma sai rubutun zagi yakeyi yana aikowa gidanmu, shine aka rubutomin ansa na maida mishi kuma takardar ta fadi, ni kuma idan na rubuta sabuwa zai gane rubutu na ne , amma ki taimakamin don Allah, ni na karanta wasikar kuma zan iya fada miki yanda take kiyimin rubutun nakai mishi don Allah……..! Ba tare da tunanin komai ba tace tou, daki ta shiga ta dauko jakar makaranta, da gani ta yara ce , a ciki ta dauko biro da paper tace min bismillah, duk ba tare da tayi wani dogon binkice ba ko yin nazarin yin hakan me zai haifar daga baya. Ni ko dadi naji sosai a zuciyata , tunda ni bazan iya rubuta uwar komai ba, amma nayi farin ciki sosai domin dai yau zanci uwar Dikko kafin in fara kashe dawanki dan iska. Bayani na farayi ta fara rubutawa, _Ka fita daga rayuwarmu yayin da ni kuma yanzun nakejin farin cikin shiga taka rayuwar, salon ka yana da matukar burgewa dan marasa tarbiyya, taya zaka fara rashin tarbiyya kuma ka gaji da sauri haka ? Ko kudin sayen gidajen ya kare ne ? To tunda kudin sayen gidaje ya kare nasan zakayi kokari ka samo kudin sayen dokuna, ina mai farin cikin sanar dakai daga yanzu d’innan har zuwa ranar da zaka bar zaman anguwar nan farin ciki zai bar zuciyarka, kuma zaman anguwar nan zai haramta a gareka kamar yanda ka haramta mana zama a cikinta, zanyi ta kashe dokunan ka harsai ciwon zuciya ya kama ka idan ka fasa kai ba d’an Babanka bane…………_ _Sultana ce, Allah ya bawa mai rabo sa’a, idan kaje Islamiya kace amin……_ Mikomin tayi bayan ta kammala rubutawa, godiya nayi mata sannan na fita, nayi tafiya mai dan nisa ina kokarin bi hanyar da zata sadani da tsohuwar anguwarmu na hango Dikko ya sauko daga saman doki……, Jar riga ce a jikinshi amma ba irin ja d’innan ba ja mai kyan kallo, sai jar hula akanshi irin wacce matasa ke gayu da ita, fesin cap, bakin wando ya saka wanda suke kira 3quater da rufaffin takalmi, sai bulalar da ake dukan doki a hannunshi, daga gani dai daga kilisa suka dawo, A fili nace shege mai kama da mata, cin cigom kamar tsohuwar karuwa, duk’awa yayi k’asa ya d’auki wani abu wanda ban iya ganewa ba, bayan ya d’auka ya koma saman dokin yayi mishi diddige tare da tsuke bakinshi irin yanda ake kora doki yayi gaba, Da gudu ya wuce ya wani d’an jirge saman dokin yayi kyau sosai bazan mishi haddasa ba gaskiya, ci gaba nayi da tafiya, kafin in ida isa wurin kuma naga ya wuce da gudu cikin mota kura tabi bayan motar sosai kamar guguwa ta taso. Hamdala nayi domin na samu damar farko da zan kashe doki d’aya daga cikin dawakan Dikko, saboda nasan wata mugunta d’aya da ake ma doki, ba’a ba doki ruwa idan aka dawo dashi daga yawo, idan aka bashi ruwa a wannan lokacin tou cikinshi k’ullewa yakeyi ya mutu. Nikaf ina na ciro na saka tare da gyara tafiyata na tun kari gidan kai tsaye, a kofar get in gidan nayi ma mai gadin gidan sallama, ya ansa cikin sakin fuska, nace mishi dama wani mutum ne da jajayen kaya a jikinshi yace in turo mishi kai yana can yana jiranka….. Na nuna mishi hanyar da Dikko ya wuce da hannuna , Cikin sauri ya wuceni ya tafi, yana wucewa na shiga cikin gidan, doki d’aya ne kad’ai wato shine dokin da Dikko ya dawo dashi, an d’aureshi a gefe kuma an cika bokiti da ruwa an ajiye shi kuma dokin yana ta bubbud’a hanci yana maida numfashi, Da sauri na kinkimi bokitin ruwan nakai gaban dokin na ajiye, aiko ina ajiyewa ya duk’ar da kanshi yaci gaba dashan ruwa, a daidai lokacin da mai gadi ya shigo dan yabi hanya baiga Dikko ba ya dawo, Kay kay kay ba’a bashi ruwa yana k’ok’arin isa dan d’auke ruwan na tareshi tare da cewa anshi yace ka ajiye mishi wannan takardar idan yazo da daddare zai karb’a, bai tsaya ansar takardar ba kuma baimin magana ba ya wuce, Murmushin nasara nayi daga cikin nik’af ina sannan naje na ijiye masa takardar a saman kujerar da yake zama na wuce abuna. Kafin ya isa tuni doki ya shanye ruwan dana ajiye mashi, sai dai abinda ba’a rasa ba, cikin tashin hankali ya ciro wayarshi daga cikin aljihu ya fara kiran wayar Dikko, Mai gida kazo akwai matsala dokin daka dawo dashi yanzu, gashi nan zai mutu, yana fad’in haka ya kashe wayarshi, Cikin k’ank’anin lokaci Dikko ya iso, a k’ofar gidan yayi parking ya fita da sauri ko murfin motar bai tsaya rufewa ba, lokacin daya shiga cikin gidan tuni dokin ya kwantar da kanshi k’asa yana ta zabura irin na fitar rai. Meya faru haka ne ? Dikko ya tambayi mai gadin shi ! Cikin daburcewa ya fad’awa Dikko duk yanda mukayi dashi , sannan ya d’ora da cewa ga takardar can daka bata ta kawo ta ajiye, ajiyar zuciya Dikko yayi tare da furta wace ce ita tayimin k’arya ? ‘Daukomin takaddar kila tana da wata manufarta a ciki, d’aukowa yayi yakai mishi, ya warware ya duba, cimimiye takardar Dikko yayi bayan ya gama karantawa ya dink’uleta wuri d’aya sannan ya jinjina kanshi, ya fito da sauri daga cikin gidan, Wurin motarshi ya tsaya, tare da kaima gaban motar duka sannan yace wallahi cikin k’ank’anin lokaci duk inda “yar iskar yarinyar nan take cikin garin nan ku d’auko min ita, yana fadi haka ya shiga mota yaja fa fafa ya tafi kamar zai tashi sama……. Har yayi nisa ya dawo, har yanzu mai gadin bai koma cikin gidan ba yana nan tsaye a wurin, yanzu daya dawo bai fito ba ya sauke glashin motar shi sannan yace, ku kawota wurina zan nuna mata nid’in d’and’an Babana ne wallahi wallahi wallahi sai tayi nadamar zuwanta duniya. Yana fad’in haka ya juya a guje ya tafi, lallai da ganin yanayin shi gaskiya ranshi a b’ace yake, tabbas idan har aka kamoni aka kawai Dikko ni a cikin wannan yanayin lallai Dikko kasheni zaiyi, Lokaci d’aya jikina ya d’auki kyarma naji fitsari ya kamani sosai, “yan hanjina suka juya ai bansan lokacin dana bar wurin ba, cikin tashin hankali na hau napep na nufi filin gidanmu, tun kafin mu isa na dire nayi gida da gudu…….. Da sallama na shiga, Babana na gani zaune dashi da abokanshi kuma sune suka amsa min sallama, cikin farin ciki ya kalleni tare da cewa daga ina kike Mamana ? Cikin inda inda na sosa kaina tare da cewa daga gidansu k’awata nake, murmushi Babana yayi tare da mik’ewa yace muje waje muyi magana, naso nayi masa gardama dan gani nakeyi kamar idan na fita zanga Dikko k’ofar gidanmu,Muna fita na fara tambayar shi ya akayi ya dawo ? Yace min su Bello sukayo belin inshi, akwai wani wasan caca da za’ayi an saka naira miliyan hamsin kin san na kware sosai a wasan caca babu wasan cacar da za’ayi a ci ni saidai ni in ciwo shi yasa ake min hassada. Gyara tsayuwar shi yayi tare da d’an jan dogon hancinsa, sannan yace Mamana kinsan ba’ayin wasan caca a bashi sai an saka k’addara, bani da k’addara sai kayan sakawata, na saka amma ance ba’asan sutura, tou Bello ya bani shawara wai in sakaki a matsayin k’addarata, Cikin rashin fahimta nace Baba kamar ya za’a sakani a matsayin k’addara bayn nima banda komai… Murmushi yayi tare da cewa Mamana kenan ai kuwa kece ma mai komai domin keda kanki kece babbar k’addara ta shi yasa na zab’eki a cikin duk “ya “yan hamsin da takwas dana aifa….. Kiyi hak’uri kawai ki yadda duk wanda yazo ya tambayeki kece k’addarata kawai kice Eh, danni na yadda da kaina babu ubanda ya isa ya ciwo uwata a wasan caca saidai ni inciwo uwarshi wallahi, Mamana ki yadda da Babanki nayi alk’awari baza a samu matsala ba, ki yadda dani kinji Uwar masu gida, ya k’arasa maganar yana mai rik’e duka hannaye na duka biyun yayi kalar tausayi. Tou Babana idan aka tambayeni zance Eh kawai ko ? Yawwa Eh zaki ce kawai ya wadatar, insha Allah gobe kamar yanzu muna cikin kud’i kuma ga Uwata a tare dani, ya k’arasa maganar cikin farin ciki, murmushi nayi mishi sannan muka koma cikin gida dan in fad’awa su Bello na yadda………. Allah yasa muyi juma’a lafiya, ubangiji ya sadamu da alkairan dake cikin wannan juma’a mai albarka, mugun ji da mugun gani tsaka mai wuya ubangiji ya tsare daga garesu, Allah ya karemu da jin kunyar duniya da lahira. Am3n, Jamila Musa ce 🤙🏻 02/08/2019⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 5 Muna shiga ciki tun kafin mu k’arasa inda suke zaune Baba ya fara cewa tou gata nan ku tambayeta kuji, a daidai lokacin da muka iso gabansu. Ina k’ok’arin durk’usawa Bello yace a , a basai na zauna ba in tsaya a tsaye akwai abinda yake dubawa. ‘Dan b’ata fuska Babana yayi tare da cewa kamar ya kana duba wani abu ? Ai a cikin sharud’d’an babu maganar wani dube dube, dan haka kabar yarinya ta zauna ka wani daina yi mata kallon k’urulla saboda rake ba sa’ar tsoho bane ba, dan koya bada kudin sa ya siya saiya ajiye tunda baida hak’oran cizawa, ya k’arasa maganar cikin sigar duniyanci. Murmushi Bello yayi tare da cewa, ai zamani tafiye yake da ci gaba ko ba’a tauna ba a tsotsa, d’an b’ata rai Babana yayi tare da cewa, kaga da Allah mubar wannan maganar muyi abinda ya had’amu, ya k’arasa maganar cikin nuna rashin jin dad’in zancen nasu. Gyara zama Bello yayi tare da cewa, haba Aliyu kasanni fa farin sani, kuma haka nima nasanka ciki da wajen ka, wane dare ne jemage bai gani ba ? Na hau tudu nabi ta gangare, kasan ko inacin kwarika wannan kwaron yayi min k’ank’anta shi yasa kaga bana cin shinge saboda na raina girmanshi duk da kuwa yana da mai sosai nafi gane kura ko da kuwa an soyata babu magi ba gishiri, kalmar dai d’ayace ake kira amma wurin hidimar da banbanci karka samu damuwa yaro ne sabon jini kuma bak’one a harka, yasan dad’in komai a duniya amma har yanzu baisan dad’in mace ba shi yasa kaga inata k’ara dubawa dan bana san a samu damuwa, Dariyar mugunta yayi tare da cewa , wash ashe na manta malamar Babanta jarumin gaske ne a harkar wasan caca, Shima Babana murmushi yayi amma da ganin murmushi kasan na b’acin rai ne, yace Bello kenan, shiga ramin kura ba abu ne mai sauk’i ba, idan har kaga na fad’i a wasan cacar nan tabbas duk wanda yayi k’ok’arin kusantar min Mama saina ga bayanshi, wannan shine sharadi na, Bello kuma cewa yayi kar muyi haka dakai Aliyu yaron nan d’an rigima ne, mu daina wannan maganar kawai dai muyi fatan Allah yaba mai rabo nasara, kallona yayi tare da cewa kin amince ? Jinjina kaina nayi tare da kallon Babana sannan nace na yadda………… Dariya Bello yayi tare da cewa magana ta k’are mata tacewa mijinta shege, Kafad’ar Babana ya daka tare da cewa Aliyu muje, juyowa yayi ya kaleni tare da cewa yarinya ki shirya, idan kinga Babanki tou fa lallai an ciki a wasan caca, idan kuma kika ga Bello tou Babanki ya cinye matashin nan, ganinmu shine zai tabbatar miki Babanki yaci caca mu kuma munzo miki murna ne, suna fad’in haka sukayi gaba abunsu, Bayan tafiyarsu ina zaune suku suku dani kamar asirin mayya ya tonu, ni ba Babana ne damuwata ba Dikko shine tashin hankalina, yace duk inda nake a gano ni, sai yanzu na gane na tafka babban kuskure dana rubuta suna na a jikin takarda, lallai na cika babban dak’ik’iya. A b’an garen Dikko kuwa nema na sukeyi kamar rai da mutuwa, babu wanda yasan inda muka koma, daga makaranta prymary babu wanda ya sake jin labarinmu, Rashin gani na yasa suka fara ba Dikko hak’uri, amma fur Dikko yace wallahi kafin sha biyun dare sai an nemoni idan har ba’a ganni ba zai iya sargafe kanshi ya mutu, Duk iyakar yanda suka so Dikko ya hak’ura ya k’iya, ba nemoni bane wahala a wurinsu suna tausayin irin a zaftuwar da zanyi a wurin Dikko, dan ya fad’a musu ba mutuwar dokin ya b’ata masa rai ba, d’an marasa tarbiya dana kirashi dashi, bama shine baida tarbiyar ba iyayenshi ne basu da tarbiya abinda nake nufi kenan,sai kuma idan ya fasa shi ba d’an Babanshi bane. Wannan sune munanan kalamai masu muni da suke ta zungurar zuciyar Dikko. Dikko yana da zuciya sosai, kuma fushin shi baya da kyan gani, idan ya nace akan abu sai yayi babu wanda ya isa ya hanashi, idan yace bayayi babu wanda ya isa ya tursasa masa yayi abinda baisa kanshi ba. Yau Dikko yana cikin matsanan cin b’acin rai, yayin da ni kuma nake cikin fargaba da tashin hankali, dan yanayin dana ga Dikko d’azu ya bani tsoro, Duk wanda yaji wannan abun yasan nice bani da gaskiya, domin ni naje har inda yake na jawoshi fad’a, ya Allah ka rabani da Dikko daga yau insha Allah bazan sake janshi fad’a ba, ka mantar mishi dani a rayuwarshi kuma ka bashi hak’uri a zuciyarshi, ya daina nemana, Misalin 10:45pm Babana ya dawo gida, dashi da abokinshi Bello a lokacin har nayi bacci Baba yasa a tadoni in samesu kofar gida…… A waje na samesu, gaishe su nayi tare dayi musu sannu da zuwa, Bello kad’ai ya ansa amma Babana ya kasa magana, Bello ne ya fara magana kamar haka. Maryam, wannan shine sunan da Babana ya sakamin, wato sunan mahaifiyar shi, darajar wannan suna ne yake kirana da Uwar masu gida ko yace Mamana, Bello yaci gaba da cewa an samu matsala mahassada suka cuci Babanki bandai san yanda abun ya faru ba gab da za’a fara wasa kwalwarshi ta juya, ba buk’atar dogon bayani kawai dai Aliyu ya fad’i wasa.Tou idan ya fad’i sai kayi ya ya kenan ? Na tambayi Bello, sai zamu tafi dake wurin wanda ya ranta masa kud’in, dan a can basu yadda da ansar mace ba, sai wani ya buk’ata dan haka ya bada kud’in yace a kawo mishi ke, Waye shi ? Na sake tambaya, a tak’aice ya bani amsa cewa idan kinje kin ganshi, zan k’ara magana Babana yace Mamana babu abinda zai faru kiyi hak’uri kuje dan bana tunanin akwai wanda ya isa yayi miki wani abu a cikinsu saboda sun san waye ni, na bud’e bakina zan sakeyin magana a karo na biyu, wanda Babana ya sake tare min numfashi na da cewa idan dai har kare zai iya farautar kura tou lallai wani abu zai iya shiga tsakaninku, idan kuwa kare bazai iya ba tabbas zasu dawo dake, dan duk rashin kunyar kare ta gida ce, bishi kuje…. Yana fad’in haka ya juya da zumar shiga gida, Da gudu nabi bayan Babana na rik’e hannunshi ina kuka nace haba Babana laifin me nayi maka zaka sayar dani ? Cikin kulawa ya kalleni tare da gogemin hawayen da suka zubo saman fuska ta sannan yace, baki sawuwa Mamana saboda nima bada kud’i nasiyo ki ba, haka kuma bakya satuwa tunda Allah shine ya azurtani dake, hak’ik’a kuma baza ki ciwo ba ta sanadiyar wasan caca ko kun tafi sai kun dawo, dan haka ki zama d’iya mai biyayya a gareni,…. Baba…..Mamana ya fad’a kafin nace komai, yaci gaba da cewa, so guda d’aya ne tal a zuciyar ko wane d’an adam, amma shi wannan san a duniya za’a kasa shi kaso mutane so adadin haka, uwa, uba, d’a da kuma mata, banda uwa banda uba, kuma ni Allah bai d’oranmin ciwon son “ya “ya ba, bare mace da ban d’auketa a bakin komai ba, wannan son nawa gaba d’aya kece na martaba ki dashi saboda ki zamo d’iya mai sharewa Babanta damuwa. Sakin hannu na yayi tare da cewa sai kun dawo, yana fad’in haka ya shigr gida. Inaji ina gani suka tasa k’eyata gaba suka sakani mota mukabar k’ofar gidanmu, tafiya mukayi mai nisa sosai, sannan Bello da abokinshi daya taho dashi suka fara magana, Bello yace, alhamdulillah na zurashi rami na gama, kasan Aliyu yana tak’ama da tasha ni kuma zan k’ure mishi tashi tashar shi dan abinda yayi min bazan manta dashi ba nima saina rama akan wannan d’iyar tashi daya d’auka san duniya ya d’ora mata, Bello yaci gaba da cewa nine na bada kud’in nan cas saida na ajiyesu sannan akayi caca, bana asara zan kaita inda za’a bani kud’ina har a d’ora mani riba, ina tsoron wai wai da bayan da Aliyu zaiyi wallahi da nine zanyi mata kaca kaca da rayuwa amma yanzu zan kaita wurin gwamnati idan zai iya yayi fad’a da hukuma in gani. Ai kaji shi wai Allah baisa mishi ciwon san “ya “ya ba, nima shi yasa ban zab’i ko d’aya daga cikinsu ba dan nasan duk wacce na d’auka abin bazai mishi ciwo ba, nima ina so in dasa masa irin tabon daya dab’a min a zuciyata wanda bansan ranar da zai gogo ba, Ajiyar zuciya Bello ya sauke tare da cewa da Allah sake kiransu ni fa ba abinda ya dameni da wani fushin banzar shi, dan ba fushi yakeyi ba ko mutuwa akayi mishi ni kawai tafiya zanyi idan munje can ayita ta k’are, abokinsa yace to idan masu gadi suka hanamu shiga fa ? Daina min ma wannan bak’ar fatar taka da Allah, duba min magungunan nan Allah yasa ban zubar dasu ba wurin wancan sakaran, wata “yar k’aramar leda ya d’auko ya mik’a ma Bello tare da cewa gasu nan, dariya Bello yayi sosai tare da cewa kasan bak’one dole saida “yan rakiya, A daidai lokacin daya fara magana a waya, nifa dama basai yana harkar mata ba, to dama banda abinka duk wanda kaga yana harkar mata ai koya yayi, nifa taimaka min zaiyi kuma na taimakeshi, saurara ka taimaka mana kazo ka shigar damu gidan idan muka shiga duk nasan yanda zanyi da Allah, tou babu damuwa gamu nan isowa ba jimawa, haka yayi wayarshi har ya gama, yakan d’auke maganar sa danjin abinda abokin wayar tasa zai fad’a, yana fad’in haka yaja motar muka tafi. Ni kuma tunanin abinda Babana yayi masa kawai nakeyi wanda har yasa zaiyi ma Baba ramuwar gayya, ina tunani naji yana dariya tare da cewa an fad’a maka ni sakarai ne ? Ai kaima kasan baiyi cacar ba dan ubanshi dasai yaci, mugu ya saki baki ya lashe kud’i mu kuma muka lashe “yar sa, dariya ya k’arayi sosai tare da kaiwa sitiyari duka yace kud’i na biya malamai suka sa banza wasi wasi……. Amma ai kasan Aliyu maye ne da yayi wasan caca da gaske dasai ya lashe kudin nan kamar yadda karuwa ke lashe sabon harka………. Ya kuma sabon harka ? Su sai suyi ta magana juyayya wanda sai su “yan bariki kad’ai suka isa su fassara yaren, ina ne nan kuma ? Na tambayi kaina yayin da muka tsaya gaban wani k’aton get, ga jami’an tsaro masu yawan gaske kowa ya kame da bindiga takai tsawo na, za’a fara magana wani daga cikin mota yace barsu su shiga tare muke, K’arfe ne aka d’age mana muka shige saida mukayi tafiya mai d’an nisa sannan muka tsaya, daidai da daidai kowa yana zaune cikin mota wanda ya shigo damu yace, Bello bana so nayi maka gardama ne kaga kamar wani abu amma na rantse maka da girman Allah Dikko baya neman mata, Wani irin tashin hankali naji yayin da naji an kira sunan Dikko sai yanzu na tuna da Dikkon da zaici uwata, hankalina na mayar a wurin Bello dake cewa kai ai sakaran banza ne idan zai nemi mata shawara zai maka ? Ai ba’a shedar namiji akan mace, murmushi mutumin yayi tare da cewa Bello na rantse maka da girman Allah har al-qur’ani zan iya dafawa Dikko bai harka mata, Tsoki Bello yayi tare da cewa muje idan zaka raka mu dare nayi, jinjina kai yayi tare da cewa muje, yana gaba muna biye dashi saida muka wuce get ukku kafin mu isa, kuma duk inda mukaje jami’an tsaro ne har muka isa bakin wata k’ofa, dukkannin mu anan mukayi parking, kulle min ido da hannu Bello yayi bayan mun tsaya. Rufe motar yayi da makulli sannan suka shiga ciki, wurin zama aka basu tare da cewa su jirashi yana zuwa, sunyi zaman daya wuce mintuna talatin sannan Dikko ya fito cikin tsananin b’acin rai dan har yanzu maganganun Sultana caccakar masa zuciya sukeyi, kuma ma koba komai dama shi Dikko ba ma’aboci sakin fuska bane, Gaishe shi sukayi, da kanshi kawai ya ansa gaisuwar tare da tsare su da ido, mutumin daya kawomu shine ya d’urkusa gaban Dikko yayi masa magana k’asa k’asa wanda babu wanda yake iya jiyo abinda yake fad’a, Kallo su Bello Dikko yayi tare da cewa da Allah kuyi hak’uri ita rayuwa sannu ake binta, babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare kuma gobe, kar kace zakayi ramuwa akan duk abinda akayi maka wannan ba d’abi’a bace mai kyau, halin mutunan kirki sukan manta da duk wani abu mara kyau da akayi musu, ka zama mai yafiya akan ko wane irin mutum idan yayi maka laifi, kaima sai Allah ya gafarta maka, miliyan nawa ne ka kud’in ? Dikko ya karasa maganar tare da tambaya, Cikin kwantar da murya Bello yace miliyan biyar ne na zuba, Dikko yace tou kai Sani kuje dashi ka bashi miliyan goma, a rik’a hak’uri kaji bawan Allah, gyara zama Bello yayi tare da cewa kayi hak’uri gaskiya ni ko miliyan d’ari zaka bani wallahi basu ne gabana ba a yanzu kawai so nakeyi ka ramamin abinda ubanta yayi min.’Daure fuska Dikko yayi domin duk cikin k’arfin hili yake magana, shi duk duniya babu abinda ya tsana irin mutum yace ya wulakanta shi, danne zuciyarshi ya sakeyi tare da cewa kayi hakuri gaskiya Dikko baya neman mata, Kayi hak’uri ranka ya dad’e ka ganta ko so d’aya ne nasan zatayi maka, kai jeka taho da ita da sauri, duk Bello ya fad’a ba tare daya bari Dikko ya sake cewa komai ba danshi Dikkon ma harya gaji da magana yayi shiru. Kamar wata b’arauniya haka ya jawoni har yanzu idona a rufe yake, lallausar kafet in dana taka da wani sanyi mai shiga jiki sai wani irin daddad’an k’amshi mai dad’in shak’a naji, hakan ya tabbatar min an kawoni inda za’aci mutunci na, har yanzu banyi magana ba amma idona ya cika da hawaye dan da ba’a rufemin idona ba babu abinda zai hana na cika d’akin da kuka….. A gaban Dikko aka durk’usar dani, amma shi ya kauda kanshi gefe d’aya bamu yake kallo ba, hankalin shi yana kan T V danma baya so ya kalli ko wace ce aka kawo dan babu zuciyar wanda shed’an bazaiyi wasa da ita ba, Bud’e min fuska akayi da sauri na bud’e duk girman idanuwana na fara kalle kalle, innalillahi na fad’a a fili a lokacin da idonuwa na sukaci karo da *Dikko* tare da fara k’ok’arin mik’ewa, Har yanzu Dikko bai juyo ba, dan haka nayi shiru dan karyaji magana ta, hijabin jikina suka ciremin da hular da na saka saman kaina, sannan aka turani saitin inda Dikko ke kallo, gaba d’aya kunya ta kamani dan haka na duk’ar da kaina k’asa, Dikko bai kalleni ba, kuma baiyi magana ba, inaa tsaye a wurin kaina na kallon k’asa hannuwana kuma suna d’aure ta baya na, ina tsaye a wurin shima Dikko bai dainaa kallon T V ba dan har yanzu bai kalleni ba bare na tabbatar daya ganeni ko bai ganeni ba, Shiru kowa yayi babu wanda ya sake magana har kusan tsawon awa d’aya, Bello ya gaji yace ranka ya dad’e zamu koma, yanzu ma kai ya jinjina ma Bello , matsowa Bello yayi a kusa da Dikko ya ajiye ledar daya zo da ita sannan yayi magana banji abinda yace ba, amma wannan karon Dikko bai ko motsa kanshi ba, fita sukayi suka tafi, shima wanda yayo mana jagora bin bayan su Bello yayi Dikko yace idan ka fita kaja man k’ofar, Cikin girmamawa yace tou, yana fita yaja k’ofar gam wanda rufeta yasa naji wani irin tashin hankali na saki baki na fara kuka da dan Allah kayi hak’uri kar muyi haka dakai, mugu kenan yaji mugunta dan haka ya fara murmushi, ashe ma yafi kyau idan yana murmushi, ‘Dan wasa yayi da idanuwan shi sannan yad’anyi motsi da kanshi kamar yaji kid’a, saida ya k’ara k’ayataccen murmushi sannan ya d’aure fuskarshi kamar baisan miye dariya ba, ya tsareni da idanuwanshi masu sa mutum yaji yanajin fitsari, da sauri na mayar da kaina k’asa gabana yana ci gaba da bugawa. Wayarshi ya d’auka yayi danne danne sannan ya k’ura mata ido, d’an tab’e bakinsa yayi a daidai lokacin daya kara wayar a kunnen shi yana cewa duk duniya me mace “yar matshi ya ta tsana ayi mata ? Kallona yayi sosai sannan yace 16 zuwa 17, mai maganar a waya ya dad’e yanawa Dikko bayani, murmushi Dikko yayi har saida kyawawan hak’oransa suka fito sannan yace yayi tare da ajiye wayar, Mik’ewa yayi bayan ya gama wayar ya kulle k’ofar da makulli ya tafi dashi ciki ya barni anan falo tsaye kamar wata gunkiya, Bayan kamar wani lokaci mai tsayi ya dawo, inda ya zauna da farko a wurin ya sake zama sannaan yace min zo nan, babu musu naje gabanshi na durkusa kamar yanda naga anayi mishi, Ya sunanki ? Suna na Sultana, da Allah me kike so nayi miki wanda zai tabbatar miki dani d’an Babana ne, shiru nayi bance komai ba, gyara zamanshi yayi tare da mik’e k’afarshi ya taka saman kafad’a ta, yace ina saurarenki. Kayi hak’uri don Allah sharrin zuciya ne, to kinga kin kasa ba zuciyarki hak’uri a lokacin dana b’ata miki , ni yanzu waye zai ba tawa zuciyar hak’uri ? Kayi hak’uri don Allah insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba, kayi hakuri don Allah, kwantar da kanshi yayi jikin kujera yana nazari har yanzu k’afarshi tana kan kafad’ata, ba tare daya taso ba yace gaskiya kamar zan hak’ura amma na fasa, Dan Allah kayi hak’uri, tasowa yayi tare da cewa wallahi bazanyi hak’uri ba yau zan nuna miki cewa ni d’an Babana ne, kuma da kanki zaki sheda ya iya haihu a daren nan zuwa safiya zaki anshi hukunci mafi munin hukunci, zan baki mamaki kuma zan nuna miki Dikko ba sa’an wasan yara bane, zan biga tambarina a zuciyarki za kiyi ta kuka daga yau har zuwa ranar mutuwar ki, yanayin farin ciki ko damuwa duk wanda kika shiga wallahi baza ki manta da Dikko ba a rayuwarki, dani dake kinga saiki fad’amin waye ciwon zuciya zai kama….. Ka rufamin asiri, ke yarinya ya fad’a tare da takamin bakina da k’afarshi, da sauri na janye fuskata gefe guda tare da goge bakina da kafad’ata, kam balasti kafatace kike gogewa baki ? Tou bari kiji in fad’a miki wannan k’afar tafi ubanki tsafta, tafi uwarki ni kuma nafiki banza kazamiya d’iyar d’an caca, saboda san duniyar da bata da tabbas ubanki ya anshi kud’i ya bada ke, mutunci da ko wace “yar mutunci da iyayen mutunci suke tattalawa amma ke ya siyar dan biyan buk’atarshi, Da sauri na kalli Dikko raina amatuk’ar b’ace nace gaka babban d’an iska da zakayi fasik’anci dani a cikin gidanku, ni ba fasik’i bane yarinya ki tambaya kiji ni babu mata a tsarin rayuwata shi yasa bana sabgarsu, amma kedai yau sai nayi miki kaca kaca wallahi yanda ko sunan Dikko kikaji sai kinyi fitsari, ya kara sa maganar tare da sake maida k’afarshi ya takamin baki, Sake janye k’afar nayi daga bakina na k’ara juya kaina gefe, dariya Dikko yayi tare da sauko kafarshi saitin k’irjina ya taka tare da tura babban d’an yatsan shi cikin riga ta sannan yaja da k’arfi, b’earr k’arar yagewar rigata, cika idona yayi da hawaye kuma ga hannu na d’aure ta baya, dan girman Allah kayi hakuri karka ciremin kayana, Sai k’ara tattakani yakeyi, gajiya nayi da iskancin shi nace sakaran banza kwance min hannuna na kaga yanda zanci k’aniyar ka a daren nan, 03/08/2019⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 6 Idan na kunce ki zaki iyamin wani abu kenan ko ? Eh na fad’a cikin kwarin guiwa, Murmushi yayi kad’an da gefen bakinshi sannan ya kuncemin hannu na, mik’ewa nayi da sauri na d’auka hijabina na saka, sannan nayi hanyar fita da gudu, Dukan k’ofar d’akin na farayi tare da kwarara ihu a kawomin d’auki, Dikko bai sake bi takaina ba ya tashi ya shige ciki, dan yasan inda nake ihuna banza ne kururuwata wofi… Alwallah yayi bayan ya shiga yai kwanciyar shi, duk abinda Dikko zaiyi bayayin shi kai tsaye zai dad’e yana tunani idan yayi abun bayan wani lokaci me zai haifar mishi ? Yana duba duk abinda zaije ya dawo kafin ya aikata….. Ni kuma gajiya nayi da doke doken k’ofa na zauna a wurin saboda har muryata ta shak’e tama daina fita sosai, a wurin na zauna har asuba banyi bacci ba ina zaune, Koda asuba a gabana Dikko ya fito da jallabiya brown a jikinshi da hula fara wacce ake cema tashi da kwakwa hannun shi d’aya a aljihu d’ayan kuma rik’e da makulli, bud’e k’ofar yayi da makullin ya fita, kuma yana fita yasa makulli ya rufe ta waje,Nima tashi nayi na shiga ta hanyar dana ga Dikko yake bi yana tafiya, hanyace doguwa sosai ta tafi d’od’arar tasha tayils sai kyalli yakeyi mai d’aukar ido, sai tukwanen shukoki da suka sakani tsakiya, wato wasu a gefen damata wasu a haggu na, Ina zuwa k’arshe naga hanya ta rabu biyu, daidai bangon da hanyoyin suka rabu kuma anyi rubutu wanda bansan abinda aka rubuta ba, saidai zuciyata ta gargad’eni da na tsaya karna fad’a inda zan kashe kaina. Dole naja na tsaya daga nan, zama nayi a wurin, ban wani dad’e da zama ba Dikko ya dawo, a daidai inda nake zaune yace taso muje ya fad’i maganar ba tare daya tsaya ba, Da sauri na tashi nabi bayanshi dan zuwa wannan lokacin zuciyata ta tabbatar min babu abinda Dikko zaimin, yanayin shi abinda na lura yanayin abu na mutuntaka, yana da ruwan mutanen kirki kila zai tausaya min. Allah ka azurtamu shine abinda na fad’a a zuciyata yayin da na shiga d’akin Dikko, banda cikakkiyar natsuwa a wannan lokaci shi yasa ban wani damu da abinda d’akin yake ciki ba, saman kujera ya zauna tare da cewa ga wurin wanka can ya nunamin da hannunshi, Ki fara wanka sannan kiyi alwalla, zaki ga ruwa yana nan na zuba miki dan karki je kiyiwa mutane kauyanci, a inda ruwan yake anan akeyin wanka kuma karki sake kimin fitsari a ciki, Banza nayi na kyale d’an iska na shige, saida nayi fitsari na a inda yace baya so sannan nayi wanka nayo alwallah na fito, wurin da zanyi sallah ya nunamin ina kabbara sallah ya shiga toilet in, Jinjina kanshi yayi sannan ya fito ranshi a matuk’ar b’ace , ko ya akayi ya gane nayi fitsarin oho ! Rashin sani ashe ya gwada ni ne yaga idan ya kyaleni bazan sake mishi rashin kunya ba, idan ya tabbatar banyi fitsarin ba zai fitar dani na tafi gida, A fili yace shawar dare zan d’auka kawai, ledar da Bello ya ajiye mishi jiya itace ya d’auka ya fita, ashe maganin maza ne a ciki, Bello yace masa duk wanda yayi masa a ciko tou shi zaisha guda d’aya, shi kuma a nashi tunanin ko wanne zaisha guda d’aya a ciki, Duka magungunan nan babu wanda Dikko baisha ba, bayan ya gama sha ya shigo, a lokacin na gama sallah ina zaune wurin da nayi sallah, gyara labuleye ya farayi lokaci guda duhu ya fara bayyana a d’akin, kashe hasken fitilar dakin yayi lokaci guda yanayin d’akin ya koma kamar dare, Bansan ya taho ba saidai naji an rik’oni cikin duhu, saida ya rik’eni sannan ya mik’ar dani tsaye amma baiyi magana ba, fitilar wayarsa ya kunna sannan ya sakata a aljihun gabar rigarshi, Kamo fuskata yayi a bakina ya cuccusa min wani abu sannan ya nad’e bakin da salitaf, hijabina da zanin jikina ya cire ya zubar awurin, ganin da gaske yake yasa naji wani irin k’arfi yazo min na kwace na fara kai duka ba tare da nasan inda yake ba saboda duhun da d’akin yayi, So d’aya na sameshi kawai ya rik’e hannuwana duka yace ni kika daka ? Waye yace miki ana dukana ? Murd’e min hannu yayi saida yayi k’ara sannan yace ko a gidanmu ba’a tab’a dukana ba kuma babu mai min kallon banza kowa so yake ya kyautata min dan insan dashi. Ke kuma kimma samu Dikko a arha har wani kai mishi duka kike ? Zanyi maganin rashin kunyarki yanzu nan. Hannun daya murd’e shine ya jani dashi har zuwa bakin gado, jefani yayi saman gadon zuwa wannan lokacin ko motsin kirki bana iyawa saboda murd’ewar da yayi ma hannu na, shima jallabiyar shi ya cire tare da hawowa saman gadon. Gaba d’aya Dikko ya zare hankalinshi da tunaninshi ya fita daga jikinshi, babu wani sauk’i bare tausayi ya nufi hanyar masar ba tare da tunanin komai ba, Wata irin gumza nayi a lokacin da Dikko ya shigeni, jikina yana kyarma saboda azaba nasa hannu na mai lafiya na kware abinda ya rufemin baki, nace kaji tsoron Allah karka b’atamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah, ko saurare na baiyi ba, da hannu na mai lafiya dashi na fara yagushin Dikko tare da cizo, nayi kuka na bashi hak’uri amma kamar an watsa ruwa a k’asa, dan gaba d’aya tunanin Dikko ya b’ace saboda duk abinda nake masa bayaji, cizo da yagin ma kamar ina yagin karfe kwata kwata bayaji. Tun ina iya Allah ya isa, cizo yagi har k’arfina ya k’are na gaji na daina bai barni ba, wata irin azabtuwa nake sha wadda tunda nake a duniya ban tab’a jin irinta ba, haka kuma bazan iya musulta girman azabar ba, wai yau nice akayi ma fyad’e, wannan bala’in ne Zainab ke zuwa ai mata a bata kud’i ?……. Wurin kamar kimanin 12:45pm dukan k’ofar d’akin Dikko akeyi babu sauk’i, kuma har zuwa wannan lokacin Dikko bai kyaleni ba, na suma na dawo bansan adadi ba, baida niyar bud’e k’ofar kwata kwata, magana mai dukan k’ofar ya farayi cewa wai har me kakeyi ne baza ka bud’e k’ofar ba.Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un, yai ta maimaitawa, tare da sauka daga saman gadon, ta jikin tagar d’akinshi ya lek’a a bayyane yace Dady…… Gajeran wando ya saka sannan ya kunna fitila, jawoni yayi daga saman gadon ya sauko ni k’asa sannan ya bud’e loka na bedsite ya d’auko gishiri, saida ya cikamin bakina da gishiri sannan ya zubamin ruwa a baki na hakan ya bawa gishirin damar narkewa yaci gaba da gangarawa cikin mak’oshina. Dakel na bud’a idona na kalli Dikko, tsoki yayi tare da cewa munafikar Allah bari kallona dan uwarki….. A hankali na maida idona na rufe, k’asa yajani har muka fito daga d’akin kuma har yanzu ba’a daina dukan k’ofar d’akin ba, Wani d’aki daban ya kaini ya ajiyeni, sannan ya kulle da makulli, saida ya goge inda jini ya b’ata daya jawoni sannan ya koma d’akin daya b’atamin rayuwa, zanin gadon ya cire ya tafi toilet dashi, Bai wani dad’e ba yayo wanka ya fito, saka kayanshi sannan ya bud’e k’ofar, hannu Dady ya mik’a wa Dikko suka gaisa yace masa Babana baka tashi ba ? Na tashi…, tou lafiya baka shigo ciki ba ? Me yake damunka ne ? Ba komai Dady, sosai Dady ya sake kallon Dikko sannan yace mu shiga ciki, Duk yanayin fuskar Dady ya canja zuwa na damuwa, jan Dikko yayi suka zauna har yanzu yana rik’e dashi a jikinshi yace Babana fad’amin abinda yake damunka, Dady nace babu, to miya hanaka shiga ka gaisheni, ba komai, tab’a jikin Dikko yayi cikin damuwa yace tou mi yake maka ciwo ? Kanka ne ? Ko bacci kake ji ? Shiru Dikko yayi duk abun duniya ya dameshi, Dady kad’ai yaketa ma Dikko sannu, yana san Dikko fiye da yanda kowa yake san d’anshi, yana tattalin Dikko ko ina Dady baya san Dikko yana zuwa dan duk fitar da Dikko keyi Dady baisan yana fita waje ba, yana lallab’a Dikko sosai gani yakeyi kamar Dikko zai mutu ya barshi, kullum addu’ar shi Allah ya k’ara kare mishi Dikko ya shirya shi ya albarkaci rayuwarshi, saboda d’a d’aya tsotsai gareshi. Yana da “ya “ya sunkai sha biyar amma duk mata ne Dikko ne kadai na namiji a gidanshi. Taso muje, Dady ya fad’a tare da dafa kafad’ar Dikko suka fita, cikin gida suka shiga, tunda suka shiga k’annen shi suka fara cewa Yaya munce ma Dady lafiyar ka qalau yace saiya ganka zai fita, kallonsu kawai yayi amma baima kowa magana ba, suma basu damu ba tunda halinsa ne shariya, sai kayi ta mishi magana ya kyaleka kamar bayajin ka. Gishirin da Dikko ya zubamin a baki nake ta tofarwa amma rabi ya riga ya gama shigewa cikin cikina, kuka nakeyi mara sauti, duk ilahirin jikina ciwo yakemin, ga kaina kamar zai fashe saboda rashin bacci da kukan da nayi. Haka na yini zubur babu Dikko ba labarinshi, ga ciwo da nakeji a k’asana kamar zai fita saboda azaba, kuma d’akin da nake babu toilet a ciki duk sallolin da akayi na yinin ranar nan inajinsu amma tun sallah asuba ban k’ara wata sallah ba. Sai dare sosai Dikko ya bud’eni, shigowa yayi yana waya, wallahi dawowa ta kenan naje Abuja kwata kwata na manta da yarinyar nan saida nayi alwalla zanyi sallah magrib ta fad’omin a rai, ko Dady basai na dawo ba kuma ina ajiyeta zan koma , ……. A , a, 06:30am ne, ai bana so Dady yaji ban tafi ba kasan yanzu sai ya shiga damuwa, bada driver nake ba, tou kudai ku sakani addu’a , yana gama wayar yace ke da Allah tashi muje, munafika kinja min tafiyar dare, daka min tsawa yayi tare da cewa ki wuce mu tafi kina b’atamin lokaci dare yana karuwa, K’iri k’iri na kasa tashi, kaina sai juyawa yake ga wani irin amai dake kai kawo tsakanin zuciyata da cikin cikina, jiki na yana kyarma nace masa bana iya tashi….. Na k’arasa maganar hawaye na zubomin daga cikin ido na, Zan tafi idan kin tashi kin basu labarin abinda ya kawo gidan nan ni kinga tafiyata, ya juya zai tafi nace dan Allah zan tashi, juyowa yayi ya kalleni sannan yace tou taso ya fad’a cikin sigar lallashi, Dakel na iya tashi amma a duk’e nake na kasa mik’ewa tsaye, yanayin fuskar shi ya nuna tausayi, akwai zafi ? Ya tambayeni, banza nayi dashi bance masa komai ba, murmushi yayi tare da cewa ki sameni ta baya, kuma kiyi hankali karda a ganki, Dakel nake tafiya har nafito, a lokacin harya d’auko motar daga inda ya ajiyeta, ina k’ok’arin shiga yace in tsaya kar in b’ata motar, ciki ya koma ya sake gyaggyara inda na b’ata sannan ya d’auko wani k’aton zani ya taho dashi, inda zan zauna ya shimfid’a sannan yace shiga, Shiga nayi na zauna ya rufe k’ofar tare da zagayawa shima ya shiga, waya ya kira yace gani nan zan fito bud’e min get in, yana fad’a ya ajiye wayar ba tare daya kashe ba, Da gudu yaja motar kamar zamu tashi sama muka tun kari hanyar fita, a daidai get ya tsaya sukayi ta masa addu’a da fatan alkairi ya amsa da amin sannan muka fice, hanyar filin gidanmu ya nufa, babu mota ko d’aya a hanya bare machine haka ya tabbatar min da dare yayi sosai, Lokaci lokaci nakan goge hawaye, tare da Allah ya isa zuciyata, saida ya kusa zuwa gidanmu ya tsaya yace ke sauka haka nan, kama murfin motar nayi sannan na kalli Dikko nace Allah ya isa ban yafe maka ba mugu azzalimi d’an isa mai bakin mata, murmushi Dikko yayi sannan yace ngode, Kuma ko zaka mutu bazan tab’a yafe maka ba, Dikko yace tou, in Allah ya yadda saika had’u da tashin hankali a hanya, bazan had’u dashi ba in Allah ya yadda, tsoki nayi tare da bud’e motar na fita, tillomin zanin dana zauna akai yayi a daidai lokacin da nace kuma wallahi sainayi k’arar ka, babu damuwa ina jiranki, azzalimi , murmushi yayi tare da cewa naji ba komai duk abinda zaki ce ki fad’a nidai nasan na more miki har abadan duniya, gwallo yayi min tare da jan motarshi ya barbad’eni da k’ura….. Wani irin bak’in ciki ya kamani nayi wani irin ihu daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saidai na farka na ganni kwance a gadon asibiti, an d’aure hannuna wanda yaji min ciwo, anmin dinkuna a k’ark’ashi na, Zainab itace ta zauna tare dani a asibiti dan Inna tunda taji abinda ya faru tayi tafiyarta tace ta gama auren Baba har abadan duniya, Sati na d’aya a asibiti aka sallame mu muka dawo gida, Babana kuma kunya tace ta koreshi babu wanda yasan inda ya tafi, tunda na dawo na samu labarin Inna ta tafi ban wani ji sha’awar binta ba, na hak’ura na zauna cikin “yan uwana. Naje nayi k’arar Dikko wurin “yan sanda abinda ma na fahimta sumo so suke suyi irin abinda Dikko yayi dani, dan haka na hak’ura na dawo gida. Babu ranar da zata zo ta koma ga Allah ban fad’owa Dikko a rai ba, ya shiga damuwa da tashin hankalin abinda yayi min, yaji bak’in ciki tare da tambayar kansa mi yasa yayi zina ? Mi yasa nayi ? Mi yasa,…..???? Wani lokaci haka zai zauna yayi ta kuka yana mai jin bak’in ciki da nadamar aikata abunda yayi, ya tambayi kanshi so babu adadi wai miye amfanin abinda yayi ? Yin hakan meya haifar ? Dadin me yaji ? Wane rayuwa yarinyar mutane zata shiga? Mi yasa saishi ne Bello ya zab’a ya farkewa Sultana mutunci ? Tabbas ya yadda ya zama babban mahauci iliminshi baida wani amfani baida banbanci da jahili, Kullum addu’a Dikko yakeyi Allah ya yafe mishi akan abinda yayi min,zuwa wannan lokaci ya fara tunanin ko ya sanar da Dady abinda ya faru kila zai bashi shawara tunda babu abinda suke b’oyewa juna, Ko isashshen bacci Dikko baya samu, daya kwanta shashkar kukana yake tashin shi daga bacci, a fili yayi magana cewa baiwar Allah kiyi hak’uri ni wannan na d’auke shi matsayin k’addara tunda nake a rayuwata Allah ma ya kulle min idona da zuciyata akan mata, Wallahi ko labarin mata bana so anayi a gabana, ban tab’a zina ba kuma wallahi ban tab’a jin sha’awarta a zuciyata ba, Allah yayi min kyankyami da tsoron sab’a masa , amma ya akayi banji kyamar yarinyar nan ba, na sab’awa Allah mi yasa na kasa control in zuciyata mi yasa wai……….? Dan Allah ki fita daga rayuwata ki barni, kiyi rayuwarki inyi tawa, hawaye ne suka sake tsirarowa daga cikon idonshi, cikin kuka yace ya Allah na rok’eka dan arzik’in annabi Muhammad S. A. W ka mantar min da lamarin yarinyar nan daga zuciyata, ka hanata zuwa man cikin bacci ta daina min wobuwa idan ina cikin mutane wallahi ina iya haukacewa, A b’angare na kuwa, zuwa yanzu na shafe babin Dikko a rayuwata, akwai wani d’an uwanmu da yake so na, kuma yayi alk’awarin aurena dama tunda ya fara zuwa Baba yace mishi ya bashi ni amma babu maganar zance kawai dai idan na isa aure zai aura mishi ni. Shima yaji labarin abinda ya faru dani, kuma yazo wurina, ya tambaye ni da gaske ne ko wasa ? Da farko naso na b’oye masa, amma daga baya kawai na fad’a masa gaskiya, yacemin tou shi gaskiya bazai iya aurena ba inyi hak’uri, ban wani damu ba nace Allah yasa haka shi yafi min alkairi a rayuwata.A hankali magana ta fara zaga gari, anyi min fyad’e kuma wanda yayi min fyad’e d’in ba’asan ko waye ba, amma asibiti sunce ina da cutar H I V, duk abinda na tab’a a gidanmu babu mai k’ara amfani dashi, duk wacce na zauna kusa dashi sai ya tashi, idan na fito mutane da sun ganni sai su dare…. Ko a familyn mu kowa baya shiga sabgata, kyara da tsana ake nunamin kamar mayya, ga mahaifiyata tayi tafiyarta garinsu, Baba bansan inda ya tafi ba, na rasa abinda yake min dad’i a duniya, banda mai bani abincin da zanci duk wanda naje wurinshi saiya koreni, azaba ta isheni na fara sana’a babu mai siye, Koda naje na fad’awa Amisty abinda rayuwata take ciki da fyad’en da aka min amma ban fad’a mata Dikko bane ba, shawara d’aya ta bani, shawarar kuwa itace, sana’a d’aya zanyi inyi arzik’i ba H I V gareni ba ko kabari ce ni sai an shigeni, Wace sana’ace ? Murmushi Amisty tayi tare da cewa zan kaiyi wurin uwar d’akina in yankar miki form zata baki lectures, lokaci guda zaki goge idonki ya bud’e zaki ga yanda maza zasu rik’a layi akanki,….. Idan sunyi layin me zan basu ? Abinda kika bawa wanda yai miki fyad’e,…………… Taku a kullum. *JAMILA MUSA* 03/08/2019 Ku kulle marecen ku da wannan………. Ku biyoni sannu a hankali danji dalilin da yasa na kira wannan labari da *KWARATA* nazo kuma nayi masa in kiya da *KALU BALE GARE KU MATAN AURE………….*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ina miki sannu da gajiya fatan kin koma gida lafiya ? Ngode sosai Allah ya bada ladar zuminci ya kuma hutar da gajiya RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE_*🅿 —— 7 Haba Amisty wannan ai ba mafita bace, Sultana kenan wannan kuwa itace babar mafita, domin mazan yanzu yawancin su yanda kika san kura da nama haka suke akan mata, d’aid’aikun su ne Allah yatsare su, sai kuma wanda suka had’u da jajirtaccin mataye. Ni nan da kika ganni Sultana nasan abinda nakeyi kuma haka nasan irin mazan da nake tarayya dasu, banajin kunya asan ni “yar iska ce haka kuma bana b’oyon iskancina dan ta haka ne kad’ai za’a san ni karuwar gidan ce har na samu costomers. Na samu dubban kud’ad’e ta hanyar karuwanci ban san adadi ba, dubu goma dubu ishirin ga kud’ina kuma inji dad’i abu na babu wanda yaji ba wanda ya gani, in rik’e babbar waya irin wacce nake so haka kuma in d’inka sutura da talakalmi da jaka, abu d’aya yasa ban sayi motar hawa ba saboda bana so Baba ya harbo jirgina da wuri amma badan babu ba, Gyara zama nayi tare da tattara hankali na wurin Amisty, nace to ke mi yasa kike sha’awar karuwanci ne ? Murmushi tayi sannan tace gaskiya daga kalle kallen B F tun inajin tsoron abun har ya fara bani sha’awa, Tsare ta nayi da ido sannan na tambayeta a ina take samu ? Tsoki tayi tare da cewa tambaya kamar “yar jarida, idan zakiyi na had’aki da wani mak’ocinmu sakaran banza baisan darajar kud’i ba, kije yai miki yaimin muci gaba da k’wak’wale banza tunda matar tasa sakaryar banza ce, kud’i gareshi na tashin hankali amma matar bata wani iya sauk’e hak’k’insa kinji yanda yake tona mata asiri ? Gata da kyau kamar ita tai kanta amma kyan ya zama hoto tunda mijinta ke neman mata. Tou ke Amisty ya akayi kuka had’u kuma ya akayi yasan kina neman maza ? Hmm yarinya kenan ! Amisty tace min sannan taci gaba da cewa……. Gidan nake zuwa ita kuma bata da wani sirri bud’e take shegen surutu kamar an sakawa radio sabon battery, Kullum naje sai ta bani labarin mijinta d’an jaraba ne, da a tunani na mafad’aci ne, sai nace mata niko sai naga yana da kirki sosai bashi da wata damuwa, sai tacemin ba fad’a na baki ba jaraba kullum zai nemeni daga dare zuwa asuba yakai sau biyar. Cikin rashin fahimta na tambayeta, ban gane ba….. Tamin bayani na gagara fahimta shine ta fahimtar dani ta hanyar nunamin vidio a wayarta,Tana kunna min ta tashi dan zuwa duba girki, ni kuma tuni dama na fara iskanci na amma a lokacin ban dad’e da farawa ba, dan haka tana tashi na sace number mijin a wayarta, tunda iskancin kawai nakeyi a lokacin amma bansan fa’idar abun ba…… Tana madafar abinci naje na bata wayarta nayi mata sai anjima, ina fita ba gida na tafi ba kawai na sharce wurin uwar d’akina, wadda nace miki zan had’aki da ita kema ta mayar dake gahurtacciya kuma abun kwatacce a harkar barikanci. To ita naje ta sake bani haske a harkar, dan haka ina dawowa gida na fara tura masa sak’on gaisuwa ta whatsApp. Shareni yayi bayan yaga sak’on baiyi reply ba, ni kuma na nace na kwakwafe banyi zuciya ba naci gaba da aika sak’on, kusan sati biyu babu wani bayani, dan haka na fara tura mishi da irin vidios in B F da nake kallo na tura mishi masu zafi da yamutsa tunani dan wani lokaci sai yakai 1:30am yana online.Wai wace ce ? Ya tambayeni bayan yaga vidio inyi, nima basar wa nayi ban bashi amsa ba na sauka online, ina sauka yana kirana a waya….. Murmushi nayi a bayyane nace ashe kuwa mayen ne ? Mu zuba dani dakai….. Kuma ban d’auki wayar ba, Text ya turomin ta inbox, kamar haka…. _Wai wace ce ke ? Ki hau Online muyi magana don Allah !_ _Ai nayi fushi nima….._ Shine amsar dana bashi, _Kiyi hakuri don Allah ki hau online muyi magana_ Shareshi nayi na kashe wata duka nayi kwanciyata…… Saida na kwana biyu wayata na kashe, ranar dana bud’e wayar kuwa sak’onsa ne yai ta shigo babu iyaka, wasu na duba wasu kuma na share. Ko online dana hau sak’unan sa birjik, dan haka naci gaba da tura vidion iskanci, kuma idan natashi sai tsakar dare nake turawa, jakar tana can tana bacci, A hankali ya saba dani, amma ban fad’a mishi kaina ba, yau da gobe bata bar komai ba, har na tambayeshi dalilin da yake kai tsakar dare yana chat, kawai cewa yayi yana da damuwa da iyalinshi, bata bashi hak’k’inshi wai tace yawan sex da mace yana sa tayi saurin tsufa…. Amsar dana bashi itace, ya barta can ta k’unshe abunta har yayi wari, indai yana da buk’ata tou ni zan rik’a bashi nawa duk lokacin daya buk’ata, kinji shine fa idan bata nan nake zuwa gidan muyi komai namu cikin sirri. ‘Dan gajeren murmushi nayi sannan nace Amisty kenan…… Idan dai har bin maza zanyi tou pha tabbas babu macen data bini ilimin iskanci, kinji hausa suna cewa d’an gado saiya zarta, nawa ba kalar naku bane, saboda naku iskanci mai arha kukeyi, tunda har banji kunyar mahalicci ba na tsab’a masa babu abinda zaisa naji kunyar wani banza, Hannu na nakai saitin prvt prt ina sannan nace idan dai wannan ne abinda maza suke buk’ata ni kuma duk saina halaka da yawansu dashi, kallon Amisty nayi sannan nace, babu wanda ya koya min saishi d’aya, ban fara ba shine ya fara, ban iya ba yayi da k’arfin bala’e, ba’ayi da zafi yayi min saboda k’eta, ke Amisty karki manta a caca aka sakani duk saboda talauci idan har ban tara kud’i ba ta sanadiyar karuwanci nayi suna a duniya lallai ni ba d’iyar Aliyu Binnaa bace, Tunda har ya bada budurci na saboda san duniya ni kuma zanci gaba da basu su bani dan na tara mishi abunda ya buk’ata, Amfanin zunubi roma Amisty, tunda zanyi kawai zanyi amma babu fashi, saidai ki sani akan sab’awa Allah babu namijin daya isa yaga ko pant ina da naira dubu goma ko ishirin, kud’in shigar ciniki naira dubu d’ari ne shine harajin da na yankawa duk mai sha’awar yin iskanci dani, idan kuma zaka shiga gidan dubu d’ari biyar, idan har haka yayi tou na siyar idan haka baima mutum ba tou ya tattara buk’atarshi ya koma, Amma tabbas duk namijin da yace zaiyi, saiya bada dubu d’ari, idan na yadda yayi idan kuma ban amince da dashi ba zai koma, amma dubu d’arinshi tazo kenan kamar gawa tazo lahira. Ki sani bana iskancin wahala, kuma bana iskancin cini incin tuwo, zan zauna gida bazan bar k’asata ba amma zan zama tarihi a duniyar nan, ki fad’awa uwar d’akin taki cewa ina gayyatar ta shigowa k’ungiyata da nake fatan kafuwarta daga yanzu zuwa ranar da numfashina zai k’are, ki sanar da ita cewa ni banda ilimin boko amma akwai na tsoron Allah kuma sanin ilimin bazai hanani bujire masa ba, nasan hukuncin mazina daga wacce tayi aure har wacce bata tab’a ba, hukunci kisa ga masu aure, bulala ce ga irinmu “yan mata, to anan duniya zan sameta ko sai naje can ? Duk na sani, kuma nasan a ina ake amso su, mik’ewa tsaye nayi tare da dafa wa Amisty kafad’a sannan nace bana buk’atar shiriya, kuma bana so a tausaya min, daga yanzu zuwa lokacin da zan gama kammalawa…….., *BARIKI ASSALAMU ALAIKUM* Murmushi nayi sannan nace wa Amisty suna na , MARYAM ALIYU BINNA, na bud’e k’ungiyata daga yanzu, idan kina sha’awar shiga bisimillah, na barki lafiya……… Ina fad’in haka ban sake magana ba na juya na fita daga gidansu…… Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un, shine abunda Dikko ya fad’a adaidai wannan lokacin, tare da cewa Allah na tuba………. 🙏🏻 Ina fita na tare napep nace malam ka kaini kambarawa, can ne anguwar da muke zama. Abinda zan bashi ya fad’amin bayan ni ban tambayeshi ba, Shiga nayi yaja muka tafi, duk inda yaga fasinja ya tsaya zai d’auka cewa nakeyi muje bana so ka d’auki kowa, har muka iso filin gidanmu da yasha ado da darnin kara…… Ina fita na wuce abuna, malama kud’in fa ? Juyowa nayi tare da ce masa nawa ne ma ? 250, murmushi nayi tare da kallonsa k’asa da sama sannan nace naci na Allah bud’a, da kuma tsarinka yamin dana baka wani abu ka kalla sai kayomin ciko,Fitowa yayi daga cikin napep d’in yana fad’in ke zanci uwarki ko ki bani kud’ina, murmushi nayi tare da cewa tayi maka tsufa…… Ina fad’in haka nayi gaba abuna, haya haya ya fara hayani tare da ci gaba da d’uramin zagi irin na “yan tasha. Ja nayi na tsaya ba tare dana juyo ba. Saida ya gama zage zagensa sannan naci tou ka zagi kud’inka, kuma naci na cinyesu duk garin nan inga mai amsar su wurina, kaina yayo da zumar kaimin duka, nace ka dakeni ka dako ma kanka bala’e da kabi ta hankali daka tsira amma tunda iskanci ne abun dani dakai dan iska ka fasa,…Wani mak’ocinmu ne yazo wucewa, na fashe da kuka tare da cewa malam lawal kaga wannan shine yayi min fyad’e, dama nace muku ina ganeshi, yana jin zance fyad’e ya ruga zai nufi napep malam lawal ya fara a kawo d’auki, a tak’aice dai kafin ya bar anguwar bayan yaci shegen duka saida aka fasa mishi gilashin mota na gaba sannan suka k’wak’ule masa cini kin da yayi yabar anguwar a wahalce…… Yana tafiya na shiga gidanmu natashi masifa cewa sai an siyar da filin nan an bani hak’k’ina, yanda na birkice lokaci guda ya bawa al’ummar anguwarmu mamaki, an nuna min cewa ayi kud’i wa filin sai a fitar min da kud’ina su kuma su zauni fili, nace bansan wannan zance ba duka nake so a siyar uban kowa ya kama gabanshi, Tambayata akayi me zanyi da kud’in ?Babu kunya bare shakku nace, karuwanci zan fara shi yasa nake so a siyar a bani kud’i na naje na siyo kayan da zan zama karuwar…… Gaba d’aya wurin salati aka d’auka ! Yayin da wasu dattawa suka fara sulalewa suna barin wurin, ni kuma na shiga cikin gidan naci gaba da yanyara ruwan iskanci na san raina, Bayan kwana biyu mak’ocinmu ya kawo kud’in filin gidanmu domin shine ya siya, aka raba aka bani nawa, sallama nayi musu tare da cewa kuyi k’ok’ori kuna ziyarta na domin inaji a jikina nan da kwanaki kad’an zanyi muku wahalar gani…….Babu wanda ya bani amsa, murmushi nayi tare da tafiyata dan dai nasan nasha dasu…. Nima bak’in ciki yasa nace duka filin za’a siyar dan kar na shiga gararin rayuwa ni d’aya kowa ya lalace dan zuwa yanzu gaba d’aya na koma kamar wata kafira dan babu sauran tausayi a zuciyata…… Bakin titi na fito na samu mai abin hawa, inda zanje ya tambayeni……….. Shiru nayi na wani lokaci sannan nace masa gidan karuwai zaka kaini, Kallona yayi sosai sannan yace ina ? Nasan yaji sarai iskanci ne yasa ya sake tambayata, dan haka nace gidan da “yan iska ke zama wanda suka gagari iyayensu, Jinjina kai yayi amma baiyi magana ba, ko har yanzu baka gane ba ? Na tambaye shi ? Shiru yayi baicemin komai ba, ni kuma nace tou ina nufin inda maza da mata ake had’uwa ayi bad’ala, kallona yayi cikin yanayin tausayi sannan yace ke yarinya ki rufawa kanki asiri rayuwar bariki tafi k’arfin ki, aure shine yafi dacewa da rayuwarki, Kai malam zaka kaini ko kuwa dai ? Tashin napep inshi yayi tare da cewa Allah ya shiryaki, amma nikam bana kaiki gidan karuwai, tsoki nayi tare da cewa jeka d’an munafika shege marar rabo… Gaki nan katuwar marar rabo duniya da lahira, indai mazan bariki ne sai sun kasheki murus kin kasa morawa rayuwarki, dan mace bata kashe namiji saidai ya kashe ta, baki san dafin namiji ba da baki hayewa mazan zamani ba kin koma gida, basu da imani haka kuma basa tausayi tunda sun san kud’insu suka biya, tou fa basa sassafta wa kamar mai gidan haya ne da “yan haya, tunda sun san ke ba tasu bace hawa d’aya zuwa biyu zasu tashe ki aiki kina kallon maza suna kallonki amma dan uwarki bazasu ciwu gareki………… Yana kaiwa nan yaja napep inshi yayi gaba. A bayyane nace komi zakace kaje kace saina zama cikakkiyar karuwa, kuma ni karuwanci nawa mai aji zanyi ba irin wanda kowa yake tunani ba. Bai dad’e da tafiya ba na samu abin hawa, kuma na fad’a masa gidan karuwai zai kaini, yace min na ina gidan karuwai d’in ? Nace inda fek’ak’k’un suke can zaka kaini, shigo muje, shiga nayi yaja muka tafi……… 05/08/2019⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA’ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari……_* *_ZAINAB ATTAHIRU B ‘ K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho…………_*🅿 —— 8 Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu’a, Allah na rok’eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik’a bud’ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci. Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k’ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad’e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne …… ? Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud’ina sauri nakeyi. Ina k’ok’arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d’abi’ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud’i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya ! Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud’i na ko in wulak’anta ki a wurin nan, d’an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak’anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci……..! Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani…… Dariya nayi sosai irin ta cikakkin “yan duniya na kashe dariyar da rangad’a gud’a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ?Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d’an iska dake fad’in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da “yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani….. Sauk’i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k’ok’arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik’e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had’u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d’an k’ank’anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad’in garinnan, sauka lafiya………. ! Ina fad’in haka na shige gidan karuwai, Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d’iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d’an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita, A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ……? K’arewa gidan kallo nayi sosai, d’akuna ne k’asa da sama, bene ya zageye k’asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud’a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d’aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito……. Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba. Bariki ba’ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k’afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had’ari guda d’aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d’auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata…..duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima, Kija da’irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d’aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d’aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d’akin zama ko nayi gaba………? Wani daga can saman bene yace ke “yar cakulkula dake har kin san dad’in namiji ? ‘Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji.Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d’aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d’auka daf bata iya d’auka, jirgi ya d’auke ka kuma ya d’au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k’aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi. Tabbas muna da masaukin ki, d’aki d’aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d’aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ? Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k’arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba………? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad’ai zanyi na k’ara gaba abu d’aya zuwa biyu nazo koya kad’ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud’in hayar ba haka na yanke.. Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata…….? Wata irin fad’uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d’auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk’ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k’are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba, Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d’aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad’a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d’auke da mugunta nace mashi idan an bani d’akin kai ka biya kud’in sannan kuma ka bani rance dubu d’ari, tukuicin d’aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d’arin ka kuma da kud’in d’aki duk zan baka su idan na fara kasuwa…… Ba damuwa a bata d’akin sama lamba 59 ya fad’a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d’akin, makulli aka bani na bud’e na shiga ina shiga na kulle d’akin ta ciki. Dudduba d’akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d’akin bacci madafar abinci da bayi, d’akin bacci katifa ce irin ta “yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k’arewa d’akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d’akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu. Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k’ok’arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had’ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad’ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d’in…… Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko……. Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d’aya d’akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k’asa tare da fara karanto duk addu’ar data zo bakina…… Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa. Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d’an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene……. Wato mai wannan gidan na karuwai. Da daddare misalin 9:30pm na sauko k’asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d’aya yana wurinsu, Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k’asa kaga zubina ai kasan nafi k’arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma. Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d’in, d’an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d’akin….. Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili. Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik’ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk’atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har “yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za’a kwanta dake, kin b’ata mishi rai yaji gaba d’aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed’an baya wasa da ita. Idan kika had’u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had’aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar……….. Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala…… Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba’a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had’a mata k’addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba. Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo, Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d’an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud’in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na…… Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik’ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak’in ciki dan zan b’ace muku b’at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani………… 07/08/2019⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA’ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari……_* *_ZAINAB ATTAHIRU B ‘ K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho…………_*🅿 —— 8 Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu’a, Allah na rok’eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik’a bud’ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci. Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k’ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad’e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne …… ? Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud’ina sauri nakeyi. Ina k’ok’arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d’abi’ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud’i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya ! Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud’i na ko in wulak’anta ki a wurin nan, d’an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak’anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci……..! Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani…… Dariya nayi sosai irin ta cikakkin “yan duniya na kashe dariyar da rangad’a gud’a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ?Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d’an iska dake fad’in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da “yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani….. Sauk’i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k’ok’arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik’e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had’u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d’an k’ank’anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad’in garinnan, sauka lafiya………. ! Ina fad’in haka na shige gidan karuwai, Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d’iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d’an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita, A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ……? K’arewa gidan kallo nayi sosai, d’akuna ne k’asa da sama, bene ya zageye k’asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud’a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d’aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito……. Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba. Bariki ba’ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k’afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had’ari guda d’aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d’auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata…..duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima, Kija da’irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d’aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d’aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d’akin zama ko nayi gaba………? Wani daga can saman bene yace ke “yar cakulkula dake har kin san dad’in namiji ? ‘Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji.Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d’aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d’auka daf bata iya d’auka, jirgi ya d’auke ka kuma ya d’au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k’aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi. Tabbas muna da masaukin ki, d’aki d’aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d’aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ? Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k’arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba………? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad’ai zanyi na k’ara gaba abu d’aya zuwa biyu nazo koya kad’ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud’in hayar ba haka na yanke.. Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata…….? Wata irin fad’uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d’auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk’ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k’are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba, Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d’aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad’a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d’auke da mugunta nace mashi idan an bani d’akin kai ka biya kud’in sannan kuma ka bani rance dubu d’ari, tukuicin d’aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d’arin ka kuma da kud’in d’aki duk zan baka su idan na fara kasuwa…… Ba damuwa a bata d’akin sama lamba 59 ya fad’a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d’akin, makulli aka bani na bud’e na shiga ina shiga na kulle d’akin ta ciki. Dudduba d’akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d’akin bacci madafar abinci da bayi, d’akin bacci katifa ce irin ta “yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k’arewa d’akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d’akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu. Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k’ok’arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had’ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad’ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d’in…… Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko……. Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d’aya d’akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k’asa tare da fara karanto duk addu’ar data zo bakina…… Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa. Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d’an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene……. Wato mai wannan gidan na karuwai. Da daddare misalin 9:30pm na sauko k’asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d’aya yana wurinsu, Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k’asa kaga zubina ai kasan nafi k’arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma. Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d’in, d’an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d’akin….. Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili. Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik’ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk’atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har “yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za’a kwanta dake, kin b’ata mishi rai yaji gaba d’aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed’an baya wasa da ita. Idan kika had’u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had’aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar……….. Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala…… Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba’a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had’a mata k’addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba. Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo, Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d’an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud’in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na…… Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik’ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak’in ciki dan zan b’ace muku b’at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani………… 07/08/2019⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 9 Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un, itace kad’ai abinda Dikko yake ta maimaitawa a cikin wannan tsalelen dare, Juyi yakeyi sosai a saman gado sai kace macen da ciwon ciki ya taso ta gaba, kifa kanshi yayi a saman lallausan bargon dake kusa da kanshi ya goge hawayen dake bi masa idanuwa. Allah na tuba…, ya fad’a a bayyane tare da gyara kwanciyar shi, girgiza kanshi yayi , yayin da zuciyarshi da kwakwalwar shi suka hasko mishi abinda yayi ma Sultana, a hankali ya lumshe idanuwanshi na tsawon lokaci sannan ya fad’a a bayyane baiwar Allah baki dace mahaifi ba, Sai kuma Allah ya jefoki a rayuwar Dikko yayin da nake nemanki, kika zo a daidai lokacin da na d’auki hud’ubar shaidan , Allah ya baki hak’uri kinji, ya k’arasa maganar tare da bud’e idanuwanshi duka da sukayi jajir saboda kuka…….. Ko ina kike ? Me kike yi yanzu ? Wane irin bak’in ciki kikeji idan kika tuna dani ? Ki zama mai yafiya a rayuwarki, manta da Dikko ki fuskanci rayuwa, ina nan ke kuma ina ki ke …..? Ina gidan karuwai,…. Ina shiga d’akina na mayar da k’ofa na rufe, ya zama lallai na gano waye mamallakin wannan gidan, sannan idan har na karb’i dubu d’ari a hannun wancan garan me ya kamata nayi da ita ne ? Ansar kud’in sune wahala Sultana anso su tuk’una idan suka zo hannu ba’a rasa abinda za’ayi ba, wannan shine shawarar da zuciyata ta fad’amin. Ajiyar zuciya na sauke tare da hayewa saman “yar k’aramar katifata na kwanta bacci. Da safe ina tashi sallah asuba nayi, na dad’e ina zaune a saman abin sallah ina addu’o’i na neman tsari d’aukaka farin jini da kuma k’war jini a harkar bariki. Sai 7:00am na tashi daga saman abin sallah, toilet na shiga nayi wanka, ina fitowa na shirya a gaggauce domin akwai inda nake so naje. Ina gama shirina na fito sanye cikin hijabina, sai nik’af dana dabkakawa fuskata, ina rufe d’akina mai kirana da irin sunan da Dikko yake kirana yazo. A k’ofar d’aki muka gaisa daga gaisuwa ban sake masa magana ba naci gaba da rufe d’akina. An mata ina zakije haka da safe ? Ban kalleshi ba nace zanje wurinka ne dama, murmushi yayi tare da cewa kuma gashi nima nazo wurinki yake nan .? Babu wani damuwa zamu iya maganarmu anan, mudai shiga daga ciki zaifi ko ? Ya fad’a yana kallo na, gyara tsayuwata nayi tare da cewa kayi hak’uri gaskiya na fito bazan koma ba, yana k’ok’arin bud’e bakinshi yayi magana nace kayi hak’uri da Allah bana san magana tayi tsayo na wuce, ina k’ok’arin tafiya yace d’an tsaya kiji mana. Tsayuwa nayi ba tare dana juyo ba, am dama cewa zanyi idan kina da hali anjima zamuje wurin Alhaji yace yana san ganin ki, ba tare dana juyo ba nace wane Alhaji ne ? Mai gidan nan, na bashi labarinki shi kuma ya matsa saiya ganki. Saida nayi shiru na wani lokaci sannan nace wurin k’arfe nawa zamu je kenan ? Yanzu ma dan zaki fita da munje saboda ba’a gida ya kwana ba yana nan bayan gidan nan yana tare da bak’i da sukazo wurinshi manyan alhazawa ne masu kud’i da suka ansa sunansu a kud’i, d’an mugun murmushi nayi a cikin nik’af ina sannan nace tou kai ya maganar kud’in da zaka bani ne ? Suna cikon mota muje, murmushin zalinci nayi irin wanda naga mugu Dikko yanayi sannan nayi gaba abuna ya biyo bayana. Cikin motarshi ya d’aukeni, muna shiga cikin motar na yaye nik’af ina tare da kallonshi sannan nace niko na tambaye ka mana ? Tambayarni mana ya fad’a a daidai lokacin daya fara tafiya da mota. Shiru nayi ban sake magana ba, shine ya gaji da shirun yace kinyi shiru kuma ! Ey zan tambaye ka amma ba yanzu ba dan na d’auka ne baka san tambaya da surutu ne kamar yanda nima bana so, amma tunda ka bani izini zan rik’a tambayarka a duk lokacin da tambayar yazo min, amma dai ya sunan ka …? Murmushi yayi sannan yace suna na Umar, gyara zama na nayi tare da cewa me yasa Babanku yasa maka suna Umar ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa sunan ubangidan shi ne, Zaici gaba da rattafo min bayani na dakatar dashi ta hanyar cewa barmin bayanin haka nan zan tambayeka wani lokaci, babu gardama ya kame bakinshi ta hanyar yin shiru…. Har muka isa bakin get in gidan babu wanda ya sake magana daga ni harshi, horn yayi mai gadi ya bud’e mana muka shiga, gida ne had’ad’d’en gida na “yan gayu yasha ado da shuke shuke na filawowi, daga gefe kuma wasu irin lafiyayun dawakai ne tsabtatacci kuma k’osashshi aka d’aure sai tattabaru masu kyau wanda suke sauka k’asa lokaci lokaci su kuma tashi sama firrr lokaci lokaci…. Gaskiya dokunan sun burgeni sun kuma bani sha’awa, amma dana tuna da Dikko yana san doki yana k’aunar doki a rayuwarshi sai kawai naji dawakan nan sun fita a raina, saima zuciyata ta fara tunanin taya zanyi in kashe su, domin na tuna cewa Dikko ya fad’a cewa yana san doki ko ba nashi bane, lallai ni kuma na tsani dawakai.. Muje Umar ya fad’a da yaga banda alamar fita daga cikin motar.Fitowa nayi tare da cewa Umar waye yake kiwon dokuna ? Wallahi na uban gidan Alhaji ne, ya bani amsa ne a lokacin da muka fara tafiya, tou shi Alhajin duk kud’inshi kenan yana da ubangida shima ? Na tambayi Umar, Umar yace Eh mana ai ubangidan nashi shine duk wata k’aryarshi, shine ya d’aure masa k’ugu shi ya tsaya masa saida ya tabbatar Alhaji ya zauna saman k’afafuwanshi , gaskiya mutumin kirki ne sosai, da yana harkar mata na tabbata idan na had’aki dashi yarinya kin warke, bake ba talauci, ke bake ba kaf zuri’arku da talauci ya k’are. Maganar Umar ta k’are ne a daidai lokacin da muka shiga palon gidan, k’aton palo ne mai girman gaske, sai wata irin dakekiyar tv tunda nake a rayuwata ban tab’a ganin tv mai girmanta ba, ko da yake ma ina naje ina na sani a wannan lokaci ? Saifa gidansu Dikko shima naga tashi tv n babba ce amma banda natsuwar gane wacce tafi girma,Bin palon nayi da kallo, d’an rumtse idona nayi na bud’e tare da k’ara d’ora idanuwana a saman hotunan dake palon, tabbas idan ban manta fuskar Dikko ba wannan shine Dikko, mutumin dana tsana nake san ganin bayanshi komin daren dad’ewa, dan ina sayen gida wa Babana Dikko shine mutum na farko da zan fara sabautawa rayuwa a duniya…… Muje suna ciki, Umar ya fad’a tare da katse mun tunani na, sauke nik’af ina nayi na rufe fuskata sannan nace mu koma gida, zai tambayeni dalili nace kawai mu koma zamuyi magana dakai daga baya. Haba Sultana har mun shigo wuri zaki ce mu koma…. Kallon Umar nayi sannan nace tunda nazo da kaina ai kasan zan sake dawowa ko ? Ina fad’in haka nayi gaba abuna…… Ina fitowa idanuwana suka cika da hawaye, tun ranar da Dikko ya ajiyeni a k’ofar gidanmu ban sake tunaninshi ba sai ranar da Umar ya kirani da An mata, ban sanka Dikko na tsani duk sunan daya fara daga kalmar D insha Allah ni zan zama ajalinka….. Kuma ta hanyar da kabi ka azabtar dani to nima ta hanyar zanbi in rama abinda kamin, yanda ka somar dani ni kuma saina kasheka…. Babana yaci darajar mahaifi na ne shi, zan tara masa dukiya ta hanyar karuwanci zaici yaci bulus amma wallahi kai Dikko bakaci banza ba….. Fitowar Umar yasa na saita kaina, na bud’e mota na shiga domin ya bud’emin ita tun lokacin daya fito, zakuji dalilin da yasa na fasa shiga ciki, Umar kad’ai yasan fuskata kuma yau ya zamar min wajibi nabar gidan karuwai domin wannan kwanakin sune kwanakin dana iba zanyi a gidan karuwai, na ga abinda nake so na gani, naji na kuma gani nima zanyi gaba dan nima in dogara da kaina. Muna fitowa yayi hanyar gida nace dakata ajiyeni nan, ina zakije ne ? Ya tambayeni , ban bashi amsar tambayarshi ba nace masa ga makullin d’akina kasa a gyara man, bani kud’in nan zanje in had’o makaman yak’i….. Miye makaman yak’i kuma ? Ba tare dana kalleshi ba nace ai kasan ba’a shiga gida dole saida sallama, gida ba shara ai baya dad’in zama, na ciki bai san akwai na waje ba idan baya kwankwasa ba, to haka bazai yuwu ba wani yaci abinci yace kai yaci mawa, kaidai bani kud’i kaji idan na dawo zan baka bayani, Kud’in ya d’auko ya bani, bayan na ansa nace samu wuri ka rubuta min number ka idan zan dawo zan kiraka kazo ka taho dani, yo ina wayarki ne ? Banda waya amma ka rubuta min zan samu aro na kiraka, rubuta min yayi a jikin takarda ya mik’omin, ansa nayi na fita daga motar tare da cewa sai munyi waya… Saida na daina hango Umar sannan nima na ibi tawa hanyar na shiga duniya……, Tafiya nayi mai tsayi ba tare da sanin inda zanje ba sannan na tsaya wani shago na samu aron waya, lambar Umar na basu nace da Allah su saka a waya su kirashi, ansa mai shagon yayi yasa lambar ya kira, babu wani b’ata lokaci aka sadani da Umar…Sultana ce, na fad’a a lokacin da Umar yace hello, Oh kin gama ne ? Ya tambayeni, maimakon na bashi ansa saina kece da dariya kamar hauka sabon kamu….. Meya faru ne ? Inji Umar, saida na gaji da dariya dan kaina sannan nace darasi. Yau na tabbatar ni bariki ta fini tabbas na tafi na barka, wannan makullin d’akin daka bani ne shine na dawo muku da kayanku, amma zan baka sak’o a wurin Dikko tunda kasanshi , ka fad’a mishi cewa Sultana tace zasu gauraya…….. Ina fad’in haka na yanke wayar na mayar da ita ga mamallakinta nayi gaba abuna…. Wata irin zufa ta ketowa Umar mai makon salati sai ashariya, ya fara luk’ak’a zagi tare dayo waje da gudu, yana cewa amma lallai yarinyar nan ni zata danfara, wato wani bazaici abinci yace kai yaci ma ba, wato nine abinci itace bakin ni zakici ki gudu ? Kuma har kike wani cewa mai gida Dikko zaki gauraya dashi ? Kai wallahi idan na yadda shege ne ni, kuma yanzu zan kira Dikkon zaki ci kutumar ubanki, kici dubu d’ari zanci miliyan daga jikinki. Jikinshi na kyarma ya fara kiran wayar Dikko har ta tsinke bai d’auka ba, k’ara kiranshi yayi bai d’auka ba, ci gaba yayi da kiran wayar babu k’ak’k’autawa, saida ya kira Dikko yakai sau goma sannan miskilin ya d’auka wayar….. Ya akayi ne ? Shine tambayar da Dikko yayi ma Umar, cikin tausasa lafuzzan shi yace ranka ya dad’e kasan wata yarinya Sultana….. ? Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un Dikko ya fad’a a ranshi lokacin da aka ambaci sunan Sultana, Me ya faru ne ? Dikko ya tambaya ? Umar yaci gaba da cewa ranka ya dad’e yarinyar nan “yar damfara ce, tazo nan gidan “yanci ne , gidan karuwai suke cewa gidan “yanci, dan idan aka kira karuwai d’in haka abun babu dad’in ji. Shi yasa su gogaggin “yan bariki suke kiran gidan da gidan “yanci. Wata irin zufa ta tsatstsafowa Dikko amma yayi shiru yana sauraren Umar, ranka ya dad’e kwananta hud’u a gidan “yanci shine yau ashe ta shirya guduwa ta raina min hankali ta ansar min kud’i dubu d’ari akan zata bani tukuici, { zasuyi iskanci } shine ta gudu, wai kuma saboda ta d’aukeni sakarai wai tayomin waya in fad’a maka wai zata gauraya dakai. Saida Dikko ya goge zufa sannan yace yanzu kayi hak’uri zan biyaka kud’inka, ai ranka ya dad’e ni ba kud’in bane yafi damuna mummunar maganar data fad’a a kanka ne, bayan zata gauraya dani tace maka wani abu ? A , a batace komai ba, amma ina ruwanta dakai ? Tana da dalilinta na fad’in zata gauraya dani, ka fita harkar yarinyar nan zan tura maka kud’inka karka ma sake kace zaka sake tashin wata magana kuma karka sake ka nemeta , Umar yace mai gida zafa ta gaura dakai ? Ka kuwa san abinda gauraya take nufi ? Dikko yace ta gaurayo dani d’in ina ruwanka ? Kaine tace zata gaura ko ni ? Shiru Umar yayi, tsoki Dikko yayi da niyar kashe waya, Umar yace ranka ya dad’e nidai idan kaine zaka biya kud’in nan na yafe maka su, Dikko yace ita zaka yafewa bani ba tunda ni banci maka ba, taci albarkacinka na yafe mata, na gode shine abinda Dikko ya fad’a tare da kashe wayarshi. Miye tsakanin Dikko da Yarinyar nan ? Shine tambayar da Umar yakewa kanshi wanda ya rasa mai bashi amsar tambayar, tou yaushe mai gida ya fara harkar mata ne ? Dariya yayi tare da cewa shegiya duniya mata bala’e ne wato duk musulinci mutum da kawaicinshi babu uztaz babu mahaukaci kowa dai yasan darajar ku, ai dole nake yafe dubu d’ari nasan wasu miliyoyi ne zan ansa, inama zanga yarinyar nan da na tambayeta miye tsakaninta da Dikko. Mi yasa zakiyi haka ? Me zaki tsinta a harkar karuwanci banda wahala ? Me kike so ne ? Me kika rasa ? Kud’i ba damuwa na bane da zan ganki da na wadaki da dukiya har sai kin rik’ajin kyankyan kud’i, k’amshisu ma idan kikaji saiya rik’a tayar miki da zuciya, ke kuma duniyar kike so ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa Allah yasa miki natsuwa ki dawo daga rakiyar shaidan. Allah ya had’ani dake Sultana in baki hak’uri in kuma nemi yafiyarki, Mutane sunamin bahaguwar fahimta, yanda kike kallona ba haka nake ba, kuna min wani tunani na daban bayan ba haka Dikko yake ba, Duk abinda ya faru tsakani na dake wallahi ina ganinshi ne kamar wasa, banso haka ba, bansan ya akayi nima na koma kamar wani sakarai ba wallahi, Allah ya tsareki fad’awa halaka, idan har kika fad’a harkar karuwanci na cuci rayuwata da zuri’ata da banma fara tunanin auren ba. Farin ciki kamar in tashi sama yau gani ga naira dubu d’ari, kud’i suna da dad’i gaskiya da farko dai saina ci kaza, sannan na gano wani abu d’aya da maza suke so a tattare da mata, suna san k’osashshiyar mace, suna san tsaftatacciyar mace, suna san mace mai aji suna san mace ma’abociya k’amshi macen data iya soyayya da tattali, ina zan nufa yanzu ? ………. 16/08/2019 Da Allah kuyi hakuri rasuwa akayi min ne kukaji shiru da dad’ewa haka, Ina ma kowa barka da sallah, Allah ya maimaita mana yasa muna da rabon ganin na bad’in bad’ad’a, amin. Barka da sallah.⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 10 Lallai idan nayi shiru da maganar nan ban fad’awa mahaifin Dikko ba nan gaba ya gano wani abu lallai zan fuskanci baraza na dagani har mahaifina, kila ma ya kora mu, ya zama wajibi naje na fad’a masa halin da Dikko yake ciki, in yaso zaiyi bincike abinda ya had’ashi da ita yarinyar, Umar yake magana duk abin yazo ya dameshi yana mamakin abinda ya had’a Dikko da mace har take fad’ar zata gauraya dashi….. Dikko mai zafi akan mata, ya akayi ya koma mai sanyi ? Wuta ne mai tsananin k’unar gaske ga duk macen data matse masa, babu abinda ya tsana duniya irin mata, amma wai shine yake godiya akan mace… Wace ce ita ? Miye tsakanin su ne…. ? Kayi shaye sheyenka ne Umar shi yasa ka manta wace ce Sultana….. Tsohuwar anguwarmu ta farko na koma, inda Dikko yayi ta siye siyen gidanjen da muke kamawa haya, gida mai sauk’in kud’i na samu na kama d’aki d’aya, bayan na biya kud’in d’aki na tafi kasuwa dan siyo d’an abinda ba’a rasa ba na amfanin yau da kullum. Na dad’e sosai a kasuwa, saboda duk abinda nasan zan nema saida na tabbatar na siya saboda ni rayuwata ta duniya babu abinda na tsana irin aro, bana san na takura shi yasa zanyi k’ok’ori na bada k’addarata dan na samu kud’i……. Umar durk’ushe a gaban mahaifin Dikko, hada wani hawayen munafirci kanshi a k’asa kamar sabuwar amarya a daren farko, Dady kuwa gaba d’aya yanayin fuskashi ya sauya zuwa damuwa bayan ya gama jin duk maganar da Umar yazo da ita, shi baya hana Dikko yayi magana da mata bane ko wani abu a , a shi baya so dai ya shiga damuwa har wani abu yazo ya sameshi, kuma idan yayi ma Dikko maganar aure sai yace shi yaro ne a bari saiya k’ara girma, ga Umar kuma yazo ya fad’i k’arya da gaskiya dandai kawai a bashi wani abu, wannan fada ce ko kuwa maulace ? Kallon Umar Dady yayi sosai sannan yace kirawo min shi…. Umar ya kira Dikko yafi so a irga amma bai d’auki wayarshi ba, ganin haka yasa Dady ya fara kiran Dikkon da kanshi, shima bai d’auka ba, jinjina kai Dady yayi tare da turawa Dikko sak’o kamar haka…. _Babana idan ka gama abinda kakeyi ka kirani._ Umar kuwa yana tashi daga wurin Dady ciki ya wuce inda iyayenshi suke, a gidan su Dikko Umar da iyayenshi suke zama, suna a k’ark’arshin su Dikko ne, kuma Umar shine mutumin da yayowa Bello jagoranci aka kawoni wurin Dikko, ni da dare na ganshi amma Allah yasa na ganeshi duk da jakanci na, amma shi ya kasa ganeni kwata kwata…. Umar bai dad’e da tashi ba kiran Dikko ya shigo cikin wayar Dady….. Da farin ciki Dady ya d’auki wayar tare da cewa ina ka shige ne ? Ko kana tunanin surukata ne ? Ya fad’i maganar cikin sigar zaulaya, d’an gyaran murya Dikko yayi tare da cewa barka da yini, ya gaishe da Dady dan kauda waccan maganar….. Ansawa Dady yayi suka gaisa cikin farin ciki da soyayya irin na d`a da mahaifi. Bayan gaisuwa Dady ya tambayi Dikko labarin yarinya da Umar yazo mishi da ita, miye tsakaninsu kuma miye gaskiya labarin …? Dady ya k’ara da cewa banso soyayya tayi min wasa da rayuwata, domin duk abinda ya tab’a hanci ido ruwa yake, tou duk abinda ya tab’oka ni ya shafa. Me ya had’aku har take zaginka ? Gyara zama Dikko yayi sannan yace ba komai, kuma ma ai bata zageni ba Dady, duba Babana yaushe ka fara b’oyemin abinda ya shafeka ? Ni zaka juyawa baya ? Me zaka b’oyemi bayan kasan ni bana b’oye maka komai ? Fad’amin abinda ya dameka muyi damuwar tare….. Shiru Dikko yayi na wasu mintoci yak’i yayi magana, Dady yace kai nake saurare Babana kaji tsoron Allah ka fad’amin abinda yake damunka idan har kana so nayi bacci a daren yau….. Har yanzu Dikko baiyi magana ba kuma bai kashe wayar ba, Dady ya k’ara cewa ka daiji tsoron Allah ka fad’amin gaskiya k’arya ba halinka bane kuma masu sunan manya basa fad’ar abinda ba gaskiya ne ba, gaskiyar mahaifina da amana irin tashi yasa na saka maka sunanshi saboda kwad’ayin kaima ka zama mai gaskiya da amana kamarshi, kuma ina fatan ka zama mai adalci ko bayan bana duniyar nan….. Ina so ka zama jigo ga “yan uwanka ka tausaya musu ka karb’i damuwarsu ka sakasu farin ciki karka barsu suyi kukan rashin mahaifi, inaji a jikina bazan dad’e duniya ba, nayi kuka kuma na shiga damuwa rashin samun d`a namiji, sai kuma nayi farin ciki a lokacin da Allah ya azurtani dakai… Idan kaga na damu da nasan abinda yake damunka saboda in d’oraka hanya idan naga zaka sauka daga saman layin gaskiya, ina fad’a maka tawa damuwar ne dan ka gane abinda duniya take ciki.Me ya had’aka da yarinyar mutane take zaginka ne Babana ? Cikin kame kame yace Dady nifa ba zagina tayi ba, kuma ma yake maganar cewa tana min rashin kunya a ina akayi haka ? Ni ba ruwana da ita sab’ani ne kawai muka samu kuma ma ai abun ya wuce…. Saidai inayin mafarkinta idan ina bacci, inajin damuwa ne idan na tuno da ita, sai kuma inji kamar tana kiran suna na wani lokaci, kuma sai inji kamar tana tare dani, inajin kamar numfashinta a jikina sai kuma shashshekar kukanta tana dai zuwa min sosai a ranaku da dama, shi yasa ma nake d’an tunani, amma bayan haka banda wani damuwa da ita. Tou soyayya kakeyi da ita ne ? Dady ya tambayeshi, no ba soyayya kawai dai rashin kunya tamin sai nayi maganin bakin tsiwa, kamar ya dady ya sake tambayar Dikko, shiru Dikko ya sakeyi ya kuma rasa abin cewa. Kai nake saurare, Dady ya fad’a, kwashe komai Dikko yayi ya fad’awa dady amma bai fad’a masa labarin wani abu ya shiga tsakaninshi da Sultana ba, kawai dai yace ya sissiye gidajen da suke haya ne, a haka aka tsaya ba maganar yayi wani abu da ita. Nasiha Dady yayi ma Dikko kamar yanda ya saba, yace yayi ta addu’a, kuma zasu tayashi har Allah yasa ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi, godiya Dikko yayi ma Dady sukayi sallama. Haka kuwa akayi domin dai Dady ya mik’e tsaye yasa ayiwa Dikko rok’on Allah dan shi a tunaninshi Sultana aljana ce, ko kuma mayu ce ko tanawa d`ansa asiri ne, dan haka Dady ya tsaya akan k’afafuwanshi saida ya tabbatar Dikko ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi sannan hankalinshi ya kwanta……….. Wannan kenan……….. *** _{ kalu bale gareku matan aure………. }_ Gidan da na kama haya gaba d’aya gidan matan aure ne babu zawara ko d’aya haka babu budurwa idan bani ba…….. Kowa da mijinta daban babu wacce ta had’a miji da wata, abinda na fuskanta da rayuwar mazauna gidan kowa yanayi ma d’an uwansa kallon hadarin kaji ne, babu wanda yake san kowa sai zazzafar bak’in ciki da jin zafi da gasa da kowa yake nunawa abokin zamanshi ido biyu kunne tsaye babu kunya bare kawaici. Gidan babu katsari kuma bashi da saiti kowa yaga dama shigowa yakeyi, sai a tara dandazon taron mata ayita maganganun sakarci da rashin kamun kai, shi yasa zawarun anguwar da “yan mata wanda suka bushe fitilarsu suka maida gidan dandalin sauke lalatarsu. Suna da wata d’abi’a d’aya dana lura da ita ta wasan banza, kuma basajin kunyar nuna tsiraici wa junansu, ma’ana kamar irin cire riga da bra a lokacin fira, irin wancan tace amma wance gaskiya kinfi wacce nono, basajin kunya sakin maganganu na sakarci da fallasa sirin mazajensu. Duk da ni yarinya ce mai k’aranci shekaru a cikinsu na raina musu wayau gaskiya, kuma na d’aukesu wawaye idan naga dama zan basu shawara kuma idan suka d’auka zata musu amfani, amma gaskiya banga dama ba, haggu zanyi amfani da ita dan ni yanzu ba shiriya nake so ba lalacewa itace na zab’a kuma duk wanda naga zai lalace saina kama mishi ya lalace, dan nayi alk’awari saina kafa tarihi a garin katsina, ina so in zama cikakkiyar karuwar da sai suna na ya shiga cikin sahun “yan iska a duniya, dan bazan yadda nayi karuwanci wahala ba. Kujerata na d’auka na nufi k’ark’ashin bishiyar da ake zaman majalisar, ina k’ok’arin kafa kujerata zan zauna wata zawara tace ke Sultana tashi nan ba wurin zaman yara bane ba kinji….. Gaba d’aya suka shek’e da dariya tare dayin gud’a, { ayyuri yuri yuriiiiik…. } aka kashe, murmushi nayi tare da ajiye kujerata na zauna, ba tare dana kalleta ba nace dan anyi ciwo an warke ai ba’a ba mutuwa haushi ba, abinda kike takamar an baki nima naci irinshi, tou me za’a b’oyewa ruwa bayan babu inda bai shiga, ansha kuma anyi wanka dashi aikuwa kinga farin wata ba bak’on dare bane ba. Duk macen dake wurin saida ta kalleni, murmushi nayi irin na “yan duniya tare da d’aga girare na duka nace muci gaba da zance ai abokin cin mushe ba’a b’oye mishi wuk’a. Sama sama dai akayi firar wannan rana babu wani labarin ci gaba da guda guda kowa ya sab’e duk wanda ba gidan yake ba yayi tafiyarshi aka barmu iyakarmu “yan gidan….. Bayan sun fashe ne kowa ta tashi ta fara aikin gabanta tunda masu labarin iskancin sun tafi, dan haka sukeyi idan dai ana wannan firar jarabar babu macen dake motsawa, idan kuwa d’anta zaiyi kukan mutuwa bata kulashi. Maganar sallah kuwa saidai a mik’ata a jimlace, wai sai an gama zance duniya za’aje ayi alwalla lokacin za’ayi azahar la’asar magrib isha’i, wata ma idan ta makara bata tashi sallah asubahi ba, har gari ya waye tou duk wacce ta fito ta samu an fara fira tou wannan sallah sai anjima za’ayi ta, nan mace zata jibge kamar asara ayita kiraye kirayen “ya “yan dan ubanki baza ki kawomin kaza ba, Saida kowa ya tashi sannan nima na d’auki kujerata nayi d’akina, buta na d’auko nazo nayi alwallah magrib na shige tare da rufe k’ofata ba kuma zan sake fita ba sai Allah ya kaimu gobe lafiya….. Dan babu abinda banda shi a cikin d’akina na masarufi, ina da indomie ina da kayan tea kuma ko wane lokaci flarks ina cike yake da ruwan zafi, saida nayi sallah isha’i tare da addu’o’in samun d’aukaka kamar yanda na saba a duk lokacin da nayi sallah. Bana buk’atar komai domin banajin yunwa, a inda na gama sallata a wurin nayi kwanciyata, ban dad’e da kwanciya ba bacci yayi gaba dani….. Can cikin bacci naji hayani wanda tak’i k’arewa muryar Nana sama sai zabgaga ashariya takeyi tare da cewa auren ka ko auren wahala, auren cida kai niba ga gidan gayu ba na bige ga zaman haya, har kunya nakeji k’awayena su san inda nake dan darajata da nasabata ta wuce in aureka haka nan Allah ya had’ani da wannan auren k’addarar da k’aranci shekaruna duk kabi ka bigar dani na koma wata abun tausayi, tou wallahi idan kaga yau na kwana dakai saika biyani duk bashin daka san inabinka…. Ajiyar zuciya na sauke tare da kallon “yar agogon dana mak’ala a jikin bangon d’akina 11:45pm, maida kallona nayi wurin da Nana da mijinta dake rik’e da wandonshi yana mata magana amma bana iya jiyosu…. Zazzaga Nana tayi tare da cewa wallahi ka mutun ba abinda ya dameni idan ma ka mutu ko ka sakeni ai dubunka suna can suna jirana, magana ya sakeyi still banji abinda yace ba, Nana kuwa ta sake d’aga murya cewa bazan koma d’akin ba, kamata yayi da kokowa yana k’ok’arin turata cikin d’aki, d’an gajeran tsoki nayi tare da tirr da Allah wadai da wannan hali…. Bansan yanda suka k’are ba na koma nayi kwanciyata naci gaba da bacci na. Tunda na kwanta ban sake farkawa ba saida aka fara kiraye kirayen sallah asuba…… 17/08/2019 *JAMILA MUSA*🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 11 Tashi nayi na fito nayi alwallah, bamma kowa magana ba na koma d’akina… Kuma koda na gama sallah kwanciya na k’arayi dan inajin gajiya sosai ga kuma bacci. Amma k’iri k’iri baccin ga yak’i zuwa, hankalina da tunani na gaba d’aya ya tafi ina tunanin irin yanda Nana ta tozarta mijinta daren jiya a cikin bainannasi, miji da yake da daraja yake da matsayi yake da mutunci abin tattalawa idan Allah ya baka, ubangiji ya rataya ma Nana rigar arzik’i amma tana k’ok’arin yagata ta ratayawa kanta rigar wahala, idan har Nana ta fito daga gidan mutunci ko a gaban d’iyanta batayi wannan iskanci ba amma shine har ta fito tsakar gida kuma gidan ma na haya dan ta nunawa mutanen gidan cewa ita ta hana mijinta hak’k’inshi. Gaskiya abinda wasu matan sukeyi bai kamata ba, duk yanda akayi a zaman jiya aka rud’awa Nana tunani, ashe kuwa idan har zaki biye ma labarin “yan iskan mata babu ranar da hankalinki zai kwanta a gidan aure, su basuyi auren ba kuma su hana masu zaman auren suyi aurensu, sai su rud’aki da zance babu labarin k’arya a samu a kakkab’oki sai kin fito daga gidan mijin kizo kiga labari yasha banban….. Maganar Karima najiyo tana cewa jama’an gida ku fito majalissa d’inki duniya ta fara tattaruwa, ga A’ i nan ta taho da labari, Nana tace ai bama labari kad’ai tazo dashi ba naga ta shigo da leda duk “yanda akayi daren jiya anci kaza mu ta ragowa sauran, kaji jakka sai kace rainon mayu dan ubanta. Hayaniyar matan gidan naji da alama kowa tayo waje, agogo na kalla naga duka 6:22am, gaskiya dai hakan bai kamata ba da zasu yadda dana basu shawara amma bara nima na fita wajen mu gani….Nana na gani tana wanke fuskarta tare da cewa ai ilimi yafi sallah ita sallar bara a jingineta idan na gama d’aukar darasin nayi ta daga baya….. Kallonta nayi k’asa da sama amma banyi mata magana ba, duk yanda akayi Nana uwayenta jahilai ne, wata zuciyar tacemin karki zargi iyayenta Sultana wallahi kina iya ganin babu laifinsu d’a nawa kake ba tarbiya idan yaga ba idonka ya barbad’ar da ita yayi wanda yake so. Ina isa inda kowa yake na kalli A ` i, nace gaskiya ki daina yo mana sabko duk fa masu gidan basu fita ba kawai sai ki baro gidanku kizo ki hana mazajen wasu baccin safe ? Irin haka da kukeyi gaskiya bai kamata ba, kallon Nana nayi tare da ci gaba da cewa gaskiya kuma matan gidan nan kuna da naku laifi da kuna zamanku a wurin mazajenku baku fito ba babu wacce zata rik’a dako muku sammako ta hanaku samun ladar kwanciya a jikin mazajenku….. Nana zatayi magana A ‘ i tace barta in bata sani ba a fad’a mata, kallona tayi tare da cewa ke Sultana kinsan makaho idan yana kashi baisan ana kallonshi ba sai an tsokalo d’uwawunshi, munsan tal munsan sal abu d’aya yasa bazan gaya miki ko waye ubanki ba da rayuwar gidanku amma yau dana bud’e miki zani cikin kasuwa. Ke harma kina da bakin da zaki zo ki wani ce an hana mazan wasu bacci , ina kika san wannan keda uban naki ma ko gidan bai kwana….. Murmushi nayi ba tare dana nuna naji zafi akan tabo Babana da tayi ba nace….. Ai duk ubanda ya ganni yasan ubana zauna gida ne, ko bai kwana ba kinsan yayi k’ok’ari kuma ya fita hak’k’in mata tunda har ga sakamakon mu ya fito, duk namijin daya zauna gida ai soko ne tunda babu k’ashin zuciyar da zaisa ya fita neman abinda zai ba iyali, niko zuciyar ubana tsaye take wurin nema ya nemo aci asha kuma ko bai kwana gidan ba da safen idan ya dawo suma matan gidan zai basu hak’k’insu kinga kuwa dan bai kwana ba ai ba aibu bane ba tunda dai abinda suka aure shi danshi d’in ai yana basu bai hanasu ba. Saboda mata da yawa wannan abun dake kika raina su sunsan darajarshi, wasu matan kuwa zasu iya hak’uri da talaucin namiji amma wannan abin d’aya da kike magana akanshi basu yadda su rasashi ba, wata macen kuma mijinta ya daketa ya hanata abinci amma idan dai zai kwanta da ita ta samu gamsuwa zatayi hak’uri taci gaba da zama dashi a haka tasan arzik’i na Allah, amma wata ita ba shi take mawa ba rayuwarta da tunaninta ya tafi wurin tunanin neman duniya, kamar dai ni dake kinga ba abun ya fiddo mu ba kasuwanci muka d’auke shi, tou haka matan gidan nan suke su ma, da mazajensu masu kud’i ne ko sunyi wani abun wani sa d’aga k’afa dan duk yanda ka raina d’an tsintsu bakacin shi da gashi, namiji ya sakarwa mace ragamar gida ai dole ta koma mijin shi ya zama matar, amma duk da haka dai ki sani Allah ba ruwanshi da kin nemo kinba miji tunda hak’k’in cida da sha sutura da wurin zama lafiya da ilimantar wa duk saida ya d’auki alk’awarin zaiyi a gaban waliyyanki , To tunda anyi auren kin gane bazai iya ba ai sai a raba auren ki huta amma bawai ki zauna kiyi ta yayar ma kanki zunibi ba, zaiyi wuya kiji mace taje gidansu takai k’arar mijinta yana basu abinci so d’aya a rana. Amma mafi yawancin mata namiji ya hanasu hak’k’insu ko baya gamsar dasu sai kinji sunyi tsegumi, aba k’awaye labari aba mak’ota labari aminiya da duk wanda kike hud’d’a dashi sirrin mijinki fallashshe ne, tou wa kikayi mawa ? Nidai shawara ce idan ta muku zafi sai kuyi hak’uri, amma ya kamata ku rik’a sirrinta sirrin mazajenku domin dai wannan sirri ba abin yayad’awa bane shi yasa yake rufaffen sirri ko an shiga d’aki sai an rufe k’ofa…. Tsoki Nana tayi tare da cewa mu idan zaki zauna kiji ki zauna idan bakiji ki k’ara gaba, Karima tace da Allah kyaleta tafi ma mill tsayuwa bamu fasa zancenmu, ke A ‘ i albishirinki ….! Saida A ` i ta harareni sannan tace goro,Jiya fa Audu yaci ubanshi da gudu ya biyo Nana har tsakar gida, kallon Nana tayi tare da cewa kai jiya fa Nana tayi bala’i gidan nan , can naji gurnanin munafiki kamar an kwacewa mahaukaciya diyarta….. Ke Nana bada dai labari da kanki kinsan masu iya magana nacewa wak’a bakin mai ita tafi dad’i, mu na waje muka gani bamu kalli na d’aki ba. Tab’o ledar hannun A ` i tayi tare da cewa da Allah idan dai namu ne ki bamu mu cinye sai miyau na yake tsikewa, mik’a musu tayi “yan iska masu kama da maguna suka rarraba suka cinye, Nana na cewa dan Allah A ` i ki kawo min ice cream rabona da insha shi tun ina budurwa, Karima ta katse ta da cewa haba da Allah bamu labarin Audu ki daina wani zancen ice cream, lashe hannunta tayi sannan ta fara cewa, in fad’a muku tunda na ganshi ya shigo da leda nasan dole yana buk’ata… Ajiye ledar yayi a gefe na tare da cewa karfa kiyi bacci, inajin yace kar nayi bacci nasan tafiye yake da damuwarshi, saida na bari ya gama abinda yakeyi tsaf yazo ya hawo ta bayana yana wani shashshafoni na fara mutsirniya, cikin raunanniyar murya magana mai fitar da numfashin wahala yace kar muyi haka dake Nana yau kusan sati biyu kenan kina hanani hak’k’ina bakyajin tsoron fushin Allah ya sauka kanki ……? Aiko na b’ata rai nace gaka k’atoton wanda fushin Allah zai saukar mawa , ai idan dai har kaga ka kwanta dani tou wallahi sai ka biyani duk bashin da nake binka….. cikin rawar jiki ya fara k’ok’arin juyoni yana cewa kiyi hak’uri Nanata wallahi ba’ayimin biyan bashin ba, kuma banyi ciniki sosai ba yau abinda na samu gashi nan na biya na dafo miki indomie, tsoki nayi tare da cewa ai sai ka cinyeta ka kwanta kayi bacci. Haba Nana idan dai har kika ga anci ko ansha saida natsuwar ci, ina tare da babbar yunwar da abinci bazai gusar min da ita ba kin sa na zama wani susutacce na zama kamar wani tab’ab’b’e banda natsuwa bare kwanciyar hankali kiyi hak’uri don Allah yauma karki ce zaki hanani…. Ai ban gama jin zancenshi ba na duro daga saman gado nayo waje….. Ni kuma naji tana wannan haukan shi kuma ya jata suka koma d’aki. Murmushi nayi tare da cewa kin burge Nana…. Tou me ya faru bayan kun koma d’akin ne ? Tunda na lura basa san gaskiya shi yasa nima zan biye musu mu zama riftattun gaba d’ayanmu, Nana tace ai koda ya maidar dani d’aki da k’arfin tsiya babu abinda na yadda ya shiga tsakani na dashi, yayi magiyar yayi nacin kuma ya jaraba ansa ta k’arfin tsiya amma ya gagare shi, dole ya hak’ura ya fita baima kwana gidan ba…… Dariya nayi tare da cewa tou ina kike tunanin ya tafi Nana ? Yo can shi ta matse mawa koma gidan uban waye ya tafi bai dameni ba wallahi saiya biyani bashi na ko zaici gaba da kwanciya dani. A ` i kuwa cewa tayi kwarai Nana karki sake ki yadda ko gidan haya kake zaune kud’in wata ya k’are idan baka biya ba no uziri tashinka akeyi, ya baki idan babu kullum yaita kwanan hak’uri, gaba d’aya suka bushe da dariya…… Banda ni da nabi Nana da kallon tausayi !!! Mijin Karima ne ya fito cikin kunya yana san ya shiga bayi amma kunya ta hanashi fitowa dan yanzu mun k’ara yawa, daya d’aga labule ya hangomu sai ya koma, k’arshe dai hak’ura yayi da wanka yasa rigarshi yabar gidan….. Fira akaci gaba dayi tunda muka zauna har zuwa yanzu babu macen data tashi koda wasa, ganin rashin aikin yin nasu bashi k’arewa yasa na tashi dan ina da wurin zuwa anyi firar dare dani idan banyi baccin wuri ba, Saida na share d’akina na gogeshi tass na kunna tsintsiyar k’amshi sannan na zuba ruwa naje nayi wanka, ina fitowa na shirya saida na gama shiri na sannan nasha ruwan tea ko biredi babu ina gamawa nayi ma mutanen gida sallama tare da rufe d’akina nayi gaba abuna….. A zaure na sauk’e nik’af ina na fice daga gidan tare da addu’ar yo babban kamu idan na fita, A ` i na gani tsaye da wani amma bansan ko waye ba, ni mamaki ma ya kamani dan bansan lokacin da A ` i ta fito daga gidan ba… Har zan wuce naji tace ina zuwa haka Hajiyata ? Yaye nik’af ina nayi tare da rage girman idona na dama nace farauta zanje kinsan sai ka gane girman gida kake sanin ta inda zaka fara shara…. Murmushi A ` i tayi tare da matsowa kusa dani ta d’an rik’o k’uguna da hannu d’aya, sannan tayi min wani irin kallo wanda ni bansan abinda yake nufi ba…… Saida ta wani yi k’asa da murya sannan tace da ganinki zakiyi tunon asiri amma ina gargad’inki da ki rik’awa bakin linzami ta k’arasa maganar tare dayin murmushi, bud’e idanuwa nayi dukansu wanda idan har na d’an ragesu na bud’esu lokaci d’aya nasan ina k’ara kyau kuma mutane sunsha fad’amin haka. Kallonta nayi da duka idanuwana sannan nace dama tunda kike kin tab’a ganin mazinacin da yayi sirri ? Miya had’a karuwa da sirri dama ? Ai da amana da kunya da sirri da gaskiya duk karuwa bata dasu, kunya tana tasowa ne daga b’oye tsiraici tou ban b’oyeshi ba zan bud’ashi wa duk wani mai kud’i ya gani, kinga nan rashin kunya ta fito, daga inda babu kunya kinga babu imani duk mutumin da baida imani kuma bashi tare da rahmar Allah, ina bud’ewa ga maza, namiji kad’ai ya isa ya gani yasha kuma ya tab’a dan haka sakarmin k’ugu daga yau karki kuskura ki sake tab’amin jiki, idan har na baki sha’awa tou ki zama namiji kizo da dubu dari shidda sai in baki duk abinda kike gani a jikina ya burgeki, na k’arasa maganar tare da sauke hannunta a jikina….Kallona A ` i tayi tare da cewa ai duk saurin anguwar zoma ta bari a haihu ? Duk saurinki kin bari kiji uzirin da nazo dashi….. Bud’e k’ofofin hancina nayi sannan nace ai tunda har aka tanaji aikin ungozance ansa haihu tana zuwa kinga kuwa duk daren dad’ewa amfaninta zaizo. Tou ni bana jira idan na gani saina tanka na dakatar dake ne tun kafin cikin ya samu bare kisa ran ansar haihuwar…. Na sanki cikinki da waje, duk macen dake gidan nan nasanta kuma tun ranar da na kwana na gama karatun halin kowa, kwalwa ta gane inda mutum ya dosa Allah ya bani amma bai bani kwalwar gane rubutu da karatu ba, ina iya gaya miki duk macen dake lesbian a cikin gidan nan , kuma ina gane duk macen da namiji ya kwanta da ita ba tare da na sani ba, ki kiyayeni ina da had’ari ne mai girma domin nima kaina tsoron kaina nake, ki fita idona tun kafin inyi miki terere……. Shiru A ` i , tayi ta kasa magana….. Murmushi nayi tare da dafa kafad’arta nace yawwa kisan wani abu gaskiya ni bana gaba da mutum ina so abun nan ya tsaya iya mu biyu, zan wuce ki gaishe min da mijin Nana kuma bazan bata labari ba , ina fad’in haka nayi gaba abuna….. Cin amana da rana k’iri k’iri wannan fa shine an raka zomo rami an dawo…. A ` i takai Nana ta barota gashi kuma tana tare da mijinta, kila ma jiya da yayi zuciya da Nana wurin A ` i ya tafi ya kwana, tabbas ma can yaje tana nan tana haukan banza mijinta yaje ya siyo ma k’atuwar banza kaza taci ta rago musu…. Zuciya ta ce tace Sultana kiji tsoron Allah zato zunibi, tsoki nayi tare da cewa wannan ai ba zato bane abinda yake filin Allah kowa yana gani dandai kawai gaskiya bata fad’uwa, sudai suka sani amma idan tayi tsami kowa yaji. Napep na tare na fad’a mishi inda zanje, ciniki mukayi na shiga yaja muka tafi. Yau babu inda zan sauke zango sai wurin Alhaji mai gidan “yanci, wato inda Umar yakai ni da farko ban shiga ba na dawo, dalilina na haka kuwa yanzu zakuji……. 18/08/2019 *JAMILA MUSA Ce* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 12 Abinda yasa banbi Umar mukaje gaban Alhaji saboda na shirya lafiyayyar yaudara da zanyi masa, sana’ar karuwanci tayi min kad’an gaskiya dan haka dole sai na had’a da sata, shekaru biyu kacal zanyi a cikin wannan mummunar d’abi’ar, ina so na shigewa Alhaji sosai a rayuwa idan ya saba dani zan kunce dawakan Dikko duk in siyar dasu, nasan duk doki d’aya za’a siya da kud’i masu yawan gaske. A wancan lokacin da munje tare da Umar Alhaji yaga fuskata tou kud’in Umar da nayi wayau na kwace masa tou Umar zai koma ya fad’awa Alhaji cewa wannan yarinyar b’arauniya ce ayi hankali da ita… Bani da tabbas kuma bani da alkibla nima kaina tsoron kaina nake bansan abinda yake damuna ba umarni kawai zuciyata ke bani ni kuma ina biye da ita….. A k’ofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, kud’inshi na bashi ya wuce nima na shige ciki, kaina tsaye na tunkari gidan babu wani tsoro fargaba bare kuma jin kunyar kowa amma har yanzun ban cire nik’af ina ba….. Ko mai gadi baiyi yunk’urin dakatar dani ba domin dai yasan mata abokan hud’d’ar ubangidan nasa ne… Hanyar da Umar yabi dani hanyar nabi naci gaba da tafiya har na shiga cikin palon gida…. Saida na shiga cikin palon na cire nik’af ina, d’an kallon palon nayi sannan na kallo inda hotunan mak’iyi Dikko yake raina ya b’aci sosai tsinan ne duk shine silar rushewar gidanmu kowa ya bazama ya shiga duniya, duk da bai sissiye ba da muna zamanmu cikin farin ciki, idan dai kud’i yasa kayi mana haka nice zan mayar dakai talakan k’arfin da yaji, uhum da kinsan waye Dikko da baki ce haka ba ….. Sallama na kwarara daidai yanda nasan za’a iya jiyoni, daga ciki naji ance shigo mana ! Inda naji sautin maganar ya fito nabi na shiga, kwance mutumin yake saman gado ya wani baje sai kace anyi b’arin asara… Kallo d’aya nayi masa tare dayin murmushi na zauna a gefen gado, kuma nayi karatunshi tun shigowa ta bakin gwargwado kuma na fahimci wasu d’abi’u nashi, da gani zaiyi sauri fushi kuma yana da saurin sauka, yanayin shi ya nuna abun duniya bai rufe mishi ido ba, amma wannan da ganin idonshi mayen mata ne lallai wannan idan ya dafi mace aradu mai ansarta sai Allah…… !!! Alhaji barka da yini, cikin sakin fuska ya amsa min da cewa barka dai malama ya kike ? ‘Dan gyara zama na nayi tare da cewa lafiya qalau ya aiki ? Kallo na yayi tare da cewa ki ganni kwance kuma kice min ya aiki ? Murmushi nayi tare da cewa ai na kwance kuwa shi yasha aiki Alhaji inba ba’ayi tuk’in zaune ba ai anyi na kwance…. Kallo na yayi tare dayin dariya irin tasu ta gogaggin “yan bariki sannan yace wace ce ke ? Kama kaina nayi tare da tattaro natsuwa ta dan ni nawa ba kalar nasu bane, saida na tattaro class ina sannan na d’an rage yawan fara’a , suna na Maryam Aliyu Binna…….. Amma anfi sani na da Sultana. Talla na kawo maka da fatan zaka siya ? Na k’arasa maganar tare da kashe mishi ido d’aya…. Dariya Alhaji yayi tare da gyara zaman belt inshi sannan yace yarinya me kike siyarwa ne ? K’addara……… !!! Kasan kowa da irin tasa k’addarar haka kuma kowa da irin k’addarar da yake siyarwa, idan talauci ya ishi mai rai yakan siyar da duk wasu abubuwa nashi daya siya ya adana, manoma sukan b’oye hatsi yayin da sai yayi tsada suke siyarwa, dillalai kuwa sukan adana k’addara ta k’asa sai tayi kud’i su siyar, macen da kud’i suka kama idan tayi ajiyar d’an kunnen zinari zobe ko awarwaro wannan talaucin zaisa ya ziyarci kasuwa, yayin da duk macen da tasan ciwon kanta take k’ok’arin adana tata k’addarar da Allah ya bata kyauta sai taje gidan mijinta,Ni kuma talauci ya dameni ba gidan zama bare motar hawa, kuma ban ajiye hatsi ba ban aje gold ba, shi yasa na d’auko nawa mutunci zan siyar amma sai na lura babu wanda zai siya da daraja idan ba kai ba, dare d’aya tak zaka more amma farashin farko kuma ba tayi miliyan d’aya ne, Ka ganni dai a fuska gwanin burgewa, masana sirrin mata sunce duk macen data cika muni zaiyi wuya tayi wani armashi, sai kuma sukace kyakkyawar mace kuma wannan riba biyu ce harda gyara ma, karfa kaga kamar ina yaba kaina ne fuskar gida ba itace take nuna tsarin sa da haduwar sa ba, sai an bud’e an duba ake ganewa…. Duk mota sunanta mota amma wata motar bata kai mota ba, tou haka take ga mata duk mace sunan ta mace amma wata macen muna mata ce….. Na k’arasa maganar tare da kallon Alhaji nayi masa kyakkyawan murmushi mai tattare da jan hankali. Saida na kauda kaina sannan nace amma ina da sharadi d’aya , idan anyi ba’a sake maimaici wannan shine sharad’in kasuwata idan zaka zuba hannun jari bisimillah, na mik’a masa hannu na da niyar mu k’ulla alk’awari…. Gyara kwanciya Alhaji yayi da niyar magana amma na lura da yanayin fuskarshi kamar bai yadda dani ba, dan haka na tare maganarshi da cewa karka cuci kanka wannan harka duk taimakekeniya ce , ka bani gishiri in baka mand’a , kaga masanya ce za’ayi fa ni wannan ba matsalata bace kud’in ne kawai damuwa ta, ka yadda na rana d’aya tak 👌🏻…….. Kallo na Alhaji yayi tare da cewa tou ai ked’in ce kin tsananta miliyan d’aya fa….. Kin kuwa san girman miliyan Sultana ? Idan na baki ita ina zaki zuba ta ? Waye zai d’aukar miki ita ? Me zakiyi da ita kuma ? Ajiyar zuciya na sauke tare da cewa, wurin zubata da d’aukarta da abinda zanyi da ita duk ba huruminka bane ba, kayi kawai ka bani idan kuma baya yuwuwa in hak’ura inyi gaba kila na dace…….Tashi yayi zaune tare da tattaro duka hankalinshi gareni sannan yace karki k’i fad’amin, kika sani ko zan iya miki maganin damuwarki ne ? Kuma kike maganar miliyan d’ayan d’aya kika sani ko in baki abinda yafi miliyan d’in ? Ni kud’i ba matsalata bane amma ina san sirri dan duk wannan harkar da kikaga inayi gaskiya banayinta da d’anyar kwalwa saboda gudun b’acin rana….. Alhaji kenan idan na fahimta kallon yarinya kake min ko ? Tabbas a zahirance ni yarinya ce amma a bad’ini ni mai tunani ce, babu wanda ya koyamin yanda ake bariki ni na koya da kaina, ban yadda da zama k’ark’ashin kowa ba nima saboda gudun b’acin rana, “yanci na, mutunci da kowa yake tak’ama dashi ya siyar akan kud’i k’alilin k’arshen wulak’anci da tozarci mak’iyina da bana k’auna shine ya taka ruwan ciki na, a cikin gidansu ya keta min hijabin da nake ta boyewa shine yayi mata kaca kaca…. Shiru nayi saboda idan dai har naci gaba da magana zan iya kamo sunan Dikko in d’ura wa uwarshi zagi. Hak’uri Alhaji ya bani tare da jawoni jikinshi yace kiyi hak’uri ku matan ne baku da amana sai a had’a kai daku a cuci mutum, murmushi nayi tare da cewa ai ko zanyi cuta bana tsaya inda aka sanni ba, kana dai da kud’i kusa dakai dan bana amfani da banki danma karka wani ce zaka turamin….. Cikin raunanniyar murya yace karki damu Sultana d’akin nan cike yake da kud’i, zan sake magana ya had’e bakina da nashi wuri d’aya labari ya fara canja salo….. Murmushin mugunta nayi tare da bawa Alhaji duk abinda nasan zaisa ya samu natsuwa…. Ya dad’e yana gurje kud’inshi kuma ban waniji wata damuwa ba, har saida ya gaji dan kanshi ya kyaleni. Sauka yayi daga saman gado ya nufi toilet ni kuma ina nan kwance, yana shiga na zaro wayata dana soke a jikin gado wanda duk abinda mukayi da Alhaji saida na d’auka, dariya nayi bayan na gama kallo sannan na mayar da wayata cikin jaka…Kafin Alhaji ya fito har na gama saka kayana na maida nik’af ina na zauna bakin gado…. Ina jiran fitowarshi ! Bai wani dad’e ba ya fito da sauri ya nufi wurin wayarshi saboda tun dazu ake kiranshi banyi gigin dubawa ba saboda ko na duba bana gane suna…. Kayi hak’uri mai gida shine dai abinda yake ta maimaitawa, bansan abinda abokin wayar yace mishi ba naji yace Eh an basu ranka ya dad’e , tou insha Allah, Allah ya tsare ubangijj ya k’ara taimakawa. Sallama sukayi dashi Alhaji ya ajiye waya sannan ya kalloni tare da cewa ke yanzu ya zamuyi ne ? K’afa d’aya a saman d’aya na d’ora sannan na ajiye hannuwa na ta baya nace bani zakayi in wuce marece yanayi, tou baza kiyi wanka ba ? ‘Dan girgiza k’afata nayi sannan nace bana sauke najasa a wurin da bai kamata ba ka bani kawai na wuce….. Tou waike taya zaki d’auki miliyan d’aya ne ? ‘Daga nik’af ina nayi tare da cewa karfa ka raina min hankali ka bani in wuce kana b’atamin lokaci kaji…. Murmushi yayi tare da cewa ya zaki d’auki zafi da wuri haka ? Tou ya zakiji idan na hanaki kud’in nan, murmushi nayi tare da cewa kai kuma ya zakaji idan ka samu hotunan vidio abinda mukayi a yanar giza gizo ….. Na k’arasa maganar ina masa kallon rainin hankali. ‘Daure fuska yayi tare da cewa sai in kashe ki, murmushi nayi da gefen bakina tare da cewa tou da suka shiga duniya kuma ya zakayi da duk wanda ya gani ? Ta ina zaka bi ko gogesu a cikin wayar kowa ? Akwai “ya “ya akwai surukai ga kuma matanka abinda kake b’oyo tou gashi a cikin wayar “yarka ko d’anka tou ya zakayi dasu……… Zufa ta keto mishi sosai, dariya nayi tare da cewa tou goge ai haka ma bazata tab’a yuwuwa ba, kawai nima nayi maka barazana ne kamar yanda kake neman hanani kud’ina, kaga abinda bazai yuwu bane bani na wuce, Ya kama kanshi sosai dan haka yace zan baki dubu dari biyar yanzu anjima ki dawo ki amsa sauran, gaskiya idan na tafi bana dawowa ka bani kawai sai mu rabo lafiya, tou wai babu zan baki ? Nace itama babun idan tana kamuwa ka bani ansa zanyi ba cemin kayi d’akin ka cike yake da kud’i ba ? Mutum cikakke mai arzik’i kamar ka ai bai kamata ya rik’a d’aga murya ba akan miliyan d’aya kacal ba, miliyoyin da suka tafi babu dalili baka san iyakarsu ba bare wannan idan ka bada ita ai kasan ta inda tabi ta wuce… Dubu d’ari biyar ya bani yace muje in baki sauran suna cikin mota, cikin jakata na zuba dubu dari3 muka fita dubu dari biyu na hannu na, muna zuwa ya bud’e mota ya bani sauran kud’in, bud’e gaban mota nayi na shiga tare da cire kallabin kaina na d’auresu a ciki nace ka ajiyeni bakin titi…. Baimin magana ba ya tada mota muka tafi, saida muka tsaya inda zai saukeni nace da Allah rubutamin number wayarka, har yanzu baiyi magana ba ya ciro biro a gaban aljihunshi ya rubutamin a jikin takarda ya bani, Nima ban sake magana ba na bud’e mota na fita, napep na tare dan zuwa gida, a k’ofar gida ya saukeni na shige, da sallama na shiga gidan sannan na wuce d’akina ina shiga na ajiye kud’in na zuba ruwa na tafi dan tsarkake jikina banyi ko azahar ba kuma ga la’asar ta kusa.. Saida na gama sallolina sannan na dafa indomie naci, bayan na gama na zazzage buhun kayana na zuba kud’in a k’asa sannan na d’auki kayan na maida daga sama, fitowa nayi tsakar gida na nufi majalissar matan aure…. Barkan ku da hutawa mata masu duniya, Karima tace wai ke duk yau ina kika shige ne ? Ban bata amsa ba na canja tambayar da cewa yau kuma zawarawan anguwar nan dame suka zo mana ne ? Karima tace ai gasu nan sai ki zauna ayi dake, zama nayi saman takalmana sannan na kalli inda Nana take kwance a saman cinyar A ` i wai tana kakkab’e mata dandirof, Karima kuma sai cewa takeyi Allah dai ya tsinewa talauci albarka, kullum a rasa abinda za’ayi ta baka sai tuwo maganar d’aya dai tuwo tuwo babu wani ci gaba kullum zance kenan, shi yasa gani nan kullum sai bushewa nakeyi ina k’armashewa kamar mai cutar kanjamau. Niko da bani da zuciya nace aiko Karima ki godewa Allah, domin dai Allah yayi miki rufin asiri ke kin raina tuwo ko ? Na tambayeta, bata bani amsa ba naci gaba da cewa yo aike cin tuwo yanzu basai wanda Allah yaso yake ci ba ? Da safe kina dama d’an kokonki da rana idan Allah ya hore zakiyi d’an wanke ko teba wata rana ma har taliya kuke dafawa, da daddare kuyi tuwo kuci ku k’oshi keda “ya “yanki kuma duk daren duniya naga sai mijinki ya shigo miki da fura, tou ina laifi ? Aike tsakaninki da Allah saida kice Alhamdulillah bawai ki zauna kiyi ta tsinewa talauci ba ai ina ganin haka kamar rashin godiyar Allah ne….. Saudatu tace, { itama ba’a gidan take ba shigowa takeyi } ai rayuwa tana san canji kullum abinci d’aya an kama dindindigau kamar kukan mutuwar uwa, ai ya kama a samu sauyi mana Sultana. Nace haba Saude ai duk namijin da kikaga ba’aci mai dad’i a gidanshi ba tou baya dashi babu namijin da yake so a tsarewa iyalinshi, Saudatu tace ai wallahi k’arya ne mijin Karima yana da kud’in da ko naman rago saiya ciyar da ita dashi, dandai kawai had’in fad’a baida dad’i amma wallahi dasai na fad’a mata abinda yakeyi da kuma inda yake kai kud’in nashi , ita ya rainawa wayau ya barta nan tana ta sassak’ar tuwo sai kace matar ladar noma. Daga wannan maganar har Karima ta kawo wuya, ta fara zazzaga luk’a luk’an zagi tana cewa ai da ganin biri yayi kama da mutum tsakanina da Nuhu sai Allah ya isa ban yafe mishi ba, kuma zai dawo gidan ya sameni saina ci uwarshi…. Kallon Karima nayi tare da cewa idan dai kuna biye ma zawarawan anguwar nan wallahi duk sai sun kashe muku aure, baku san maganar d’auka ba baku san abinda kuke fad’a musu ba ku biye musu su kaiku su baroku, su basuyi aure ba kullum suna biye daku suna halakar daku, Karima tace ai wallahi Sultana na yadda da maganar Saude saboda rabon da muyi kwanciyar aure dani da Nuhu yau anfi k’arfin wata d’aya, dama idan ba neman mata yakeyi ba ai kema kinsan abunda bazai yuwu bane ba…. Tsoki nayi tare da cewa ai wallahi saina fad’a miki ko zatai miki zafi, ba Nuhu ba wallahi koni dakel nake iya zama kusa dake, mace da aka santa da gayu da kwalisa da k’amshi da tsafa da tsaftacewa tou ku matan gidan nan ba haka kuke ba, kullum safiya kunzo kun jibge a k’ark’ashin inuwa ba wanka ba wanke ido babu sallah bare salati, baki cuwai cuwai ba abinda kuka sani saidai inuwa ta k’are ku ja tabarma ku k’ara gaba, Kun fito tun kafin mazajen ku su fita daga d’akin ku kun rigasu fitowa, yara sun kwana zabga fitsarin kwance baku tsaya kun gyara kun wanke ba, yanda namiji yabar d’aki haka zai dawo ya taddashi, baku iya magana da mazajenku ba kuna ma mazanku magana muryarku ta kere tasu mace da aka sani da sanyi, kina ma miji magana tsawa tsawa kamar yaron gidanki, duk daren duniya idan Nuhu ya dawo sai yayi wanka ya tsaftace jikinshi a haka zai rungumeki ki b’ata mishi wanka ? Kalli kanki Karima ji k’afafuwanki waike matar aure ! A haka har kike tunanin namiji zai samu kwanciyar hankalin da zai baki natsuwa ? Aini wallahi ko toilet na shiga mara tsafta banda natsuwar da zanyi komai a cikinshi wuta wuta zan fito dan kar in d’aukowa kaina cuta, gashin hamatarki ma kad’ai wallahi abin zubar da yawu n……. Mik’ewa Karima tayi tare da kaimin duka dan uwarki ni kike cewa kazama ce ? Rik’e mata hannuwa nayi duka tare da cewa saurara kiji ni bance miki k’azama ba kawai dai ina fad’a miki matsalarki ne, amma kiyi hak’uri ni ba’a fad’a dani gaskiya ce baki so kuma daga yau na daina insha Allah, amma duk da haka zan baku shawara d’aya dake da Nana wala Allah tayi muku dad’i wala Allah tayi muku zafi Nana tace ki rik’e banzar shawararki kila ta miki amfani can gaba….. Murmushi nayi tare da cewa tou ba damuwa na gode amma kuma ku sani bazan daina zaman majalissar nan ba, yanzu ma sallah magrib zanyi na dawo… Babu wanda ya bani amsa dan haka naje na d’auk’i buta ta naje nayi alwallah, saida nayi sallah isha’e sannan na fito majalissar su…… 19/08/2019 *NICE DAI…* *JAMILA MUSA…* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 13 Sallama nayi musu amma babu wacce ta amsamin, na maimaita sallamar har sau ukku amma dukansu babu wacce ko kallona tayi bare nayi tunanin zasu amsa min, murmushi nayi tare da cewa aikin banza kare da gudun layya. Wuri na samu na zauna, ina zama gaba d’ayansu suka tashi suka bar wurin aka barni zaune ni d’aya kamar mayya, banji wani damuwa ba haka banji bak’in ciki ba domin dai nasan gaba d’ayansu nafi su ta ko ina da ko ina, tunda kuwa nafi su ai babu dalilin ni na biye musu muyi gaba, bawai dan ban iya ba na iya kuma idan na fara nawa bashi da kyau…. Ban tashi a wurin ba na haska wayata na fara kwafar lambar Alhaji daga saman takarda zuwa cikin wayata da nayo mishi vidio, nafi minti biyar ina rubutawa karantawa ne dai bana iyawa amma ina kwafar abu, idan kuwa zan kwafa da guda guda nake d’aukarshi, kuma zansa a bud’emin whatsApp amma ya zamar min na “yan gaisuwa saidai duk wanda zanyi magana dashi inyi masa voice note, na ajiye number shi a wayata, abinda na saka mishi shine lamba 1 Mik’ewa tsaye nayi tare da cewa bak’in ciki da fushi ba naki bane Sultana tunda kina da aikinyi, d’aga muryata nayi tare da cewa waye yake san k’amshi mu bashi turare ? Tou tabbas maik’o saidai a barwa balangu ansha gaban mai tsiri…… Kujerata na d’auko na zauna k’ofar d’akina tunda na lura suna neman su haramta min zaman tsakar gidan ne kuma aradu basu isa ba, watsa kunnuwa na nayi ina jiyo firarsu k’asa k’asa bana iya cewa naji abinda akace duka ba amma da yake Saude bata iya maganar sirri ba, bama itama ba duk matan gidan ga haka suke, ji nayi tana cewa ai wallahi ki had’ani dashi in nemi taimako…. Daga inda nake zaune nace hattara dai matar aure, idan dai an ciza a busa, ki kiyayi duniya da rayuwar mutanen cikinta, ita duniya da kika ganta juyi d’an magwaro takeyi yayin daya fad’i k’asa zai kwaso k’asa da tsakuwa, idan kika wanke zak’in zai fita idan kuma kika sha baki wanke ba zaki ci da k’asa duniya tafi karfin kowa, wanda yafiki iskanci yazo yayi ya koma ki kama kanki kuma kiyi k’ok’ari ki koma gaban Allah kina mai kamanta gaskiya, amma na horeki da ki kiyaye darajar aurenki tun kafin duniya ta juya miki baya…. Cikin hayagaga Nana tace ai ba tsoronki akeyi ba a gabanki ma za’ayi maganar dan kutumar ubanki idan kin isa ki hana wani abu in gani, tirr na fad’a tare da cewa kutumar ubana tafi k’arfin kaff zuri’arku wallahi, saboda ko da yake raba kutumar wa mata badai irinku masu tsamin daud’a ba… Kaina Nana tayo da gudun bala’i kafin ta iso na d’auki kujerata na rik’e nace wallahi kika kuskura kika iso nan saina raba miki kai gida biyu, tsoro ya hanata ta iso taja tayi tsaye, tsoki nayi tare da cewa k’aryar rashin kunya sakarkarin banza daku, insha Allah ko gani nayi zaku shiga wuta saina watsa muku fetir, ina fadin haka na shige d’akina na kyale jahilai, dan gaskiya na lura wallahi jahilci ne kawai yake cizar musu kwalwa, inma banda b’atar basira matar aure za’a kai wurin wani namiji ta nemi taimako….. *** *** *** Sati na d’aya kenan bana shiga safgar kowa a gidan da nake haya, ni dama fil’azal magana bai dameni ba, shigowa na ma gidan nan ne naga har na iya surutu idan dai har magana da sune zaisa su raina ni har kowa yake k’ok’orin magana kad’an ya dakeni tou na fita sabgarsu danni ina da wata irin zuciya da idan har na gama da abu tou fa tabbas na shafe labarinsa a babin rayuwata, niko nace hada Dikko Sultana ? Cikin kud’in da Alhaji ya bani na shiga kasuwa na kwankwaso tsadajjiyar sutura, na siyi kaya na kece raina, gyale takalmi jaka turaruka mayuka na shafawa irin ya wayayyun mata, agogo sark”a da “yan kunne “yan hannu zobuna saida na tabbatar nima na zama gogaggiyar mace ta sahun farko a fanni sutura. Sannan naje nakai dinki wurin telan da nasan shima yasan hannunshi, kuma da naje kai d’inkin na fad’a mishi cewa irin d’inki karuwai nake so yayi min, nace yamin d’inkin dako tuk’i namiji yakeyi idan na wuce saiya dakaya saiya manta da kan sitiyari yake ya tsaya ya kalleni, mukayi tsada dashi na biyashi kud’inshi tare da sharadin idan fa ya lalatamin kayana wallahi saiya biyani, yace kuma yaji ya yadda. Na gyara d’akina sosai nasa kayan kallo na sake katifa mai kyau na saka ledar tsakar d’aki na saka fanka amma ta k’asa, na kuma k’ara biyan kud’in haya daga lokacin da suka k’are daga lokacin zan siyi gida haka shine tsarina na gaba… Saina sayi gidan zama sannan zan sayi mota kuma duk zakuji ta inda kud’in zasu rik’a fitowa babu b’ata lokaci…. Hankalina kwance banda wata damuwa, banda rashin ci haka kuma babu rashin sha, cikin “yan kwanaki k’alilan na fara sauyawa, k’oshi babu abinda ya bari dan duk daren duniya sai naci nama abinda nake so ci nake ci kuma duk abinda naga dama shi nakeyi babu mai kwab’a kuma babu mai kyahra, jikina kuwa yasha mayuka gani bana jin wahalar wanka dan ko agwagwa bata kaini san ruwa ba, ya jama’a ku tayani hasko kyau ya had’u da gayu, ku tayani ganin gayu ya had’u da wanka, ku tuno wanka ya had’u da k’amshi…… Wuta Sultana lokacina ya fara…… Kalu bale gareku k”azaman mata….. Kwance nake saman katuwar katifata da tasha shinfid’a da tsaftataccen zani, { bedsheet } iskan fanka sai kad’ani yake ta ko ina, ga wani ni’imtaccen k’amshi dake tashi daga d’akin har jikina, yanzu tunani na bai wuce in addabi Bello ba abokin Babana….. Dan yanda ya haramta wa Babana wali a cikin garin shi, inda aka haifeshi ya girma a ciki yayi iyali, amma ya gudu ya bar “yan uwa da “ya “ya da matanshi tou shima katsina zata haramta yayi wali a cikinta, idan kuma yayi iskanci saiya d’aure kayanshi yabar birinin katsinar gaba d’aya…. Hannu na, na saka k’ark’ashin katifa na jawo wata “yar k’aramar kwalba dana anso hannu wani d’an daba, ya fad’amin sunan abun amma wallahi kafin inzo gida har na manta, abun fesawa gareshi kamar na turare, kud’i na bashi ya siyomin nace mishi abinda idan na fesawa mutum kawai zai kama bacci babu b’ata lokaci shine ya kawomin shi…. Tashi nayi na rufo d’akina dan ina so in gwada inga ko abun yanayi, saman katifa na kwanta sannan na fesa shi a fuskata….. Luuu wani bak’i na gani ya gittamin daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saida 11:30am tayi….. Salati nayi tare da godewa Allah dana farka na ganni a duniya, d’auko kwalbar nayi tare da sunbatar ta, tabbas kece abokiyar tafiyata, amfani biyu zakimin daga Bello sai Dikko daga nan aikinki ya k’are zan yadaki shikenan….. Wanka naje nayo tare da d’auro alwalla nazo nayi sallah asuba da ban samu nayi ba, ina gamawa na hau shiri domin yau ba abinda zai dawo dani gida sai nayi ido ido da Bello kuma saina tabbatar da k’udurina akanshi…..Mai da powder na shafa sai kwalli dana shafawa idona, ban shafa jan baki ba saboda bakina baya buk’atar shafe shafe sai kuma lura da nayi da irin manyan mata mawuyaci kuga sun daddab’awa fuskarsu irin abinda muka shafawa, irinsu jagira aishadow duk basa shafawa shi yasa idan suka shiga wuri suke fita daban, bana buk’atar bilicin koda na kasance ni b’aka ce shima ku lura da kyau bilicin na maciyata ne, d’iyan masu kud’i basa shafe shafe mayuka gaskiya…. Doguwar rigar shadda getzner na saka bak’a, kuma tayi matuk’ar martabani domin dai ta zauna min a jikina ciff na d’aura d’an kwalina coge, na kawo gyale na ida kafe wankan dashi komai dai dana san zai martabo min mutunci na saida na saka a jikina, sannan na yayyafa ruwan turare nayi gaba… Tun kafin in fito k’amshin turarena yakai tsakar gida, a lokacin dana fito ina rufe k’ofar d’akina kuma gaba d’aya hankalin duk wanda ke gidan saida ya dawo kaina, ina rufe d’aki na saka makulli na a jaka na wuce abuna banma kowa magana ba… Da kallo suka bini domin dai sun gane kura ba sa’ar kare bace ba….. Tunda na fito gida har nakai bakin titi na zama abin kallo ga jama’a , ban damu dasu ba domin dai duniyar yanzu gaba na bata ba baya ba….. Napep na tare na fad’a mishi inda zai kaini na shiga muka tafi, cikin “yan mintoci kad’an muka isa, na sauka na bashi hak’k’inshi, majalissar ciki take kamar zata fashe saboda yawan dandazon mazan dake cikinta, ina fitowa napep duk wanda ke wurin idonshi ya dawo kaina… Banji fargaba ba haka kuma ban daburce ba, banji bazan iya tafiya ba dan ana kallona duk wani bargaba da kunya ko tsoro duk basa tare dani a wannan lokaci, tafiya na farayi zuwa wurinsu na k’addara ma kawai ba maza bane mata ne…. Tsofaffin banza tun daga yanayin kallon da sukemin zaku gane duk sun fad’o rami, kallon tarko suka faramin kamar mage ta ritsa bera. Sallama nayi musu yayin dana isa wurin, kusan gaba d’ayansu saida suka amsa kamar ana biyawa dalibai karatu…. Nima kujera naja na zauna sannan na gaishe su, duka suka amsa cikin sakin fuska, inda Bello yake zaune na kalla tare da cewa Baba wurinka nazo , tou yace amma ban ganiki ba, sadda kaina k’asa nayi sannan na d’an murmusa cikin sigar bariki nace d’iyarka ce ta wurin Aliyu Binna…… Na k’arasa maganar tare da d’ago kaina na kalleshi da kyawawan idanuwa na da suka sha da ado da kwalli nakai karshen maganar tare da d’an sassauta kallo na, sannan na bud’e idanuwan dukansu, Yashe baki yayi yana dariya kamar yaga wawan zama, sannan yace ahaf tou tou Uwar masu gida ce ? Murmushi nayi tare da cewa Eh, kinyi aure ne ? Ya tambaye ni ? Da kaina na bashi amsa cewa A , a, tou kina ina ne haka ? Ba tare dajin kunyar kowa ba nace ina bariki ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa “yar gari kenan yarinya ta gane makoma….. Nima dariyar duniyanci nayi harsai da kyawawan hak’orana suka bayyana idan dai nayi irin wannan dariya ni kaina nasan tana k’ara min kyau sosai sannan na kalleshi nayi murmushi sai kuma na kama kaina, kallon maita ya bini dashi kamar ya cinyeni a bakin titi sannan yace ina kike zama haka ne ? Ina nan tsohuwar anguwarmu daka sani dai…. Tou taso mana ya fad’a tare da mik’ewa, a raina nace wato tunda na zama karuwa bari a bini a lalace ! Zakaci ubanka domin nima kaina tsoron kaina nakeyi, duk a zuciya ta nayi magana…. ‘Daukar kujerata nayi muka matsa gaba, zama nayi na d’ora k’afa d’aya saman d’aya sannan nace ya ake ciki Baba ? Am tou aike zan tambaya kinga tunda ga gida ai ba’a kai k’aruwa waje ba…. ‘Dan gajeren murmushi nayi sannan nace gaskiya kam, amma yanzu kana da mota kuwa ? Eh akwai mota hannuna mana, wace iri ce ? Na tambayeshi yana k’ok’arin fad’amin nace dakata ma barshi kawai kasan ko ka fad’a bazan rik’e ba zan manta ne , Duk’owa yayi kusa dani waini zai tambaya yanda muka k’are da Dikko kwanaki, dariya nayi sannan nace ai Dikko ba abinda yayi min kuna tafiya yasa aka dawo dani gida, tsoki Bello yayi tare da cewa kaji sakaran banza wannan tunjumemiyar mace ya bari baisha ruwa ba ? Murmushin mugunta nayi tare da d’aga girarena nace kila bayajin k’ishirwar ne, tou waike kawai sai kika fara bariki abunki ? Nace sosai ma, tou ya akayi kika zab’i wannan harkar bayan baki san yanda abubuwan suke ba ? Duk zan baka bayani idan kana da wurin saukeni mu tafi kaji komai…. Tou ina zuwa, ya fad’a tare da tafiya wurin abokansu, sallama yayi musu tare da cewa zai dawo da daddare duk zasuji bayani, wani ne daga can yace kayi min register idan ka gama ina layi nima…. D’iyar abokinku maimakon kuyi k’ok’arin d’orani hanya A , a, saidai kuyi k’ok’arin k’ara dilmiyar dani…. A mota ya d’aukeni muka tafi, ko a hanya sai wani kyarma yake yana k’ok’arin kai hannunsa cikin rigata, kallonshi nayi tare da cewa saurin me kakeyi haka ne wai ? Ban bari ya bani amsa ba naci gaba da cewa ko da kayi tunanin yau zaka sameni ? Yace a , a nace tou kasa ma ranka natsuwa har muje inda zamu baje kolin iskancin namu muci karenmu babu babbaka babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani… Kyah kyah kyah ya kyalkyale da dariya tare da cewa gaskiya ne Uwar masu gida, kunji ihu kura ta samu nama, wannan dariya itace yayi shi ya samu Sultanar banza zaije ya gurji banza a tunaninshi, baisan ni nafi shi iya iskanci ba domin dai ni naci uwarshi nasha ruwan kanwa maganin kwarnahin ciki…. Har muka iso ban sake magana ba, horn yayi mai gadi ya yaye mana get muka shige ciki, parking yayi sannan yace muje, kai jama’a kuji rashin kunya don Allah dan kwatawalci d’iyar abokinka, uhum cije lebona na k’asa nayi sannan nace masa rubutamin number wayarka don Allah a takarda, yo baki da waya ne ? Ya tambayeni cikin gatsali, murmushi nayi sannan nace aini ko a cikin kwarin k’arama ce har yanzu da sauranmu kafin mu gama nuna Baba…. Hahaha a haka ma baki nuna ba ? Nace yo dana nuna ka ganni a napep baki da dama yace tare da fara rubutamin number wayarshi, mik’omin yayi bayan ya gama, yana k’ok’arin fita nace ka sallameni kafin mu shiga mana….. Dubu biyar ya mik’omin , ansa nayi tare da jujjuya kud’in nace ashe gara da bamu shiga ba, yo Baba banda abunka wannan ai ko kud’in fira baka biya ba, zaro ido yayi tare da cewa dubu biyar ? Ke kin raina dubu biyar ? Murmushi nayi tare da cewa tou turaren dana shafa idan akace maka kayi tukwuici ai kasan nafi k’arfin ka bani 5k , koni ai nayi kyautar dubu biyar wallahi, ka bani kud’i masu yawa idan kana bani kaji malam…. Daga gaban motarshi ya jawo wani wuri kud’i na gani kamar in zabgaga ihu saboda yawansu , saida na gani sannan ya maida ya rufe kin gansu nan kud’in da zamuyi caca ne na had’a gobe na k’ara miki ki anshi 5k in mana… Babu gardama na ansa muka fita daga motar dukanmu muka shiga ciki, saida ya rurrufe ko ina mu kuma mukayi ma junanmu masauki saman gado.. K’ik’iy k’ik’iy ya cire riga ya cire wando, jakata na bud’e na d’auko kwalbata sannan nayo wurinshi cikin karairaya, yana k’ok’arin rungumata nayi ma shege feshin maganin sauro, babu b’ata lokaci ya tafi bacci rik’eshi nayi har yakai k’asa sannan na cire mishi gajeren wandonshi na dauki d’an iska hoto, nayi mishi kuma vidio ko ina saida na d’auka, bayan na gama na janye shi daga saman hanya, saida na lalube aljihunan shi kaf sannan na zauna gefen gado na shigar da numbershi cikin wayata, bayan na gama na ajiyeshi da lamba 2. Makulin motar na d’auka da jakata na bud’e d’akin na fita, cikin mota na koma saida na kwashe kud’in nan kaff sannan na rufe na maida makullin kusa dashi na ajiye, fitowa nayi na tunkari hanyar fita daga gidan, dubu biyar d’in daya bani itace naba mai gadin gidan kyauta, yana ta godiya na wuce abuna ban tsaya saurarenshi ba na fice daga gidan abuna………. 20/08/2019 *JAMILA MUSA…*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 14 Saida ma na fita daga gidan nakejin wani irin bak’in ciki ya tokaremin zuciyata, wallahi dana iya mota saina taho da motar Bello, zanje gida na jira zuwan shi domin dai nasan nabar baya da k’ura babu yanda za’ayi ya barni na ci kud’in nan , murmushi nayi sannan nayi magana a bayyane cewa Allah ya kawo ka lafiya Baban kwali Baban tusa….. Ban tsaya wasa ba haka kuma banyi gigin biyawa gidan kowa ba na yanki santa na fara neman gidan da nake kwana…. Tafiya mai zurfi nayi kafin na fito bakin titi, Allah kuma ya taimakeni ina fitowa na samu abin hawa ban wani b’ata lokaci ba, ko ciniki ban tsaya yi ba na afka nace muje. Inda zamuje ya tambayeni, ni kuma na fad’a masa yaja muka tafi, raina fes zuciyata dunk’ule da farin ciki na isa gida, ko mai napep 1k na bashi yayi ta zabgaga min godiya tare da jawo addu’o’in samun nasara a rayuwata… Godiya nayi masa sannan na shiga gida da sallama kamar yanda na saba bawai dan zasu amsa min ba, a , a, inayi ne dan fita hak’k’in musulinci, kai tsaye k’ofar d’akina na tsaya na ciro mukulli na bud’e na shige abuna…. Saida na fara adana kud’ina a ma’adana mai sirri sannan na fara neman abinda zanba baba uban ba’u, { ciki } saida na d’ora girkin abinda zanci sannan na fita nayo alwallah dan ganawa da mahalicci na… Bayan na fito daga bayi ne naji su Saude suna fira kuma ga dukkan alamu zance Dikko ne sukeyi, da wutsiyar ido na kalli wurin, wata bak’ar cikakkiyar buduwarce na gani tsaye, amma ban tab’a ganinta ba sai yau, kallo d’aya zakayi mata ka tabbatar tanaji da hutu domin ta huta d’in, duk inda ta fito yarinyar can d’iyar wani attajiri ne… Fasa alwallar nayi na tashi na koma d’aki na kashe d’an gass d’ina na d’auko asawaki dan inaso inji inda labarin nasu zai tsaya, dawowa nayi na zauna ban kalli inda kowa yake ba kuma banyi ma kowa magana ba na tusa buta a gaba naci gaba da gogo asuwaki a bakina…. A ` i ce ke cewa kai amma gaskiya Hafsat baki da hankali ai da ki nemi d’an mai kud’i da asiri gara ki tafi tsirara kawai ki huta, kina ganin ubanshi banza ne ? Wannan Dikkon da kike gani tun yana ciki an gama dafashi da asiri yanda Babanshi yasha wahala kafin ya samu namiji kina ganin daya sameshi da wahala zai barshi ne yai ta yawo figifigi a duniya ba tare da an bashi dafa’i ba ? Kai wallahi kimayi hak’uri , Cikin muryar sakataccin “ya “ya tace no ai da ina kiranshi wani lokaci yana d’aukar wayata amma yanzu ya daina d’auka kwata kwata, da sauri na d’aga kaina na kallesu sai kuma na basar kamar ina kallon wani wuri, wato ita tana ma da number Dikko, tunani na farayi yanda wayarta zata zo hannuna na, ba ansar wayarta zaimin wahala ba yanda zan gano sunan Dikko shine wahala a wurina…. Kawai gaba d’aya tunanina ma har ya tashi daga d’aukar number, kawai harma na hango gani nan na d’auko tsiraicin Dikko na balbad’a a social media, tabbas Dikko saina had’a shagalin partyn wulak’anta mishi rayuwa…. Tunani na ya dawo ne a lokacin da naji Saudatu na cewa aiko ki dage yarinya dan nan da shekara d’aya Dikko baya rik’uwa, tunda shi dama bai dogara da kud’in gidansu ba gaskiya Dikko yana da sa’ar rayuwa idan kika auri shi kin more rayuwa domin dai cikakken namiji ne… Banyi musu magana ba dai naci gaba da goge hak’ora na, wayau sukayi ma Hafsat suka amshi kud’i masu yawa a hannunta da sunan za’ayiwa Dikko asiri, ci gaba da tattaunawa sukayi amma hankalina baya wurin firarsu ya tafi wurin karatun halayyar Hafsat, tab’e bakina nayi a bayyane nace itama dai “yar mad’igon ce { Lesbian } Kallona tayi nima na watsa mata mayatattun idanuwana masu sa mutum ya rikice na k’ura mata su sosai domin ina so ta yabani idan har ta shigo hannu na nice zan koya mata barikin da zata kawo min Dikko k’asan k’afaafuwana nima in rama wulak’anci da yayi min dan nayi alk’awari nima sai Dikko ya lashi k’afata kamar yanda yasa na lashi tashi… Shegiya ta kuwa daskare ta kasa barin kallona, kyakkyawan murmushi nayi mata tare da cewa sannu ko ? Na k’arasa maganar tare da d’an wasa da idanuwana… Murmushi tamin tare da cewa ya kike ? Ban bata amsa ba naci gaba da alwallata… Ina gamawa ban sake bi ta kansu ba nayi d’aki inajin tana ta magana amma na basar da ita, nadai juya ta ganni maza ma sun gani sun rikice ina ga mata mayun mata kuma ? Ina shiga na kunna gas ina na kabbara sallah. Bansan yanda suka k’are ba, amma nasan tabbas saita dawo saboda taga ina da irin k’addarar da suke nema… Bayan na gama sallah na zuba abinda zan dafa a tukunya sannan na zuba ruwa na tafi wanka, lokacin da nayi wanka na dawo har ya dahu, dan haka kashe gas ina nayi sannan na shafa mai da powder, d’aurin gaba nayi sannan na zuba abinci na naci gaba daci…. Bayan na gama duk abinda nake na kunna kallo, sannan na saka kayan bacci na koma saman katifa na kame kamar d’iyar wani shege… Kai gaskiya inajin dad’in wannan rayuwa tawa, saida na kwanta sannan na bud’e data ta, lamba d’aya na gano bayan na ganoshi na tura mishi vidion dana d’auko , tare dayin voice note na tura mishi. Ina turawa na sauka online na kashe wayata gaba d’aya, na kashe kallo na rufe d’akina nayi kwanciyata……. Tashin hankali shine kalmar da Alhaji ya fad’a a lokacin da yaga vidion dana tura mishi, wata irin gagarumar zufa ta yayyafo mishi a lokacin da ya saurari voice note ina, tashi yayi tsaye cikin tsananin tashin hankali ya rasa gane a wace rayuwar yake rayuwar mutuwa ce ko ta duniya ? A gefe kuma wayarshi ce take ta kwarara ihu, lambar mai gida Dikko ce keta tsalle babu k’ak’k’autawa amma Alhaji yau kam bata Dikko yake ba, saida kiran ya tsinke sannan Alhaji ya sake kunna maganar Sultana yana sauraro, ga abinda take cewa…. _Ina mai farin cikin sanar dakai wannan mummunan labari, d’abi’a na ne yin albishir da farin ciki yayin fad’ar abu mai munin gaske, kuma nakanyi farin ciki yayin fad’ar abun farin ciki, wannan vidion dai dani dakai ne a ciki kuma kaga irin bad’alancin da muke aikatawa a ciki, nidai banajin komai idan wani ya gani domin ni iyayena tuni sun sallama ma duniya ni, saboda haka ni duniya itace uwata kuma itace ubana, idan na yad’a wannan vidio banajin komai tunda biye nake da mutanen cikinta ina basu, nayi tunanin maidashi faifayin filet na sidi dan in siyar na samu kud’i , sannan kuma in watsashi a yanar giza gizo dan inyi suna, kai kuma kana da dama d’aya tak data rage maka, idan har ka bani naira miliyan d’aya nayi maka alk’awari zan goge shi sai in hak’ura basai nayi suna a duniya ba…… Idan kuma baka dasu in turawa “ya “yanka ko suna da kud’in fansar ka ! Sultana, Sultana ce yarinyar mai dogon zamani, idan kuma kace zakayi gigin sako hukuma a ciki na riga dana turama k’awata nace da taji an kamani firr zakaji su sun watsu a duniya kamar saukar tsuntsaye. Ka huta lafiya habibinah muah_ 💋 Goge zufa Alhaji yayi tare da cewa Allah ka tsinewa yarinyar nan albarka, shegiya tsinanniya ubanta da uwarta basuyi addu’ar kwanciyar aure ba yayin da zasu kwanta Allah ya basu cikin d’ebabbar albarkar yarinyar nan, a daidai wannan lokacin kiran Dikko ya sake shigowa. Jiki a sanyaye Alhaji ya kalli wayar tare da cewa mai gida kayi hak’uri wannan abun kunya ina za’a dashi na watsu cikin duniya ina zina, abun bak’in ciki da d’iyar da nayi d’iya da ita, garin ciye ciye na har naje na ciwo ma kaina bala’e, kila sai ta k’arar da arzik’ina, kuma tace idan na fad’awa hukuma taba k’awarta vidion zata yad’ashi wannan shine ciwo ya riga ajali zuwa… Kuka Alhaji yayi tayi tare mitar ya shiga 3 ya bani ya lalace, wannan labarin abun kunyar waye ma zai fad’a mawa bare kuma yasa ran zai samu wata sahihiyar shawara, kai ya bani ya bani ya bani……..😰🙆🏻♂😭, a daren nan Alhaji baiyi bacci ba kuma baibi kiran Dikko ba, wayar Sultana kuma ya kirata yafi so adadin yawan dutsinan da ake jifar shedan dasu amma maganar dai d’aya ce cewa a kashe……. Da safe , tunda nayi sallar asuba na koma bacci, can cikin bacci naji ana dukan k’ofar d’akina, addu’ar tashi daga bacci d’auke a bakina bayan na gama nace waye ? Na tambaya cikin muryar bacci tare dakai idona saman agogon dake lik’e a saman bangon d’akina k’arfe 10:36am, cikin muryar murna Nana tace “yan sanda aka d’auko miki Sultana…. Murmushi nayi tare da jawo wayata na kunna sannan nace ma Nana da Allah kije kice waye ya d’aukomin “yan sanda ? Cikin farin ciki ta koma zaure sannan ta tambayi d’an sanda waye yake k’arata ? Fad’a mata yayi tayo cikin gida da har yanzu tanajin dad’in k’arata da akayi, a bakin k’ofar d’aki ta tsaya sannan tace wai abokin Babanki Bello, jinjina kaina nayi tare da cewa tou ina fitowa…. Data na bud’e na nemo lamba 2, hotunan dana d’auke shi jiya na tura mishi tare da yin voice note na antaya ma banza, ina gamawa na kashe wayata, saida nayi wanka naci gayuna na watsa turare na d’auku iyakar yanda hankali baya tunani duk wanda ya ganni saina burgeshi, fitowa nayi banma kowa magana ba na tunkari zaure, dan zuwa wurin hukuma a yanayin talauci yana jawo ma mutum raini…. A k’ofar gida na samu d’an sandan nan ya gama shak’e b’acin rai daga gani yana jira muje can yaci uwata, a yangance na fito cikin aji na kalleshi tare da cewa “yar labai barka da aiki…… ‘Dan sakin fuska yayi tare da cewa yawwa, gaishe shi nayi tare da ce masa nice Sultana, kallona yayi sama da k’asa sannan yace tou hajiya muna gayyatarki zuwa ofishinmu ai anyi miki bayanin mai k’ararki ko ? murmushi nayi tare da cewa babu damuwa muje amma Allah yasa ba’a cikin motar “yan sanda zaka d’aukeni ba, murmushi yayi tare da cewa ai hajiya napep zamu shiga, ajiyar zuciya nayi cikin sigar jan hankali sannan nace tou ai har naji natsuwa.Napep muka hau muka nufi c p s , kuma nice na biya kud’in 1k ne na bayar kuma daya anso canji nace ya rik’e yasha ruwa, tunda muka fita a napep gaba d’aya wurin saida hankalin kowa ya dawo kaina, na farko dai ga wanka ga gayu ga k’amshi uwa uba kyau Allah yayi min kyawun da mutum baya gajiya da kallona, ga gashina na tik’ashi nayi mishi wani irin parking irin na wayayyin mata, baka isa ka rainani ba ko waye kai domin sitirar dana saka ita kad’ai ta isa ka gane ni ba sa’ar wasan yaro bace ba….. Ofishin d c o muka nufa, a ciki na samu Bello zaune tare dashi da wasu abokan Babana, sallama nayi sannan na gaishesu dukansu cikin kyakkyawan yanayi, bayan mun gaisa nima na samu wuri na kame kamar yanda naga kowa yayi….. Kallona d c o yayi bayan ya gama karanta wata takarda dake gabanshi sannan yace Maryam miya had’aki da Bello ne ? Murmushi nayi tare da gyara zamana nace ranka ya dad’e ai Baba Bello abokin kasuwanci ne, halak’a ta mutunci ne a tsakani na dashi bayan wannan babu komai…. D C O yace tou jiya ina kika had’u da Bello ne ? Ranka ya dad’e majalissar su naje gaishe su, bayan mun gaisa kuma ya tambayeni nayi aure nace masa A , a, yace yanzu ina nake zama ? Nace masa ina zama a tsohuwar anguwarmu daya sani, ya tambayeni ko ina kasuwanci ne ? Nace masa Eh yace me nake siyarwa ranka ya dade nace masa karuwanci nakeyi, tsakanin mai saye da mai siyarwa ai babu fushi anan muka daidai suka d’aukeni muka tafi wani gida, nuna yawan duka abokan Babana nayi sannan naci gaba da cewa ranka ya dad’e dukansu nan babu wanda baiyi ba kuma duk saida suka k’ara zagayawa “yar labai, kuma gasu nan ka tambayesu idan nayi musu k’arya. Kuma cikon kud’in ma har yanzu basu bani ba.. Kowansu zaro ido yayi tare da dafa k’irji cikin yanayin mamaki yace ke mune mukayi iskanci dake ? ‘Daure fuskata nayi kamar gaske nace aini banajin kunya tunda dai banji tsoron Allah ba nayi zina wallahi banajin kunya gaban kowa in fad’a nayi, kunyi mana ko k’arya zan muku ne ? Lokacin da bakuyi ba nace kunyi ? Gaba d’aya wurin hayaniya ta tashi har bakajin bakin wani, d c o ya dakatar dasu tare da cewa suyi mishi shiru, bayan kowa yayi shiru ya kalleni sannan yace ke Sultana Bello yana tuhumarki kud’in shi da kika d’auka. Cikin natsuwa nace wasu iri kud’i kuma ranka ya dad’e ? Bayani d c o yaimin kamar yanda na sani, jinjina kai nayi tare da cewa idan sun gama k’arata nima zanyi k’ararsu saboda b’atamin suna da sukayi, ranka ya dad’e a gaban idon waye na d’auka kud’in ne ? Nifa bana sata amma ina neman maza gaskiya, duk abinda nakeyi bana jin kunyar asan inayi domin dai duk sana’a sunanta sana’a, idan ma na d’auka aka tambayeni idan nasan na sata kawai zan dawo musu da kayansu in basu hak’uri tunda karuwanci da nakeyi ai ban b’oye ba na fad’a tunda ba abun kunya bane…. Tambayar Bello D C O yayi ko yana da wata sheda ne ? Baida ita tunda an tambayi mai gadi yace shidai bai ganni cikin mota ba, duk iyakar binciken da akayi dan asamu wata sheda babu ita, dan haka aka rubuta takarda cewa an janye k’ara, bayan an gama rubutu aka bani na saka hannu da larabci nayi sigining ina, an mik’e za’a tafi nace ma d c o naga fa sunamin wani kallon hadarin kaji sufa fita ido na, d c o yace ai duk an rubuta, nace to ranka ya dad’e cikon kud’ina kuma sai yaushe zasu bani ? Hak’uri d c o ya bani tare da nunamin tunda anyi masa sata inyi hak’uri inma barshi da ramuwar biyan kud’in mutane, babu kunya ba komai nace kenan ni yanzu ranka ya dad’e sunci banza ? Duk wanda ke cikin office in saida ya kalloni, nace ranka ya dad’e kafa duba lamarin nan gaskiya ni ba’amin adalci ba, shiru wurin yayi wutar kowa ta d’auke, murmushi nayi tunda basu da amsa nace nawa ake yankar sammaci ? Sammaci ma ake cewa abin ko miye ? A kotu ake yankar sammaci d c o ya bani amsa tare da fad’amin abinda ake kiran nasu da turanci, oho dai da yake kan baya ganewa kasa maimaitawa nayi saidai kawai nace nawa ne ? Kud’in aka fad’amin na bud’e jakata na bada sannan nacewa d c o ga wanda nake k’ara nan Bello ina tuhumarshi akan b’atar mahaifina daya tafi babu wanda yasan ina yaje………. 21/08/2019 *JAMILA MUSA…*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 15 *_Had’inkai group ina tare daku aminan albarka, Allah yabar so da kauna ubangiji ya k’ara yadda da aminci, HALIMATU SADIYYA {{ Leema }} HABIBA IDRIS {{ Hubbie }} HAUWA’U USMAN {{ Smasher }} MAIMUNA O . G {{ Aunty Munari…. }} muna tare_* *_Mrs Abdul-aziz ina godiya sosai da dogon sharhi kuma ngode sosai page 14 na baki shi kyauta…._* Lahaula walakuwata illah billah, kiji tsoron Allah ke uwar masu gida a ina na b’atar da mahaifinki ? Sharri zaki min ? Kiji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani daidai da kwayar zarra ubangiji bazai barshi ba, ki daina ganin kin samu dama ta tak’in lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba, karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana….. Gaba d’aya jikina yayi sanyi tsoron Allah ya kamani nasan k’azafi da sharri ba abu ne mai kyau ba, kuma addini na bai koyar dani haka ba, amma d’an kamewa na sakeyi sannan nace ni rayuwar dad’i baza ta tab’a zama takaitacciya a wurina ba, jin dad’i na d’aura insha Allah daga nan har zuwa ranar da numfashi na zai k’are, ina Babana yake wai ina ka kaishi ne…………? Cikin nadama Bello yace na rantse da ubangiji daya bani aron lumfashi ya bani aron lafiya nake ganinki nake kuma saurarenki ya bani hankali da tunani idan nasan inda mahaifinki yake Allah ya tsinemin albarka. Wallahi Uwar masu gida bansan inda ya tafi ba na rantse miki da girman Allah. Tausayi ya bani yana rantsuwar yana wani kwantar dakai kamar an ritse macen da tayi cikin shege ta haihu kuma ta kashe d’an…. Kallon D C O nayi tare da cewa “yar labai shikenan tunda yayi rantsuwa baiyi ba kawai na janye, zan iya tafiya ? Na tambayi D C O, cewa yayi na zauna zamuyi magana, zama nayi su kuma su Bello aka sallamesu suka tafi ni kuma naci kud’in banza Ehe…. Ta wutsiyar idona na kalli d c o bayan fitarsu Bello domin ina son na gano tashi manufar a kaina, murmushi nayi bayan na gama fahimtar shi, a bayyane nace lamba 3 tazo kenan, ajiyar zuciya ya sauke tare da tattaro duka hankalin shi wurina yace ranki ya dad’e ya hak’uri da jama’ a ? Kallonshi nayi ba tare da nayi magana ba domin wallahi tsarin bakinshi kwata kwata bai burgeni ba. Amma ba komai zan hak’ura nayi maleji dashi haka nan saboda idan na taro watan aug zai gina min gada nabi na wuce ba tare dana sha k’ashin ruwa ba…. Wayan cewa nayi tare da gyara zama na nace Allah dai yasa aiki zaka d’aukeni mai girma d c o, murmushi yayi tare da komawa ya kwanta saman kujerarshi irin masu juyawa d’in nan, sannan yace wai gida zan saukeki idan ba matsala, d’an yamutsa baki nayi tare da cewa na gode amma ni ba gida zanje ba… Ina zakije haka da rana ? ‘Daure fuska nayi dan ya fara cika min ciki nace wurin aiki zanje, wane irin aiki ? Tsoki nayi tare da cewa kai komai sai anyi maka b’aro b’aro kake ganewa ko ? Tou abokin lalata zanje nema….. Murmushi yayi tare da cewa ke bakya gajiya ? Cikin wuta wuta nace ka tab’a ganin inda mutum yake rayuwa babu abinci ? Yace a , a, nace tou ni da kud’i da karuwanci sune abokan rayuwata, domin sai nayi nake samu sannan naci nasha na kuma d’aura har in fito na burge abokan harka , idan kuma kaima d’an hannu ne karka wani cuci kanka kawai kayi magana idan kajira sai an maka tayaki tou fa lallai zaka kwana da yunwa, amma kayi hak’uri da tambayar da zan maka tsakanin ka da Allah nawa ne albashin ka…… ?Kallona yayi tare da cewa hajiya maryam kenan , miya shafi albashi da harkar bariki ne ? Bai shafa ba amma ni ina duba nasabar namiji da cancantar shi kafin wata sahihiyar mu’amula ta shiga tsakani na dashi, dan duk wanda ya jawo maganar aure a rayuwarshi tabbas ya tara abun hidima, bata yuwuwa na biye maka ka k’ok’ar dani ba tare da ka sake bani kud’in da zan sabon fenti ba, dan kai kanka da ban d’aukar maka ido ba duk yanda nake barikin baza ka taya ba, Kallon agogon dake d’aure a tsintsinyar hannu na nayi tare da cewa zama wuri d’aya tsautsayi inji kifi, malam d c o zan wuce ka rubutamin number ka a jikin takarda idan ayyuka sukamin sauk’i akwai dawowa…… Babu musu kuma ba tunanin komai ya d’auki biro da takarda ya gwagwad’amin number wayarshi, ansa nayi tare da mik’ewa tsaye sannan nace sai ka jini, baki bari mu tafi in ajiye ki ? Ya tambayeni, juyawa nayi na fara tafiya tare da cewa ban hawa mota sai napep a daidai lokacin dana fice daga ofishin…. Ina fitowa wuri na samu na tsaya, wayata na fiddo nayi saving in no d c o da lamba 3 , sannan na kira wayar Alhaji, babu b’ata lokaci ya d’auka tare da cewa ranki ya dad’e tun jiya inata kiran ki wayarki a kashe ko yau da safe ma na kira a rufe…. Ban bashi amsa ba nace kawomin kud’in yanzu nan ina nan c p s ina jiranka kuma karka b’atamin lokaci, ina fad’a na kashe wayata…… Lambar Bello na kira amma bai d’auka ba, daga kira d’aya nima ban sake kira ba, domin dai nasan idan yaga abunda na tura mishi shi da kanshi zai nemeni, k’ok’arin maida wayata nake cikin jikka naji ana cewa shegiya k’awata kece kika koma wata hajiya haka ? Da sauri na d’ago kaina domin jin muryar Amisty da nayi… Cikin farin ciki muka rungume juna, bayan gaisuwa sai kuma muka shiga firar duniya, yayin da nake tambayarta wane ci baya ta samu na bariki naga har yanzu bata fara hawa mota ba, ajiyar zuciya Amisty ta sauke tare da cewa kinsan mazan babu kud’i hannunsu kullum tsuwwa da kukan babu…… ‘Daure fuska nayi tare da cewa waye ya fad’a miki ana hawan jirgin sama bashi ne ? Ai filin jirgi ma baka shigarshi dole sai kana da tikitin tafiya, haka nan kike basu suna hayewa basu baki kud’in mai, tou ina uwar d’akin taki ne ko bata nan bata fad’a miki illar maza ba ? Haba Amisty idan baki ridowa da yawa wallahi bariki kasheki zatayi, niko kin ganni nan ni zanyi gwanjo bariki kafin ta wurgar dani gefen titi, kinsan bariki bata da tabbas d’auka da ajiyewa gareta, ni zan kashe bariki bazan yadda ta kashe ni ba, zanyi amfani da talata ta kafin laraba ta, ta riskeni, wannan uwar d’aki taki k’atuwar jahila ce batayi karatun komai ba haka nan ta tara yawan dalibai, har yanzu kuna da dama ki nemi canji makaranta ki dawo makaranta ta zan baki ilimi akan namiji, kud’i kike so ko suna ……? Horn Alhaji yayi da mota wanda tun d’azu yakeyi amma magana ta hana na saurareshi, juyawa nayi tare da nuna mishi da hannu ina zuwa, ni kuma naci gaba da magana da Amisty, wata matace ta fito daga ciki tayo wurinmu kuma ga dukkan alama tare suke da Amisty, gaisawa muka yi yayin da Amisty ta fara tambayarta ya aka k’are, basu bani labari ba suna ta maganar ne cikin munafinci, ni na fahimta suna magana ne kamar tayi ciki.. Datsar maganar nayi da cewa keko ya akayi kikayi cikin shege ? Gaki a fuska kamar wayayya taya akayi haka ta faru ? Ita kuma a tunaninta Amisty ta fad’amin dan haka tace kin gane ni bawai cikin bane matsala a, a mijina yau watanshi bakwai baya nan kuma ga ciki wata hud’u, kuma nayi a zubar da cikin shi wanda yayi cikin yace wallahi bazai yadda ba saboda bai tab’a haihu ba, idan wannan abu ya fito ai kinsan akwai matsala….. Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un na fad’a tare da cewa ke matar aure kike zina ? Hasbinallahu wa ni’imal wakim, amma kinyi k’atuwar asara, kallon Amisty nayi tare da cewa zance zaune ba na tsaye bane idan kuna neman taimako ku sameni gida, ina nan tsohuwar anguwarmu idan kika shigo ki tambayi gidan da nake haya za’a kawoki, ina fad’in haka nayi wurin motar alhaji ina zuwa na kama na bud’e na shige nace muje…Har muka isa gida banyi ma Alhaji magana ba domin ni yau naga macen da tafini kafirci kina k’ark’ashin bautar aure amma kina aikata sab’o, wannan wai wane irin zamani ne muke ciki lallai ya kamata nasan ita kuma wane rud’un duniyar ne yaja mata neman mazan waje ga nata mijin da yake hak’k’inta amma ta tsallake shi ta tafi wurin na wasu , gaba d’aya jikina yayi sanyi kuma na dawo daga rakiyar duniya…. Ansar jakar da Alhaji ya zubomin kud’i nayi tare da direwa daga motar, zaiyi min magana nace mishi muyi waya kawai nayi gaba abu na, lokacin dana shiga gida bana ko ganin gabana saboda bak’in ciki da kishin aure, d’akina na bud’e na shiga, saida na adana kud’ina sannan naje nayo alwalla nayi sallah azahar, yinin ranar haka na yini sukuku kamar wata mara lafiya, koda nayi sallah isha’i kwanciyata nayi , duk yau banda ruwan shayi babu abinda ke cikin cikina, haka na kwanta da tunani iri iri, ko bacci nayi na farka abun yakan fad’omin a rai har gari ya waye da tunanin matar nan a zuciyata.. Da safe bayan nayi kalaci na gyara d’akina naje nayi wanka na shirya cikin doguwar riga ta atamfa da tasha d’inki buba, hula mai raga { net } na saka kaina na fice tsakar gidan…. Kujera na sa a k’ofar d’akina na zauna tunda fitowa wajen ya zamar min dole, kallon inda Karima take nayi sannan na maida kallo na wurin Saude dake zaune saman turmi, babu ko breziya jikinta kuma babu kaya sai siket ondie da taja saman kirjinta, amma komai na halittar ta babu abinda ya b’oye duk a bayyane yake….. ‘Dauke idona nayi gefe na kallo inda Nana take kwance A ` i tana durk’ushe ta duk’a samanta sosai suna k’ushin k’ushin, jinjina kaina nayi sannan na sake kai idona wurin Saude nace ke Saude wai da Allah in tambaye ki ? Murmushi tayi tare da cewa tambayarni kanki tsaye, b’ata rai nayi sosai sannan nace nan gidan ubanki ne wai da zaki zo ki rik’a zama mana tsirara dan baki da kunya ?Gaba d’ayansu dariya sukayi ,sannan Saude tace tou ke mai tambayar gidan ubanki ne ? Ni nan ba gidan ubana bane amma ya zama na ubana tunda na biya kud’in haya, d’aki d’aya na kama amma ina da hurumin da zan sauke ubana a ciki, ke ko fa ? Nana ta anshi maganar da cewa yanda kike tak’amar kin kama haya muma kamawa mukayi kuma muma muna da hurumin da zamu kawo mutanen da muke so su zauna tare damu, kedai kawai kice kina so ayi dake. ‘Dan gajeran murmushi nayi tare da cewa duk wanda yaci naman arne tabbas zai iya cin mushen alade , banda abinki miya had’a makaho da ganin wawan zama ? Ni bana iya cin naman jaki amma idan na samu doki zanci duk da an yanka shi nasan wata rana zanyi hazaka, ko banyi gudu ba tabbas nasan zanyi tafiya, magana ce na fad’a miki a jimlace idan kina da ilimi sai ki warwareta banzanye da ku masu wahalallen bariki…..Gaba d’aya wutar kowa d’aukewa tayi sukayi shiru babu wanda tace komai, murmushi nayi tare da cewa ba’a bariki dole saida ado kuje ku ibi ruwa kuyi wanka kusa toka ku wanke baki ko ya rage k’annin koko, daga haka ban sake ma kowa magana ba kuma suma babu wanda ya sake cewa komai, Bayan Alhaji ya bani kud’i ya dad’e k’ofar gidanmu ya kasa tafiya, hankalinshi a tashe saboda yaso yayi magana dani na goge vidion nan kuma yaji ina na dosa ? Amma samsam ban saurare shi ba, kuma yasan lallai saina sake tambayarshi wasu kud’in tunda akwai vidio a hannuna ban goge ba, Rasa yanda zaiyi yayi zuciyarsa ta yanke mishi kawai ya fad’a wa Dikko komai yasan babu mai iya magani na saishi amma fa a nashi haukar , d’aga waya yayi ya kira Dikko kuma har zuwa wannan lokacin yana k’ofar gidanmu bai tafi ba. Bayan Dikko ya d’auki waya Alhaji ya gaishe shi cikin girmamawa kamar yanda ya saba, Dikko ya amsa shima cikin mutuntawa, dan a haife Alhaji ya haifi Dikko amma igiyar naira tasa yana k’ark’ashin Dikko kuma k’asan k’asa ma, dan ubangidan Alhaji na ainahi shima yaron Dikko ne na biyu, tou abinda yasa Alhaji yake kiran Dikko kai tsaye saboda yanajin dad’in yadda yake kularmishi da dokunan shi, shi yasa shi Dikko da kanshi ma ya anshi number Alhaji ko wata matsala ta taso ga dokunan shi, dan dama ubangidan nashi na farko kafin yasan Dikko wurin kula da dokuna ajiye shi Alhajin….Alhaji yace mai gida kayi hak’uri don girman Allah wallahi jiya daka kirani ina cikin yanayin da bazan iya magana ba, cikin jimami Dikko yace meya faru haka ? Wato ranka ya dad’e ina cikin tashin hankalin dana zab’i mutuwa ma da rayuwa, salati Dikko yayi tare dayin murmushi domin shi yaji mugunta, sannan yace Alhaji duk dad’in duniyar wato tai maka d’aci ko ? Alhaji yace Eh wallahi ranka ya dad’e, Dikko yace tou Allah ya kyauta… Da sauri Alhaji ya fara bayani wa Dikko dan yasan daga Allah ya kyauta kawai zai kashe wayarshi ne yasan baya doguwar waya, ranka ya dad’e wato wallahi wata yarinya ce muka d’an keb’e da ita, tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya dad’e tana d’auka cikin waya ban sani ba, tou ta rik’e vidion sai wahalar dani takeyi tana ansar kud’ad’ena, yauma na bata kud’i kuma a police station nakai mata kud’in inaji wani ne ya d’aure mata gindi take iskanci a garin nan…. Murmushin mugunta Dikko yayi tare dayin kamar bai gane ba, yace wane irin vidio ne ? Gyara zama Alhaji yayi tare da goge zufa yace wato ranka ya dad’e harka daice irin wadda muka saba, Dikko yace wadda ka saba dai , wato ka samo daidai dakai ko ? Tou turomin vidion in gani ya fad’i maganar cikin sigar zaulaya, Alhaji yace ranka ya dad’e vidion fa irin na kafirawan nan ne masu d’aukar tsiraicinsu suna yayad’awa a duniya……. Dikko yace tou banda abunka kace taje ta yad’a ba hada ita a vidion ba ? Alhaji yace ranka ya dad’e ina za’ayi wannan abun kunya tsiraicina a yanar giza gizo cewa tayi fa har “ya “yana zata tura su gani, Dikko ya gaggab’e da dariyar mugunta tare da kashe wayarshi, irin wannan abun Dikko kadai yake ma dariya a duniya, duk abin burgewa ko na nishad’i Dikko baya mishi dariya kuma baya murmushi idan kaga murmushin shi ko dariya yaji ko yaga k’eta, amma kai kana iya ganin abinda zai baka tausayi kayi kuka wallahi Dikko sai yayi mishi dariya saboda tsabagen shi cikakken mugune…. Cikin sanyin jiki Alhaji yaja motarshi ya tafi, Dikko kuwa saida yasha dariyarshi ya gaji sannan ya sake kiran Alhaji, bayan ya d’auka yace tou waikai kawai sai tayi maka vidio ? Alhaji yace Eh ranka ya dad’e Dikko ya sake shek’ewa da dariya sannan yace kai amma wallahi yarinyar nan tantiriya ce ta fad’a a duniya, Dikko yace tou yanzu me kake so nayi maka ne ? Alhaji yace ranka ya dad’e so nake kayi min maganinta, dariya Dikko yayi sannan yace nima so kake ta d’aukeni ? Cikin biyayya Alhaji yace haba ranka ya dad’e kada Allah ya had’aka shegiyar yarinyar nan….. Dikko yace aini ko ta had’u dani bata da yadda zatayi dani, nidai bana neman mata kuma bana sabgarsu bana shiga huruminsu gudun raini, kayi hak’uri insha Allah zanzo katsina jibi idan Allah ya kaimu zata goge vidion dan wahala, ranka ya dad’e ai tace ta turawa k’awarta ne, Dikko yace k’arya take kadai jira zuwana ….. Godiya Alhaji yayi sannan sukayi sallama da Dikko, Murmushi nayi a daidai wannan lokacin sannan nace duk mai niyar yin magani na nice zanyi maganin d’an banza, zomon bana shike maganin karen bana, maganin d’an iska kuma karen maguzawa, dani dakai dashi mu zuba duk wanda ya fasa yaci k’aniyarshi……. Sallamar Hafsa ce da wasu zugar tantiran mata, a ciki kuwa harda Amisty, kila sunzo ne suci min uwa tunda nace uwar d’akinsu k’atuwar jahila ce, oho koma dai miye su shigo ina jiran isowarsu wurina inji su kuma da wace suka zo…………….??? 22/08/2019 Taku a kullum mai san farin cikinku wato . *MEELAT MUSA*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 16 *_Bandai ji komai ba , 71 , 29 babu damuwa zamu rama muma…_* _____“`^^=°°— Basarwa nayi tare da d’auke fuska ta daga dubansu, mutum dai bai isa yazo har gidana ya dakeni ba, kallon banza ko maganar banza mutum yamin wadda batamin ba wallahi ina da Lamba3 d c o zaici k’aniyar mata…. A daidai lokacin da suka iso gabana maganar zuci ya k’are, Amisty ce tace wurinki fa muka zo kina yi kamar baki ganmu ba, saida na gama kallesu tsaf sannan nace sannunku da zuwa tare da mik’ewa zan shiga d’aki dan d’auko musu tabarma… Gaba d’ayansu rufa min baya sukayi suma suna k’ok’arin shigamin d’aki, ja nayi na tsaya tare da tambayarsu ina zasu je ? Amisty tace ciki zamu shiga ? Murmushi nayi tare da cewa kuyi hak’uri ku jirani ni bana kai mata cikin d’akina… Hafsa zatayi magana Amisty ta dakatar da ita, kallonsu nayi tare da cewa barta ta fad’i cikinta, Amisty tace barta kawai d’auko mana kedai, munafikin murmushi nayi tare da juyawa na shige cikin ɗaki, domin ita Amisty tasan wace ce ni, tabarma na d’auko nazo na shimfiɗawa banza nace su zauna… Dukansu zama sukayi lokaci ɗaya, su A ` i da Saude Nana da Karima duk suka taso suka dawo ƙofar ɗakina, nima zama nayi tare da cewa meke tafe daku ne ? Na ƙarasa maganar tare da kauda kaina gefe ɗaya….Amisty tace Sultana ke kikace mu sameki gida ! Kallonta nayi tare da cewa sai akayi ya ya ? Amisty tace ai shine muka zo ! Kallon tantiran mata nayi sannan na maida hankalina wurin Amisty nace da Allah daga yau idan zaki zo wurina kidai min kwashe kwashe , da sauri Amisty ta kalleni sannan tace haba Sultana mi yasa haka kuma ? Kai tsaye nace kinsan bana san munafirci kuma ban tare da munafikai, waccan bak’ar yarinyar da kika gani na nuna Hafsa budurwar Dikko sannan naci gaba da cewa gaskiya aminci take da mak’iya na saidai ta zab’a ni take so ko su A ` i , murmushi Hafsa tayi tare da kallona sosai ni kuma na d’an gyara zama yanda zan d’aukar mata hankali sosai, saboda ina so na rabata tarayya dasu A ` i idan ina tare da Hafsa suma suna tare da ita riƙa zugamin ita zasuyi har su hanani na cimma buruni tunda na lura ita Hafsa doluwa ce kuɗinne kawai ba wayau sai tsabar neman matan bala’e. Kwazzaba tasa har bata iya tantance kifi bata gane kwad’o, Cikin ruɗewa Hafsa ta fara magana irin ta “ya “yan masu kuɗi, kin gane Sultana nifa ba abokaina bane kawai gaisawa mukeyi sai kuma wata huɗɗa tamu data haɗamu amma ba komai tsakaninmu gaskiya,Ɗaure rai nayi tare da cewa nifa ba abinda ya haɗaku nake so na sani ba cewa nayi kawai ki faɗa ni zakiyi abokiya dani kibar su A ` i ko kuwa su A ` i kika zaɓa, Hafsa tace haba aike tawa ce kuma ina tare dake, murmushi nayi tare da cewa magana ta ƙare mata tacewa mijinta shege… A ` i zatayi magana nace dakata malama ta bakin gulbi, ki taka sannu da lafiya kafin insa a ɓatarmin dake cikin garin nan, nuna yawan su Amisty nayi tare da cewa nan da kika gansu duk dalibai na ne, zan fara basu karatu daga jibi idan Allah ya kaimu, na kafa ƙungiya ta mai take *kwarata* duk wacce kika gani anan mabuƙaciya ce, zan haɗa ne zanba mace namiji idan an sallami mace zata fiddani, zan haɗa mata da mata amma a tafiyata ban tafiya da taron banza, sabbin ɗalibai ku na ɗaukeku kyauta basai kunyi register ba, amma daga ba yanzu ba duk wacce zata shigo cikinmu saita ajiye dubu talatin kuɗin register haƙƙina neman maza da mata masu abun hannunsu…. Miƙa hannuna nayi tare da cewa duk wanda yake tare dani ya ɗora hannunsa a saman nawa, kowa ɗora hannunshi yayi harsu Nana matan aure ba’a barsu a baya ba, ku ɗauki alƙawari babu cin amana , gaba ɗaya suka amsa munyi alƙawari bazamu ci amana ba, nace kuyi alƙawari zaku zama ɗalibai masu biyayya, munyi alƙawari zamu zama ɗalibai masu biyya nace idan kun samu ina nan ko bana nan zaku ajiyemin nawa kason, shima suka maimaita, sannan nayi addu’a tare da neman Allah yasa albarka a cikin wannan ƙungiya tamu mai albarka wanda nayi ma laƙabi da *KWARATA* saboda dukanmu lalatacci ne , Bayan an gama nace tou kowa ya tashi ya tafi nima zan fita inda fuskar jama’a take na samu gida na siya idan kuɗina yakai, idan basu kai ba kuma zamu kama shago, wannan shago zai zama nan ne kowa zataci gayu da safe taje ta zauna, yayin da zamu kafa ƙaton allonmu ya kalli al’umma, za’a rubuta a gaban shagon ko gidan tambarin *KWARATA* idan ma baka iya ba kazo za’a koya maka. Zamu rubuta a jikin takarda mukai kuma a buga mana su da yawa, ni zanbi manya ofisoshi da kasuwa da kuma kamfaninika da inda “yan siyasa ke zama saina zabo mana manyan alhazawa sai mu raba musu, duk wanda ya gani ya karanta dama ga number wayata nan a jiki, ku kuma kuna shago kunsha wanka kunayi kuna ƙara powder da jagira ina binku ina muku wanka da turare, da mutum yace zaizo zance ya iso akawai kaya a ƙasa, yana shigowa ya ganku wayyo shikenan labari zai canja salo, ni kuma ina da wata dabara ɗaya amma bazan faɗa muku ba saboda karuwa bata da amana, Nana tace tou mu da muke da aure fa ? Kallon ta nayi ƙasa da sama sannan nace duk iskanci da kukeyi keda A ` i sai yanzu kika tuna Allah ? Tsoki nayi tare da cewa tunda na lura kema kinasan duniyar sai in ɗaukeki aiki ki riƙa sharewa kina gogewa, ke kuma Karima idan mijinki ya barki zan zuba miki kayan mata da maza na gyaran harka duk wata zan baki dubu biyar ko anyi ciniki ko ba’ayi ba, amma idan mijinki ya barki fa. Tun kafin in rufe bakina Karima tace koma bai barni sai naje wallahi, dubu biyar fa ? Ina nan kullum zaune gida naira hamsin ma wahala take min , kuma Sultana ki rubuta a jikin takarda duk wanda zaizo ya taho da kaza kinga idan anci an rage ai muma zamu maida miyanmu….. Kallon Karima nayi sannan nace kazar Lbura’uba, an faɗa miki *kwartancin* wahala zamuyi ? Kudai kuyi ta addu’a a samu bakin titi, addu’a sukayi tayi Allah ya taimaka ya bada sa’a, daga ƙarshe dai kowa ya kama gabanshi, nima na kulle ɗakina na fantsa ma cikin gari… Ina bakin titi tsaye naji wayata tana ta kururuwa dan haka dole na dakata, fiddota nayi na duba dan ganin mai kirana, Lamba 2 wato Bello kenan, ɗauka nayi tare dayin sallama, bayan ya ansa na gaishe shi, bai ansa gaisuwar ba yace ke Uwar masu gida hotuna na gani ? Amma ai ka gane ko waye a jikin hotunan ko ? Eh nine , tou kuɗi zaka bani naira budu ɗari biyar nan da gobe idan Allah ya kaimu idan kuma kace babu sai ina watsa su duniya kowa ya kalla kyauta…. Ɗanka da matarka da abokanka duk suna kwance a saman gado zasusha kallo abunsu… Sirikinka da surukarka zasusha kallon siriki tsirara… Tou nabarka lafiya, ina faɗin haka na katse kiranshi, ina duba yanayin samun mutum kafin na yanka mishi haraji, Bello baida ko sisi kuma baida wata sana’a data wuce caca, kuma caca ba kullum akeyinta ba, gashi kuma na sace kuɗaɗanshi kaff da na gani a mota ba damuwa na bane nidai kuɗi kawai, ina gama waya da Bello na kira lamba3 wato d c o, mai girma ɗan sanda yarinyar jiya ce, Maryam Sultana Aliyu Binna, ya garin ? Haka nayi masa bayani bayan ya ɗauki wayata…. Hajiya ya kike ? Lafiya qalau kana ta ina haka ne ? Yace naje ganin gida ne baby, cikin salon cuta na kwantar da murya ƙasa ƙasa nace kuma “yar laɓai maimakon ka kirani inyi rakiya ? Murmushi yayi sannan yace wallahi nima tafiyar bazata ce wife ina ce bata lafiya, tou lallai wannan kuwa da sa’a take wace ce ita, dan bansan abinda wife in take nufi ba, dana dangantata da mace saboda naji yayi magana da sunan jinsin mace ne, yace wife itace ba lafiya, D c o yace matata nace, danshi yanda yake kallon wayewa ta ya ɗauka wata shegiyar baturiya ce, danaji yace mata nace ai shine nace wannan tana da sa’a, da kaji kuma nace wace ce ita ina tambayarka amarya ne ko uwar gida ? D c o yace ai mata ta ɗaya ce, nace tou yayi kyau yaushe zaka dawo ne ? Zan dawo amma sai ta samu sauƙi, to Allah ya sawaƙe ya bata lafiya, d c o ya amsa da amin mukayi sallama….. Lallai duk yanda akayi wannan matar tashi tasan damarta ne, idan ta riƙe d c o sosai taya zamu samu wani abu a wurinshi ne to ? Wato ita munafika nufinta ita ɗaya zataci ? Taci gidansu bari dai d c o in ya dawo bata ƙara ganinshi dan ubanta ba rashin lafiya ba ko mutuwa tayi sai anyi jana’izarta baije ba…. Napep na hau na nufi gidan Alhaji marenin wayau na, tsoho ya tsufa amma zuciyar bata mutu ba, buɗe na samu gidan dan haka na banka kaina tsaye na shiga, babu dawakuna ko guda ɗaya duk an fitar dasu an share gidan ƙwal gwanin burgewa, sai cire yana akeyi ana wani kakkaɓe kakkaɓe get in gida sai wanke shi akeyi ana goge duk inda yayi ƙura…. Cikin masu sharar na tamabaya lafiya ko Alhaji ya tashi ne ? Yace lafiya qalau bai tashi ba ubangidan shi ne zai dawo gobe, tsoki nayi tare da cewa shine ake ta wani share share ? Yace Eh , Dikko ko ? Na tambayi yaron yace Eh ai ance ma ya iso yana Abuja ko zasuyi me ne ne ? Amma dai naji ance jirgin safe zaibi yaje kano akwai abinda zasuyi sannan zai shigo katsina…. Jinjina kai nayi sannan nace tou shi ina Alhajin ne ? Ai sun tafi kano taroshi, daga nan har kano suka tafi su taho dashi saboda tsabar basu da aikinyi ? Yaron yace ai ba rashin aikinyi bane ba hajiya duk abinda kika ga sunayi dan sun san zasu samu, Alhaji fa baya saida fari baya saida baƙi kiwon dokuna yake amma kiji irin dukiyar dake gareshi, sun san suna samu da D —K ɗin ne shi yasa suke laƙafe dashi, da yana nan da baya nan kuɗi suke samu kamar tashin hankali… Tou zan tafi kawai mayi waya dashi, jakata na buɗe nayi ma yaron alheri godiya yayi tayi tare da cewa Allah ya kareki ya ƙara arziƙi hajiya ubangiji yasa kifi haka Allah ya ƙara lilka darajarki ngode sosai. Ban saurareshi ba nayi waje abu na, Gida na koma saida nayi sallah isha’e sannan na fara nazari akan Alhaji abinda zance masa kawai ya bani mota da gida sai in fita daga harkarshi, dan ni duk inda zanji ƙamshi ko labarin sunan D —K na tsani wurin tsakani da Allah bana san Dikko na tsani rayuwarshi wallahi, amma idan har Allah yayi min cikakken arziƙi saina wulaƙanta ma Dikko rayuwa, Wani irin baƙin ciki naji yana tasomin hawaye ya cikamin ido na abinda ya faru tsaƙanina da Dikko ya dawomin sabo fil a zuciyata, zuciya ta tace min ƙaryane baza a fita daga harkar Dikko ba sai na halakashi, kamar mai aljannu lokaci guda na burkuce nayi nayi na saita kaina amma na kasa wuƙa na ɗauko tare da kwarara wani irin ihu nace wallahi saina kashe ka…….. Na ƙarasa maganar cikin kururuwa. Duk wanda ke gidan nan babu wanda baiji ihuna ba, da gudu Nana da Karima sukayo ɗakina amma banda su A ` i saboda yau da wuri suka tafi gida. Lokacin da su Nana suka shigo duk na yanyanki wasu wurare na jikina da wuƙa, abin ya tada musu hankali dakel suka riƙeni suna tambayata waye Sultana kallon Nana nayi cikin kuka nace wallahi saina kashe shi gobe zai shigo katsina bana ko ƙaunar jin irin sunanshi a rayuwata…. Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un, shine abinda Dikko ya faɗa a daidai wannan lokacin tare da janye ruwan dake gabanshi, hankalin kowa yayo kanshi tare da tambayar lafiya ranka ya daɗe ? Dafa ƙirjishi yayi tare da cewa gabana ke faɗuwa babu gaira babu dalili. Duk kusa dashi suka matsa suna mishi sannu, kallon babban yaronshi yayi sannan yace maza kiramin gida, ɗaukar waya yayi ya kiro dadyn dikko, babu ɓata lokaci dady ya ɗauka D — K babu ko gaisuwa yace Dady lafiyanka qalau kuwa ? Murmushi Dady yayi tare da cewa mi kuwa zai sameni ? Bayan ina nan zaune cikin iyalina muna farin ciki saboda zuwanka ! Dikko yace Dady karka ɓoyemin dan Allah miye ? Dady yace tsaya ma kaji, saida ya haɗa Dikko da kowa yayi magana sannan yace kaji ko ?Ajiyar zuciya Dikko yayi kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi sannan yace kawai haka nan naji gabana yana faɗuwa, Dady yace saboda zaka ga ganni ne, kayi ta addu’a Allaah ya tsare kuma kayi bacci da wuri, jinjina kai Dikko yayi tare dayi ma Dady sallama suka ajiye waya…. Dakel su Nana suka lallasheni nayi shiru, Karima tace inyi ta addu’a don Allah sharrin shaiɗan ne, nace tou amma har yanzu ban daina baƙin ciki ba, saida suka tabbar hankalina ya kwanta sannan suka tafi bayan sunsha fama na faɗa musu ko waye naƙi faɗa musu… Suna fita na rufe ɗakina nayi addu’a na kwanta bacci, Da safe kuwa misalin 12:45pm na fara gwagwaɗawa Alhaji kira, bawan Allah banda zufa babu abinda yake haɗawa, idanuwanshi sunyi jajir saboda tsabar tashin hankali duk wanda ke wurin saida Alhaji ya bashi tausayi duk da babu wanda yasan abinda yake damunshi, amma banda Dikko dakeyin kyakkyawan murmushin dake fito masa da tsananin kyawunshi, da yasan yanda yakeyin kyau idan yanayin murmushi daya dawwama yanayin fara’a, duk da ko baiyi murmushi ba yana da kyau sosai gaskiya, taunar rainin hankali yake ma cingom in bakinshi sannan yace wai har yanzu ta hanaka ka huta ne ? Kamar Alhaji yana jira yace Eh ranka yadaɗe, Dikko yace bani ita, Alhaji yace ai kiran ya tsinki, ɗaure fuska Dikko yayi sannan yace kirawo min ita…………… 23/08/2019 *JAMILA MUSA* 🤙🏻 Ina mana barka da juma’a,⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 17 _Don Allah kuyi haƙuri mu dukanmu mubi labarin nan a hankali, wannan labari na faɗa muku yanda yake, an rage wasu abubuwa ne wasu kuma an gyara su, labarin yana da yawa sosai ba’ayi komai ba yanzun muka fara wasan , kuyi haƙuri muje a hankali, ni jamila musa nake cewa asha karatu lafiya…._ Gajiya nayi da kira ba’a ɗauka ba dan haka na haƙura banyi yunƙurin sake kira ba, ina ƙoƙarin ajiye wayata kira ya shigo a cikin wayata mamaki ya kamani sosai ganin kiran Alhaji, taya zai kirani bayan ni na kirashi da kaina bai ɗauka ba ? Haka nan naji tsikar jikina ta tashi zuciyata namin wasi wasi lallai akwai wata ƙullallah da ake son ɗaura min, duk yanda akayi wani baƙon lamari zai faru tou amma bansan ko miye ba, kashedi zuciyata tamin tare da hanani ɗaukar wayar, sau biyu aka kira ban ɗauka ba dan haka suka haƙura basu sake kira ba… Kallon Alhaji Dikko yayi sannan yace yarinyar nan zata kai shekaru nawa ? Saida Alhaji ya kwantar da kai cikin biyayya sannan yace baza ta wuce sha shidda zuwa sha bakwai ba, D — K yace tou wallahi wannan yarinya tasan abinda takeyi kila shekarunta ya wuce yanda kake tunaninta tana abunta da lissafi, amma baka taɓa kiranta a waya ba ko … ? Alhaji yace Eh gaskiya chat kaɗai mukeyi da ita, sai ranar da ta turomin vidion nan shine na kirata, amma daga ranar ban sake kiranta ba saidai ta kirani, Dikko yace tou jikinta ya bata ba kaine kake kiranta ba shi yasa bata ɗauka waya ba, amma nasan zata kiraka zuwa anjima zatayi tunanin wayar ta koma hannunka, ajiye wayar yayi a gefenshi suka ci gaba da abinda sukeyi.. Ina ajiye wayar kiran Bello yana shigowa, ɗauka nayi bayan mun gaisa yace min Uwar masu gida nifa har yanzu ban samu kuɗin da kike magana ba, jinjina kaina nayi tare da murmushi nace kanajin wasa bazan iya tura hotunan ka ba a yanar giza gizo ko ? Tou wai babu zan baki ne ? Cikin faɗa yace tou banda su ko satowa zanyi in baki saboda inajin tsoronki to ki turawa uwar yanar giza gizo dan kutumar ubanki ko an faɗa miki tsoronki nakeji ko inajin tsoron a ganni tsirara, idan baki sani ba har gasar fitowa tsirara nayi daga ƙofar gida na har bakin masallacin juma’a naje ranar juma’a babu kaya a jikina na dawo, ni zaki ɗauka hoto kimin hauka ? Tou bake ba ubanki ma nafi ƙarfinshi ki riƙe kiyi ta kallo mtsw ya kashe wayatshi….Murmushi nayi tare dabin wayar da kallo, har zan haƙura wata zuciyar tace wallahi ƙarya yakeyi bai wani fita tsirara ba idan kika fahimci maganar shi ta farko a sadudance yayi miki magana, karki sauƙaƙa mishi number wayar matarshi zaki fita ki samo ki tura mata zata bashi labari, idan kin tura mata ni na sani sai ya kiraki, idan ya kiraki sai kice kin turawa ɗanshi ma, shi kuma ɗan ba hoton za’a tura mishi ba voice note za’ayi mishi da wasu maganganu masu zafi zuciya zata tunzurashi yayi ma baban magana, tashi dai ki fita duk ki samo numbobinsu ki dawo sannan musan abunyi… Bello kuma shida abokinshi suka kashe sannan yace na faɗa mata, abokin yace tou yanzu zata shafa maka lafiya kaga kun rabu lafiya zata gaji da ajiyar hotunan ta gogesu, Bello yace ni tsoro na ɗaya tace ta turawa wata ƙawarta hotunan fa, karka damu sun gaji su goge dan ubansu, dariya sukayi tare da ƙara kashe wa cikin duniyanci…. Ina fitowa daga wanka nace ba’asan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, zakayi dana sanin hanani kuɗin nan, kila kuma rabona ne yake da yawa kuɗin zasu sake yawa. Har na gama shiri da abinda nake saƙawa nake warwarewa, Nana na kwaɗawa kira ta kwararo da gudunta tazo, kallonta nayi sannan nace Nana aiki yamin yawa zan fita neman wurin zama sannan kuma zanje wurin wani Alhaji dake tamin rainin hankali, ai kinsan majalissar babana ko ? Nana tace Eh na sani, nace ai kinma san Bello abokinshi ko ? Nana tace sosai ma, tou lambar wayar matarshi da babban ɗanshi zaki kawo number wayoyinsu zan baki dubu ɗaya… Yashe baki Nana tayi sannan tace godiya nake Sultana, wani sauran biredi da naman da naci jiya na rage na miƙa mata ansa tayi taita kwarara godiya harta fita, tana fita nima na tattara nawa ya nawa na fita nabar gidan… A ƙofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, wasu irin zuƙa zuƙa motoci tun daga ƙofar gida har cikin get in gidan, kuma yauma get ɗin a buɗe yake daga inda nake tsaye ina hango komai na gidan !Matashin jiya daya faɗa min cewa Alhaji yayi tafiya shine yazo wurina da sauri ya gaisheni cikin girmamawa ansawa nayi cikin sakin fuska sannan nace gidan naku lafiya naga taron motoci ? Lafiya qalau ubangidan nasu ne ya dawo ko gida ma baije ba ya fara da ganin dokuna, jiya da aka fidda dawakunan doki ɗaya ya kare a ƙafa shine ya fara da ganinshi kafin ya wuce. D — K ne ya fito daga cikin palon yana magana daga ganin yanayin maganar shi faɗa yakeyi, saida ya fito tsakar gidan sannan ya riƙe ƙugunshi da duka hannuwan shi biyu yaci gaba da magana amma bana iya jiyo abinda suke cewa saboda tazarar dake tsakaninmu. Zubinsu da yawansu ya bani tsoro gasu ƙosasshi, inda Dikko yake tsaye na kalla, gaskiya Dikko ɗan gayu ne wankakken namiji yasha wanka ya ƙoshi tsaftatacce dashi ya cika ya fito cikakken namiji har wani gemun rainin hankali ya ajiye kamu ɗaya gaskiya duk da bana ƙaunar shi jarumin namiji ne duk inda mace take san namiji Dikko yakai tsakani da Allah zan faɗi gaskiya, domin Allah Dikko yana da kyau mai burgewa da ɗaukar hankali , sauke hannunshi ɗaya yayi daga riƙon da yayi mishi ya saka a aljihu ya ciro ibadar tashi, ya ciro cingom in daga cikin takardar shi ya jefa a bakinshi sannan suka fara taho wurin motocinsu… Murmushi nayi kaɗan yayin da wani sashe na zuciyata yake cewa kira sunanshi idan ya juyo ki caccakawa uwarshi zagi komai zai faru ya faru idan ma ta tafasa ta ƙone, yayin da wani sashe na kwalwata yake bani shawara cewa duk abinda zakiyi kisa nazari da lissafi kiyi ma takonki linzami mai kyau duk daren daɗewa Dikko sai kinci ubanshi.Zuciyata tace kiyi masa magana dan ya tunaki kuma yasan kina nan kuma ki faɗa masa cewa zaki ci ubanshi idan babu yau akwai wata rana…. Sallama nayi da matashin daya faɗa min Dikko ne yazo sannan na wuce ciki, a lokacin dana isa wurinsu tuni D — K ya zauna cikin mota ana ƙoƙarin rufe masa mota na riƙe murfin motar , Kowa kallo wurin hannun daya riƙe murfin mota yayi dan ganewa idonsa ɗan rainin hankali daya isa yayi wannan iskancin, kwantar da kaina nayi saman murfin motar cikin tausasashshiyar murya nace Dikko, kallo na yayi tare da cewa na’am ya tsareni da idanuwa, shiru na wani lokaci ya ratsa wurin bai daina kallona ba kuma nima ban daina kallonshi ba haka kuma babu wanda yayi mana magana… Nice na fara cire idona daga kanshi dan idan har ina kallonshi tou lallai babu abinda zai hana in burma mishi wuƙa, kaina yana kallon ƙasa nace ka kuwa gane ni ? Na ƙarasa maganar tare da ɗago fuskata amma ban sake kallon idonshi ba… Cikin ɓacin rai yace Al ‘ Ameen mtsww muje ya faɗi maganar tare da jan murmufin motar da ƙarfi ya rufe, zuciya bata da ƙashi ganin Dikko zai maidani sakara yasa na dunkule hannuna na kaiwa gilashin motar duka saida ya tarwatse , jini kuwa yace gashi nan zuwa… Duk da haka Dikko baiyi niyar tsayawa ba saida nace kai ƙaramin ɗan iska yau itace rana ta ƙarshe a gareka kamar yanda na dasa lissafin kwanaki mutuwarka , idan har kayi nasarar guduwa ina nan tafe gareka sai ka ɗanɗani azaba kwatankwacin irin wacce ka ganamin baka da aiki sai cin cingom kamar wata karuwa sakaran banza daƙiƙi ɗan gidan matsiy…… Wanda aka kira da Al ” Ameen shine ya ɗaga hannunshi da niyar kwarara min mari Dikko ya riƙe hannunshi tare dayin murmushin mugunta yace waye yace maka irinsu ake duka ? Tsaya daga gefe kaga maganin ta, Allah ɗaya nake tsoro amma yau dasai nayi mata allurar natsuwa, amma ka barta nayau zan mata kaɗai idan na sake ganinta tou nasan abinda take buƙata, Al ‘ Ameen yace mai gida ka sakeni in koya mata hankali, murmushin mugunta Dikko yayi tare da cewa bari in bata abinda ta roƙa… Sakin hannun Al ‘ Ameen yayi sannan ya matso kusa dani, ɗan kauda kanshi yayi gefe kamar yana nazari fuska a ɗaure ya juyo ya kalleni ni juyowar da yayi gaba ɗaya wurin kowa ya juya baya, hannuwana ya haɗa duka biyun ya maidasu ta baya ya riƙe, hannu ɗayan kuma ya riƙe fuskata, ƙasa ƙasa yayi magana cewa. Naga dai kina san cingom in nan kinsan kwanaki da muka haɗu ban “yan maki shi ba, kuma sai kiyi ta abu babu kawaici a gaban jama’a sai kiyi ta wani zalamar Dikko kuma ko an baki ni nayi miki yawa ba inda zaki je dani dan ruwa ba sa’ar kwando bane, kina da daraja ɗaya a wurina kuma albarkacinta kike ci amma wallahi dasai na nuna miki ni tantirin ɗan iska ne, darajar tasa kawai bazan wulaƙanta ki ba, amma idan kina neman rainin hankali da tsantsagwaron rashin mutunci daga kaina an rufe littafi. Tattaunawa yayi cingom in cikin salon jan hankali saida ya busa cingom in yanda ake cewa kwai, sannan ya kalleni da wani iri salo sai kuma yayi murmushi da gefen bakinshi, hannun daya riƙe min fuska ya ciro cingom in sannan ya tura minshi cikin bakina, tuf tuff na fara tofar da cingom in , murmushi yayi tare da rufemin baki yace ai ƙarya kikeyi sai kinci…. Iya ƙoƙari nayi na tofar yaƙi fita ga kuma ya riƙe min hannuwa duka, daidai saitin maƙoshi na yayi min wani duka wanda yasa dole saida na haɗi cingom in, dariya yayi sannan ya sakeni tare da turani baya yace sai mun sake haɗewa an mata…. Tangal tangal na tafi kamar zan faɗi su kuma suka shige motocinsu suka tafi aka barni a filin tsakar wurin daga ni sai Alhaji, dakel na iya haɗiye yawun bakina saboda azaba da raɗaɗin da maƙoshina yakemin saboda nushin da yayi min.Kallon hannu na nayi da jini yake ta ɗiga sannan na kalli Alhaji nace kaini asibiti, cikin damuwa yace muje, dani dashi muka nufi wurin motarshi muka shiga gaba ɗayanmu muka nufi asibiti, Muna zuwa babu wani daɗewa akamin diresin , bayan an bincike hannun kaf ko akwai wani gilashin a ciki, magunguna aka bani sai kuma allurai da akayi min duk Alhaji ne ya biya kuɗin bayan an gama komai ya ɗaukeni muka tafi gida ! A ƙofar gida yayi parking duk muna cikin mota daga ni harshi, shiru mukayi na wani lokaci sannan Alhaji yace hajiya dan girman Allah ki goge wannan vidio dan darajar manzan Allah S. A. W, ki taimaki rayuwata ki goge don Allah, badan halina ba, Ajiyar zuciya nayi sannan nace tou nima ka taimakeni dan darajar manzan Allah S. A. W dani dakai duk mu taimaki juna daga yau nayi maka alƙawari zan goge vidio sannan kuma zan fita rayuwarka babu dawowa… Tattaro hankalinshi yayi wurina sannan yace faɗamin me kike so idan har ina da hali zan miki ! Ba tare dana kalleshi ba nace mota kawai zaka bani daga ita na rantse maka da Allah na fita sha’anin ka vidiwo kuma zan goge… Goge zufa Alhaji yayi sannan yace wace iri kike so ne ? Ni bansan mota ba amma dai mai kyau nake so, kallon motarshi yayi sannan yace kina san wannan ? Ba tare da ɓata lokaci ba nace Eh tamin kuma ina santa, Alhaji yace tou na baki ita, kina da wurin ajiyarta ne ? Yanzu ma zan ajiye miki ita insa azo a tafi dani amma ki goge hotunan nan dan Allah, karka damu zan goge wallahi, a , a nidai ki goge a gabana don Allah, tunda nace zan goge ai zan goge, Alhaji yace tou bayan wannan sai me ? Abu na gaba ina so ka faɗamin waye Dikko ? Miye asalinshi waye babanshi a garin nan ? Wane irin matsayi gareshi kuma wane dalili ne yasa yake ɗagawa ta rayuwa ina san ka faɗamin asalin Dikko da kuma tarihin rayuwarshi….. Gyara zama Alhaji yayi sannan yace fara bani mazaunin motarki na ajiye ki goge vidio sannan sai muyi magana kinga lokacin ina cikin natsuwa, ba damuwa na faɗa tare da buɗe mota na fita na shiga cikin gida !:’, Kuyi haƙuri don Allah yau ina can gidan uwar ɗakina nima inacin shagali da miyar mutunci, wurin uwar ɗakina wato *RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE* ina alfahari dake uwar ɗaki ɗaya tamkar da dubu banda kamarki kuma kina da matsayi na musamma a zuciyar *MEELAT MUSA*….. 24/08/2019 *JAMILA MUSA CE…*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 18 *_KOMAI DADIN DUNIYA KIYAMA TA FISHI , daga alƙalamin Ummerherny Nerserllerh idan kika bari aka barki baya bazan baki labarin wannan ƙayataccen labari ba wanda ya fito daga alƙalamin haziƙar marubuciyar zamani, Allah ya taimaka surukuta yasa a kammala lafiya amin…_* Ina shiga gidan ko sallama banyi ba yaro ya shigo da saurinshi wai ance Sultana tazo Alhaji yana kiranta , Nana ta fara miya sameki naga hannunki a ɗaure … ? Duk hankalin su A ` i ya tashi sunga uwar ɗakin kwarata hannu da ɗamara, murmushi nayi tare da cewa yawwa A ` i da Allah inda zan ajiye mota nake so nayi maganar dan kauda tambayar abinda yaji min ciwo, Hafsa tace ina motar take ne ? Ba tare dana kalleta ba nace tana waje, dan haushin Dikko ya fara shafar Hafsa saboda soyayyar da take mishi bana san Dikko haka kuma bana soyayya wa duk wanda yake ƙaunar Dikko, Hafsa tace sai in ajiye miki a gidanmu, ban bata amsa ba nabi yaron muka koma waje… Motoci biyu na gani a ƙofar gida , wurin motar Alhaji na tsaya daidai saitinshi sannan nace gani, wani wuri ya buɗe ya tattaro wasu takaddu ya bani ansa nayi naɗan basar ina kallo a zahirance karatunsu nakeyi amma wallahi a baɗinance bansan ko na miye ba… Fitowa yayi daga cikin motar ya bani makullin tare da cewa ga motar nan zanje mai gida yake kirana dana gama zan dawo insha Allah amma ki rufamin asiri Sultana ki goge vidion nan don Allah, wallahi karkaji komai Alhaji zan goge amma kaɗan bani na kati plz, yace ina zuwa bara in gama tattara tarkacena a motar nan… Komai nashi ya kwashe a mota ya zuba cikin motar dana gani, bayan ya gama ya ciro wayarshi yace kalli ki gani, kallon wayar nayi yace kinga na goge nawa ko ? Nace Eh nima zan goge insha Allah, godiya yayi sannan ya bani kuɗi amma basu da yawa yace idan ya dawo anjima insha Allah zai bani tukuicin goge vidio, godiya nayi masa sannan mukayi sallama ya shiga mota tare da cewa karfa kiyi wasa da takardun motar nan ki adana su kinji ko ? Sai yanzu na gane abinda takardun suke nufi godiya nayi masa suka wuce ni kuma na koma gida… Ina shiga gida Hafsa na ba makullin nace kije ki ajiyemin zan ɗauko ta ƙarshen satin nan insha Allah, ansar mukulin tayi taci gaba da maganar ta, kallonta nayi sannan nace saurara kiji, kije ki ajiyemin mota ki dawo, tashi tayi ita dasu Saude suka tafi ni kuma na shiga ɗakina, ban daɗe da shiga ba Nana ta shigo tare da bani number matar Bello amma bata samo na ɗanshi ba , ansa nayi da nayi niyar bata 500 sai wata zuciyar tace kawai in bata 1k in ka nema ma ka samu ai arziƙi ne… Jakata na buɗe na bata 1k nayi godiya, itama godiya tamin ta fice a ɗakin, tana fita na kulle ƙofa na kwanta saman katifa na fashe da kuka mara sauti , duk duniya babu wanda ya taɓa wulaƙanta ni kamar Dikko nice zai bawa cingom in bakinshi da yawun bakinshi na haɗe a cikin cikina , duk duniya babu abinda yakai miyau saurin sadar da shaƙuwa, shi yasa masu wayau ko bariki suke basa yadda suna haɗa bakunansu da na wasu, waccan ranar bai haɗa bakinmu ba amma shine yau ya ciro abu daga cikin bakinshi ya bani, yana da wata manufa ta daban shine dalilin da yasa yace ma Al ‘ Ameen bara suga magani na, wato wannan dalilin ne yasa kowa ya juya mana baya ko ? Saida na goge hawaye na sannan nace ƙarya kakeyi yawun bakin ka bazai taɓa zama hukunci a gareni ba…Nayi kuka har na gode Allah daga baya kuma bacci ya kwasheni wanda bansa lokacin daya zo ba kuma baiyi shawara dani ba, Washe gari koda na tashi nayi sallah bacci na koma bayan na gama kwashewa Dikko karama , misalin 09:30am Alhaji yasa aka kirani a waya, bayan na ɗauka nayi sallama dakel Alhaji ya amsamin sallamar cikin nishi yace Sultana ina federal medical center { F M C } saida ya sake yin nishi cikin yanayin wahaltuwa sannan yace ina nan Accident & Emargency kizo yanzu don Allah inasan zanyi magana dake…. Har a zuciyata banji daɗi ba cikin muryar tausayi nace kayi haɗari ne ? Hawaye ya gangaro masa daga cikin idonshi yace kizo dai dan bana tunanin zan ƙara awa ɗaya a cikin duniyar nan…. Subahanalla da Allah ka daina wannan maganar gani nan zuwa insha Allah, cikin rawar jiki na kashe wayata, da sauri na sauko daga saman katifa na zuba ruwa, a gaggauce naje nayo wanka tare da wanko bakina, mai fauda da kwalli kaɗai na shafa, baƙar riga ta jallabiya na saka na yana gyalen a saman kaina na zagoyo dashi har gashin kaina saida ya fito ta ƙasan gyalen jallabiyata, gilashi mai saukin duhu na saka sannan na wanke jikina da turaruka masu sanyi ƙamshi, masha Allah na faɗa a lokacin da naga kaina a cikin madubi, nayi kyau sosai na fito kamar baƙuwar balarabiya a nigeria, Wayata na ɗauka da jakata, na fito ina tsaye ina kulle ɗaki Hafsa ta shigo, ita ɗaya ce babu abokan nata su Saude, su Nana ma duk basa tsakar gida, ɗan gangarowa tayi da wani irin salon tafiya, ta wutsiyar idona na kalleta sannan na ɗaure fuskata na kallota dukanta a daidai lokacin dana gama rufe ɗakina… Wow uwar ɗakin karuwai kinyi kyau fa kamar dai ba’a mutu ba, share maganar nayi tare da cewa da mota kika zo ne ? Eh ta faɗa tare da bina da kallon cin wanka , gaba nayi tare da cewa muje ki saukeni f m c biyoni tayi muka fito a tare, a ƙofar gida muka haɗu dasu A ` i hada Amisty da Saudatu…. Amisty tace wurinki zamuje munji shiru har yanzu, kuma mun rubuto takarda an tsara jaddawalin yanda zai ƙawatar ya kuma tafi da hankalin maza gaki kuma zafi fita, buɗe gaban mota nayi na kame sannan nace ku shigo muje kuma, baya suka shiga, Hafsa kuma ta zauna mazaunin tuƙi taja muka tafi…. Saida muka fara tafiya sannan nace karanto min ina saurarenki, Amisty fa tasan komai tasan bana ganewa bana rubutawa kuma bana iya karantawa amma sai tace kidai duba ki gani Sultana, basar da ita nayi tare da miƙa hannuna ta baya na anso takarda ko buɗewa banyi ba na ajiye shegiya ban sake bi ta kanta ba kuma ban sake magana ba har muka isa asibitin… Wani irin tuƙin ganganci Hafsa tayi tare da sakin sitiyarin saboda taga D — K , a tare muka iso dasu sai leƙawa take tana kiranshi, wato abinda na fahimta idanma ka nunawa mutum ka damu dashi sai yayi ta ɗagawa, kallon Hafsa nayi tare da cewa ke kuwa baki da aji a haka kike tunanin zan riƙa haɗaki da zafafan mata babu class, raina ya ɓaci sannan nace uban waye Dikko da kike ta hauka kina kiranshi mutane suna kallonki kamar wata zararriya…. A daidai lokacin da muka fito mu dukanmu daga mota shima Dikko ya fito kuma yaji zagin da nayi masa , bai kallemu ba yayi gaba ana take masa baya nima gaba na shiga su Hafsa suka rufomin baya, murmushi Dikko yayi a daidai lokacin da muka tsaya bakin ƙofar ɗakin kowa da muƙarrabenshi a bayanshi, kallona Dikko yayi tare dayin murmushi sannan yace zaki ci ne an mata yayi tambayar tare da ɗaga gira ? Ya ƙarasa maganar tare dayimin wani irin kallo mai tattare da mugunta, yaci gaba da cin cingom inshi cikin salon jan hankali gemunshi yana motsawa a hankali cikin salon ɗaukar hankali , murmushi nayi saboda gaskiya yanayin da yayi ya burgeni, ƙarshen harshenshi ya kawo cingom in yayi wasa dashi a daidai lokacin da aka buɗe mana ƙofa duk muka shiga, daga waje bai sake kallona ba kuma bai sake murmushi ba babu magana har muka isa gaban gadon Alhaji… Duk matan da muke tare ihu muka farayi saboda tsoron yanayi da Alhaji yake ciki yayin da wasu suka nufi hanyar fita, dani da A ` i aka bari yayin da A ` i ta duƙushe tana kuka ni kuma na cire gilashi na wurgar a gefe na rufe idanuwa na naci gaba da dire dire ina kuka saboda na kasa gaba na kasa baya…. Shi kuma Alhaji burinshi inje wurinshi in taimaki rayuwarshi na goge vidio sai kirana yake cikin dasasshiyar murya da yayi magana sai jini ya kwararo , Dikko yace ya daina magana amma yaƙi saurarenshi Sultana kawai yake kira, Kusa dashi Dikko ya ɗuka sannan ya tambayashi me zan mishi ne ? Hawaye na zuba a idon Alhaji yace ma Dikko ya rufa mishi asiri ya kawoni wurinshi magana zamuyi ta sirri, Dikko yace faɗamin na faɗa mata kaga ta firgita wani abu zai samunta, cikin wahaltacciyarar murya Alhaji yace kayi min wannan arziƙin na sauran mintunan da suka ragemin a duniya lokacina yana tafiya zan iya mutuwa ko wane lokaci, yanda yayi maganar ne yasa Dikko ya kallo inda nake tsaye ina ta direre kamar anyi ma lafiyayyan diko allurar hauka. Ɗauke idonshi yayi daga kaina sannan ya kalli zugar daya zo da ita, Al ` Ameen ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar bashi ne yayi maganar ba, gaba ɗaya waje suka fita harda A ` i aka fita, inda gilashina yake Dikko yaje ya ɗauko sannan yazo kusa dani, ta gaban rigata ya jawo ya sagala gilashin sannan yace buɗe idonki, jikina yana kyarma na buɗe na kalli Dikko, dakel ya haɗe yawun bakinshi sannan ya tofar da cingom in bakinshi gaba ɗaya yanayin Dikko ya canza ɗaure fuska yayi sosai sannan yace miye tsakaninki da mara lafiyar nan ? Miye dalilinki na zuwa ganinshi ? Me kikaje yi gidanshi ? Kema “yar iska kike so ki zama ko ? Cikin gatsali nace Ey “yar iska zan zama ina ruwanka da iskanci na ne ? Jinjina kai yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe wuce muje yana kiranki, tirjewa nayi tare da juya zan fita da gudu ya riƙoni yace ai ƙarya kike sai kinje, har gaban Alhaji ya jani ya kaini sannan ya zaunar dani saman kujera ya tsaya ta bayana yace gata nan me tayi maka ne ? Ko kaima taci kuɗinka kamar yanda taci na Umar ? Ɗaga kaina nayi na kallo Dikko ɓacin rai kwance a cikin idonshi zare min idanuwa yayi tare da cewa bari kallona kar fashe miki kwayar ido wallahi, jiki a sanyaye na sauko kaina daga kallon da nake ma Dikko naci gaba da kallon Alhaji ina kuka, dafo kujerar yayi ya duƙo kusa dani sosai saitin kunne na yace na rantse da girman Allah idan na gano akwai wani abu tsakaninki dashi saina kashe ki, ya faɗi maganar tare da shaƙemin wuya sosai na fara ƙoƙarin ƙwalƙwale hannunshi na kasa, tun ina iyawa har nasa wani abu na fara halbe halbe har na faɗo daga saman kujera Dikko bai saki wuyana ba naci gaba da halbe halbe, yanda nake halhalbe ya jawo hankalin mutane suka yo kanmu amma an kasa cire hannun Dikko daga wuyana, Hayani tayi yawa sosai wanda yasa su Al ` Ameen suka shigo ciki da gudu amma wallahi duk yawan mazan nan suka kasa ɓanɓareni daga hannun Dikko harsai dana suma, riƙe Al ` Ameen yake da hannun Dikko yana cewa don girman Allah mai gida ka ƙyale yarinyar nan karta mutu, zaro jajayen idanuwan shi yayi kamar yaci mutuwa yace fita idona Al ` Amenn ya faɗi maganar yana fitar da wani irin lumfashi kamar ranshi zai fita, Al ` Ameen kuwa ƙin sakin hannun Dikko yayi saboda tunda yaga Dikko a wannan yanayin yasan komai zai iya faruwa…. Yace mai gida karta mutu, Dikko yace ta mutu idan ta mutu kaine ka kashe ta ko kaine zakayi azumi ? Ya ƙarasa maganar tare da kwalalo idanuwanshi waje , sannan yace duk abinda ya faru da ita nine ya ƙarasa maganar tare da nuna kanshi, haƙuri akayi taba dikko dakel aka samu ya sakeni , Bakin gadon Alhaji ya koma ya ɗauki wayarshi iyakar bincike Dikko yayi bai samu komai ba, kuma number na dama Alhaji baiyi saving ba, jerin kira ya dawo yaci gaba da binke, saida ya gama sannan ya ajiye wayar , kallo gadon da nake kwance yayi har an sakamin ƙarin ruwa da taimakon Al ‘ Ameen dayayi tsaye yace a bani taimakon gaggawa, Kusa da Al ‘ Ameen yaje tare da cewa bani makullin mota, cikin girmamawa ya ɗauko ya bashi baiyi mishi musu ba saboda yasan Dikko baya san gardama idan yace ayi kawai ayi mishi idan yace a bari barin kawai za’ayi sai a zauna lafiya, Cingom ya ciro daga aljihu ya ɓanɓare ya saka bakinshi yaci gaba daci, Al ‘ Ameen kuwa bin Dikko yayi da kallo harya fita daga ɗakin yana mamakin hali irin na Dikko zuciyarshi tayi yawa idan ya burkuce wani lokaci kamar bashi ne yakeyi wasu abubuwan ba… Ta jikin window ya leƙa Dikko, har ya shiga motar yaja ya tafi cikin tuƙinshi na ganganci wanda baya kaucewa kuma baya ɗagawa kowa ƙafa idan ya tafi sai yakai inda zaije hankalinshi yake kwanciya, Allah ya tsare hanya Al ‘ Ameen ya faɗa tare da dawowa wurin gado na ya tsaya, su Hafsa da Saude da A ` i da Amisty sunyi jigum kowa yana jiran farfaɗowa ta yaji abinda ya haɗani da D — K…… Dikko kuwa tuƙi yake amma yana tunanin maganar Alhaji ranka ya daɗe wato wallahi wata yarinya ce muka ɗan keɓe da ita , tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya daɗe tana ɗauka cikin waya ban sani ba…. Dukan sitiyari Dikko yayi tare da cewa tabbas yacemin yarinyar nan shekarunta bazai wuce 16 zuwa 17 ba daidai saitin zuciyarshi ya daka tare da cewa kece …. ? Akan titi duk ƙurewar wuri Dikko ya juya kan sitiyarin mota ya koma baya ba abinda ya dameshi da halin da wani zai shiga kanshi kawai yakeji amma baya sauraren talakawansu, da gudu ya ibi shararra ya komo asibiti, a lokacin su Al ‘ Ameen sun fito zasu tafi ganin Dikko ya dawo yasa Al ‘ Ameen ya dawo cikin ɗakin da gudu yasa aka ɓoyeni, danshi Alhaji tuni Allah ya anshi rayuwarshi har an tafi da gawarshi, duk zunubin da Alhaji ya cacumar ma kanshi an samu wani marar rabo a lahira ya dira gidanshi yayi mishi caccakar wulaƙanci aka kawoshi asibiti dan ceton rayuwarshi Allah yasa ikar ibar da yayo kenan, Allah ya jiƙanshi yasa mu cika da imani ubangiji ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo… Ana ɓoyeni su Al ` Ameen suka fito, a waje suka haɗu da Dikko yana ƙoƙarin shiga suka faɗa mishi mutuwar Alhaji ni kuma an canja min asibiti, Allahu Akbar Dikko ya faɗa tare da cewa ubangiji ya ƙarɓi baƙuncinka Muntari Allah ya kyautata tamu bayan taku, da Amin kowa ya ansa sannan suka tafi a tattare baki ɗayansu… 25/08/2019 Taku a kullum *MEELAT MUSA…*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 19 Har yanzu kalar idon Dikko bai koma fari ba, idon nan jajir kamar yaci bala’e, amma a hankali yake washewa zuwa kalarshi ta ainahi, fuskar nan a murtuke ya jingina bayan shi da kujerar mota kana kallonshi kasan yana tattare da tsantsar damuwa. Ɗan gajeren tsoki yayi tare da gyara zamanshi, hannunshi yakai ya shafe gefen fuskar shi, tunanin safiyar haɗuwarshi da Sultana ya fara dawo mishi sabo fitikil kamar yanzu ne abun yake faruwa, da sauri ya rumtse idanuwan shi tare da haɗe leɓunan sa wuri ɗaya ya danne su da haƙoranshi ta ciki, buɗe ƙofafin hancin shi yayi saboda lumfashin da yake shaƙa yayi mishi kaɗan ya buɗe ƙoƙofin hancin ne dan iskan ya yalwace shi. Har suka isa gidan rasuwa Dikko bai sake ma kowa magana ba, tunda dama shi ba ma’abokin surutu bane, mota nayi parking ya fita cikin damuwa danshi dama kullum haka yanayin shi yake , farin ciki da ɓakin ciki duk yanayin iri ɗaya ne a wurin shi, babu wanda ya isa yasan lokacin farin cikinshi kuma babu wanda ya isa yasan lokacin da yake damuwa. Tunda ya fito aka fara gyara mishi wurin da zai zauna dan zamanin ga mutane basa abu domin Allah basa darata girma shekaru da mutumci amma suna ba naira matsayi na musamma, Dikko yana da rashin mutunci amma alherinshi yasa mutane basa ganin rashin mutuncin nashi dan Allah yayi masa kyauta idan dai kukayi ido ido dashi tou tabbas zai baki kuma baya da kwauro idan zai bayar mai yawa yake baka, tou kyautar itace ta danne rashin mutuncin shi ga idanuwan al’ummar gari… Sabuwar tabarma aka amso daga cikin gidan aka shimfida mishi, takalman shi ya cire ya taka tabarmar da safa, saida ya zauna sannan kowa ya zauna kuɗi suka fara nuna ikonsu domin masu neman asan dasu sukayi ta zubewa suna bada gaisuwa, saida ya jinjina kai dan shi kaɗai yasan tsutsar baƙin cikin dake lasar masa zuciya… Wanda suka bawa duniya gaba ne suka fara bawa Dikko labarin yadda abun ya faru amma a zahirance yana jinsu amma a baɗinance hankali shi yana wurin Sultana so yake kawai a dawo jana’iza yaje ya ganota wallahi sai ta faɗa mishi miye tsakaninta da Muntari, inma banda take daƙiƙiya dan ta tona mishi asiri shine zai haɗa kirji da ita taje ita kuma ta haɗa da yaronshi… Wayarshi ya ciro yayi “yan rubuce rubuce bayan ya gama ya tura, wayar shi ya maida aljihun gaban riga a zuciyarshi kuwa yana tunani Sultana ta gama barbaɗashi a duniya kowa kallon ɗan iska yake mishi, Mikewa tsaye sukayi gaba ɗaya dan an fito da mankara, sai yanzu wasu keyin alwalla shidai yana da ita takalmin shi ya saka suka fita sarari dan sallatar gawar Alhaji Muntari , Allahu Akbar ubangiji kayi mana kyakkyawan ƙarshe hanyar dai ɗaya ce duk wanda yazo sai ya koma Allah kasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo ameen…. A asibiti kuwa ina kwance cikin tsaka mai wuya, ina tafiya ne tsakanin rayuwa da mutuwa, duk wanda ya ganni saiya tausayamin ga hannu na naɗe da bandej wanda na fasa shi a jikin gilashin motar Dikko, su A ` i kuwa suna bani kulawa ta musamman tare da tattalina kamar mun fita ciki ɗaya ! Tsaye suke zagaye jikin gado na hankalin kowa tashe, jami’an tsaro ne suka shigo gaba ɗaya suka fatattaki su A ` i , kujerar da ake tura marasa lafiya aka ɗauko aka ɗorani a samanta suka tun kari hanyar fita dani daga cikin ɗakin, wani irin ihu Saude tayi tare da cewa ina zakuje da ita ne ? Basu saurari kowa ba suka fito dani, cikin mota aka sakani mazaunin baya sannan aka rataye ƙarin ruwan a jikin kujera yaci gaba da shiga cikin jikina, A wurin suka bar kujerar duk suka shiga mota sukaja muka bar asibitin, kuka su Hafsa sukayi tayi tare da tambayar kansu wane irin laifi nayi wanda har hukuma bata ragamin ba ina kwance a gadon asibiti, sunsha kuka har sun godewa Allah daga ƙarshe suka haƙura suka tafi gida… Daga maƙabarta Dikko basu dawo gidan rasuwa ba gida suka wuce kai tsaye, tun a get na biyu ya sauka tare da cewa zai shiga yayi bacci , Al ‘ Ameen yace ranka ya daɗe bara muje get in ƙarshe sannan mu sauke ka amma daga nan ai zakasha tafiya, ba tare daya kalli Al ‘ Ameen ba yace nan zan sauka ya ƙarasa maganar tare da kallon Al ‘ Ameen , tuba nake ranka ya daɗe Al ‘ Ameen ya faɗa tare da jan motar yayi gaba… Saida ya daina hango ɓurɓushin motar sannan ya fiddo wayarshi yayi “yan lashe lashenshi sannan ya kara a kunnenshi , bayan wani lokaci yace kuna ina ne ? Magana na cikin wayar yayi sannan Dikko yace ku shigo ta get in baya, yana faɗin haka ya kashe wayarshi tare da kiran wata wayar kuma. Ta baya ya dawo ya bi wata hanya daban , tafiya mai nisan gaske yayi wurin tsitt bakajin ƙarar komai sai motsin tafiyarshi tunda tsakuwowi ne baje a wurin irin wannan fararen wanda idan ana rana har kashe ido suke, idan ya taka sai kaji tsus tsuss ƙarar tafiyar shi , Wata hanya ya bullo sai gashi jikin wani makeken get, masu gadi yayi ma magana suka buɗe motarmu ta shigo cikin gidan, gaba yayi motarmu tanabin bayanshi saida mukayo nisa da get in sannan ya tsaya, shima matuƙin motar tsayawa yayi tare da fitowa Dikko bai mishi magana ba ya shiga mazaunin dirver yaja motar yayi gaba. A bakin ƙofar falonshi yayi parking sannan ya fito yaje ya buɗe ɗakin, dawowa yayi ya buɗe baya inda nake kwance rai hannun Allah, ciro robor ƙarin ruwan yayi ya fara riƙewa sannan ya ɗaukeni ya shiga ciki, a falo ya kwantar dani saman kujera 3sieter saida ya gyara ruwan suka ci gaba da shiga sannan ya fita tare da rufe ɗakin ta waje… Motar ya ɗauke daga bakin ƙofar falon sannan ya ajiyeta a inda suke ajiye motoci, motar ta gidansu ce kuma jami’an suma na gidansu ne yayi amfani dasu… Dawowa yayi tare da rufe ɗakin sannan ya wuce ciki, wanka yayi ya cire manyan kaya zuwa ƙanana, falo ya dawo ya zauna yana jiran lokacin da zan buɗe idona ya haɗa partyn shagalin wulaƙantani, Zama yayi saman kujera wacce take kallona, ba abinda yake tashin shi a wurin saidai yaje yayi sallah ya dawo, idan yazo ya zauna kuwa lokaci zuwa lokaci yakan kalli agogon hannushi sannan ya kalli inda nake kwance, waya kuwa idan an kishi saida ya duba kawai ya latse, Ruwa ma daya ƙare shine ya cire min, bai daɗe da zama ba aka fara dukan ƙofar ɗakin, ɗan latse baki yayi tare da cewa waye ? Dikko buɗe nice, muryar yayarshi yaji miƙewa yayi yaje ya buɗe ƙofar suka shigo cikin falon tare, Salati nayi a daidai wannan lokacin jin muryar Dikko da sunanshi da aka kira, wani irin abu naji ya daki zuciyata, na ƙara lafewa bamma yi gigin tashi ba haka kuma ban kuskura na buɗe idona ba, amma jikina ya mutu murus , zama yayi a saman kujerar da yake itama kusa dashi ta zauna saman hannun kujera sannan tace ina ka samo larabawan daji ? Ta faɗi maganar tare dayin dariya… Banza yayi baice mata komai ba, dariya ta sakeyi tare da jan gemunshi sannan tace dan ubanka bakaji ina maka magana, tayi maganar cikin sigar zaulaya, tsoki yayi tare da cewa ni bana san irin abinda kikemin yayi maganar cikin haɗe rai kamar dai yanda ya saba, kaiji ɗan iska ni zaka ɗaure ma fuska ko mutuwa zakayi na faɗa maka bazan daina janka ba, duk wannan haɗe haɗen fuskar gabana aka haife saida ma nayi aure dan ubanka kazo duniya wane girma zakayi gabana, ko inda take bai kalla ba, kuma baiyi murmushi ba bare tasa ran zaiyi dariya, sansar wauta dai tayi ta nunawa da sakarci amma Dikko tunda yace mata baya san abinda take mishi bai sake magana ba saida ta ƙari rashin wayanta sannan ta taho inda nake kwance… Ko kallonta baiyi ba dan hankalinshi ma yana kan wayarshi amma yana kallonmu da zuciyarshi, tsaye tayi gabana idona da jikina suka ɗauki kyarma da sauri na buɗe ido na kalleta a tsorace sai kuma na kallo inda Dikko yake zaune amma yanzu bayacim cingom maido kallona nayi wurinta kawai sai na fashe da kuka…. Sai yanzu ya ɗago kanshi cikin tsawa yace ki rufemin baki, da sauri na haɗe kukan tare da rufe idona dan wallahi a halin yanzu tsoron Dikko nakeji dan na fara tunanin kila mahaukaci ne amma har yanzu jikina bai daina kyarma ba. Juyawa yayar tashi tayi tai mishi magana da yaren arna { turanci } bansan abinda sukace ba, ɗan ɓata fuska yayi sannan ya ajiye wayarshi shima yayi mata magana cikin irin harshen da tayi masa, Allah ya bata lafiya ta faɗa tare da cewa zan koma wurin momy da Allah kayi ƙoƙari ka shigo, da kanshi ya amsa mata, saida ta ƙara kallona sannan ta kalli Dikko ta sakeyin magana da yaren ɗazu, kyakkyawan murmushi yayi sannan yace ngode ya faɗi maganar tare da ɗauko cingom ya fara ci, abinda na fahimta cin cingom in kila yana da ƙa’ida domin yafi amfani dashi a wasu lokutta wanda shi kaɗai yasan su… Fita tayi daga ɗakin tare dajan ƙofar garam, har yanzu idanuwa na a rufe suke jikina kuma bai daina kyarma ba, tashi yayi yaje ya kulle ɗakin sannan ya dawo ya zauna, cikin kujera ya tura hannunshi ya zauro wata irin zureriyar wuƙa sai kyalli takeyi saboda sabinta, Ke zo nan , kamar ina jira na tashi dan nasan babu wata ke a ɗakin sai ni, da sauri na isa gabanshi na durƙusa cikin tsoro na sauke kaina ƙasa, cikin natsatstsiyar murya yace kalli , ɗago kaina nayi na kalleshi amma ba ido cikin ido ba, cikin murya maisa natsuwa yace mi yasa bakijin magana ? Shiru nayi naci gaba da lissafin “yan yatsu na, bana san ina magana ina maimaitawa, raina yana sauri ɓacin ne , banda haƙuri zuciyata a kusa take ina tambayarki kawai ki bani amsa… Mi ya haɗaki da Muntari kikayi mishi vidio ? Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji kardai Alhaji ya nunawa Dikko vidion nan, Dikko kuwa ɗoro tsinin wuƙarshi yayi daidai saitin maƙoshina, wanda ya shaƙeni a gaban mutane lallai zai iya kasheni tunda babu mai ganinmu sai Allah, ina san ganin idonshi domin ta nan ne kaɗai zan iya gano idan Alhaji ya bashi labarin vidio, Ɗan kartar min wuya yayi da wuƙar tare da cewa ke nake sauraro, cak na ɗauke numfashina tare da kallon kwayar idonshi sannan nace waye Muntari ? Na tambayeshi ne dan san gano ko gaskiya ne ? Da ƙafarshi ya takamin baki sannan ya halbi daidai saitin hancina har saida jini ya fita. Ƙasa ƙasa yayo da wuƙar daidai saitin ƙirjina inda daya burma min ita tawa ta ƙare, cikin kuka na riƙe wuƙar tare da cewa to yanzu kuma laifin me nayi maka ? Na ƙarasa maganar hawaye na kwarara daga cikin idona, shima hawaye ne kwance a cikin kwayar idonshi cikin damuwa yace saki wuƙar kinji, sakin wuƙar nayi sannan yace zaki iya kasheni ? Cikin rashin fahimta nace kamar ya zan iya kisa bayan nasan ba abune mai kyau ba ? Dikko yace tou mi yasa kika zaɓi zunubi mafi muni a rayuwarki ? Kin kuwa san illolin dake tattare da zina ? Kinsan bala’en ta kinsan matsalolin da take haifarwa ? Kina ƙaramar yarinyarki ki tunkari mazan bariki, kinsan bala’e kuwa irin na mazan bariki ? Kinsan haɗarinsu ? Mazan bariki basa taɓa jin tausayin macen bariki kuma basa tattalata basu san darajarta ba haka kuma bazasu taɓa raga mata daidai da ɗigon kwayar zarraba bariki ta fito kuma shi za’ayi da ita tunda sunsan idan sun lalataki gobe ma wata zasu nema, kinga kuwa da wannan bala’e da kika bashi gaba kawai gara ki sokawa Dikko wuƙa ki huta ya ƙarasa maganar tare da miƙomin wuƙar…. Kallonshi nayi amma banyi magana ba, murmushi yayi tare da ciro cingom in bakin shi yace na ƙoshi ko zaki ci ne ? Banza nayi kamar banji ba , ɗaga kafaɗun shi yayi tare da cewa kin huta 🤷🏻♂, ya faɗi maganar tare da maida cingom inshi cikin bakinshi yabi ni da kallon rainin hankali, Shiru na wasu mintoci sannan yace kinsan abinda yasa nazo dake gidan nan ? Keda ke gidanki idan kinyi magana tou na tankawa Dikko, ci gaba yayi da cewa anan kaɗai zanyi magana dake cikin natsuwa, ki daina hayemin kuma ki rage rashin kunya sannan ki taka a hankali duniya taƙaitacciya ce ga kowa amma babu kamar mace, Ki taka sannu An mata ki faɗamin duk abinda kike so a duniyar nan ko miye zan miki kuma zan baki idan dai zaisa ki kwantar da hankali ki natsu, kuma ba yau kaɗai ba zan ci gaba da kyautata miki daga nan har ranar da numfashina zai bar gangar jikina zanci gaba da kyautata miki dan kiyi farin ciki , ke yarinya ce baki san komai na rayuwa ba, amma zan sake faɗa Allah ya baki sa’ar rayuwa da har kika shigo rayuwata sheɗan kuma ya samu galaba a kaina, tunda ni zina ba aikina bane ban taɓa ba tunda nake wallahi sai a kanki. Kinsha dani kuma kin gama dani har badan duniya, kina da matsayi na musamman da bazai taɓa goguwa a zuciyata ba kuma kin shiga cikin babban tarihin da bazai taɓa gogewa ba a rayuwata har abadan duniya , duk wacce ta shigo kece farko, ni haɗuwata dake na barshi matsayin ƙaddara kuma bansan abinda ubangiji yake nufi da ita ba.Daga ni harke babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare gobe, amma ina riƙonki da Allah kiyi haƙuri kuma ki yafemin akan duk wani abu daya faru tsakanina dake, taɓe bakina nayi tare dayi magana ƙasa ƙasa amma baiji abinda nace ba, Eye ? Ya tambayani tare da yatsina fuska yace banji me kike faɗa ba , Kai tsaye na kalleshi tare da cewa bazan yafe maka ba har abadan duniya, jinjina kai yayi tare da cewa to ba komai Allah yasa rashin yafiyar shine alkairi a rayuwata, kina buƙatar wani abu ne daga gareni ? Ni bana san komai saboda baka da abinda zaka bani ni bakayi kuɗin da zaka taimakeni dashi ba har yanzu, bai sake magana ba, ya ɗauki wayarshi ya kira mutumin daya kawoni yace yazo ya mai dani gida…Ci gaba nayi da zage zagena ƙasa ƙasa yanda bazai iya juyoni ba, anan nayi ganganci ɗaya kunsan masu iya magana sunce idan mutum matsiyaci ne ko an sakashi a tandun man shanu aka tsamo shi haka nan zai fito jikinshi ƙamas. Babu wani ɓata lokaci mutumin ya iso, Dikko yana jin tsayuwar mota yaje ya buɗe ɗakin ki ya dawo ya zauna, da sallama mutumin ya shigo tare da kallona yace muje, tashi nayi tare da ƙara kallon Dikko har yanzu bakinshi yana motsawa cikin salo mai burgewa da ɗaukar hankali yana cin cingom inshi cikin kwanciyar hankali , gaskiya nidai yanamin kyau idan yana cin cingom, amma fa bana ƙaunarshi, bai kallemu ba kuma baiyi mana magana ba hankalin shi yana saman wayarshi, Nayi tunanin DK zaiyi ta haɗani da Allah ko kuma idan yaga zan tafi zai kirani amma ko ɗaya ba abinda ya faru, haka nan naji babu daɗi haƙura kawai nayi na shiga mota muka tafi, 11:30pm a cikin ɗakina tayi min, daga Nana sai Karima kawai a gidan sunata jajantamin. Kuma sune suka faɗamin mutuwar Alhaji, nayi kuka sosai musamman ma a lokacin dana ga vidion dana ɗauka muna ai kata saɓon Allah wani irin imani da tsoron Allah ya tsargamin zuciya tare da ganin kamar mutuwa zanyi yanzu yanzu, Na daɗe ina kukan mutuwar Alhaji a cikin kwanaki ukku daga nan kuma na ɓarar da lamarin zance mutuwarshi muka fuskanci rayuwar bariki….. Bani canzawa, kuma yanzu aka fara…. Muje zuwa…. 26/08/2019 *JAMILA MUSA…* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 20 *_Shafin ga gaba ɗayanshi kyauta ne ga group mai albarka da mutanen cikinshi masu mutunci MEELAT MUSA FANS kuna fa sakani nishaɗi idan kuna sharfi nakanyi dariya sosai domin kuma ilimi ne na musamma ngode sosai Allah ya ƙara haƙuri da juriya, wata ma dai wai cewa tayi Oga Dikko ! Star Dikko ubangidan KWARATA , nafa gode Allah ya baku wayoyi masu riƙon caji da caja mai saurin cika hand set amin… Ni Meelat ko ince JAMILA MUSA nake cewa asha karatu lafiya…._* *_Ina miƙa saƙon ta’aziyya ga “yar uwa kuma abokiyar aiki haziƙar marubuciya Fadeela Lamiɗo ina tayaki jimamin rashin ɗan uwanki Allah ya jiƙanshi ubangiji ya amfani zuri’ar daya bari , Allah ya baku haƙurin rashin sa annabi yasan da zuwanshi, mu kuma Allah ya kyautata namu zuwan bayan nasu ubangiji yasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo….. Am3n ya Allah…_* Duniya sabuwa inji masu iya magana yayin da wani yake kuka a lokacin wani yake farin ciki, kukan mutuwa da jimimmamin rayuwa yana gidan Alhaji Muntari yayin da a gidan da muke haya yau muke shagalewa muna raƙashewa muna cin duniyar mu da tsinke… Zaune muke a saman tabarma yayin da ni nasha riga da zani na atamfa nayi ɗaurin ɗan kwali na irin na sabbin karuwai, na nemi bakin kwalli na daddaɓawa bakina, ga kitso na matan bariki da aka yanyaramin ɗinki rigata ya kameni sosai duk rabin halittun jikina sunyo waje, kallo ɗaya zakamin kasan ni tantiriyar karuwa ce wacce ta anshi lasisin iskanci bada jimawa ba, yanayi na ya fita a cikinsu kana gani na zaka gane nice uwar gidan *kwarata…* Miƙe ƙafafuwa na nayi a saman tabarma nayi zama irin na matan da basu da kamun kai, a gefen damata Amisty ce zaune da jaddawalin sabuwar bariki mai fara aiki a cikin satin nan.. Nana , Karima , Hafsa , Amisty , A ` i da Saude duk suna wurin daga gabana suna ta bani wani irin matsayi na musamman sai kace nayi musu asiri zakayi mamakin yanda suke darajani, yaran nawa dai su shidda ne duk dani mun zama bakwai mune sabbin *kwarata* a cikin wannan zamani kuma nice shugaba kuma zanzo da salon da tarihina bazai gogu ba a cikin tarihin birnin garin katsina… Juyawa nayi gefen hagguna zuga ce ta “yan daba dana ɗauko su haya zan riƙa basu albashi duk ƙarshen wata, dalilina kuwa na ɗaukarsu duk yana cikin labarin, sunsha kitso irin na ɗiyan kafirawa kallo ɗaya dai zakayi musu ka tabbatar sunsha iskanci sun ƙoshi… Saida na gama kallesu tsaff sannan na fara nazari da tunani , na farko dai zamanin ga ya canja rayuwa bata tafiya dole saida ilimi, waye zan samu mai amana da zai riƙa karantawa rubutuwa da fassarawa idan anmin turaci, babu shi zuciyata ta bani amsa tare da cewa karki sake ki yadda da matan bariki dan basu da amana… Kallon Amisty nayi tare da cewa karanto min ina saurarenki, miƙomin takardar tayi , murmushi nayi bance komai ba na ansa, biro na ɗauka na juya bayan takardar nayi rubutu da labarci kamar yanda nayi a police station miƙa mata nayi bayan na gama rubutawa sannan nace haɗa dukansu ki karanto ina saurarenki… Zazzare ido ta farayi ta ƙurawa jaddawalin ido, alifun kanshi idan zaki kasheta bata iya karantawa ba, ganin ta kasa nace tou ki kiyayi kanki da duniya duk baiwar ki wani yafi ki, kece kika rubuta kuma kece zaki yaɗa ba kowa ba, karki damu basai naji abinda ke ciki ba, kije kawai…. Ku tashi muje na faɗi maganar tare da miƙewa tsaye, ɗaki na koma na ɗauko gyale na sannan na fito, gaba nayi zugar daba ta da tasha suka biyoni baya harsu Nana ba’a bari ba, ina gaba suna bayana “yan daba kuma suna gaba cikin siga mai kalar bada tsoro, Gidan da zan siya a cikin anguwarmu mukaje dubawa, ƙaton gida ne sosai akwai ɗakuna birjik ɗaki yakai goma sha ukku, sai bayi guda biyu sai baranda inda ake dafa abinci, amma gidan gidan ƙasa ne irin tsufin ginin da can can, akwai yalwataccen filin tsakar gida…Nidai gidan yamin sauƙi gaskiya ko dan ina matse na siya ? Miliyan biyu aka masa kuɗi babu gudu babu ja baya gaskiya yayi arha dan da a bakin titi yake bazan iya siya ba , daren jiya na bada miliyan ɗaya da rabi, nace zan cika sauran yau idan Allah ya kaimu…. Shine muka zo gani da kowa , gaskiya sun nunamin farin ciki sosai kuma basu nunamin hassada ba, bayan mun gama dubawa muka fito, tunda muka fito yanayin yadda naga anguwar tayi shiru ya taabbatar min Dikko ya shigo… Shine kuwa ɗan iskan , ya fito daga gidan dokunan shi na anguwarmu da yake daga get in gidan zaka iya hango komai na cikin anguwar idan aka shigo santar kuma gidan dokunan Dikko yake kallonka, A tsiyace ya fito kamar yadda ya saba, duk tawagata suka koma da gudu baya suka kauce daga saman hanya yayin da ni kuma na shigo hanya hankali kwance Amisty ta taho da gudu zata jawoni wani mutum ya riƙeta dan a ganinshi biyu babu za’ayi tunda dai ni na tafi sunamin addu’a Allah ya jiƙana, ihu Amisty ta farayi tare da cewa Sultana don Allah karki biye wa zuciya ki dawo ko ki gudu bana so ki mutu yanzu wayyo Allahna, kowa duƙar da kanshi yayi yayin dana tsaya cas kuma Dikko ya sheƙo da gudun tashin hankali, wallahi da bani bace ko wacece sai Dikko yabi ta kanta ya wuce babu abinda ya dameshi… Gab dani ya taka wani irin wawan birki ya fito cikin tsananin ɓacin rai ko mota bai tsaya rufewa ba , hannushi ya ɗaga da niyar marina kuma ko meye ya hanashi ya mareni Oho, ganin ya juya zai koma mota nace Allah ya auna maka arziƙi yau dasai nasa anyi maka fiɗa irin wacce akewa raguna, daka takani ko ka bigeni dasai naga ko waye ubanka a garin nan… Uhum yace tare dayin gajeran murmushi da gefen bakinshi sannan yace ake yarinya ce a tunaninki kama nayi miki da ɗan wa a garin nan ? Dake da babanki da kowa naki da kike taƙama dashi talakawan mahaifina ne , ni kuma abinda na ɗauki talaka takalmi na ne zan takashi yayin da nake sha’awa in kuma cire na jefar a duk lokacin dana gaji da ganinshi, ke abinda na ɗaukeki baki da banbanci da dabbar layya a wurina ina kiwonki ne kafin ranar da zan yanka ki , abinda yasa kuma banbi takanki na wuce ba idan na kamaki zaki basu labari… Murmushi nayi tare da cewa duk takalmi takalmi sunanshi amma ko a cikin takalmin wani baka sakashi yayi maka daidai, talakawa suna taku amma kai da mahaifinka bata tasu kuke ba, duk wadda yace kayi takanshi ne baka zo ba, ba’a saka ka kayi ba’a saka ka daina zakin roba dana sanin mafarauta mugu ɗan gidan mugaye kana mugunta amma kana daɗa suna azzalim baƙin cikin talakawa, kafin ka gama ciwo na ni na gama naka ka saurareni ina dawowa ƙarshen shekaru biyu masu zuwa nan gaba nice maganin tsagerancinka…. Ina faɗin haka ban saurari abinda zaice ba nayi gaba na shige cikin gidanmu da muke haya , tafiya nayi irinta in ka isa wannan ma ka sayeshi…. Murmushin mugunta yayi mai nuni da na gama dake yarinya zaki nemi Dikko ruwa a jallo, juyawa yayi ya koma mota ya fita daga cikin anguwar… Ban daɗe da shigowa gida ba su Nana suka shigo harda ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita police station tayi cikin shege da aurenta, ɗaki suka sameni ina waya da Bello dan tunin duniya na turawa matarshi hotuna anyi tashin hankali na idon duniya kuma shima hankalinshi ya tashi ya yadda zan iya turawa media hotunan, ya yadda zai bayar da kuɗin anjima bayan sallah isha’i.Sannu nayi ma kowa bayan na gama waya nace ku zauna mana, wuri kowa ya samu ya zauna, kallon ƙawar Amisty nayi mai cikin shege sannan nace sannu hajiya, murmushi tayi tare da kallon ƙasa cikin yanayin jin kunya, Ɗan kauda kaina nayi gefe tare da cewa ya akayi da cikin ne ? Ba tare data kalleni ba tace… Wallahi har yanzu bai yadda ba, murmushi nayi tare da cewa bariki da ciki ko goyo wahalalliyar bariki kenan , bariki da tsarin iyali magani ko allura halaka ne saboda baki gwada mahaifarki ba kika tabbatar kina aihuwa ko bakyayi , kallon su Amisty nayi sannan nace tashin farko dai kowa ta nemi gishirinta ta saka a jaka yayin da buƙatar namiji ta gama kammaluwa akanki ki zuba gishiri a bakinki sai ki kora da ruwa,Nana ta tambayeni maganin me ? Kallonta nayi ido cikin ido sannan nace maganin hana ɗaukar ciki, waye ya faɗa miki haka ne ? Murmushi nayi tare da cewa wani feƙaƙƙen dan bariki mai bariki cikin gidan iyayenshi , tunda kuwa har yasan gishiri yana hana ƙaramin ciki zama a cikin mahaifa ai kinsan ya gogu a harkar bariki. Dariya kowa yayi tare da cewa wannan dai ai mugunta ce gishiri ai saida yasa maka cuta , ba tare dana kallesu ba nace shigar wata cutar itace take kore wata, Allah dai yasa mu fita bariki lafiya , kowa ya amsa da amin… Fira dai mukaci gaba dayi daga baya A ` i tace bara suje ita da Saude su anso mukullen shagon da muka kama haya tasan zuwa yanzu sun kammala fenti , sai sun dawo nayi musu suka fita daga ɗakin yayin da Nana da Karima suka fita suma, aka barni dani da Amisty sai Hafsa da ƙawar Amisty matar aure… Kallona Hafsa tayi tare da cewa uwar ɗakinmu idan babu damuwa nikam ina so na tambayeki. Hankalina yana kan wayata ina ganin rubutun da d c o ya turomin nace ina saurarenki yayin dana kanga wayana daidai saitin bakina nace ni aiki nakeyi ko ka kirani a waya, ko kuma kayomin voice note idan na kunna saina saurara , ina faɗa na tura , yayin da Hafsa tace wai miye tsakaninki da DK ? Ajiye waya nayi a gefe na sannan na tattara duk hankalina da natsuwa ta wurin Hafsa nace idan na faɗa miki abinda DK yayi min ke kanki sai kinci ubanshi da yake taƙama dashi yana ma mutane iskanci saboda shi , yau ya taɓo ubana yace talakan babanshi ne , nima kuma na taɓo babanshi a cikin magana na, nuna Amisty nayi tare da cewa duk wanda nace ya faɗamin waye uban Dikko a garin nan ba’a bani amsa idan zaki faɗamin Dikko ko waye ubanshi zan faɗa miki abinda ke tsakani na da Dikko…. Hafsa tace Gwamnan garin nan shine uban Dikko, shiru nayi banyi magana ba Hafsa taci gaba da cewa dole sai kunyi haƙuri sannan kuma kunyi ma Dikko uzuri soyayyar da ake nuna masa a gidansu da yadda ake tsoron mishi faɗa yasa yake ganin duk abinda yayi daidai ne a rayuwarshi , wallahi ba’a dakawa Dikko tsawa ba’a masa kallon banza domin mahaifinshi gani yakeyi kamar duk idan akayi masa zai mutu ne , ya ɗauki soyayyar duniya ya ɗora akan Dikko yana mishi soyayyar da duk duniya babu wanda yake ma irinta a rayuwarshi , fitar da Dikko yake yi da duk wannan iskanci da wulaƙancin da yakeyi ubanshi baisan yana fitowa ba , yasan dai ya baro ɗanshi gida… Cikin jin haushi na kalli Hafsa tare da cewa nikam bazanyi haƙuri ba kuma bazanyi masa uziri ba , can gidansu ya zama dole suyi masa duk abinda kika lissafo amma badai ni ba , wallahi ko Dikko zai mutu saina tozarta shi , saina wulaƙanta mishi rayuwa a garin nan , ki jira zaki ga yanda zanci uban da ya haifi Dikko saina maida shi abun tausayi da kwatance uban nashi kuma duk daren daɗewa saiya gama gwamna ya sauka tunda gidan gwamnati ba gidan ubanshi bane ba… Shiru Hafsa tayi bata sake magana ba , bayan wani lokaci tacewa Amisty ku tashi mu tafi , gaba ɗayansu suka fita tare da cemin sai Allah ya kaimu , ban basu amsa ba na ɗauki wayata naci gaba da abinda ya dameni. Hafsa kuwa kamar ubanta na zaga , tana shiga mota ta fashe da kuka tare da kiran wayar Dikko har ta gaji ta haƙura bai ɗauka wayar ba , daga baya ta yanke shawarar tura masa text duk zagin da nayiwa Dikko komai dana faɗa saida Hafsat ta rubuta ta ƙara da nata dan sharrin ya tafi daidai , bayan ta gama ta tura mishi. Sannan taja motar ta suka bar ƙofar gidanmu… Su Hafsa basu daɗe da tafiya ba su A ` i suka dawo kuma sun tabbatar min cewa shago yayi yanda ake so an tsara shi gwanin burgewa , naji daɗi sosai suma sunyi farin ciki idan Allah ya kaimu gobe lafiya zamu fara fita aiki , saida akayi sallah magrib sannan suka tafi gidajensu. Bayan sallah isha’i kamar yanda Bello yayi alƙawari ya kawo min kuɗi , a gurguje ya bani ya tafi dan yacemin suna da wasa jiranshi akeyi , a daren nakai cikon kuɗi kamar yanda nayi alƙawari zan bayar a gaban shedu aka rubuta takarda aka bani …. Umar ne durƙushe a gaban Dikko cewa mai gida kaga dan Allah tunda kazo gashi har zaka koma gobe don Allah kafin ka tafi ka taimaka ka siya gidan wallahi matar tana buƙatar taimako, Umar yana magana amma hankalin Dikko yana kan saƙon Hafsa , a fili yayi dariya tare da cewa rigima kenan Allah ya baki sa’a akan duk wani kudirin ki akaina An mata , murmushi yayi sannan yace Umar ni babu abinda zanyi da gida , amma nawa ne kuɗin sai in bashi ayi mata aikin… Ba’a mugun sarki sai mugun bafade , kuma wani abu za’a bashi a cikin kuɗin gidan idan an siyar dashi, dan haka ya gyara zama tare da cewa mai gida dan Allah tunda dai yafi so ka siya ka siya ɗin kawai , kila gidan ne ya gaji dashi tunda da taimakon yake so da zaice ka taimaka mishi. Dikko yace tou tunda yanzu yayi maganar siyar da gida ai kowa yasan taimako yake nema insha Allah kafin in tafi zan baka ka bashi , Umar yace mai gida abinda yasa nace ka siya gidan kusa da gidajen daka siya ne kaga idan ka siya sai shima a rushe maka a haɗe wuri ɗaya, Baiyi magana ba sai ƙara kallon text in Hafsa yake yi yana mamakin ɗabi’u irin na An mata da ba gobe zai tafi ba dasai ya ƙara zuwa ya jawota faɗa kuma yanzu dare yayi dasai ya firgito mata hankali , lallai zai haƙura ya riƙa waya da Hafsa dole kodan dan ya riƙa jin halin da Sultana take ciki. Umar yace mai gida kayi shiru baka ce komai ba , kallonshi Dikko yayi tare da ajiye wayar shi gefenshi yace wato so kake in ƙara baƙin jini ko ? Cikin rashin fahimta Umar yace wurin wa zakayi baƙin jinin ne ? Ajiyar zuciya Dikko yayi tare da kwantar da bayanshi jikin kujera lumshe idanuwanshi yayi cikin shauƙi sannan yace wai An mata ne tace zataji min mutunci bayan shekaru biyu masu zuwa, Ya ƙarasa maganar yana murmushi , Umar yace haba ranka ya daɗe ina ma zata ganka ? Kafin shekaru biyun masu zuwa kayi mata tazarrar da baza ta sake ganinka ba har abadan duniya , kai babbar ƙaddara ce da kayi nisa da tazara ga duk wani ɗan ƙaramin sakarai , ka siya gidan kawai ka manta da sha’aninta me zata iya maka ne ? Buɗe idonshi yayi tare da cewa baza ta iya min komai ba kuma badan inajin tsoron tayimin ba kawai dai tana bani tausayi ne…Umar yace bata da kunya ta raina hankalin mutane ka daina tausayinta shegiyar kanta ce , Dikko yace ba itace shegiya ba nine shegen barni dai da Dikko take wasan , zan bada kuɗin gidan na siya , wani irin farin ciki Umar yayi tare dayi ma Dikko godiya saida ya koɗashi sosai sannan ya fita, Fitar Umar Dikko ya ɗauki waya ya turawa Hafsa saƙo cewa shifa baima gane yarinyar da take magana ba , tayi masa bayani na yadda ya sani ta tuno masa asibiti da dai duk wani abu daya shiga tsakanina dashi Dikko yace sam bai ganoni ba amma idan tana da hotona ta tura mishi , Hafsa tace bata da hotona amma zamu haɗu da safe insha Allah zata ɗauko masa ni ya kwantar da hankalinshi , Dikko yace ai dama hankalinshi a kwance yake amma ya zama lallai zai koyamin hankali , Tunda gari ya waye muka sha gayunmu kamar yanda muka tsara , motoci biyu aka ajiye a ƙofar gidanmu ɗaya ta Hafsa ɗayar kuma tawa ce sai kenap ɗaya wacce “yan dabana zasu riƙa amfani da ita kuma ni na siyi , Dukanmu a ƙofar gida muka fito , muna ƙoƙarin shiga mota mai gidanmu da muke haya yazo bayan mun gaisa yace ya siyar da gidan nan saboda haka duk abinda muke so zuwa jibi mu kwashe kayanmu, Cikin ɓacin rai nace wai miya sa kuke abu babu adalci a rayuwarku ? Kai kuma nawa ya baka ya siyi gidan dan nasan za’ayi haka tunda har yaga gidan dana shiga nasan wallahi saiya siya , sakaran banza matsiyaci dashi tou idan ka ganshi ka faɗa mishi nayi gidan zama idan yanajin shi wani mai kuɗine yazo ya sayi anguwar nan duka… Ina faɗin haka nace ku shige muje , gaba ɗayanmu kowa ya shiga mota , Hafsa ta tuƙa nata , tawa kuma driver na samu saboda har yanzu ban iya mota ba , zugar daba ina kuwa suka shiga napep muka tafi, ashe duk abinda na faɗa Hafsa vidio tamin ta turawa Dikko dan ya gani da idonshi ya kuma ji ina faɗa da bakina , ni kuma bansan anyi ba tasan idan ya gani da idonshi dai zaici mutunci na yadda ya kamata bansan abinda ke cekin zuciyar Hafsa akaina ba… 28/08/2019 *JAMILA MUSA* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 21 Cikin farin ciki muka isa bakin shagonmu wanda yasha fenti kuma aka gwagwaɗa masa tambarin *kwarata* , tsayuwarmu da fitowarmu shine ya jawo hankalin al’umma masu wuce da wanda suke zaune saboda munzo da sabuwar shiga mai matuƙar bada al’ajabi a karon farko da ta zama abin kallo ga jama’an gari… Takardun da aka gurzo wanda yake ɗauke da tallar karuwancin mu nasa “yan daba suka raba titi biyu duk motar da zata wuce aka ci gaba da basu babu sauƙi babu sauƙaƙawa ! Bakin shago mu mata muka koma muka jera layi amma babu wacce ta zauna tsaye muke , Nana da Karima suna daga gefe suna kallon ikon Allah , Waya Hafsat ta fiddo ta fara latse latse daga baya kuma sai naga ta koma gefe guda tana waya , ta ɗauki tsawon lokaci bata gama wayar ba haka nan kawai naji na tsargu da wayar , bayan ta gama sai ta goge number data kira… Ƙurawa Hafsa ido nayi harsai data kama kanta , tabbas akwai cuta a tare da rayuwar Hafsa akwai abinda take shiryawa ko kuma take so ta aikata idan kuwa na ganota da wani laifi na cin amana babu abinda zai hana na tona mata asiri, Yana gama waya da Hafsa ya buɗe saƙon da tace ta turo mishi , ɗan soɓaro baki yayi irin na sakatattun “ya “ya sannan ya cire vidio ya ɓoyeshi a gellery vault bayan ya gama gani… Saman kujera ya zauna ya saka takalmi har yanzu bakinshi a soɓare yake , saida ya gama sannan ya kalli Al ‘ Ameen yace mu fara zuwa ta wurin An manta sannan mu wuce don Allah , Al ‘ Ameen yace mai gida da Allah ka fita hanyar yarinyar nan , murmushin Dikko yayi sannan yace wallahi sai anje idan baza kuje ba sai ku jirani ina dawowa , yana faɗin haka yayi gaba , Al ‘ Ameen biyo bayanshi yayi ƙaramin yaron daya girma kawai zai riƙa juya su dandai suna ƙasansu…Da sauri ya wuce Dikko ya buɗe mota , ɗan ɓata rai Dikko yayi sannan ya shiga ya zauna tare da kwantar da bayanshi saman lallausan kujeran motar , wayarshi ya ciro yayi mata kyakkyawan riƙo da duka hannayen shi biyu , sannan ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya yake faɗawa Hafsat yana zuwa yanzu babu daɗe wa zaizo mata bankwana ! Wata irin kururuwa Hafsa tayi ta farin ciki sannan ta koma motarta da gudu , ƙara barbaɗa powder tayi tare da ƙara shafa turare sosai , sannan ta gyara ɗaurin kallabinta ta fito… Kallon mamaki nake ta bin Hafsa dashi anya yarinyar nan bazan zameta daga harkata ba ? Tafiyar nan kuwa zata tafi kodai in fita inyi harkata ni ɗaya ? Ina wannan tunanin zuƙa zuƙan motocin Dikko sukayi parking a ƙofar shagon mu… Cikin rawar kai Hafsa ta tashi tayi wurin motar Dikko , ƙafarshi ya ɗora saman murfin motar , kafin Hafsa ta isa wurin ya zura hannunshi aljihu ya ciro cingom , a daidai lokacin da Hafsat ta isa wurin motar , ko inda take bai kalla ba ya cire cingom inshi a cikin takaddar shi , Tahowa ya farayi zuwa wurina tare da ɗora cingom in saman “yan yatsunshi na hannun haggu ya daki tafin hannunshi na haggu da hannun shi na dama , buɗe bakishi yayi cingom in yayi tsalle ya shige , Ɗan tsuke bakinshi yayi kamar zaiyi kiss sannan ya lumshe idanuwanshi tare da nuna yanayin kamar abin harin sumbatar nashi yana kusa dashi , muah ya saki kiss a daidai lokacin daya tsaya gabana yaja kujerar rober ya zauna , sai yanzu ya fara tauna cingom ɗin cikin izza da nuna shi wani isashshe ne , ɗago ƙafarshi yayi ya biyo da ita ta saitin fuskata kamar zai takamin fuska naɗan ja baya , murmushi yayi tare da ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya :• Robar ruwa Al ‘ Ameen ya miƙowa Dikko bayan ya zauna , ɓalle murfin robar ruwan yayi yakai bakinshi yana kallona , shan ruwan yayi sannan ya cika bakinshi dashi ya miƙawa Al ‘ Ameen robar ruwan , murmushi yayi da gefen bakinshi sannan ya fara bultso ruwan daga bakinshi suna watsowa saman fuskata… Ƙoƙarin tashi na farayi dan banda lokacin Dikko a yanzu sai bayan shekarun dana iba , ina ƙoƙarin tashi ya maidar dani ya zaunar da ƙafarshi nayi na tashi na kasa saida ya gama watsa min ruwan sannan na buɗe idona daya cika da hawaye na kalleshi , Murmushi yayi sannan yayi magana cikin sigar lallashi haba ke ko an mata komai saurin kuka ke baki san wasa ba ? Karfa ki ɗauki abin da zafi albarka na saka miki , kin zageni tass amma zagin yamin daɗi bayan shekaru biyu idan muka fara farautar juna a ranar zaki gane Dikko ba zakin roba bane , zakin gaske ne farin ciki mafarauta , maganar dana faɗa mishi jiya, cewa zakin roba dana sanin mafarauta, ci gaba yayi dacewa dani dake duk wanda ya fasa , ya jinjina kainshi tare da nunani da hannu , Tura kujerar da nake zaune yayi da ƙarfi da bango bai tareni ba babu abinda zai hanani faɗuwa , Al ‘ Ameen ya kira da sauri yazo tare da miƙo mishi wata “yar ƙaramar jaka tashi yayi ya duƙo kusa dani sosai lumfashin shi yana sauka saman jikina , saman jikina ya ɗora tare da cewa ga cingom nan zai isheki amfani daga nan har zuwa lokacin da zamu fara wasa , ɗan taɓe baki yayi tare da kallon wani wuri daban sannan ya juyo ya kalleni da magana zaiyi kawai sai fasa… Miƙewa yayi ya juya ba tare daya sake cewa komai ba , bayanshi Hafsa tabi saida ya shiga mota ya zauna sannan yasa Al ‘ Ameen yayi rabon kuɗi wa duk wanda muke tare dashi har “yan dabana saida Dikko yasa aka basu kuɗi amma nidai bai bani ba kuma ban damu ba saboda dama ni basu nake jira ba ! Al ‘ Ameen yana gama rabon kuɗi ya koma mota , har yanzu Dikko ni yake kallo gilashin saitin shi Al ‘ Ameen ya ɗage zuwa sama sakamakon da yake ƙasa , bai daina kallona ba har Al ‘ Ameen yaja motar suka tafi ,Goge fuska ta nayi da hannu na , sannan na buɗe jakar da Dikko ya ajiye a gabana , irin cimgom in da yake amfani dashi ne sai farar takarda da akayi rubutu a samanta , suke nan a cikin “yar jakar , ban buƙatar dubawa sabona nasan gani kawai zanyi bazan iya karantawa ba, kuma babu wanda zan ba ya karanta min saƙon Dikko daga nan har lokacin da zan iya karantawa da rubutawa…. Tunda Dikko yayi min wannan wulaƙancin ban sake magana ba har aka gama raba takardunmu muka koma gida ban sake magana da kowa ba , kuma tunda nayi wanka na shiga ɗaki ban sake fitowa ba saida gari ya waye ‘ Bayan na gama duk abinda nakeyi na fito tsakar gida na zauna saboda ba yau zamu fara fita ba sai an fara kira a waya lokacin zamu tabbatar da cewa tallarmu ta samu karɓuwa a wurin jama’an gari, Nana na gani riƙe da kwalar rigar mijinta tana zazzaga jikinta irin abin nan da yara keyi idan suna faɗa , zama nayi ba tare dana kalli inda suke ba amma hankali na da kunnuwa na suna wurin su , wallahi sai ka sakeni kalmar da naji ta fito daga bakin Nana kenan kuma har yanzu bata saki rigar mijin ba. Audu yace ba ƙin sakinki zanyi ba amma sai kin faɗamin abinda nayi miki wanda yasa kike so na sakeki ! Nana tace lallai bama ka da kunya da har kake tambayar abinda kayi , tou na gaji da zaman cida kaina zaman wahala zaman kunci kullin muna can barbaɗe kayanmu a saman kai bama ƙerau bama sabuwar anguwa zama gidan haya , tou wannan aure dai a sahalewa juna uban kowa ya huta… Daga inda nake zaune nace Audu wai duk meya haɗaku ne wai ? Ku kullum faɗa ke Nana kamar kece kaɗai matar aure a gidan nan ? Duk wadda kika gani da mijinta haƙuri takeyi ko suna wani saɓani basa fitowa tsakar gida ke kullum dake da mijinki kamar abokan faɗa ? Gaskiya ki daina wannan rayuwar kece ƙasan Audu dole sai kin kiyaye idan har kina san ganin daidai a rayuwarki. Sakar mishi riga kizo kiji wata magana, babu musu ta sake rigar mijinta ta taho wurina, shi kuma Audu fita yayi ba tare daya sake cewa komai ba, A ƙofar gida kuwa A ` i ce ta tare Audu bayan gaisuwa tace mishi naji shiru ya kamata kayi wani abu don Allah , zama Audu yayi a saman dakali sannan yace ki ƙara haƙuri , murmushi A ` i tayi tare da cewa ba komai Allah ya tsare ya dafa maka akan duk lamuranka , da amin ya amsa sannan ya wuce ita kuma ta shigo cikin gidanmu… A ƙofar ɗakina A ` i ta samemu ina bawa Nana shawara , amma tana zuwa gaba ɗaya ta jagula komai ta ida firgita Nana har na kasa gano gabanta bare bayanta, Ajiyar zuciya nayi tare da bin A ` i da kallo ban sake magana ba ina dai jinta tana ta ɗora Nana a hanyar banza ita kuma tana ta karɓewa dan a ganinta shawarar A ` i itace mafita a gareta , Ƙawar Amisty da tayi ciki suka shigo da sallama ita da wata mata , inda nake zaune suka nufo gaisawa sukayi dasu Nana sannan sukace wurinki muka zo , miƙewa nayi tare da cewa ku shigo na faɗi maganar tare dayin gaba suka biyo bayana ! Wurin zama na basu sannan nima na zauna muka gaisa , bayan gaisuwa ƙawar Amisty tace Sultana kin ganeni kuwa ? Murmushi nayi ban bata amsa ba , taci gaba da cewa idan da hali nima zan shiga ƙungiyarki , ga ƙawata itama zata shiga, kallo nabi su dashi bayan wani lokaci nace ita ƙawar taki tana da aure ne ? Dukanmu matan aure ne , Ni suna na Fadeela inji ƙawar Amisty mai cikin shege , sai kuma ta nuna ƙawar da suka zo tare tace ita kuma sunan ta Zalifa , saida na ƙara kallesu tsaf sannan nace miye dalilinku na shiga wannan ƙungiya … ? Wacce aka kira da Zalifa tace wato ina da wata damuwa ce ta musamman wacce bazan iya biyanta ba ko cika burina ba dole saina shiga wannan ƙungiya mai albarka , ina so na samu goyon baya da taimakon tantiran dake cikin wannan ƙungiya ,Murmushi nayi sannan nace wannan wace irin damuwa ce ? Gyara zama Zalifa tayi tare da cewa wato ina da wata maƙociya wacce na ɗauki amana da yadda na bata , bana ɓoye mata sirrina ko kaɗan .Wata rana ta shigo gidana sai taji muna hayaniya da mijina , bayan mun gama mijina ya fita sai take tambayana abinda ya haɗamu , ban ɓoye mata ba kamar yadda na saba na kwashe komai na faɗa mata , Na ƙara da cewa bansan abinda nayi masa ba duk abinda bai taka kara ya ƙarya ba sai yayi ta faɗa akanshi wani lokaci ma hada duka , sai tacemin yadda Allah ya halittani da kyakkyawar siga mai burgewa na kashe aurena zan samu wanda yafi mijina , Nuna mata nayi cewa bana iya kashe aure na amma zan haƙura gaskiya na zauna dashi a haka tunda ina sansa wata rana zai gaji ya daina , sai tacemin ai sai anbar zomo yake zama guza , mazan yanzu da asiri ake ladaftar dasu in bada kuɗi taje ta nemo min asiri inyi maganin mijina. Banji wani komai ba na bata kuɗi masu yawa dan tacemin itama mijinta da yake mata biyayya malamin yayi mata maganinshi , kuma naga yadda mijinta yake mata biyayya sosai kuma yanajin shakkunta dan haka na bata kuɗin nima a samomin asirin in riƙa dawwara mijina… Haka kuwa akayi tayi ta kawo magani ina barbaɗawa mijina a abinci ina zuba mishi a ruwan wanka da abin sha laya ƙarƙashin filo wasu layun a ƙarƙashin gadonshi , tunda safe kafin ya fita na kunna hayaƙi , shirka dai iri iri da ƙazanta nayi ta barbaɗawa mijina yana lashe wa , Haka tayi tamin wayau tana karɓemin kuɗaɗe , murmushi tayi tare da cewa kinsan me ya faru ? Nace mata A , a, tace kwasam sai ta tayar da fitina wa mijinta da yake aurenta , kuma yanayi mata wani irin azababben so yana ƙaunarta fiye da duk yanda zan faɗa muku , amma saida ta kunno masifa ya saketa , har wannan lokaci bata daina kawomin asiri ba , A daren ranar data kawomin magani na zubawa mijina a abinci yana gama ci babu laifin zaune babu na tsaye ya gwagwaɗamin saki 3 ita kuma ta aure min miji gani nan na fito bani ga tsintsu bani ga tarko kinji hukuncin da tayi min….Murmushi nayi kaɗan sannan nace kin aihu da mijin ne ? Tacemin a , a , nace ita ubanta yana raye ne ? Tace min Eh nace ya yanayin samunshi yake ? Tace babu laifi gaskiya yana da rufin asiri , da kyau nace tare da cewa mijinki kina san ki koma gidanshi ko kuwa ya kike so ? Zalifa tace gaskiya bazan koma ba so nake kawai ku riƙe mishi wuya ku jawo shi a cikin ƙungiyarku ku ƙare duk wani tattalin arziƙinshi babu asiri Sultana ki fitar min ita daga gidan… Jinjina kai nayi tare da cewa ni bana asiri amma sharrina da kaidina yafi asiri bala’e a rayuwar ɗan adam , waya na bata tare da cewa sakamin lambar mijinki ki ajiye min ita da lamba 4 , ansa tayi ta sakamin tayi saving kamar yanda nace , bayan ta dawomin da wayana nace babanta a wane anguwa yake ne ? Zalifa tacemin gaskiya bai cika zama ba , nace to karki damu zai zauna dan dole ki samo numbershi ni kuma nayi miki alƙawari su dukansu zamuyi musu aiki … Zalifa tacemin ina da motar hawa idan zakuyi amfani da ita , nace tou yayi kyau mun gode , jakarta ta buɗe ta fiddo kuɗi har naira dubu ɗari ukku tace gashi taba ƙungiya tata gudumawar , godiya nayi tare da ƙwalawa A ` i kira nace ta kawo musu form su cika , Zalifa tace karki damu zan cika anjima idan muka dawo akwai inda zanje yanzu , nace tou babu damuwa sai kun dawo… Miƙewa sukayi zasu tafi nabi bayansu dan rakiya amma ban wuce ƙofar ɗakina ba , anan na tsaya nayi musu addu’ar sauka lafiya , bayan sun fita na koma ɗaki naci gaba da “yan hididdumu na , na tattara kaya saboda zamu tashi daga gidan yau zuwa sabon gidan da na siya , kuma duk nace matan gidan subini mu koma gidana da na siya , sauran ɗakunan da suka rage zan nemo “yan gidanmu na tattara su wuri ɗaya hadashi gogon wato Babana dan nafi so nayi karuwanci a gaban idonshi ya gane cewa ba’ayiwa iskanci haye…. 29/08/2019 *JAMILA MUSA …* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 22 Saida na tattara duk wani abu da nasan ina buƙata na adana shi a ma’adar da nasan bazai wulaƙantu ba , ko wace macen da zamu koma da ita gidan nice nasa aka kwashe kayan kowa aka kai gidan da zamu koma da zama… Kafin azahar har mun gama saboda babu mai gado a cikinsu duk dai katifa ne kuma babu macen dake da ledar tsakar ɗaki saini ! Saida na tabbatar an ajiye komai a mazaunin daya kamata , sannan na shiga wanka , kafin in fito an share gidan ƙwal gwanin burgewa , Hafsa tazo sai kashe sulfie sukeyi ita da sauran jama’ar tamu , Ina fitowa daga wanka tace uwar room maza ki shirya kizo ayi dake kar a baki labari , Amisty ce tace babu wani uwar room uwarmu ce gaskiya a wani cire room kawai mu kirata da mother , shewa sukayi dukansu lokaci ɗaya suna cewa uwa… “Yar gajeriyar dariya nayi cikin sigar barikanci na wuce ɗakina banyi musu magana ba , hotuna sukaci gaba dayi har na gama shiryawa nima na fito !Ina fitowa suka ɗauki sowa domin sun san mother tasu ba daga baya ba wurin iya ɗaukar wanka , banje koya ba kuma babu wanda ya ɗorani nice na koya dakai na kuma ni na ɗaura kaina , banda uwar ɗaki nice uwar ɗakin kaina kuma nice uwar ɗakin wasu , Amisty ce ta bani kujerar roba na zauna, da “yan daba da duk wata kwartuwa mun hallara wurin, bayani na farayi musu kamar yadda muka saba a duk lokacin da muka zauna… Hafsa kuwa ciro wayarta tayi ta faramin vidio kamar yadda naga ta koya kwanakin nan, saboda haka sai nayi shiru yayin da su Amisty suka ci gaba da goga bayani tare da ƙara ƙwarara wa kowa guiwar shi a cikin harkar bariki ! Komai ɓaro ɓaro sukeyi suna sakin maganganu yadda harshen kowa yake iya furtawa, Hafsa kuwa abinda yasa banyi mata magana ba na lura da halayyarta tana da saurin hasala sannan kuma tana da ɗauka da ajiyewa , na ukku kuma abinda na lura da ɗabi’ar ta zatayi tonan asiri haka kuma zatayi cin amana zata tona asirin wanda suke tare idan suka rabu … Ni kuma banda haƙuri idan abu ya ɓatamin rai saina bigi mutum nake samun natsuwa , tou zan ƙyale Hafsa amma nasan irin zaman da zanyi da ita , sannan nikam dai sirri na ƙarya takeyi taji shi kuma anƙi a rabun da ita dan idan har na rabu da Hafsa zata yankamin ƙunya biyu dani da “yan team inta zamu zama abokan hamayya , kuma babu abinda zai hana asirce asirice saboda su sun ta allaƙa da malam tsibbu amma maganinta ɗaya shine zan sace wayarta ta ɓace kwata kwata babu layi babu wayar bare kuma tabi tsohon tarihin jerin kira ta samu wasu lambobi, idan taƙamarta sabko tabbas ni a wurin na kwana , Har aka gama zaman ban sake cewa umm umm ba, bayan an gama duk suka zagayeni akayi ta hotuna , duk wanda yaga hotunanmu yasan ni iskanci na ya fita daban a cikin nasu, yadda suka bani shugabar iskanci tabbas iskanci ya fito a tattare dani… Bayan an gama hotuna muka fito ƙofar gida , saman motar Hafsa nayi tsalle na haye , Hafsa tace bari in ƙara ɗaukarki hoto murmushi nayi tare da cewa ngode , ɗaukana tayi nanma kowa ya ƙara yayyaɓeni sai an mana maza da mata duka Hafsa taci gaba da bamu filasha ! Saida ta gaji da ɗauka sannan mukayi sallama da ita , ta wuce gidansu mu kuma muka koma namu gida , dukanmu a ɗakina muka sauka , har dare suna nan domin Amisty zata kwana wurina ne kuma ma dai ta dawo wurina da zama kwata kwata… Bansan abinda yasa ba kuma ban tambayeta dalili ba , sai dare sosai su A ` i suka tafi gida , Nana da Karima kowa ya shige ɗakinshi muka rage daga ni sai Amisty, addu’a nayi na kwanta bacci , A ɓangaren Hafsa kuwa dan ta wulaƙanta ni ta tozarni a idon Dikko idan ina da sauran mutunci ko ƙima ta kakkaɓe a wurin shi , duk hotunan data ɗauka gaba ɗaya ta tura mishi su , da vidio maganar dana fara da kalaman batsar dasu Amisty sukayi , da kirana da uwar gidan kwarata da akeyi duk saida ta bawa Dikko labari bayan ta gama tura hotunan da vidio ‘, Idan ran Dikko yayi dubu saida ya ɓaci amma bai nunawa Hafsa ba ranshi yayi mishi babu daɗi ba dan baiyi tunanin irin wannan hotunan zata riƙa kawo mishi ba , kawai dai ya ɗauka hotunan Sultana zata turo sai kuma idan tana zaginshi sune kaɗai zata faɗa , amma wannan vidio ya girmi ganin idanuwanshi maganganun sun girmi jin kunnuwanshi , Tabbas zai takawa Hafsa burki da irin wannan vidio kuma zai tsawatar da ita zai gwalashe abun idan ba haka ba irin wannan vidion na An mata zasuyi ta yawo a social media shi kuma idan har haka ya faru baiji daɗi ba, Tunani dai barkatai a zuciyarshi , amma ranshi da zuciyarshi yafi bashi cewa kayi mata magana gaskiya shekaru biyu idan suka tafi a haka kaga zakayi takon saƙa da karuwa mutuncinka martabarka da ƙimarka zai zube a wurin al’umma ga siyasa bata raina abun magana, sai ka tsaya takara zaka gane abun ya zama shirme, shawarar da zuciyarshi ta yanke shine ya fita daga harkar taron yara don asali nasaba da mutunci gidansu ba iri ɗaya ne dana gidansu Sultana ba. Burun duniya akan shi ɗaya tal mahaifinshi ya dogara yayi tsayuwar arfa wurin ganin ya zama mutumin kirki ya fito cikakkan mutum ya kashe kuɗaɗe da yawa wurin ganin ya tsaida ni a saman ƙafafuwana , mutane suna cewa duk “ya “yan da aka ɗauki soyayyar duniya aka ɗora musu gurɓatacci ne , mafiya yawansu basu da tarbiyya , ni kam ba lalatacce bane domin idan nayi duba da yadda nazo… Tsoki yayi tare da kiran Hafsa yayi mata tatas yace daga ita harma Sultana duk zaici mutunci su bayasan maganar Sultana haka kuma itama bayasan ta sake shiga sabgarshi ko kiranshi ta sakeyi ko text wallahi sai yasa an kulle mishi ita , yafa ci uban Hafsa sosai ya ƙara da cewa itama Sultanar ta sake ambatar sunanshi wallahi zaici ubanta ne, saida ya tata iskanci mai isarshi ya kashe wayarshi, Al ‘ Ameen yace mai gida lafiyarka kake ta faɗa , idanuwa jajir Dikko yace Al ‘ Ameen idan aka ce maka na taɓa zina tsakaninka da Allah zaka yadda ? Al ‘ Ameen yace mema yasa kake faɗar wannan maganar don Allah ka daina abinda ma bazai taɓa yuwuwa bane ba… Idon Dikko cike da hawaye yace kasan yarinyar dana shaƙe a asibiti ? Al’ Ameen yace Eh nasanta mai gida , Dikko yace kaga ai yarinya ce sosai ko ? Al ‘ Ameen yace Eh , Dikko yace wallahi da nayi auren wuri ina iya haifar yarinyar nan , amma tsautsayi da ƙaddara yasa na saki wani irin ƙatoton layin da inaji kamar in cakawa kaina wuƙa in mutu kawai in huta, Murmushi Al ‘ Ameen yayi tare da cewa haba mai gida ina kai ina haifo mai shekarun yarinyar nan , da kayi aure kam da wuri baka tsaya karatu ba kuma gashi har yanzu duniyar nemanta akeyi duk wanda kuɗi yayi ma yawa so kawai yake a kirashi ranka ya daɗe , duk dai haka gaskiya baka haifi yarinyar nan ba , tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayoyinshi ya shige ciki , gefen gado ya zauna tare da zagba tagumi ya fara tuno wa kanshi ko shiɗin waye….. *_WAYE DIKKO…?_*Dikko Umar Kurabau shine cikaken suna na… Mu cikakkin asalin “yan cikin garin katsina ne , bamuyi rayuwa a ƙauyen kurabau ba haka mahaifina da kakana basu rayuwa a wannan ƙauye ba , amma kakan dadyna shine yayi rayuwa a cikin wannan ƙauye dake ƙarƙashin kauyen rimi local government… Mutane ne masu cikakken arziƙi da wayewa kuma sarautar kauyen a gidansu kakana take wacce suka gada suma tun iyaye da kakanni , ko a wancan lokacin mutanen kurabawa tuni su wayayyu ne kuma tuni suka waye da ilimin zamani ! Kakan dady na duk da yake bakauye baya da kidadanci haka kuma bashi da jahilci , wayyen tsoho ne da yasan rayuwa , kuma tsohone mai cikakken ilimin addini, Abinda ya kawo kakana cikin birni shine neman ilimin zamani , kuma shima mahaifinshi shine mutumin daya fiddoshi dan neman ilimi bayan ya tabbatar daya haddace al’kur ani mai girma a saman kanshi kuma yasan littafai na musulinci . Karatun boko bai wani bashi wahala ba saboda yana da ilimin addini sosai , saida kakana ya gama karatun sikandire sukul { Secondry school } ya koma kauyen kurabau, Mahaifinshi yace tunda ya ɗagawa ƙauyen na wasu shekaru ya haƙura kawai ya koma cikin garin da zama , dan a samu ci gaban rayuwa ! Mahaifinshi da kanshi yazo ya nema mishi wurin zama sannan ya bashi kuɗaɗe ya kama kasuwanci ya nemi abinda zai dogara da kanshi, dan a wancan lokacin idan mutum yayi secondry sch anan yake tsaya dan duk wanda yazo wannan matakin gani ake an ƙure. Allah kuwa ya saka ma nemanshi albarka dan kano yake zuwa sarin atamfofi da shaddoji da yadika ,kafin shekar ya zagayo abubuwa sun fara canzawa domin Allah yasa ma neman albarka kuma Allahn ya yaddar mishi ! Dan ubangiji dayace maka zama zaka zama…. Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin ƙanƙanin lokaci sunan Dikko Muhammad wato kakana ya fara zagawa a cikim garin katsina dan zuwa wannan lokaci ya baza yara suna neman mishi kuɗi dan kasuwar tafi ƙarfin mutum yanzu, kuma mutum ne shi mai kauta , Shi kuwa Muhammad baban Dikko wato kakan babana ganin dukiya ta fara yawa hankalinshi ya fara tashi gashi har yanzu Dikko baiyi auren farko ba , kuma zuwa wannan lokaci ya rage zuwa gida dan sai yayi wata shidda ko fiye da haka baije gida ba , idan yaje malam yayi mishi magana yana daɗewa baizo ganin gida ba sai yace abubuwa sunyi yawa yanzu ma dakel ya samu yazo, Ganin haka yasa malam ya yanke shawara aura wa Dikko mata kuma “yar nan cikin ƙauyensu dan malam yace idan “yar gida ce yake aure dole za’a riƙa ganinshi ko baizo dansu ba zaizo dan matarshi,Haka kuwa akayi malam ya aurowa Dikko mata bada saninsa ba yasa aka kawo mishi amarya har katsina, saida aka kawo amarya akayi masa bayani malam ya auro masa ita , bai wani ji komai ba yace Allah ya basu zaman lafiya, Zaman lafiya sukeyi da matarshi Binta saboda matace mai haƙuri da kuma kauda kai da duk wani abu na rayuwa , saboda itama sai tayi wata nawa bata ga Dikko ba dan shi ba auren yake saurare ba duniyar kawai yake nema ita kuma Binta bata wani damu ba tunda ci da sha har sutura bata rasa ba , idan Dikko yazo mata as miji zasuyi rayuwar aure idan baizo ba babu abinda ya dameta… Haka dai rayuwarsu taci gaba da tafiya , kuɗin Dikko kuma har an fara zarginsu a cikin gari cewa tsafi yake yi , dan shima kanshi zuwa yanzu baisan iyakar abinda ya mallaka ba , koda Binta ta samu ciki gida Dikko ya maida ita ta aihu , tunda ya kaita bai sake komawa ba har ta aihu ta gama wanka baije ba, abinda ta aifa ma bai gani ba babanshi yayi duk abinda akeyi ma duk macen data aihu komai anma Binta da ɗanta da yaci suna Ummar wato mahaifina… Har Umar ya iya tafiya Dikko bai dawo ba kuma bai aiko ba yana can yana neman duniyarshi danshi matan ma basu ne gabanshi ba kuɗi kawai, baisan komai ba kuma baya gane komai sai naira , abun ƙauye aka fara tira iyayen Binta su kashe auren su mayar da Baban Dikko ɗansu tunda dai ɗanshi ya zama ɗan iska, Binta kuwa ta kifa kanta ƙasa tace ita duk duniya babu wanda ya isa ya kashe mata aure, Ganin za’a kashe mata aure dole yasa ta saɓe abunta ta dawo wurin mijinta , koda Dikko ya dawo gida ya sameta yaji daɗin dawowanta yace tayi haƙuri abubuwa ne sunka sha mishi kai da yawa da yawa shi yasa baizo ba , tace ba komai da yake itama bata da matsala. Can ƙauye kuwa da aka tabbatar da Binta ta koma wurin Dikko iyayenta sunsha zagi da tirr da Allah wadai da halin ɗiyarsu, basu da yadda zasuyi tunda suma basu san Binta zata koma wurin Dikko ba dan batayi shawara dasu ba ta tafi. Tun lokacin da Binta ta dawo wani abu bai shiga tsakaninta da Dikko ba , ita kanta wahalar gani yake mata dan yanzu kasuwancin nashi ya fara ketarawa , kuma babu damar taje ta faɗa gida dan tun abun baya damunta yanzu harya fara damunta. Yau kam ta hana idonta bacci ko Dikko zai kai safiya bai dawo ba zata jirashi kuma yau za’ayita ta ƙare , koda Dikko ya dawo gida daɗin bakin yayi ma Binta kuma ta haƙura amma kam a daren nan sunɗan caskaɗe dan tunda ta dawo wannan shine haɗuwarsu na farko, Tou haka kwanciyar auren ta koma duk lokacin da Dikko ya kwanta da binta wani rantsetstsen rabo zai fita , adadin yawan “ya “yansu adadin yanda Dikko ya kwanta da ita , yanzu tayi yara bakwai ,Kuma rabonshi da gida tunda ya maida Binta aihuwar Babana bai sake zuwa ba har Binta tayi “ya “ya bakwai , saida itace kaɗai take zuwa, mahaifin Dikko kuwa yayi danasanin kai Dikko birni , Haka rayuwar taci gaba da tafiya saida malam ya rasu Dikko yaje ƙaunye ta’aziyya, mahaifiyarshi kuma tayi kuka da tir da rayuwar birni, da yake shegen wayau ne dashi lallashinta yayi saida ya kwantar mata da hankalinta sannan yace tunda bata da komai a ƙauye zai tafi da ita birni ! Haka kuwa akayi bayan addu’an bakwai suka tattaro suka dawo tare da kakar babana, zaman kakarsu dady ta gano Dikko bata mace yake ba , ta jinjina wa Binta da wannan haƙuri, ita dai batace komai ba tana dai kallon ikon Allah.. Ummar wato Dadyna, yana gama secondry sch Dikko ya korashi ƙasar waje karatu dan bayasan ganin yara kusa dashi, tafiyar Ummar babu daɗewa kaka Dikko ya tsirawa kanshi aure rana guda aka kawo mishi mata biyu shi mai kuɗi, idan an haɗa da binta sun zama 3 kenan.Nan fa haihuwar gasa ta tashi mata sunga kuɗi duk shekara sai an direwa Dikko “ya “ya amma banda Binta dan ita tana mamakin ma yaushe Dikko yake kwanciya dasu sakamakon ita ? Ko kuwa dandai su shine ya auro su da kanshi Oho, Tunda Dady ya tafi karatu Kaka Dikko ya hanashi dawowa , da yaga mai zai matsa mishi saiya dawo ya tusheshi da kasuwa can yace ya nemi kuɗi ya manta da rayuwar nigeria shima haka babanshi yayi mishi. Duk da Ummar yana ɗan farko saida Binta tayi magana a maido mata ɗanta karya halaka cikin duniya , Dikko yace bazai maido ba, shi ya akayi bai ɓace ba da babanshi ya kawoshi birni, dole Binta ta haƙura ta dainawa Dikko maganar Ummar , itama kakar Dady tayi harta gaji Dikko bai dawo da Ummar ba, Kwanci tashi asarar mai rai , abubuwa da dama sun faru a ciki kuwa hada rasuwar Kakar Dady , Dady kuma yayi shekaru kusan 15 yana ƙasashen yahudawa, tun yana marmarin gida shima harya goge ya janye zance gida a rayuwarshi. Shi kuwa Dikko yanzu hankalinshi ya tashi saboda mata sun tara tulin ɗiya sai meeting ɗin kasheshi sukeyi su kwashi dukiya , wannan dalili yasa ya cire Binta a gidan ya sake mata mazauni ita kaɗai daga ita sai “ya “yanta dan ya lura itace kaɗai take masa san tsakani da Allah. Tou wannan dalili ne yasashi ya ɓanɓako dady daga ƙasar waje shi kuma zuwa wannan lokaci baya san dawowa nigeria dan shima ya riga ya kafa kanshi a can yayi kuɗi wanda saida suka tadawa Dikko hankali duk neman duniyarshi, yace Ummar da nasan zakayi kuɗi duniya da na zauna na mori rayuwata ban ba kaina wahala wurin tara abun duniya ba, Dikko dai bai ɓoyewa Ummar komai ba ya sanar dashi cewa mata zaku kasheshi su gaji duk dukiyar daya sha wahala wurin tarawa , dan haka abinda Dikko yayi shine , duk abinda ya mallaka tsakanin gidaje filaye motoci filazozoji Dikko ya kasasu 10 ya bawa Ummar kashi 9 sannan yayi rabon gado da kashi ɗayan daya rage, Duk wacce ta samu kuɗin nan ruɗewa tayi dan wannan kuɗi da Dikko ya bada gado wa duk “ya “yanshi iyakar almubazzarancin mace rayuwar duniya dai ba ƙiyama ba ya isheka, ganin kuɗaɗe a hannunsu kuma sun tabbata babu saura yasa kowa ta tsige aurenta ta kama gabanta… Aure Dikko ya nemowa Dady ɗiyar wani aminishi suma attajirai ne na gaske , babu wani ɓata lokaci suka anshi tayin Dikko bikin bai wani ibi lokuta ba aka daura mishi aure da matarshi Maryam , mai irin sunan Sultana… Dady bai daɗe da aure ba , Kaka Dikko da Kaka Binta sukayi gobara gaba ɗaya gidan babu wanda ya fita , duk wanda suke uwa ɗaya da dadynmu wuta ta cinyesu sun mutu har lahira, Dady yayi kuka na tashin hankali duk mai imani saida ya tausawa Dady, Rayuwar dai haka taci gaba da tafiya , kakana na wurin uwa shine ya cusawa dady ra’ayin siyasa kuma Allah yasa ya shiga siyasar da sa’a domin ya riƙe manya manyan muƙamai dan siyasa tayi dashi kuma tana cikin yi dashi daga baya kuma ya tsaya takarar gwamna kuma Allah ya bashi yaci , Matan dadyna 2 a yanzu suka rage masa dan shima ya ɗan ɗana aure aure dan samun namiji amma Allah bai bashi ba , harya haƙura ya fidda rai Allah yasa ya sameni daga tsakiya dan mata sune samana kuma suke ƙasa na a cikinsu na rayu dasu nake gogayya banda aboki sai mata shi yasa ni ban ɗauki mace komai ba dan duk wani feleƙe da iyayi na mata babu abinda za’a layancemin , zancen cin cingom da duk wasu ɗabi’u na mata duk a wurin “yan uwana na koya, amma bana ɗabi’u irin na “yan daudu kuma bana magana irin na mata… Ina da ilimin addini domin nima sittin ce cikin kaina nasan hadissai sosai duk ƙaunar da ake nunamin da sangarta baisa na zama sakarai ba nasan abinda nake , tunda nake dadyna da mom ina basu taɓa dukana ba babu mai dakamin tsawa kuma babu wanda yakemin kallon banza tunda nake ban taɓajin kalmar zagi akaina ba saida Allah yasa an mata ta shigo rayuwata, itace mutum ta farko data fara zagina a rayuwa. Nima haka tunda nake ban taɓa neman mata ba kuma bana sabgar su akan ta ne na nuna mazantaka na, ni ba sakaran namiji bane ƙaddara ce kawai kuma bansan abinda hakan yake nufi ba , Gashi ta shigomin rayuwa banda isashshen lokacin da zanyi maganinta dan nima babana ya ƙusani cikin siyasa, ya fiddo ne akan wata kujera ta abokinshi daya rasu kuma inaji a jikina nine dan ban taɓa nema na rasa ba tun ina ƙarami duk abinda naso a rayuwata bai taɓa wuceni ba , dan bana san siyasa a rayuwata amma dole sai nayi ta. Mu fitaccin mutane ne muna da cikken asali bama da wani tambari na ɓatanci haka kuma bamu da sata bamu da maita , mu ba ɓoyayyin mutane bane sananni ne kuma fittaci tun zamanin iyaye da kakanni, haka nima sananne ne kowa ya sanni kasancewar ɗa ɗaya tal namiji a wurin mahaifina , shi yasa ban ɓoyu ba domin dady ya ɗaukeni kamar abokinshi baya ɓoyemin komai duk wani samunshi a tafin hannuna yake , ragamar komai a hannuna yake , dan zaka tara matashi kamarni wanda akeji dasu ko sukeji da kuɗi wallahi ka tara matashi talatin maiji da kuɗi da motoci basu Dikko ɗaya duk yawansu wallahi. Daga yau wallahi nayi rantsuwa idan har Sultana ta sake shigowa rayuwata saina keta mata mutunci wanda yafi wanda nayi mata a baya….. Taff wannan shine ƙudirin Dikko , ita kuma bara muji nata .Hafsa kuwa tunda Dikko ya zageta fess take kuka, Ni kuma bacci ɗaya nayi na farka ina tunanin yadda zan hudowa lamarin Hafsa……. 30/08/2019 *MEELAT MUSA* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 23 Har gari ya waye ban sake komawa bacci ba , da safe bayan na gama duk abinda nakeyi na fara kiran lamba 4 , lamba 3 wato d c o kuma na haɗashi da Amisty bana iya wata mu’amula dashi saboda gaskiya baida tsabtataccen baki danni Allah yayi min ƙyanƙyami idan na raina maka tsaftar baki tou na raina maka kuma bazan yadda inyi wata mu’amula dakai ba gaskiya. Lamba 2 wato Bello shi yana nan kuma muna tare har yanzu babu wani abu daya shiga tsakani na dashi saidai ina fereshi yadda ya kamata ina kwalkwalar kuɗinshi babu dare babu rana, daya bani haƙuri ma cewa nayi saiya nemo min Babana sannan zan ƙyaleshi ! Lamba 1 Alhaji ne kuma ya rigamu gidan gaskiya , na goge komai nashi a wayana daga number har vidio babu abinda na bari, Lamba 4 shine mijin Zalifa kuma yanzu shine abun hari na, ɗan wasa na, domin shine zan jijjiga zanyi wasan kura dashi kuma saina lashe kaf tattalin arziƙishi saina cinye komai zan maidashi matsiyacin ƙarfi da yaji, idan kuma yana da rabo akaina tou in sameshi mai tsafta idan dai ɗan gayu ne kamar Dikko zan riƙe mishi wuya ya zama abokin tafiyana… Kiranshi nayi amma har ya tsinke bai ɗauka ba , haka tsarina yake kira ɗaya nakeyi idan ba’a ɗauka ba bana sake kira , idan kuma ya biyo kiran ina maraba dashi , Daga tsakar gida naji Amisty ta luƙaƙa wata irin ashariya irin na shararrin “yan tasha , saida gabana ya faɗi , ban gama saita kaina ba naji taci gaba da cewa na rantse da girman Allah wannan karon bazan bar Sultana tayi haƙuri ba , saita wulaƙanta shi ko waye ubanshi …Da sauri na miƙe na fito tsakar gida jikina sai kyarma yakeyi saboda ni hayani da zage zage ɗimautani sukeyi , ina fitowa na kalli Amisty nace wai mene ne ? Kusa dani Amisty ta matso tace ke wai mu Hafsa zata tonawa asiri , kallon inda Hafsa take tsaye nayi sannan nace wai miye ? Wayar Hafsa, Amisty ta miƙo min tare da cewa shiga kiga cht insu da Dikko , bayan ta tura mishi saƙo ta whatsapp ya kirata tsakanin minti 10 bayan tura saƙo, kiji zagin da yayi miki Mother ƙarshen hukuncin da yayi yasa an rushe shagonmu kuma yace idan dai yana lumfashi kika fito karuwanci yace sai yayi miki wulaƙancin da ko ance ki faɗi kalmar iskancinci da bakinki sai kince kin tuba , Yace zai baki azaba mai azaba ɗaya daga cikin irin azabobin daya tanadar miki shekaru biyu masu zuwa , kuma idan kinyi taurin kai yace zai tafi dake ya ɓatar dake inda babu wanda zai sake jin labarinki daƙiƙiyar banza dake…. Zuciyata ta kawo maƙoshi amma ban nuna ɓacin rai ba nace ma Amisty wai duk inji shi Dikkon yace haka ? Amisty tace imana kinsan dai bana miki ƙarya idan baki yadda dani ba ki samo wani ya karanta miki duk duniya Sultana babu wanda nake ma soyayya irin wacce nake miki , nabar uwa da uba na zaɓe ke , rayuwata da komai nawa sadaukarwa ne a gareki idan ba duk abinda na faɗa miki Dikko ya rubuto ya turo ba Allah ya tsine min albarka ! Murmushi nayi sannan na kalli Hafsa nace to ke Hafsa mi ya kawo har kukayi magana na da Dikko ? Latse banzan bakinta tayi sannan tace niba magana nayi mishi ba shine yayi min maganarki , Amisty tace ke jira kiji zan ubanki ƙarya zan miki ko me kike nufi ne ? Kallona Amisty tayi sannan tace vidionmu ta tura mishi da hotuna kuma itace ta faɗawa Dikko muna da shago inba haka ba ya akayi yasan wurin harya zo ? Hafsa tace tou naje na faɗa Amisty kiyi magani na , ai tun kafin ta gama rufe bakinta Amisty ta rufe ta da duka tana cewa amanar ƙungiya zaki ci dan ubanki , an yadda dake zaki ci mana amana , ko an faɗa miki muma bamu iya karatun da rubutawa ba ? Tana magana tana dukan Hafsa , kokowa har ƙofar gida saboda cikin gida mata sun kasa ansar Hafsa dama su “yan gayu basu iya faɗa ba sai sakata suka iya… A ƙofar gida dakel masu aikin rusa tsohon gidanmu suka raba faɗa , kuma sukayi sasanci cewa da Allah mu daina faɗa ayi haƙuri , candai ake basu haƙuri niko wuri na samu na zauna wai nice daƙiƙiya , kamar ni abokin hamayya zai faɗa cewa ni daƙiƙiya ce , wallahi wannan kalmar tafi komai muni a rayuwata , itace kalmar da aka taɓa faɗamin ta ɓatamin rai kuma tamin ciwo ta kartar min zuciya har sai da naji masassara ta saukomin , wai ni Dikko yace ma daƙiƙiya , gumi naji yana bimin kumatu ina kai hannuna na shafo kunci na naji lema , ganin ruwa a hannuna ya tabbatarmin da kuka nakeyi….Bayan an raba su Amisty shine suka zo kusa dani suka zauna hada Hafsa dan kunsan su “yan duniya basu fushi duk yadda aka cakusa dole sai an koma an jone , kowa tambayata yakeyi abinda yasa nake kuka amma banyi magana da kowa ba , Hafsa ce ta fara bani haƙuri akan abinda tamin murmushi nayi amma ban mata magana ba , Muna na zaune ƙofar gida a saman dandamali har su Nana mun jera layi babu mai mayafi a cikinmu mundai fito karuwan na zahiri da zahiri, saboda wancan hannu duk Dikko ya cinyesu babu gida ko ɗaya filin wurin ne kawai saboda duka wurin ya sayeshi harya tsallako gefen gidanmu yaci gaba da siyewa. Muna nan zaune muna jiran tsammani Umar yazo , yaron Dikko wanda ya yakaini gidan Alhaji , yana fitowa daga mota ni ya fara gani , shegiyaaaaa , ashe da kina nan ina kuɗi na da kika cinye “yar damfara ? Murmushi nayi da gefen bakina sannan nace zaki ya shiga gaban ɓauna , idan dai wanda ya mutu zai dawo tou ka kwantar da hankalin ka kuɗinka zai dawo aljihunka babu ɓata lokaci , Aiko kuɗina baza su ciwo wurinki ba sai kin bani abuna , dariya nayi tare da cewa wallahi basu ansuwa wurinka bakai ba kayan banza ko Dikko naci gabanshi naci uwarshi naci ubanshi a iskanci ai shine dai kake taƙama dashi ko ? Kusa dani Umar yazo yana ƙoƙari wanka min mari na riƙe hannunshi tare dayin wani irin lafiyayen fito , babu ɓata lokaci “yan dabana suka bayyana , kallonsu nayi tare da cewa ku shiga dashi ciki ku bashi ruwa yasha , ɗaukarshi sukayi sama sukai cikin gida dashi , saida suka bashi kashin bala’e sukai mishi lullusar fitar hayyaci , saida suka tabbatar jikinshi yayi tsami sannan suka tillo banza ƙofar gida… A lokacin ni kuma ina saman mota ta nayi kwanciyata , yayin da Amisty ke gefe na tana shan sigari A ` i da Saude kuma suna zaune kan dakali suna lido, Nana da Karima kuma nace su koma cikin gida saboda su matan aure ne , Dakel Umar ya miƙe ya shiga motarshi yaja ko masu aikin da yazo dubawa bai duba ba ya tafi , bai zame ko ina ba sai wurin “yan sanda , muna ƙofar gida zaune muka ga motar “yan sanda , wai anzo kamani , Bayan mun gama magana dasu nace su jirani ina zuwa , cikin gida na koma na shirya cikin shiga ta alfarma, wata riga na ɗauka na saka a leda bayan nasa anyi mata kitar wulaƙanci ga kuma jikina da yasha sahun akaifun Hafsa nasa ta yayyakushe ni dan na shirya ƙullawa Umar sharri na gaske. Dani da Hafsa da Amisty da A ` i da Saude muka tafi domin ni sune sheduna , mu biyu a gaba ukku a baya , cikin mota ta muka tafi saboda itace motar kece raini Hafsa ta tuƙa har muka isa police station, Umar na zaune a waje jini sai bin jikinshi yakeyi tuni ya kira Dikko ya faɗa mishi, Dikko yace da an kamoni a rufeni duk abinda yake zai shigo katsina gobe idan Allah ya kaimu , dan hankalinshi ya tashi da yaga dukan da nasa akayi wa Umar. Office ɗin d c o aka kai case inmu , ga gaske ni kuma gani nazo da kwarata masu biyawa mutum buƙatarshi , dan suma sunyo shiga mai ɗaukar hankali duk namiji mai lafiya ya gansu sai yaji hankalinshi ya tashi , Kujera Amisty ta jawo min na zauna sannan suka koma bayana suka tsaya , shigo da Umar akayi a daidai lokacin da ni kuma na fara gaishe da mai girma d c o , kafin ya ansa gaisuwar tawa Umar ya miƙa mishi waya Dikko ya sake kira domin ya faɗawa Dikko munzo station in , Faɗa Dikko yakeyi tare da cewa bai ce a jira aji abinda ya haɗamu ba kawai rufeni yace ayi , D C O yace ranka ya daɗe ai sai anyi binceke Dikko yace ba abinda za’a bincika umarni yaba d c o a rufeni kawai , d c o zai sake magana Dikko ya daka masa tsawa dole d c o ya dauke wuta , jikina fa yayi sanyi amma ta maza nayi tare da miƙewa na anshi wayar daga hannun d c o nace Dikko faɗa a cikin waya bashine ke nuna jarumta ba , kuma rufeni na kwana a ofishin “yan sanda bashi ne zai nunamin kai cikakken jarumi bane ba , Kaine kaɗai maganin fitsarata idan ka isa kazo kayi magani na basai kasa an kulleni ba , kuma kake cewa kar ayi bincike kasan abinda shi yaron naka yayi min ne ? Cikin ɗaga murya nace tou mutunci na fa zai buɗe kaga yadda ya yayyage min jiki ? Kuma da aka mishi magana cewa yayi kai ka tsaya mishi ya hau duk macen da yaji tayi mishi, kuma D C O ya faɗa maka idan bai yayyageni ba , da sauri Dikko ya rufe idanuwanshi tare da matse gwangwanin maltinar da aka kawo mishi baisha ba , azabar matsa yasa gwangwanin ya fashe maltinar ta watse… Har a zuciyarshi ya yadda da abinda na faɗa mishi dan yasan Umar manemin mata ne na ƙarshe yayin da Umar ke cewa wallahi mai gida ƙarya takeyi kawai naje duba masu aiki tasa “yan daba sukai ta dukana ! Cikin wata irin hayagaga Dikko yace rufemin baki ɗan iska mutumin banza idan na sake jin maganar ka saina ci mutunci ka wallahi , Tausasa murya yayi tare da cewa ba d c o wayar , miƙa mishi nayi Dikko yace da gaske ya yayyakushe ta ? D C O yace Eh ranka ya daɗe , to dole zaice Eh tunda ga sahun akaifa a jikina ya fito sosai, nidai bansan yadda suka ƙare ba D C O yace muje kawai , Muna shiga mota na sauke ajiyar zuciya , kai Dikko ɗan bala’e ne na ƙarshe baida mutunci gaskiya Allah ya rufamin asiri yau da sauro da zarnin fitsari ya hanani bacci , kallon Amisty nayi sannan nace kinji ɗan bala’e da saboda ni zaizo lallai dana yabawa aya zaƙinta , dariya nayi tare da cewa aidai mun daki banza…. Bayan wata ɗaya… A halin yanzu suna na ya fara zagawa a cikin gari, domin dai harkar iskanci ta buɗe mana sosai muna ganin maza daga shiyyoyi da dama , a cikin gidana nan maza ke zuwa su zaɓi macen da suke so a tafi hotel acan ake raƙashewa, yanzu bamu da shago domin Dikko ya saye wurin kuma yasa an rushe shi , tou ina gidana anan nake baje kolin iskanci na dani da yarana…Cikin wannan wata bakin gwargwado kowa ya samu ci gaba na rayuwa Nana namiji yake zuwa wurinta ta kora mishi sharfi akan kayan mata da maza , itama a hankali idonta ya fara buɗewa ta iya gogayya da maza , dan daga ita har Karima yanzu bata mazansu suke ba, A fanni na kuwa ni har yanzu ban samu tsaftataccen namiji kamar Dikko ba , amma idan aka zo tafiya da mace ni nakeyin ciniki namiji ya bani kuɗi kuma itama macen idan ta dawo zata bani kasafi na , tunda kafin a tafi nasan ko nawa za’a baki , na zama kawaliya kenan.. Idan namiji yazo ya duba a cikin matanmu bai samu wacce tayi masa ba ya faɗamin irin mace da yake so ni zan nemo mishi ita walau budurwa walau zawara har matar aure ma , Mijin Zalifa munyi waya dashi amma har yanzu bamu samu haɗuwa ba , yadai bada an kawo min kuɗi masu yawan gaske ta dalilin waya da mukeyi ta ɓatsa dashi , na siyar da motar da Alhaji ya bani nayi ciko na siyi mota ta gani ta faɗa , kuma ni nake tuƙa abuna domin yanzu na iya mota , jikina yaɗan ƙara ginuwa ya kuma goge hutu ya zauna dan dole dan idan baka san gidan da nake rayuwa ba zakace daga G. R. A na fito, na ƙara waye kuma idanuwana sunyi fashewar da duk mutum yayi mamakinshi, Shirye muke cikin shiga mai nuni da mutanen gari ga naku , ma’ana maza ga matan bariki, biki akeyi a gidan ƙanin Babana yana aurar da ɗiyarshi, dan haka nace kowa ya shirya muje , mota ukku mukayi hada Zalifa, mota ta , ta Hafsa sai ta Zalifa sai napep ɗaya ta “yan daba… Tunda mukayi parking idanuwan jama’a ya dawo kanmu, fitowa nayi tare dayin magana ƙasa ƙasa nace gafa “yar gado nayi gado amma kuma har na zarce… Ina gaba tawagar karuwai suna bin bayana , duk wanda ya ganni sai ya kauda kai tare yin gulma ta , a cikin gidan biki kuwa hankalin jama’a ya tashi ganin iskanci dana taro bamai riƙuwa bane , ƙanin Babana yana tsakar gida shima da mutane ana ta mishi Allah sa alkairi dan ba’a daɗe da ɗaura auren ba , mazauni su Amisty suka nemomin na zauna na ɗauki ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora… Kallona yayi tare da cewa Sultana haka kika zama karuwa ? Saboda shi irin mutanen nan ne masu sakin magana babu tsafta , murmushi nayi tare da gyara zaman ɗaurin kallabi na sannan nace Eh wallahi ai shine nazo na nuna muku tunda nasan duk wani ɗan uwa da abokin arziƙi yazo shine nazo wanda basu gani ba suma su gani….Dariya Amisty tayi tare da buɗe jakarta ta jawo shigarinta ta banka mata wuta , saida taja ta bada hayaƙi sannan tace wannan gaskiya ne Mother , ƙanin Babana yace nan zaki zo ki kawo mana iskanci ? Tou ki tashi ki koma inda kika fito tunda ke kin lalace karki zo nan ki gurɓata mana tarbiyyar “ya “ya kije can ki ƙari iskancin ke ɗaya…. Kallon Baba nayi tare da cewa gaskiya ne dan naga idan guguwa ta taso wuri ɗaya takeyin borinta amma tsawar hadari tana gaurayi kaf faɗin sararin samani , ruwan sama ko na sarari yake jeƙewa bai taɓa baa na cikin ɗaki kashi duk wanda kaga yasha kashin ruwa cikin ɗaki tabbas kwanon ɗakinsa ya huje , idan yayi dibara saiya doɗe wannan haryar da zai bawa ruwa damar shigo mishi ɗaki. Gyara zamana nayi tare da ci gaba da cewa duk na kirki baya san na banza amma ni mutanen kirki sune abokan rayuwa….. Miƙewa nayi tare da cewa ka bada tarbiyya a gida zamanin Sultana yana warware tuggun kowa , duk wanda ya kalleni a taron nan yace tir da halina ya saurari zuwan zamani na akan “ya “yanshi, har na fara tafiya na tsaya tare da juyowa nace yawwa idan kaga ɗan uwan naka Babana , ka faɗa masa cewa ina matuƙar kewarsa a kusa dani… Sallama nayi da duk wanda ya kamata tare da buɗe bakin jakata nayi alkairi , banga “yan gidanmu ba ko ɗaya amma nace idan sunzo ace musu ina nan tsohuwar anguwarmu , gidan karuwai kawai zasu tambaya za’a kawosu har ɗakin magaji Sultana , na ƙarasa maganar tare dayin murmushi sannan nayi gaba masu sauran imani suka bini da addu’ar shiriya yayin da wasu ke cewa ubana yajamin… Muna fitowa daga gidan kowa ya shiga mota muka ibi sararin hanya….. 31/08/2019 *JAMILA MUSA…* 🤙🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 24 Muna fita gidan biki Baba ƙarami ya ɗauki wayarshi ya fara kiran Babana abin alfahari na , mai nunamin soyayya ta zahiri da gaskiya , wayayyan mahaifi mai tafiya da rayuwarshi daidai da zamani… Bayan Babana ya ɗauka suka gaisa , bayan gaisuwa Babana yayi masa ya taro tare da addu’ar Allah ya bada zaman lafiya wa ma’auranta , Baba ƙarami yace ameen , Bayan Babana ya gama addu’a Baba ƙarami yayi gyaran murya tare da cewa wato Aliyu ɗiyarka dai ta zama cikakkiyar karuwa , ka shige ka ɓoye kabarma dangi baƙin ciki su gani… Rabbi annee massaniyadh dhurru wa anta arhamur rahmeena , Abdullahi Uwar masu gida baza ta taɓa zama karuwa ba ban haifi karuwa ba akanta amma karuwai suna zuwa kuma zasu tabbata akan duk wanda yake dangana min ɗiya da siffar karuwanci , ban gudu ba kuma ban ɓuya ba tunda har kuna nema na ku sameni ku bugo kuma in ɗauka muyi magana , na ƙauracewa zaman ne saboda duk duniya babu hawaye mafi ɓakin ciki inga suna gudana tsakanin idanuwa zuwa saman kumatu irin na Uwar masu gida, Duk kuwa ranar da naga kukanta tou tabbas shekarar mutuwa tane ya tsaya , ɗiya ɗaya tak a cikin taron yuyuyun “yan uwa , saita tallafeni sai ta tallafe ka sai ta taimakeni sai ta taimake ka sai ta taimakesu sai tayi ma kowa taimako kuma ko bana raye wallahi ka riƙe wannan maganar karka sake ka manta ta uwar masu gida cikakkiyar mai arziƙi ce ,Idan ina da rabo inci idan banda rabo dangi su amfana ko ƙasa ta rufemin ido nasan nabar baya mai amfani , burin duk uba yabar baya jaruma ba lusara ba , idan kalmar karuwan ta sake fitowa bakinka akan Uwar masu gida na rantse da girman Allah gaba ɗaya zuri’ar ka sai sun zama karuwai….. Zufa ta ketowa Baba ƙarami tare da cewa Allah ya baka haƙuri Aliyu ban faɗi wannan maganar dan in ɓata maka zuciya ba , jarumin uba kenan murmushin “yan duniya yayi Babana tare da cewa nima ban faɗa maka dan zuciyarka ta ɓaci ba ina tunatar da kai dai ko waye Aliyu Binna dan naga tafiyana yasa ka manta me binna ɗin take nufi, haƙuri dai Baba ƙarami yaci gaba da bawa Babana saida ya tabbatar daya sauka sannan sukayi sallama… Wata irin ƙuna mai kartar zuciya Babana yaji wacce tasashi zaman dole , saida yasha kuka harya godewa Allah sannan yace ki yafemin Uwar masu gida ƙaddara tayi makauniyar waiwaya , an cuceni anci amanata banso ƙaddarar rayuwarki tazo miki a haka ba , amma na rantse da Allah daga Dikko har yaronshi Alhaji sun shiga uwatar bala’e duk wadda yaci yaciwo ma kanshi masifa , Abinda Bello ya guda kenan shi yasa shi baiba , amma yakaiki inda akayi nayiwa Dikko uzuri kuma na yafe mishi saboda nayi imani da yasan waye ubanki ko a santa ya ganki tsirara baya kallonki bare har yayi sha’awarki , duk abinda kike ciki na sani kuma ina da labarinshi , daga Dikko da Alhaji babu namijin da zai sake keta miki mutunci har abadan duniya , idan tsafin ne ba’a fini iyawa ba , cikakken ɗan caca manemin matan aure za’a nunawa iya sihiri ? Gaki nan zakiyi yawonki tare da rayuwarki cikin “yan ci kamar yadda ko wace ɗiya mai gata zata yi amma wallahi babu namijin da zai sake kwanciya dake sai mijinki na sunna in Allah yadda… Murmushi kasan dai Dikko yafi ƙarfinka duk wani ɗan ƙaramin tsafinka baya tasiri akanshi, kaine kaɗai halakakke ɓatacce wadda baka dogara da Allah ba ka dogara da tsafe tsafe, duk wanda ya riƙe Allah kuma ya dogara dashi Allah zai isar mishi duniya da lahira…. Dariya nayi adaidai wannan lokaci na daki sitiyarin mota ta domin fira mukeyi tunda muka taho , kallon Amisty nayi tare da cewa yaufa nasan na daki zuciyar maƙiya , mutumin dana burge a wurin bansan iyaka ba , tou dole ince mana , Kinga Sultana ga mota Sultana ga wayewa ga iskanci uwa uba karuwancin nan yamin kyau domin yasa na zama wata babbar hajiya da mutane ke ganin girmana , kuma nayi musu hauka da kuɗi zaki ga ikon Allah makwaɗaita sai sun biyoni saboda wannan zamani mai badawa shi ake mannemawa, Haka dai rayuwarmu taci gaba da tafiya ! Kullum iskanci na da lalacewa na gaba yakeyi amma har zuwa wannan lokaci ban samu wani cikakken namiji kwatankwacin Dikko ba , mijin Zalifa kuma har yanzu baizo ba da nayi masa magana bai zo ba saidai ya toshe ni da kuɗi tun abun baya damuna har ya fara tsaremin rai… Tsaye da kyau zaune da kyau babu inda Allah ya rageni amma mazan bariki idan sunzo basu tayani saidai idan nayi kawalci in samu kuɗi abunfa ya fara damuna na rasa inda zan saka raina dan ba irin wannan sana’ar na zaɓa ba gaskiya nafi so a nemeni ayi kuma a bani kuɗi , Amisty ta lura da halin da nake ciki ta tambaye ni abinda ke damuna , ban wani ɓoye mata ba na sanar da ita , dariya Amisty tayi tare da cewa wallahi hannu aka saka miki ,Cikin rashin fahimta nace ina aka saka min hannun ? Na tambayeta ina kallon jiki na ! Dariya Amisty tayi sosai sannan tace haba uwar ɗakina bafa a jiki ake saka hannu ba , abinda ake nufi da sa hannu magauta zasu je wurin malaman tsubbu su biya kuɗi suce a toshe musu samunki a rufe duk wani ci gaba naki…. Tsoki nayi tare da cewa aisai suje suyi ta fama can su Allah ya azamawa , Amisty tace tou ai sai anyi maganin matsalar sannan zamu barsu suyi ta fama , kallon Amisty nayi tare da cewa wallahi kun cika canfe² babu wani jarabta na rayuwa sai asiri , an saka miki hannu , tou idan sun gaji da sa hannun zasu goge da kansu , Daga ƙofar ɗaki Nana tayi magana cewa Mother zamu ɗan shiga maƙota , daga inda nake zaune nace me akeyi maƙotan ne ? Nana tace Mother baƙi ne suka bayyana a cikin daren jiya anguwar nan , kinga matar wayayya ? Daga tsakar gida Saude tace matar kodai mijin ? Zamu shiga muga halinsu idan munga da lasa zamu yankawa mijin kati zai dawo gidan nan uwar ɗakinmu… Murmushi nayi irin namu na “yan duniya sannan nace tou ku dawo lafiya , saboda ni dama Allah baimin shige² ba ina nan inda Allah ya ajiyeni duk wadda nake tare dashi shine yake zuwa ya sameni dan gaskiya bana san raini shi yasa na tsare mutunci na a gidana… Gyaran murya Nana tayi tare da cewa ko zakije ne ? Cike da izza nace ku dawo lafiya , Amisty tace nima kam zanje , murmushi nayi amma ban sake magana ba , gaba ɗaya suka ɗinguma suka tafi gidan amma ni banbisu ba…. Gaba ɗayansu a palon matar suka sauka , kowa ta kama kujera ta haye kamar baƙon namiji a harkar mata , bayan gaisuwa kowa ta faɗawa matar sunanta tare da cewa sune maƙotan gidanta , itama sunanta ta faɗa musu Asma’u sannan ta kora da cewa bata taɓa aihuwa ba , Gyara zama Amisty tayi tare da cewa shekararku nawa da aure ne ? Asma’u tace gaskiya munkai shekara 8 , tou kina da abiyar zama ne ? Amisty ta tambayeta , Asma’u tace Eh mu biyu ne ? A ` i ta anshe da cewa tou kun taɓa neman maganin aihuwa ko itama abiyar zaman taki bata taɓa aihuwa bane ba ? Asma’u tace kai tana haihu sosai ma , Amisty tace tou matsalar daga wurinki take idan mun fahimta , Asma’u tace gaskiya , daga haka dai suka tsaya domin sun shiryo barikinsu wa Asma’u zance yau iyakarshi haka…. Miƙewa sukayi gaba ɗayansu cewa zasu tafi , Asma’u tace haba tun yanzu ? Murmushin “yan duniya A ` i tayi tare da lumshe idanuwa ita mayyar mata tace ai zamu sake shigowa , rakiya tayo musu har bakin get tayi godiya sosai , Tunda suka fito faɗa ya kaure tsakaninsu , yayin da A ` i ke cewa ta kama matar Saude kuma ta kama mijin , Amisty tace A ` i dani zaki haɗa hanya ? Bayan ni na fara isar da saƙo na zakice kin kamata ? Nana tace kai matar fa tana da mazauna sosai gaskiya , rikici dai sukeyi sosai , dan haka Amisty ta taka musu birki da cewa duk abinda zasuyi suyi shi a waje kar su bari naji wannan labarin domin sun san babu abinda na tsana irin harkar mace da mace…. Tun a waje sukayi ma Hafsa waya suka sanar da ita sun samu lafiyayyar mace kuma daga gani zatayi shan mai domin yarinyar da zafinta , Hafsa tace gani nan zuwa , Amisty tace karki zo yanzu kina zuwa uwar ɗakinmu zata gano wani abu kinsanta da saurin fahimta , duk satin nan karki zo ki bari sai cikin sati na gaba , Hafsa tace wallahi bazan iya ba sai nazo na ganta , Amisty tace saurara kiji yarinya , ba’a garaje ya kike abu kamar baƙuwar harka don Allah ? Ki natsu ki kwantar da hankali wallahi babu mai yarinyar nan sai mu , ki dai bari mu ɗorata hanya ita da kanta zata riƙa kawo kanta , dakal Amisty ta lallashi Hafsa ta haƙura, Tsakar gida suka sameni kowa tayi dabur ² murmushi nayi tare dabin Amisty da kallo sannan na kalli idon A ` i na kalli na Nana saboda sune “yan lesbian a cikinsu , da kinga sunayin kame² mace suka gani , sai kuma Hafsa itama manemiyar mata ce , jinjina kaina nayi sannan na tsare Amisty da kallo idanuwanta sunyi wani irin ja kamar taci tsidagu, Ƙafafuwan Amisty na kalla sannan na ɗago idona zuwa daidai saitin cibiyarta sannan na dauke kaina , ɗaki ta wuce Nana ma ɗakinta ta shiga yayin da A ` i ta samu wuri ta zauna , kallon inda A ` i take zaune nayi sannan nace sannun ku *kwarata* daga zuwa maƙota har hankalinmu ya tashi ko ? Duk yadda akayi matar gidan ta burgeku , Allah ya tsallaketa daga kaidinku…. Ɗaki na shiga Amisty na samu kwance saman katifa tayi ruf da ciki , tsoki nayi tare da halbinta da ƙafa nace tashi ki fitarmin daga ɗaki ni gaskiya bana san irin wannan ɗabi’ar , Allah ya baki haƙuri uwar ɗakina , tana faɗin haka ta miƙe tabar ɗakin ta nufi ɗakin Nana , da yake itama Nana naga yanzu taɗan waye tana wanka tana shafa turare , har akayi sallah magrib Nana da Amisty da A ` i suna ɗakin bansan abinda sukeyi ba gaskiya….Kuma ban damu da sanin halin da suke ciki ba danni Allah baimin sa ido da bin diddiƙin abinda wane yakeyi ba , sai bayan isha’i Amisty ta shigo da ɗaurin gaba da alama wanka tayo , Ko inda take ban kalla ba , itama bata kalleni ba kuma batamin magana ba taci gaba da shiri saida ta gama abinda takeyi tsaf sannan tace min dame² za’a siyo ne ? Can zaki kwana ne ? Na tambayeta , tace ba’a can zan kwana ba wurin 1:00 zan dawo , indomie da madara kawai zaki ƙaro mana , kallona tayi sannan tace ke babu abinda kike so ne ? Ba abinda nake so na bata amsa tare da cewa Allah ya bada sa’a a dawo lafiya , da amin ta amsa sannan ta fice daga ɗakin… Kwanciya nayi bayan Amisty ta fita dan banda inda zanje , Nana ta shigo ɗakin da sallama ta ɗauki magunguna ta fita saboda mu yanzu garin “yan gidanmu ya waye , Ganin Nana ta ɗauki magunguna na tashi na feshe jikina da turaruka masu ƙamshi na ɗaukar hankali , doguwar riga ta shadda na saka nayi ɗaurin ɗan kwali irin namu na karuwai dan banda daurin ɗan kwalin daya wuce ture kaga tsiya… Tunda na fito daga ɗaki su Karima suka rufamin baya dan ko gyale tuni na daina sakawa , cikin isa da nuna ni wata shegiya , cike da izza nayi gaba sai baƙin rai nake na tun kari ƙofar gida su Nana duk suna biye dani , tsayuwa nayi a ƙofar gida nabi motocin dake ajiye a ƙofar gidan da kallo kamar anayin wani taro. Murmushi nayi yayin da aka ajiyemin kujerar roba na zauna , ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora sannan mazan bariki suka fara kawo gaisuwa kamar yadda suka saba a duk lokacin da wani zai ɗauki wata domin nice uwar ɗakinsu , suna bani girmana basu rainani ba shi yasa duk wani *kwarto* yake ganin girma na… Duk namijin da yake zuwa wurin matan waje babu samari manyan mutane ne masuji da kansu wani ma wallahi yayi ɗiya da wacce zai kwanta da ita , ko me yasa suke baro matansu na gida suzo na bariki ? Gaskiya ina san insan wannan dalili … Bayan na gama samun kuɗina na miƙe na koma ciki ,ɗakina na shige nabar musu filin tsakar gidan dansu ji daɗin harkokinsu , mace ɗaya tana iya kwanciya da namiji biyar saboda tsabar haɗama , *** *** Safiyar yau gidan Asma’u su Amisty suka sauka , acan suke baje kolinsu ranar da suka fara zuwa banje ba kuma yauma da zasu koma banbi su ba , gaba ɗayansu suka tafi ni kuma na fita ƙofar gida nayi zamana a saman dakali… Wayata na ciro na fara kiran mijin Zalifa , bayan ya ɗauka yace ina gida idan na fito zan kiraki , jinjina kai nayi tare da cewa ka fito lafiya ranka ya daɗe ina faɗin haka na kashe wayata…. A gidan Asma’u kuwa ga yadda lamarinsu ya kasance a yau , 02/08/2019 *JAMILA MUSA…* 🧚🏻♀⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 25 Tunda suka shiga sukayi ta kwarara sallama shiru babu wadda ya amsa , Hafsa itace ta basu ƙwarin guiwa cewa kawai su shiga palo , gaba ɗayansu sunkayi na’am da wannan shawara dan haka suka ɗinguma suka shiga cikin palon tare dayin sallama… Daga cikin bedroom Asma’u ta amsa sallamar tare da cewa ku zauna ina zuwa , murmushi Amisty tayi tare da cewa ko munzo da wuri ne mai gidan bai fita ba ? Daga cikin ɗaki Asma’u tace ya fita amma yana dawowa babu jimawa wanka dai na fito ina ƙoƙarin saka kayana ! Wani irin ajiyar zuciya Hafsa ta sauke tare da cewa zanyi fitsari ta faɗi maganar cikin sigar kwartanci ma’ana tayi maganar a sakantace tare da kasalanci yanayin maganar dai sune kaɗai suka san fassarata , Akwai toilet a nan waje inji Asma’u tare da ƙoƙarin fitowa daga bedroom in dan nunawa Hafsa inda toilet in yake , towel ne ɗaure a jikinta ko guiwa bai kawo ba saboda tana da wani irin kugu ne shi yasa towel in ya haye saman ɗuwawunta shi ya hana towel in saukowa sosai ‘ Idanuwa Amisty ta zaro sosai kamar zasu faɗo ƙasa tare da jan wani irin gauron numfashi sannan tace babu toilet a bedroom inki ne ? Ta faɗi maganar kamar numfashinta zai ɗauke , murmushi Asma’u tayi tare da cewa akwai bara dai ta shiga na wajen ! A ƙofar palo sukaci karo da mijin Asma’u , tunda ya ganta ya haɗe girar sama da ƙasa tare da cewa wannan wane irin sakarci ne ? Ke wawiyar inace zaki fito haka ….. ? Cikin biyayya Asma’u tace ai ba kowa gidan ne duk mata ne , matan banza matan wofi da Allah wuce kije ki saka hijabi malama , yayi maganar cikin kausassar murya tare da ƙara ɓata rai kamar zai daki Asma’u , Simi simi Asma’u ta wuce ta koma ciki , saida ta shige sannan yabi bayanta , a palo ya samu su Amisty zaune riɗi² , duk gaishe shi sukayi amma babu wacce ya kalla bare su saka ran zai ansa gaisuwar wata daga cikinsu ya wuce ciki abunshi…. A bedroom kuwa faɗa ya rufe Asma’u dashi tare da cewa ina kika samo wa’anan karuwan ? Kai ƙasa ² tace maƙontanmu ne , zama yayi a gefen gado tare da ci gaba da cewa gaskiya ni bana so suna zuwa gidan nan kima taka musu burki kar na sake ganin kowa na faɗa miki , Cikin yanayin damuwa Asma’u tace haba Baban Abdul babu daɗi na ce su daina zuwa , cikin ɗaga murya yace tou wallahi idan baki musu magana ba ni da kaina zan musu magana zance kar na sake ganin ƙafar ko wace a gidan nan , daga shiga bayi kilbibi zai fara yaɗuwa , miƙewa yayi tare da cewa tunda tsoronsu kikeji ni bara inje in faɗa musu… Da sauri su Amisty suka miƙe kafin mijin Asma’u ya fito tuni sun fice daga gidan , koda ya fito palo bai samesu ba , dan haka ya koma yana cewa sun rufawa kansu asiri da suka gudu , ita kuwa Asma’u bataji daɗi ba saisu Amisty su gani kamar itace tasa mijinta ya tozarta su kuma tabbas nasan sunji kana faɗa irin haka babu daɗi… Cikin ƙara faɗaɗa faɗanshi yace ai dama bana so suji daɗin kuma idan na sake ganinsu gidan nan saina ci mutuncinsu , Asma’u tace tou shikenan ka haɗa hadani kaci mutunci gaba ɗaya , tou zanci hada naki ki barsu suci gaba da zuwa gidan nan kiga yadda zamu ƙare dani dake…A ƙofar gida su Amisty suka tsaya tare da saka takalminsu ko wanne yana maida nunfashi saboda gudun da sukayi daga cikin gida zuwa ƙofar gida , ajiyar zuciya A ` i ta sauke sannan tace kai wannan ɗan masifa ne zamu sha fama dashi domin zai ɓata mana lokaci gaskiya , Nana tace babu wani ɓata mana lokacinmu da zaiyi kawai mu haɗashi da Mother kunsan Allah ya bata ilimin saka namiji lungu , Hafsa tace idan muka haɗasu me kuke tunanin zai faru ? Kunfa san halin Sultana tana iya faɗa masa cewa ya hanamu shiga gidanshi mu maneman mata ne tunda ita bata wannan harka kuma sanin kanku ne baza ta rufawa mai irin halin asiri ba “” , Amisty tace tabbas zata aika wallahi , A ` i tace kuzo kuji mafita , haɗuwa sukayi wuri ɗaya sukayi magana ƙasa² dariya sukayi bayan sun gama tare da tafawa sannan suka nufo gida. ! A ƙofar gida suka sameni zaune ko inda suke ban kalla ba , zama sukayi yayin da Amisty ta ciro sigarinta daga cikin jaka ta kunna mata wuta saida taja ta sannan tace uwar ɗakina barka da hutawa , Bance yawwa ba kawai nace mata faɗi damuwarki , gyara zama tayi tare da cewa wallahi wani alhajin wuta ne muka samu , ga ƙira ga sarho { kwarjini } uwa uba hatimin nasara mota saidai ya shiga wannan ya fita a waccan , ga gida daya gina mai tafiya daidai da zamanin ƙarshe , jiya mata biyu yaba mota kuma nice sheda saboda na gani kuma na hau dan taya murna , matashi ne wayyan namiji ga aji kamar abokin gabarki { Dikko } Dariya nayi tare da kallon Amisty sannan nace kiyi magana kawai ki daina shiga buhu , kashe tabar hannunta tayi sannan tace nidai shawara zaki bani ina so ko ta halin ya nima in ɓata dare ko yini dashi , a gidanshi yake kai matan bariki idan matarshi bata nan , ki taimakamin ki faɗamin taya zan nemeshi… ? Kallon Amisty nayi sannan nace ke kin tabbata manemin mata ne ? Amisty tace ko ban tabbata ba dai inaso yayi akaina , karfa ki manta kece kikace mu nema ga mai nema kuma idan ya nema mu bashi , kuma kece kika ce idan mun gani munji muna da buƙata kar mu cuci kanmu muyi ƙoƙari mu bashi tun muna bashi yana tofarwa har mu samu ya fara haɗiyewa , nidai gaskiya ina so ya kwanta dani koda so ɗaya ne . Kallon Amisty nayi sannan nace a gidanshi kike so kuyi alaƙa dashi ? Amisty tacemin Eh , murmushi nayi tare da cewa kawo kunnenki a baki , matsowa tayi tare da miƙomin kunne na fara mata raɗa , har ga Allah ban kawo komai a raina ba kuma ban taɓajin sha’awar kowa ba a cikinsu , inawa Amisty raɗa ta kwanto a jikina sosai tare da lumshe idanuwanta , ashe ita daɗin maganar takeji ,Ta bayana ta tura hannuwanta duka biyun cikin rigata ta fara shafawa a hankali tana wani ƙara mannewa a jikina tana nunfashi a hankali ² , ban gama maganar ba nayi tsoki tare da tureta daga jikina nace wannan wane irin ɗanyen iskanci ne kuma ? Dariya Hafsa tayi yayin data lushe idanuwanta sannan tace haba mother daga an riƙeki sai ki tayar da hankali ? Ba komai bane ba natsu kawai kici gaba da faɗa mata tunda kin fara kuma mu bakya so muji ! Ban kalli Hafsa ba nace bazan faɗa ba “yan iska masu guntuwar sha’awa ku ko kunyar Allah bakwaiji da kunga mace duk sai ku wani fitittike karuwai marasa aji , idan kunajin bala’e da tsabar maganin iskanci ku nemi maza sai kusan kunyi iskanci da hujja , mace me zata miki ? Inda kike buƙatar kije kafin ki sauka wurin kinsha wahala , Murmushi Amisty tayi tare da kishingiɗawa ta bini da kallon mai tatttare da tsabagen sha’awa sannan ta sauke ajiyar zuciya , miƙewa nayi Amisty ta jawoni ta zaunar dani , ta sake tsareni da wani irin mayataccen kallo , tsikar jikina naji ta tashi , lahira tazo min kusa kusa da sauri nace A’uzubillahi minashshaɗainir rajim , Gaba ɗayansu suka sheƙe da dariya , ɗaure fuska nayi tare da sake miƙewa , ƙara riƙo hannuna Amisty tayi juyowa nayi tare da cewa karki sakemin irin wannan abun daga yau bana so , makirin murmushi tayi sannan ta sakemin hannuna na tafi cikin gida ,Suna ganin na shige A ` i tace Allah ya ɗoramu akan ni’imarki yarinya zamuyi wasan kura dake kowa saiya yagal galaki san ranshi wai ita a dole mai tsoron Allah , tuni na daɗe da haɗiyewa akan yarinyar can amma ta balɓaɗa min rashin mutunci tun kafin in furta , duk daren daɗewa saina afkawa yarinyar nan saidai duk abinda zai faru ya faru , Zama Hafsa tayi tare da cewa nifa na ɗauka “yar hannu ce ! Ganin farko da nayi mata itace ta fara nunamin wallahi a tunani na ta tafiya ce , ashe ba haka bene nima duk ranar data shigo hannuna saina horata , hawan farko zanyi da ita saita koma gidanmu da zama…. Ido ɗaya Amisty ta kashewa Hafsa tare da cewa ashe kuwa za’a haɗa rigima dan dai kinsan my Sultana tawa ce ni ɗaya , kinsan haɗarin dana fuskanta akanta kuwa ? Nabar uwa nabar uba na dawo zama da ita ? Lumshe idanuwa Amisty tayi tare da rungume duka hannayenta a ƙirji tace wallahi idan har na samu Sultana na more duniya , zan rabata da kowa da komai na ɗauketa na tafi da ita , A ` i tace ki ɗauketa ki kaita gidan uwar wa ? Ai yadda kikayi kowa sai ya more Allah dai yaba mai rabo nasara, sun daɗe suna ƙullawa da warwarewa yadda zasu samu nasara akaina daga karshe dai suka yanke shawara zasu kaini gidansu Hafsa acan zasu baje kulinsu dani…Tun daga wannan ranar na canjawa su Amisty fuska na daina cin abinci tare da ita , na daina kwanciya wuri ɗaya da ita , idan ta kwanta a katifa saina sauka ƙasa , gaba ɗayansu na rage musu fuska ko dariya na daina musu tunda dai na lura dukansu iskancinsu ya girmi nawa , Amisty kuwa muguwar tare tayiwa su Nana A ` i da Hafsa , ita kaɗai take zuwa gidan Asma’u basu sani ba ta shige mata sosai , har ta gane kwanakin da mijinta yakeyi a gidanta da ranar da baya gidanta … Yau mijin Asma’u ba’a gida zai kwana ba tunda Amisty ta shigo gidan taƙi ta fita , har dare yayi sosai , gajiya Asma’u tayi dan taso Amisty ta tafi ta rufe gida , kasa haƙuri tayi tace wai nace ko yanzu zaki tafi dan kwanta ne bacci nakeji, Murmushi Amisty tayi tare da cewa ai yau nine zan tayaki kwana , Asma’u tace haba ai babu wani damuwa ni ɗaya ma nake kwana nan babu komai , ajiyar zuciya Amisty tayi tare da cewa ai nasan bakyajin tsoro tunda duk girman kwanakin da kikayi kina kwana bani nake tayaki kwana ba., Asma’u tace Eh kawai karki damu kya iya tafiya… Lemun dake gaban Amisty ta ɗauka tasha a bakinta sannan ta miƙe tsaye ta tunkari inda Asma’u take tsaye , Asma’u ganin Amisty a wani irin yanayi yasa taɗan ja baya , yaudararren murmushi Amisty tayi kamar yadda ta saba idan hankalinta ya tashi akan mace, Asma’u tana ƙoƙarin ƙara ja baya Amisty ta fizgo ta , Asma’u tace haba Amina miye haka ? Tayi tambayar tare da fizge hannunta ta ƙara yin baya , binta Amisty tayi har takai maƙurar bango maida hannayenta tayi duka ta baya ta dafa bango dasu ta tsaya tana kallon Amisty , Da duka hannayenta ta riƙe ƙugun Asma’u sannan tace wai miye duk kika wani firgice ? Kwanan da nine bakya so ko miye ? Asma’u tace ba haka nake nufi ba , ƙara fizgo ta tayi jikinta sosai sannan tayi magana mai tattare da ɗaukar hankali tace tou miye ? A wurin Asma’u ta sandare ta kasa cewa komai , sakin ƙugunta tayi ta jawo hannenta ta ɗora su a saman ƙirjinta sannan tace mu kwana tare ko ? Tayi maganar cikin rarrashi , kai kawai Asma’u ta iya ɗagawa Amisty , murmushi Amisty tayi sannan taja Asma’u ta zaunar da ita saman kujera , kamar ɗakin uwarta itace taje ta rufe ɗakin dan dama gidan rufewa sukeyi sai an ƙwanƙwasa take buɗewa, a inda tabar Asma’u a wurin ta dawo ta sameta , kusa da ita Amisty ta zauna sannan ta jawota jikinta tace miye ? Ko kinajin babu daɗi ne ? Cike da kasala Asma’u tace tsoro nakeji , ƙara jawota Amisty tayi sosai a jikinta sannan tace wane irin tsoro bayan gani ina tare dake ! Riƙo fuskar Asma’u tayi ta kalleta ido cikin ido sannan tace kin taɓa ? Asma’u tace a , a Amisty tace a kaina zaki fara kenan ? Jinjina kai Asma’u tayi alamar Eh , Amisty tace tou muje ciki , 04/09/2019 *JAMILA MUSA…* 🧚🏻♀⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 26 Ƙiri² Asma’u ta kasa tashi , kusa da bakinta Amisty ta matsa da nata bakin sannan tace sweetheart miye ? Kallonta Asma’u tayi sannan tace na gaji , murmushi Amisty tayi da gefen bakinta sannan tace kin gaji tun yanzu ? Idan na fara suma zakiyi kenan saboda daɗi ko ? Shiru Asma’u tayi batayi magana ba , Uhum Amisty tayi tare da laso bakin Asma’u taɗan taɓo ƙirjinta ta waje , ƙara lasar saman luɓunanta tayi saita ɗago sannan ta ƙara tare da haɗa bakinsu wuri ɗaya tana mata wani irin sumbata wadda Asma’u ta danganashi da ko mijinta bai iya irinshi ba ! Tun a palo suka fara lalacewar su hankalin Asma’u yakai ƙololuwar tashi cikin sarƙayƙiyar murya tace muje ɗaki don Allah……Amisty ta taimaka mata ta tayar da ita suka nufi bedroom , jikin Asma’u yana kyarma ta cire kayanta kaf sannan ta haye saman gado Amisty ta rufa mata baya suka ci gaba da halakewarsu ! Har ƙarfe 10:30pm babu Amisty babu labarinta , na kira wayarta yafi a irga bata ɗauka ba dan bata saba fita bata faɗamin taje wani wuri ba , duk wadda na tambaya ina Amisty sai yacemin baisan ina taje ba saboda suma kansu bata faɗa musu zata fita ba , Gajiya nayi da kiranta na haƙura nayi kwanciyata dan na huta , ina kwanciya Amisty tazo ta tsayamin a rai , tun lokacin da tamin abun nan a ƙofar gida duk lokacin dana raɓe ni ɗaya sai abun yazo ya tsayamin a rai , Tsoki nayi tare da gyara kwanciyata na rufe idona danyin bacci , murmushin Amisty nake gani sai kuma kallon da tamin , innalillahi wa’inna ilaihir raji’un nayi tare da miƙewa na ɗauki buta nayi waje …. Hafsa na gani ita da A ` i rumgume da juna , a’uziyya naja tare da cewa wai ku wane irin “yan iska ne da Allah ? Na rantse da girman Allah idan baku daina min wannan muguwar ɗabi’ar ba duk sai na tashe ku a gidan nan , Dariya A ` i tayi tare da sakin Hafsa tace Allah ya baki haƙuri uwar ɗakinmu , ban sake magana ba nayi gaba , bayi na shiga ban wani daɗe ba na fito ina fitowa nayi alwallah na shige ɗaki na , wannan rana kusan kwana nayi ina sallah dan banajin daɗin ganin Amisty a zuciyata ko kwalwata ! A ɓangaren su Amisty kuwa kwana sukayi suna baɗalancinsu Asma’u taji dadin wannan harka domin Amisty bata da ƙyanƙyamin taba Asma’u gamsuwar da ko a wurin mijinta bata taɓa samu irinta ba , ga Amisty ta iya soyayya domin ta daɗe a harkar lesbian gwanace kisan farko , koda safe itace ta wanke Asma’u a toilet kuma itace ta shafa mata mai da powder ta taimaka mata ta saka kaya sannan tace zata tafi gida. Asma’u tace da Allah karki tafi ? Murmushi Amisty tayi tare da jawota jikinta ta lumshe idanuwanta sannan tace karki damu ina dawowa anjima bana so mijinki yazo ya sameni a safiyar nan za’a samu matsala kinji ko ? Jinjina kai Asma’u tayi saida Amisty ta sumbace duk wasu muhimman wurare a jikin Asma’u tare da cewa ki kula , Asma’u tace to, sakinta tayi ta fito da sauri daga ɗakin dan har 9:00am tayi bata so mijin Asma’u ya ritsesu dan shima zata mishi horon da Sultana ta bata zata haɗasu dukansu taji dasu zata huta da Asma’u mijin kuma zatayi harka dashi dan ta samu kuɗi , dan da tana da wata sana’a ko hanyar samun kuɗi da baza ta bi maza ba , amma dole sai ta nemi maza sun bata sannan itama zata samu nayiwa karuwan matanta hidima… Tunda Amisty ta fito Asma’u ta koma gefen gado ta zauna , tunanin Amisty takeyi gaskiya ta yaba da jarumtar ta kuma Allah yasa yau ta dawo su kwana tare , Ina tsaye ina saka caji Amisty ta shigo ɗakin kamar an jefota , rumgumeni tayi tare da cewa oyoyo my Sultinah na dawo jiya inata kewarki sweetynah fatan dai kinyi bacci mai daɗi ? Kwantar da kanta tayi a saman ƙirjina , murmushi nayi tare da cewa tou sakarni mana , ƙara ƙanƙameni tayi tare da cewa uumm umm cikin sagwaɓa , har a raina abin yamin daɗi dan haka ban sake cewa Amisty tashi ba , jin nayi shiru yasa Amisty taɗan jijjigani sannan ta ɗago ta kalleni da kallo mai ɗaukar hankali tace me kika dafa mana ? Saida na zauna sannan nace ni ban wani dafa komai ba , idanuwa Amisty ta zaro tare da cewa tou me zanci kenan yunwa nakeji wallahi , sai kici haƙuri na faɗa , Amisty tace saida mai bada haƙurin kinsan ina ƙoshi da komai amma bana ƙoshi da mata… Tsoki nayi tare da kallon Amisty nace aike “yar iska ce wallahi , dariya tayi tare da ɗagamin gira ta kwanta sannan tace ai iskanci abun so ne wallahi danma baki san daɗin da akeji ba idan anayinshi…. Shiru nayi ban sake mata magana naci gaba da sabgar gabana , ita kuma wayarta ta fiddo bayan tayi latse latsenta ta kara a kunne , bayan an ɗauka tace ranka ya daɗe kana gari kuwa ? Banji abinda yace ba tace yawwa da Allah yunwa nakeyi aɗan kawomin abin ci yanzu ina jira , magana na cikin wayar yayi , wata irin dariya Amisty tayi tare da cewa tou babu damuwa idanma akwai wani mai ɗan ƙwari a tahomin dashi , tou babu komai ina jiranka , tana faɗin haka ta kashe waya…Kallona tayi sannan tace mother da Allah a fitar da lido waje yau banajin daɗin zama ɗakin nan , miya sa ? Na tambayeta ! Ba tare data kalleni ba tace idan ina ganinki a hakan nan komai zai iya faruwa ji nake kamar in haɗiyeki , ban kalleta ba nace Amisty ramin gafiya ba irin na maciji bane , wuta bata kamuwa haka kuma iska bata riƙuwa, domin fito da maciji daga rami dole saida hayaƙi , kamun maciji badai yaro ba saboda silɓinshi ,ki sani kama Sultana ba abune mai sauƙi ba dan kamun kifi dole saida fatsa…. Murmushi Amisty tayi tare da cewa aike sai kiyi ta magana da yaren da bana ganewa , nima murmushin nayi tare da cewa kamar yadda bakya gane yaren haka baza ki taɓa gane gaban Sultana ko bayanta ba domin shan ruwa da haɗiya lokaci ɗaya ba dai bakin mage ba , a fitar da lido ina nan fitowa idan nayi wanka…Fita nayi tare da ɗaukar ruwana na wanka na nufi bayi , Amisty kuma murmushi tayi tare da cewa zan kamaki yarinya zaki basu labarin fito da maciji dole saida hayaƙi ban taɓa neman mace ban samu ba zanyi waya da malam zulyadain na gaji da ganin abinci yunwa na damuna , lido ta ɗauka tayi ƙofar gida ita da sauran “yan tashar , Lokacin dana fito daga wanka babu kowa a tsakar gidan sai mijin Nana yana wanki , ban kalli inda yake ba nayi ɗaki abuna , ina shiga na fara shiryawa riga da sikat na saka na atamfa bayan na gama shafa , kayan kuwa sunyi matuƙar karɓar jikina ƙuguna ya fito sosai sai kace na wata uwar mata , turaruka na fesa tare da ɗaura kallabi wayana na ɗauka nima nayo waje bayan na gama , A ƙofar gida na samesu zaune saman dakali kuma da alama magana na sukeyi saboda naga sunyi shiru a lokacin da nake tahowa wurinsu , banma kowa magana ba na samu wuri na zauna naci gaba da latsa wayata , Amisty tace ga abinci nan idan zaki ci ! Ban kalleta ba kuma banyi magana ba , Amisty tace mother ina magana kinyi shiru , tsoki nayi tare da cewa na ƙoshi , cikin yanayin damuwa Amisty tace haba ya kuma kin ƙoshi ? Ban sake magana ba naci gaba da sha’anin gabana… Lido insu sukaci gaba dayi amma kaf hankalin Amisty da tunaninta yana wurina , ni kuma ina tunanin yadda zan fara kore mazan dake zuwa gidanmu dan na gaji da zama dasu Amisty idan babu mazan bariki tou kowa zai fita ya kama gabanshi… Ina wannan tunanin naji Amisty tace tou idan bazaki ci abinci ba kisha ko lemin mana , banyi magana ba na miƙe na matsa can wurin filin gidajen da aka rosa na zauna , Halbar da robar lemun Amisty tayi tare da cewa wallahi malam zulyadain bazai min ƙarya ba duk bala’en yarinyar can saina maida ita abun tausayi ta bana haɗiye miyau akan mace bansha ba wallahi , duk wacce tamin taurin kai asiri zaiyi tasiri akanta , tabbas itama Sultana zata yaba aya zaƙinta , Ban san gaibu ba amma tunda na lura da yanayinta bazan sake yadda da ita ba , ko yunwa zai kasheni na daina cin duk wani abu daya fito daga hannun Amisty kuma zan huro ma mazan bariki masifa duk wani kwarto saiya daina zuwa gidan nan , dama nina buɗe ƙungiyar kuma zan rufeta da kowarar kowa , Saida aka kira azahar na koma gida danyin sallah , har yanzu mijin Nana bai gama wanki ba tana can balbaɗɗiyar saman dakali sunayin lido , bayan na shiga gida ne Amisty take ba su Nana labari cewa malaminta yace duk daren daɗewa sai ta mallaki Sultana a hannunta kuma zata juyani san ranta ta kwantar da hankalinta lokaci ya kusa , amma a labarin malamin yace akwai wani yana nan shi zaizo ya tafi dani mutane dasu daɗe basuji labari na ba kuma yana nan ya kusa zuwa shima bada jimawa ba ,Shine tace idan ta sameni zata maidani kaduna kafin wannan mutumin da yake magana yazo , dan malam yace babu makawa mutumin zai tafi dani kuma idan har yazo komai na rayuwata zai canza dan ko iyayena bazan sake gani ba gida ne zai kaini ya ɓoye ina ne ? Shine Allah bai nuna ba , idan ta kaini kaduna zatayi ta badani haya wa manyan hajijoyi tasan idan har tayi kasuwa dani ba kuɗi ba kuɗiɗina sai tayi… Hafsa tace tou waye wannan mutumin ne ? Amisty tace malam yace matashi ne kuma duniya ta tsaya akanshi , yace mai mulki ne kuma cikakken attajiri ne , shin mai mulki ne ko basarake wannan shine ban sani ba , jinjina kai Hafsa tayi sannan tace karki zubar da abincin nan kiyi mata wayau sai taci shi , murmushi Amisty tayi sannan tace kwantar da hankalinki wata ma jiya a ice cream na zuba mata da zan tafi saida tayi kuka , dariya sukayi dukansu tare da tabawa sukace Allah ya nuna mana Sultana tana kuka akanmu zamusha shagali domin yarinyar gaskiya Allah ya hore kayan marmari a tattare da ita , haka dai sukaci gaba da labartawa akaina da kuma yadda zasu mayar dani inyi ta binsu kamar wata karya… Suna ƙofar gida har bayan magrib suna hauka , da daddare bayan ƙofar gidanmu ya ɗauki harami kamar yadda ya saba a ko wane dare , bayan na fito nakejin labari cewa Dikko ya samu kujerar da yake nema yayin da mutane ke cewa yaron yana da sa’ar rayuwa gashi kamilin namiji , Magana ta karaɗe gari Allah ya bawa ɗan gwamna kujerar abokin babanshi daya mutu , duk inda ka nufa a gari maganar Dikko akeyi yayin da wasu keji idan sune a irin wannan damar ba ƙaramin farin ciki zasuyi ba , gashi Dikko ko auren farko baiyi ba amma ya shiga sahun manyan mutane da duniya zatayi alfahari dasu , wasu kuma cewa sukeyi tauraruwar ɗaukakarshi ne ya tsaya shi yasa na saman kujarar ya mutu dan Dikko ya hau , Har ga Allah naji baƙin ciki , yayin da naji dama baici ba shege munafikin Allah ɗayan mazinaci ya ɓoye ya saɓawa Allah amma a idon al’ummar gari suna masa kallon mutumin arziƙi bayan ni nasan mazinacin ne kuma shima yasan yayi zinar , hawaye ya cika min ido nace Allah ka kwace kujerar mulki a hannun Dikko babu mulki ma a hannunshi ya wulaƙanta al’umma inaga ya samu, Wani naji yana cewa yo ai wallahi yaron nan tsaron da zai samu ko gwamna baya samun irinshi kai kana wasa da kujerar kaza , mutumin ya faɗi sunan kujerar da Dikko ya samu nidai bansan ko miye yace ba kuma wallahi bana iya maimaitawa , Wani daban naji yace ai naji ance har gwamnan jigawa ya bashi ɗiyarshi , Eh ai mutane basu abu dan Allah Dikkon ne wallahi dole sai ka bashi ɗiyarka ga ilimi gashi ya fito tsatson mutanen kirki ga kyau ga ilimin addini ga ilimin boko Dikko ga kuɗi ga mulki Allah dai yasa muna da rabo duniya da lahira , wani yace kai saidai mu tara lahirar amma a duniya su Dikko duk sun tare komai… Tsoki nayi tare da juyawa na koma cikin gida ina tsinewa Dikko albarka wallahi idan dai ina da rayuwa ba tsaro ba ko tsoro yake tsare Dikko saina ci mutuncishi kamar yadda na ɗau alƙawari , Tunda na shigo ɗaki damuwa ta dameni na rasa inda zan saka raina naji sanyi wuri na samu na zauna a ƙasa na jingina da bango tunanin ta inda zan hudowa lamarin Dikko na farayi nasan ba lallai bane ya sake shigowa anguwarmu ba saidai ya bada umarni a duba dokuna kila ma yanzu babu wani ruwanshi da labarin doki Sultana kuma yasha banza kenan… Murmushi Dikko yayi a dai² wannaan lokaci sannan ya kalli Al ‘ Ameen yace bansha ba , ruwa ne aka ajiye shine Al ‘ Ameen yayi tunanin ya gama zai ɗauke Dikko yace baisha ba , fita Al ‘ Ameen in yayi Dikko ya kalli hoton Sultana a wayarshi sannan yace ki daina tunani kona manta dake daren daɗewa Dikko baza taɓa mantawa dake ba , kina da matsayi na daban a rayuwata dalilin abu ɗaya yasa nake ɗaga miki kuma bazan daina ganin mutunci ba har abadan duniya zanzo bada daɗewa ba ki ƙara haƙuri kuma ki zama mai yafiya banda yadda zanyi dake haka kema baki da yadda zakiyi da Dikko , ina cikin farin ciki a yau dan haka kema kiyi farin ciki a daren nan An mata…. Wallahi bazanyi ba , ni kuma Amisty ke tambayana abinda ke damuna nace mata babu dan ba wadda yasan abinda ke tsakani na da Dikko ban taɓa bawa kowa labari ba zuciyata da rayuwata kaɗai suka san wannan sirri , Amisty tace tou kiyi shiru kallon Amisty nayi tare da cewa yanzu na fara kuka kuma bansan ranar da zan daina ba , inaji a jikina baƙin ciki da ƙunci na rayuwa banma saka hannu ba zan haɗu da wani gagarumin tashin hankali da bansan ranar zuwanshi ba , zan rasa wani abu mai mahimmaci a rayuwata zan zama abin tausayi da kwantacci wata rana na ƙarasa maganar ina murmushi…. Simi ² Amisty ta miƙe dan a tunaninta na samu warwarewar tunani , a wurin na kwanta naci gaba da kuka har bacci ya ɗaukeni , Yauma Amisty saida ta shirya sihirinta ta tunkari gidan Asma’u , cikin farin ciki Asma’u ta tari Amisty tana maijin daɗin zuwanta , yauma ice cream aka bata ta lashe kamar wata mayya , idan babu kwaɗayi ba wahala, Babana zaune a gaban malamin shi , yace a zana masa ƙasa a duba masa halin da uwar masu gida take ciki ? Waya ɓata min waya faranta min ? Ina cikin farin ciki ko ina cikin damuwa ? Akwai wani dake harina kuwa ? …… 05/09/2019 *MEELAT MUSA CE…* 🧚🏻♀⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 27 Gyatsa malam yayi sannan ya ɗauko wuri ya feshe da turare irin nasu na matsubbata , a saman farin ƙyalle ya watsa wuri in suka watse ko wanne bai haɗu da ɗan uwansa ba sai guda biyu suka haɗe a wuri ɗaya… Kallon Babana malam yayi sannan yace waye wannan yake tare da ita ? Baba yace Allah ya gyara aikin malam aikai zaka warware mana komai wannan ɗin shine yake tare da ita uwar masu gida kenan ko ? Girgiza kai malam yayi tare da cewa bana tunanin wani namiji zai sake shiga rayuwar Maryam saidai mu bincika muga waye wannan ! Cikin damuwa Babana yace aiko idan bai fita harkar uwar masu gida ta salama ba zai fita da ƙarfin bala’e ko waye , Iyakar bincike malam yayi amma ya kasa gano ko waye yake tare da Sultana , an buga ƙasar an zana an goge an sake rubutawa amma abinda binciken ya nuna wai a kulle yake , wai prvt istihara jama’a kun taɓa ji ? Hankalin Babana ya tashi yace malam babu abinda ya gagareka ,{ kai jama’a saboda an taɓo ɗiyarshi harya manta da Allah yana iƙirari wai babu abinda ya gagari malam } duba min miye kuɗirinshi akanta malam !Bincike malam yayi sannan ya ɗago ya kalli Babana yace kaga ka fita harkar rabata da ko waye wannan domin duk wanda akazo istihara aka kasa kamashi shirin duniyarshi ba ƙarami bane gaskiya , wannan yayi zarra kuma yasha gaban duk wani mai tada mishi ƙura abinda yasa nace haka idan har kace zakayi wani sihiri akanshi wallahi zaka lalace… Babana yace lalacewa kuma na nawa ? Aiko asiri zaka ma mutum idan kaga yana caca kawai ka barshi , tou Binna ba’a caca kaɗai ya tsaya ba ga caca ga neman mata idan akwai lalacewa wacce tafi wannan akan uwar masu gida na yadda zanyi wallahi ! Ƙara duƙufa malam yayi zuwa wani lokaci ya fara magana ba tare daya ɗago ba yace Aliyu wannan mutumin da muke magana yana gaf da Maryam kuma yana zuwa wurinta babu jimawa zaizo da farin ciki amma zai koma da ita yana mai baƙin ciki , abinda zai kawoshi da abinda zaisa ya tafi da ita duk ban gani ba amma tabbas zai tafi da ita kuma zata ɗauki tsawon shekaru babu wanda zaiji labarinta , Cikin tashin hankali Babana yace ina zai kaimin ɗiyata ? Malam yace ina zai kaita nima ban sani ba amma tafiya babu makawa , waye shi ? Malam yace sanin ko waye shi da ƙudirinshi duk sai mu jira zuwanshi , cikin ɗimaucewa Babana yace kafin yazo ina tare da “ya ta ina nan ina jiran zuwanka a gabana ka taɓa uwar masu gida saina gana maka azaba mafi girman azaba a duniya , ka fara lissafi daga yanzu kwanakin mutuwarka na tunkaro ka muddin ka tunkaro rayuwar ɗiyata kazo ina jiranka……. Ya ƙarasa maganar jikinshi yana wata irin kyarma idanuwanshi jajir kamar an watsa mishi yaji sai zufa yakeyi kamar wadda maciji ya sara…. Malam ya tausayawa Babana dan haka yaci gaba da bincike amma Allah ya ɓoye mutumin da zai shigo rayuwata , cikin tausayawa yace Aliyu kayi haƙuri tunda nake dakai baka taɓa nema baka samu ba sai wannan , kai kanka kasan iskancin da Maryam ta taro ba ƙarami bane banda muka dage akanta da yanzu bata taruwa a garin nan sanin kanka ne , Da sauri Babana ya rufe idonshi dan duk duniya ya tsani a danganani da kalmar iskanci , laya malam ya miƙowa Babana yace gata nan kaje ka samu jaririyar mage sabuwar haihuwa wacce dai bata buɗe ido ba , tou a yage bakinta a saka wannan layar sannan a kashe magen a jefar da ita a tsohuwar rijiya , bazan maka bayanin komai ba zaka zo ka bani labari yadda Maryam zata watsar da kowa da komai ta dawo gareka… Hahaha Babana yayi dariya irin ta basawa tare da cewa godiya nake malam uwar masu gida zata dawo gareni , zata manta da duk wani abun daya faru a baya ta dawo nutsatsitsiyar ta kamar baya , godiya Babana yayi sannan ya tashi ya tafi…. Baccin dai babu daɗi dan ko da nayi bacci ɗaya farkawa nayi daga nan na shiga tunanin rayuwa da tunanin mutuwana wacce zata iya riska na kai tsaye ba tare dana shirya ba , ina ƙoƙarin koyawa zuciya tsoron Allah na canja halayya amma sam sai zuciyata ta karɓi huɗubar sheɗan cewa yarinya dake ? Duka shekarunki nawa a duniya ? 17 zuwa 18 ne ai mutuwa ma baza ta wani zo wurinki ba ki dage kawai ki more talatarki kafin larabarki ta riske ki….Karki kuskura ki bar bariki ba tare da kin kafa tarihi ba , ki zuge rayuwarki kaf wata rana zata tofo domin rayuwa ita da zogala basu da wani banbanci kinga dai zogala kullum cikin zugeshi akeyi amma kafin wani lokaci ya sake fitowa , mafita ɗaya ce su Amisty kawai zaki kora sai ki shiga cikin ahalin Baba ki sake haɗo wata daba , yess 🤷🏻♀ dama Baba ƙarami yacemin karuwa zan koyawa “yar sa karuwancin idan an tashi kwatance a cikin ahalimu za’ace karuwai biyu idan har na bari na zama karuwa ni ɗaya gori bai ƙare ba har ɗiyan ɗiyana amma idan na taɓo wasu a ciki shiru zakuji ustaz ya samu mace…Da safe bayan na gama duk abinda nakeyi wanka nayi na shirya cikin riga da zani na atamfa nayi ƙofar gida , dukansu a saman dakali na samesu zaune hada Amisty sallama nayi musu sannan na samu wuri na zauna , a cikinsu babu wadda yaimin magana kuma babu wadda ya ansa min sallama , sukaci gaba da labarinsu , Ban damu ba domin dama su ba ma’abota ansa sallama bane ba , cikin girmamawa Amisty ta taso tazo gabana ta durƙusa da wainar filawa an daka mata tashshi mai shegen daɗin ga tumatur da albasa tasha kallo ɗaya nayi ma wainar yawu na ya tsinke , Amisty tace ga abinda kike so nayo miki mother , Cikin farin ciki na ansa tare da fara kwararawa Amisty godiya sannan nabi kowa nace yaci , murmushi Amisty tayi tare da cewa ai kowa yaci taki ce ke ɗaya uwar gidan kwarata , jinjina kai nayi tare da miƙawa Amisty nace tou kici kema , no nikam bana ci kinsan waina bai wani dameni haka ba , miƙewa nayi tare da cewa ai wannan shagalin sai an rufe ƙofa , Dariya sukayi gaba ɗayansu tare da cewa sai kace dai kin samu mijin zalifa ? Nima dariyar nayi ba tare da shigewa ciki , umm waini za’a cuta da gwangwanin fulawa ɗaya tashshi naira talatin da manjan naira hamsin , Amisty kenan idan har bakisan halina ba har yanzu lallai babu ranar da zaki gane wace ce Sultana… Ina shiga cikin gida ɗakina na shiga na kwashe wainar na zuba a leda bayan na gama na fito na zubar a bola , ɗaki na koma naci gaba da danƙarar tashshina saida na haɗa zufa na tabbatar bakina ya kama tashshi sosai sannan na fito ƙofar gida da tissue ina goge majina , A gaban Amisty na ajiye flet in tare da ƙara fyace majina idona yayi jajir sannan na zauna kusa da Amisty , murmushin mugunta tayi tare da lasar bakinta kamar mayyar da ta daɗe batayi kamu ba , nima murmushin nayi tare da kallon Amisty nace ɗan matsa daga gefe kar ayi abun kunya bisa titi ! Kallon su Hafsa tayi tare da ɗaga musu gira alamar tayi nasara, ɗan cije leɓona na ƙasa nayi tare da ƙanƙance idona na dama , kallona Amisty tayi sannan tace wane irin abun kunya za’ayi ne ? Murmushi nayi tare da cewa ji nake kamar in lashe ki , na nuna lashewar da harshena sannan na haɗe haƙorana na gaba sukayi ƙara ƙass. Uhum kwarata kenan gaba ɗayansu sukayo kaina kamar an watso mutane a doka daji , yadda namun daji ke kawo hari kowa ya ɗauka karya rasa , murmushi nayi tare da ajiye hannuwana ta baya na jigina dasu ina kallonsu , Hafsa tace uwar room ya kikeji ne ? Rufe idanuwana nayi tare da girgiza kaina sannan nace ai bama zan iya musultawa ba ,Nana ta riƙo ƙuguna tana kallona bayan wani lokaci tace ɗan daure ki misilta mana yadda kikeji ! Har yanzu idanuwana a rufe yake nace misali kece aka rufe a ɗaki kwana biyu babu ci babu sha idan aka fito dake kika ga abinci wane irin ci zaki masa ? Amisty tace ai ƙalu bale ga duk abincin dana damƙa , buɗe idona nayi sannan nace tou idan aka ajiye miki farfesun kaji sai aka kawo miki kwaɗon ganzo ko garin kwaki a ciki wane zaki ci ? Hafsa tace ai kowama kazar zaici , dariya nayi tare da cewa me yasa zaki ci kaza kibar ƙanzo ? Amisty tace saboda itace tafi daɗi da amfani a rayuwata , Gyara zama na nayi nace to idan kika samu namiji kika samu mace a ciki wannen zaki ɗauka wane zaki bari ne ? Amisty tace ai mace ba’a haɗata da kowa domin ita tafi kaza daɗi ke wane zaki ɗauka wane zaki bari ? Ta ƙarasa maganar da tambayana…. Gyara bakina nayi tare da cewa gaskiya dani namiji amma yanzu mace nake so nima , age agegege….. Kunji wani sabon taken iskanci wai agege , gaba ɗayansu suka faɗi age agege , Saida na gama kallesu tsaf sannan nace amma ina da sharaɗi fa ! Amisty tace faɗi sharaɗinki mother , yawwa idan dai zan faɗa harkar lesbian gaskiya sai kun bani haɗin kai na tsaya saman ƙafafuwana mun kora duk wani namijin bariki ta hanyar tambayarshi abinda yake bashi sha’awa a bariki , ta haka zamu gano inda matsalar take zamuyi gyara domin ceto matan auren da suka rasa mazajensu , domin gaskiya bana iya haɗa bariki da harkar mata , Shiru sukayi suna kallon junansu , nima ban sake magana ba ina saurarensu abinda zasu ce , Hafsa tace meya shafi harkarki da rashin kula namiji kuma ? Salon nawa ne a haka gaskiya dan idan baku manta ba yanzu maza nake bana mata , amma tunda zan ajiye maza na ɗauki mata dole saina fitar da maza a rayuwata …. Da ido sukayi magana sannan sukace har zuwa yaushe zamuyi aikin ne ? Na sati ɗaya ne , na basu amsa , tou munji mun yadda suka amsa gaba ɗayansu , jinjina kai nayi alamar na gamsu , Hafsa tayo ta kusa da fuskata da wani banza bakinta zata sunbaceni , murmushi nayi tare da tare bakin ta da ɗan yatsa na nace yi haƙuri hajiyata lokacin naku bai fara ba , A hankali taja baya , murmushi nayi a zuciyata tare da cewa Mother ta ibi ruwa ta jefa guga duk wanda yai wannan yazo da zamba , ko akan wannan zasu ɗau misalai , domin Sultana tayi naɗi da lauje , “yar birni tayi nitso da ƙoƙo gani naci banza zan zare adda , kowa yayi ƙuri sai yayi muzu a ƙarshe mu zuba dani daku… A ƙofar gida muka yini dukanmu amma ni ina tashi naje nayi sallah idan lokaci yayi kuma dana gama nake dawowa domin duk iskanci su Amisty a saman tafin hannuna yake , duk wani barbaɗe² ankare nake dasu domin suna sakin layi cikin magarnarsu , ni banci ɗiyar kowa ba uwata batayi ba babu wanda ya isa yayi akaina kallon biri sukemin ina musu kallon ayaba zasusha mamaki ranar da film in ya ƙare…. Da daddare , kamar yadda ƙofar gidan ya saba a ko wane dare haka ya fara ɗaukar harami motoci suka fara layi ƙamin yadda suka saba , kamar yadda muka saba muma a ko wane dare haka muka fito ina gaba su Amisty suna biye dani a baya , dan yau a gida zata kwana tunda mijin Asma’u gidanta yake yau… Wani zafaffen Alaji ne yace Allah ya taimaki uwar gidanmu , harna wuce nayo baya dan haka aka ajiye min kujera na zauna suka koma bayana dukansu suka tsaya kamar yadda suka saba , gaisawa mukayi na tambayeshi iyali ? Lafiya qalau yace tare da ɗan maida idonshi ga waya , murmushi nayi tare da cewa Alhaji wai matanka nawa ne ?Shiru yayi baiyi magana ba yaci gaba da kallon wayarshi , Alaji na sake kiran sunanshi , miƙomin wayar yayi tare da cewa ko kema zaki kalla ne ? A face buk sai maganarshi akeyi Allah dai yasa kar bakin duniya ya kashe shi mutane suke tayin posting hotunanshi suna tayashi murna…Ya faɗi maganar tare da miƙomin wayar , ƙin ansa nayi Hafsa itace ta ansa bayan wani lokaci tace Alhaji ya naga ana haɗashi da wata mai siffar maguna , dariya sukayi gaba ɗayansu Amisty tace ke kuma mai siffar kisau , duk kallo sukayi dukansu A ` i tace aiko wannan mai kyau ce gaskiya kedai kawai kice kinajin kishi , Alhaji yace ai itace zai aure ɗiyan gwamnan jigawa ce , sai yanzu na gane ko hoton waye ake kallo , Amisty tace yaushe za’ayi bikin ne ? Alhaji yace ƙarshen watan nan shi gwamnan keta sauri dan yaga Dikkon so yake ya zuƙe dandai suna da zuminci amma da bana tunanin za’ayi auren nan gaskiya… Miƙomin wayar Amisty tayi tare da cewa kalli mutuminki zaiyi aure , tsoki nayi tare da cewa ta ina ya zama mutumi na kuma ? Hafsa tace wanda kukayi faɗa asibiti wai mother mema ya haɗaku dan a lokacin naga kuna abu cikin gayya² dadai gani akwai azazza a tsakaniku. Murmushin ƙarfin hali nayi tare da ansar wayar amma banba Hafsa amsa ba , kallon hoton nayi yayin da wani hadarin baƙin ciki ya taso min , tsoki nayi tare da cewa Hafsa siffar me gareta kika ce ? Hafsa da baƙin ciki ke gurgurawar zuciya tace shegiya tsinanniya mai siffar karnuka ai in Allah ya yadda wannan auren babu ubanda zaiyi shi , Kawai dai haka nan nakejin babu daɗi a raina , zuciyata kuma tana kwaɗayin ƙara kallon hoton Dikko , amma na hanata tare da cewa kwantar da hankali keda zakici mutuncishi saurin me kike bayan lokaci ya kusa…. Maida hankali na nayi wurin Alhaji tare da cewa Alhaji matarka nawa ne wai ? Mata ta ɗaya mene ne wai ? Ba komai na bashi amsa tare da cewa tou me yaja ra’ayinka na faɗowa matan bariki haka rana kwatsam ? Kallona yayi cikin ɓacin rai yace me yasa kikemin irin wannan maganar da Allah ? Nima kallonshi nayi ido cikin ido sannan nace haka tsarinmu ya koma dole duk wani namijin dake cikin barikin nan saiya faɗa mana abinda ya kawoshi bariki , idan ya faɗa mu kuma sai mu bashi tsula²n mata ya more daga garesu saboda munyi oder manyan mata daga jahohi da dama , haka tantancewa mukeyi mu gano namijin da ya kamata muje dashi a cikin wannan tafiya tamu mai taken bariki ta giga….. 07/09/2019Taku a kullum … 👇🏻*JAMEELA MUSA…* 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 28 Kallo Alhaji ya bini dashi mai nuni da yama rasa abinda zaicemin , murmushi nayi tare da cewa da Allah kar kaga kamar cin fuska ne ko wani abu ko zaka taimakamin naga hoton matar ka ? Me yasa kike son ganin hoton matana ko zakije ki haɗamu da ita ne ? Ya ƙarasa maganar cikin sigar barkwanci , murmusawa nayi tare da cewa haba Alaji yadda da arne shi yake sa aci yankashi , kuma daɗin aure kesa mata tace miji Baba… Ganin hoton iyalinka bashi ne yake nuni zan faɗa ba , nasan gidanka komai da komai naka na sani hoto kawai zan gani sai nayi gaba abuna… Amma kafin na tafi don Allah me yaja ra’ayinka ka afkowa matan bariki bayan ka baro naka matar gida ? Ɗaure fuska yayi tare da cewa me yasa kike so kimin haka wai ? Dani dake da ku dukanku taimakekeniyar juna mukeyi manta da lamarin matana da kuma abinda yasa na faɗo barikinku mu fuskanci abinda ke gabanmu ! Miƙomin wayar yayi da hoton zuƙeƙiyar matarshi wacce ta gaji da haɗuwa duk inda ake neman mace takai kuma duk inda ya nuna matanshi abun kallawa ce , gaba ɗaya tafi su Amisty komai na morewa amma bata kai diddigen Sultana ba , danni a tara mace dubu baza’a iya samo ɗaya kamarni ba , Caf na faɗa tare da kallon Alhaji sannan nace wannan kyakkyawa ya akayi ka baro kyau siga da nagarta ka faɗowa kwarin mata ? Me matan bariki suka fi matar ka ? Me yasa ka kashe sunna kake ƙoƙorin ɗabbaƙa zunubi ? Me yasa kabaro inuwa ka dawo rana ? Ya akayi kabar rahama ka dawo azaba ? Me matan bariki sukafi matar ka don Allah ? Me ya ɗaukar maka hankali da macen bariki har ka baro taka kazo wurinmu……. ? Kallo Alhaji ya bini dashi na kece abun tausayi mai ƙaramar shekaru dake kina ɗaukar kayan daya fi ƙarfinki , kamar nasan abinda ke zuciyarshi nace manta dani ka fuskanci taka rayuwar , nasan matsayin zina , illolinta matsalolinta wahalhalunta tashin hankalin dake cikinta da kuma bala’en dake tare da ita , san zuciya da ɗaukar huɗubar shaiɗan ya mantar dani , domin yawan kusantar saɓo yana hana ganin girman zunubi , kasan surar da Allah ya sauke akanmu mu mazinata , ina matsalar take tsakanin kai da matar ka ne ? Gyara zama Alhaji yayi sannan yace :• me yasa matan bariki suka fi iya jan hankalin namiji ? Ba tare dana kalleshi ba nace shaiɗan ne yake ƙawata maka su domin yasan zina hanyace da take kai mutum ga halaka , zina tana zubar da mutinci tana rage ma mutum daraja a wurin ubangiji sannan mutuncin shi zai ragu a wurin al’umma kuma zina tana rage ƙwarjini fuska , Har yanzu baka bani amsar tambaya na ba , miya ja ra’ayinka shiga harkar bariki wai ? Alaji yace matan bariki kullum a shirye suke basa taɓa gajiyawa da ansar buƙatarka duk lokacin daka zo musu zasu anshe ka cikin farin ciki ba tare da gajiyawa ba , zaka kwanta da mace babu wari a jikinta babu ƙarni ko zarni bare kuma hayaniyar “ya “ya , yayin da zaka kwanta da matarka lokacin zata fara cewa batayi ma yara shimfiɗa ba , kana mata magana tana wani fiffizge kai tun kana sha’awar abun har yazo ya fita akanka , Kallon Alaji nayi sosai sannan nace , filawar bisa hanya tasha banban data cikin gida , mace kamar filawa take idan ta samu wuri mai kyau kuma akayi mata ban ruwa yanda ya kamata idan dai tasha ruwa ta ƙoshi duk wanda ya gani sai ta bashi sha’awa , lokacin da filawa ta rasa ruwa zata bushe ta soye duk wadda ya kalleta baya sha’awar ƙara kallonta , to haka mace take , matan bariki wayau suke muku kuna basu kuɗi suna gyara jikinsu a cikin kuɗin da kuka basu a ciki suke siyan abunda zasu ja muku hankali dashi , matarku ta sunna tana can viseline in da zata shafa wahala yake mata , taya zata gyara bare har ta baka sha’awa ? Idan baza ka damu ba zanyi magana da matarka idan Allah ya kaimu idan har tabi shawarata tabbas zaku samu rabauta , kai kuma zan koya maka yadda akewa mace ban ruwa …. Shiru Alaji yayi zuwa wani lokaci yace babu damuwa kije na yaddar miki , godiya nayi masa sannan na miƙe ɗauko kujerar sukayi suka biyoni da ita yayin dana tsaya wurin wata motar… Ajiye min kujera akayi na zauna , motar a buɗe take dan haka na ɗora ƙafata ta haggu a saitin mazauni driver tare da cewa malam barka da dare ! Allah ya taimaki uwar ɗakinmu ya haƙuri damu ? Alhamdulillah na faɗa tare da cewa ya iyali ? Kamar jira yake yace tana can shegiyar saida nayi mata jakin duka na fito , kallon agogon hannuna nayi ba tare dana kalleshi ba nace me tayi maka ne ? Ta rainani idan na shigo da leda takemin sannu da zuwa idan banzo da itaba ko daga ɗaki bata fitowa , yau na yanka rago dake duk sati nake yankawa , mahaifiyata tazo nace a ibar mata shine tayi mata rashin kunya ni banji daɗin abunba shi yasa nayi mata duka na baro gida , Kallonshi nayi sannan nace to me kazo kayi nan ? Dariya yayi irin ta sakarkari sannan yace nazo a ban natsuwa , jinjina kai nayi sannan nace tou yau babu maganar bariki kaje gida ka lallashi matarka muna zuwa gidan idan Allah ya kaimu , ina faɗin haka na miƙe nayi gaba , ɗauko kujerar sukayi suka biyoni domin cikin gida na nufa… Hayani mazan suka farayi tare da cewa ya zanyi musu haka ne ? Ai haka ma babu adalci , a zuciyata nace wannan matsalarku ne ba nawa ba , Ina shiga gida na shige ɗakina , Amisty ta rufomin baya , itace ta kulle ɗakin domin dare yayi kowa a gajiye yake babu abinda yake buƙata sai bacci , kayan jikina na cire na ɗaura zanin bacci , Amisty kuwa da kayanta tayi kwanciyarta , Tunda na kwanta fuskar Dikko kezomin a idanuwana , ya ƙara kyau abu ga farar fata ga hutu ga gayu gemunshi yasha gyara sai kyalli yakeyi , an gyara ƙasimbar ta kwanta sosai dake farine sai abun ya bada wani irin sirrintaccen burgewa , shi ba wani tsoho ba amma dole sai ya zama tsoho me yasa yakeyin haka ne ? Dan yaga gemun yana mishi kyau gaskiya fa yayi mishi kyau shi yasa yake ɗaukar hankalin mata , gemu da ƙasimba make up in maza kenan… Ajiyar zuciya na sauke tare da gyara kwanciyata , damuwa nakeji sosai ina ta ƙoƙarin molaƙe rayuwata ashe shi Dikko yana can yana ƙoƙarin gyara tashi , zaiyi aure ya barni ina cikin karuwanci , ina ganin zan masa rata ashe shine zaimin rata , ya zama shugaban al’umma ta wani gefen ni kuma na zama shugabar rusa rayuwar farin cikin wasu da tawa rayuwar ? Hawaye ya cikamin ido bayan sun gangaro na maida numfashi dakel sannan naci gaba da zancen zuci ! Me yasa na zaɓi na zama karuwa ? Me yasa banyi ƙoƙarin zama ta gari ba ? Mai makon na zama waraka ga al’umma sai na zama cuta a garesu… Kukan zuci naci gaba dayi irin mai kartar zuciyar nan wanda kesa mutum yaji kamar zai mutu shi naci gaba da yi numfashi na naji yana ƙoƙarin fita daga jikina dolena na tashi zaune da sauri naci gaba da fita dan ceto tawa rayuwar…. Zaune yake ya hakince irin zaman nan da yakeyi na ya raina mutane , ɗage yake kallon kowa yayin da bakinshi ke motsawa a hankali cikin kwarewa da goguwar iya cin cingom , Al ‘ Ameen ya kalla sannan ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi yace wai mema zance mata idan tazo ? Murmushi Al ‘ Ameen yayi tare da shafa kanshi yace tuba nake ranka ya daɗe , dan tunda akayiwa Dikko kyautar Sadiyya bai taɓa zuwa ba sai yau , baya ko waya da ita yauma Dadynshi ne ya matsa mishi shi yasa yazo ! Dan ko hotunansu dake yawo a social media haɗawa akayi bashine da ita suka jera suka ɗauka ba , Dikko baiyi magana wa Al ‘ Ameen ba Sadiyya ta shigo cikin palon , gaisheta Al ‘ Ameen yayi sannan ya fita… Cikin karairaya da kwarewa da bariki tayo inda Dikko yake zaune , ɗan taɓe baki yayi a zuciyarshi yace bari inga rashin kunyarki , bai gama tunani ba ta zauna tare da ɗora kanta a saman kafaɗarshi tana mai sauki ajiyar zuciya cikin yanayin mai nuni da tana cikin shauƙi, daga waje har ciki Dikko baiji wani shock ba , dan haka yace sauke kanki mace bata hawana , na miki uziri nayau idan kika sake zaki samu matsala…. A shagwaɓe tace haba diye { dear } … Yanayinka sch ne amma ya kake abu kamar class ? Banza Dikko yayi baice komai ba , jinyayi shiru yasa tace ya hanya da mutane ne ko ? Nan ma bai bata ansa ba , zagba surutu taci gaba dayi tare da cewa idan sukayi aure zata mishi soyayya , ba komai kake ta wani jan allo dana fara rubutuna zaka sauke , hauka dai tayi ta zuba mishi tare da son ƙara kwanciya jikin Dikko amma abun ya mata girma , Bayan ta gaji da surutun tayi shiru , can kuma taci gaba , kasha drinks mana , ta ci gaba da lissafo duk abinda aka kawoma mashi , har ta gaji ta sake ɗaukewa , ganin Dikko bazaiyi magana ba yasa ta fashe da kuka cikin kuka take cewa haba Yaya wai me yasa baka so na ne ? Ina ta magana amma kamin shiru ka mayar dani kamar wata mahaukaciya ! Nifa “yar uwarkace ka soni dan Allah kodan zumunchin dake tsakaninmu…. Kallonta yayi sannan yace ya isa , kije ki kwanta a gajiye nake muyi magana anjima , goge hawayenta tayi tare da cewa ai ko na kiraka ma baka ɗauka , karki damu zan ɗauka insha Allah , murmushi tayi tare da miƙewa cikin farin ciki , shima murmushin yayi zuciyarshi tace dama An matane a wannan yanayi , wata “yar jakace a gefenshi ya nuna mata yace ɗauka… Ɗauka tayi babu ko godiya ta fice a palon , wayarshi ya ɗauka ya nuno hoton Sultana , ya ɗauki tsawon lokaci yana kallonshi bayan wani lokaci yayi magana a bayyane cewa kuka kikayi , ina gane yanayin farin ciki da damuwa idan na kalli hotonki , duk yanayin da naji na shiga tou kin shiga yanayin meke damunki ne ….? Banda ajiyar zuciya babu abinda nake saukewa har yanzu zaune nake ban kwanta , ɗan ɓata rai Dikko yayi a daidai wannan lokacin ya kalli hoton Sultana sannan yace ki daina damuwa ki zama mai farin ciki a ko wane lokaci , taɓa screen in wayarshi yayi tare da cewa kiyi bacci cikin aminci da salama …. Ajiyar zuciya na sauke tare da komawa na kwanta , ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni , ….. Koda Dikko ya koma masauki wanka ya farayi duk saida ya gama abinda yakeyi sannan ya cire wayarshi daga airplane mode , kamar wani munafiki wai ba’a kunna waya sai dare sosai zai duba saƙon da aka turo masa , a lokacin zai shiga yanar gizo , a lokacin zai ansa waya idan aka korashi itama sai wacce yakeji zai iya ɗauka , da zaran kuma ya gama abinda yake zai sake rufewa sai kuma wani daren , wayarshi ɗaya kuma da ake samunshi ba kowa yake da number ba , daga gidansu saida wanda shine yaga dama ya bashi , dan dayaji an kirashi da wayar to yasan kirane mai mahimfaci , Wani vidio ya buɗe da abokinshi ya turo mishi , kafin vidion ya buɗe ya fara karanta rubutun ƙasan vidio da akayi , _Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un , Allah yayiwa Fatima rasuwa sakamakon fyaɗe da akayi mata , abun babu kyan gani kuma ko su waye da gayya sukayi mata sun wulaƙanta yarinya bataji bata gani ba , sannan suka ɗauki vidio a waya suka bada wayar a cikin envilop aka kaiwa Babana har Office dan lokacin kwananta ɗaya da yini ba’a ganta ba , gawar kuma suka zo suka jefar a ƙofar gida…_ La’ilaha illa anta sub’hanaka inne kuntu minaz zalimeen Dikko ya furta a lokacin daya gama karanta saƙon ya fara kallon vidion , ƙattin maza ne sunkai su biyar amma duk sun rufe fuskarsu da maX , ihu Fatin keyi amma babu abinda ya damesu kowa burinshi ya biya tashi buƙatar , wani irin motsi Dikko yaji kwalwarshi tayi kanshi ya yamitsa da sauri ya ajiye wayar tare da dafe kanshi da dukan hannuwanshi biyu abinda yakeji da game da Sultana ya dawo mishi sabo…. Lahaula wala kquwwata illa billahil ‘ aliyyil azeem , Dikko yake ta maimaitawa ya ƙurawa kafet ido kamar Sultana ce a wurin , saida natsuwa tazo mishi yaci gaba da zancen zuci lallai ya cuci rayuwar Sultana shima bashi da banbanci da mutane biyar ɗin nan domin magungunan daya sha sun bashi wani irin ƙarfi wanda ko allura hauka akayi ma doki iyakar abinda zaiyi kenan dan nuna shi mai ƙarfi ne , hawaye ya cikawa Dikko ido tausayin Sultana ya ƙara kamashi lallai ya cuci yarinyar nan !Yau wane irin baƙin ciki iyayen Fatima suka shiga ? Wane irin ɗaci sukeji idan sukaga wannan hoto ? Ya Abbakar zaiji yayin daya ga wannan hoton akan ƙanwarshi ? Da nine ya zanji idan haka ta kasance akan ahalina ? Kwantar da kanshi yayi a saman hannun kujara ya rufe idanuwanshi duk yanda akayi akwai abinda Baban Abbakar yayi suka ɗauka fansa dan yanayinsu ya nuna a lokacin da suke aikatawa kamar biyan bashi ne sukeyi , Allah na tuba ka gafartamin ka sakawa An mata soyayya ta mai girma a zuciyarta , sona ya hanata bacci da tunanin kowa a duniya saini , ta daina jin maganar kowa sai tawa , ka saka mata san kasancewa dani inuwa ɗaya kasa mata firgici idan ta yini ko ta kwana bata ganni ba , ka ɓadda mata tunanin kowa da komai na duniya saini , ka saka mata san jin muryata ka goge mata kuɗirin fansa akaina , nayi alƙawari zan zamar mata natsuwa zan zama uwa da uba data rasa masu kishinta bazan barta tayi kuka ba haka kuma zanyi ƙoƙarin sakata farin ciki , duk wanda ya ɓata mata ko yasa taji damuwa nine zan tsaya harsai naga tayi farin ciki , Allah ka gafar tamin ka goge damuwata a zuciyar an mata ta zama soyayya mai ban al’ajabi ga kowa , Buɗe idanuwanshi yayi tare da goge hawayenshi , sannan ya ɗauki wayar ya goge vidio ba tare daya gama gani ba , wayar Abbakar ya fara kira dan jajanta mishi kafin yaje mishi ta’aziyya , Sadiyya koda ta kira Dikko text ya tura mata idan ya gama zai kira , koda ya gama abinda yake ba wulaƙanci ba da gaske ya manta da labarin kiran Sadiyya , da tunanin An mata yayi bacci…. Da safe wanka nayi na shirya cikin riga da zani na atamfa , hijabi na saka sannan nacewa Amisty zanje in dawo ! Ina zakije tunda safe haka ? Ta tambayeni ! Takalmi na saka tare da ce mata zanga wani a bakin hanya , addu’ar a dawo lafiya tamin ni kuma na fice daga ɗakin…A ƙofar gida na anshi makullin mota na dana sa aka ɗaukomin , ɗan daba ɗaya na dawo dan ya rakani gidan Alaji koda an samu ɓacin rana , abinda yasa ban tafi dasu Amisty ba saboda kar ya zama naje gyara kuma gyaran ya zama ɓarna….. Tafiya mai nisa mukayi zuwa gidan Alaji , a ƙofar gida nayi parking sannan na fara kiran wayarshi dan dama banzo ba saida izininshi……… 09/09/2019*JAMILA MUSA…..* 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 29 Bai ɗauka wayar ba ya fito daga cikin gidan , ina cikin mota zaune nima ban fito ba , shine yazo har wurin mota ya buɗe gidan baya ya zauna amma bai rufe ƙofar ba , juyawa nayi ina kallonshi tare da cewa dana kira naji baka ɗauka ba nayi tunani ko baku tashi bacci ba ! Gyara maɓallin rigarshi yayi tare da cewa ai ina ganin kiranki nasan kina ƙofar gida shi yasa nace kawai bara na fito basai na wani tsaya ɗaukan waya ba , murmushi nayi na juyowa ina kallon gabana wato na juya daga kallon Alaji nace muje ciki to… Tou muje amma bata nan ta shiga maƙota , ɗan zaro ido nayi amma banyi magana ba , a zuciyata nace maƙota tun wannan safiyar ? Lallai akwai ƙatuwar matsala , sauka nayi daga cikin motar tare da cewa muje *Wane Yaro* ɗan daban da nazo dashi ,Rufe mota ta nayi muka nufi cikin gidan dukanmu , a ƙaton palon matarshi ya saukemu gafa kujeru har kujeru amma datti yasa sun tashi aiki , bakajin wani ƙamshi ko na tsitsiyar ƙamshi bare kayi tunanin zaka samu turaren wuta banda zarnin fitsari palon kaca ² a firgice babu abinda ke tashi sai wani ƙanni² a palon…. Saman hannun kujera Alaji ya zauna ni kuma kallabin kaina na ciro na shimfiɗa a matakalar da zata gangaro dakai cikin palon dan wannan kujerun idan har na hau su yau babu abinda zai hana ƙurajen ƙyama su fito jikina…. Fira muka farayi da Alaji ya ɗan fara karanto min matsalolin da yake fuskata , yace ga ƙazanta ga rashin ragowa ga fita babu gaira babu dalili , ga rashin godiya ko zai kashe kanshi ya bata bata taɓa masa godiya ba , wallahi idan har zai kwanta da ita sai ankai ruwa rana sannan kuma babu wanka bare yayi tunanin zai ji wani ƙamshi da zaisa mishi yaji wani shauƙi yayin da yake kwanciya da ita… Uhum har ga Allah ba sasanci ya kawoni gidan Alaji ba a wannan lokaci , ina da wani ƙudiri nawa na daban , ina so inga yanayin yadda yake hidima da gidanshi , surutar da matarshi take amfani da ita kuma har store insu yau sai naje dan inga idan naci gaba da tarayya da Alaji zai iya ɗaukemin duk wasu buƙatu na ? Dan nima in samu wanda zai tayani kula da tawa rayuwar , zan kuma bigi cikin matarshi ta faɗamin komai nasu da wasu sirrika na Alaji daga nan ni kuma zan ɗaukeshi sai tayi da gaske ma zata sake ganinshi… Babu ko sallama ta faɗo cikin ɗakin daga ita sai ɗaurin gaba hijabinta riƙe a hannunta , Abbu Afsar ka tashi kenan ? Bai kalleta ba yace na tashi daga ina kike ne ? Kallona tayi sannan tace wallahi gidan Naja naje tace zata shigo bata samu damar shigowa ba kusan kwana biyu mijinta ya hanata fita shine nace ta bari ni nazo , kallonta Alaji yayi tare da cewa ita da bata raina mijinta ba ! Ya hanata ta hanu ke kuma da kika raina naki sai kika fita babu izini na. Tsoki tayi tare da zama saman kujera tana cewa baka gajiya da tsegumi haba da Allah dan naje tou miye ? Murmushi nayi ina mai kallonta , gaskiya kyakkyawa ce sosai , ga kyawu har kyawu amma an kashe kyawun da ƙazanta , yarinyar mace kamar wannan tana zama da ɗaurin gaba , gashin hamatar ta kanshi idan kika kamashi zaki iya kitsashi saboda yawanshi , tana da haƙora masu kyau amma ta kashesu da rashin wankewa , kanta kuwa ƙaramar ƙarya kila yayi shekara rabonshi da a kwance , kitsone saman kan amma baka isa ka gane ta ina aka ɗauko tsagar kitson ba , Tou bamu dai gama maganarmu ba da Abbu Afsar Ummu Afsar ta shigo gidan , tsokin da tayi masa yasashi tashi ya fita daga ɗakin , ina kwana na gaisheta , ansawa tayi tare da fyace majina da gefen zaninta , sannan tace ban gane ki ba , Uhum ai baki sanni ba na faɗa ina sadda kai ƙasa cikin nuna mata ni ta gaskiya ce tunda nasha hijabi daga sama har ƙasa , kallona tayi sannan tace Allah sarki sannu da zuwa , ki dawo saman kujera mana !Nan ma yayi na bata amsa , bara na kawo miki ruwa , tou na faɗa yayin data miƙe tabar palon , babu wani ɓata lokaci ta dawo da wasu irin haɗaɗɗin kulololi masu matuƙar kyau da tsada , ta wuce taje ta ajiyesu a saman tebirin cin abinci , Saida ta ajiye sannan tace bisimillah mana , ta faɗi maganar cikin sakin fuska , banyi magana ba na tashi na nufi tebirin cin abinci yayin da Wane Yaro ya zauna a wurin dana tashi , Kujera taja itama ta zauna kusa dani sannan muka sake gaisawa, ɗora hannuna nayi saman kular da take ƙoƙarin buɗewa nace suna na *Sultana* ɗiya ga Aliyu Muhammad Binna , Babana sananne ne kuma ya shahara a harkar caca , dani da Babana da kowa nawa muna zama a gidanmu cikin kwanciyar hankali , nazo wurinke dan gyara miki wani kuskure Allah dai yasa banyi shishshigi da yawa ba….. “Yar gajeriyar dariya tayi sannan tace ke kuma me yace miki nayi masa ne ? Kallonta nayi sosai dan na fahimci yanayin rayuwar tata , bata da babbar ciwon dake damunta wanda ya wuce rashin ɗaukar shawara , tana da taurin kai sannan kuma abinda taga dama shi takeyi babu wanda ya isa ya sa tayi ko ta bari sai ciwon rashin wayau dake ɗawainiya da rayuwarta… Kauda kaina nayi daga kallonta sannan nace ni bai faɗamin komai ba , gyara zama tayi tare da cewa baya da aiki sai kai ƙarata bana san wanka bana shara bana goge ɗaki ban iya girki ba , ban iya kwanciyar aure ba , cikin hayani tace yaje ya nemo wacce ta iya duk wannan abun dana lissafo ban iyaba ta ƙarasa maganar da dukan tebirin data ajiye kulolin da ƙarfi… Cikin tsoro nace saurara kiyi haƙuri ba hayani ta kawoni ba , shin ko kina fama da matsalar rashin abinci ne ? Ko rashin sutura sabun wanka ko na wanki ? Rashin turare ko man wanke baki ? Cikin ɓacin rai tace babu abinda na nema na rasa dalili dai bazai yuwu ba kullum namiji yayi ta sussukata ni ba gero ba , Dariyar mugunta nayi mata tare dayi mata kallon wawiya , data riƙe mijinta ram a hannu da bai kallo matan waje ba , wannan ba matsalar Alaji bace itace ta kai mijinta ga halaka , na rasa abinda yake damun matan ƙarshen zamani , babu biyayyar aure ba ladabi mace ta mayar da mijinta kamar almajirin gidanta baida wani mutunci ko daraja a idonta…. Yake “yar uwata ki sani aure yana da babbar matsayi haka kuma namiji yake da babbar daraja , mijinki shine sirrinki suturarki aljannarki sai kin gyara rayuwar aurenki sannan zaki samu rayuwa mai daɗi a gidan duniya da ƙiyama dan miji ba abin wasa bane , mijinki ba abin wulaƙantawa ba ne sannan kuma mijinki ba abokin gabarki bane , abin ƙauna ne abun tausayawa ne a gareki , ki kwantar masa da hankalinsa sai Allah ya kwantar miki da naki , ki bashi natsuwa sai Allah yasa kema ki samu natsuwa , kisa mishi farin ciki sai Allah yasa kiyi farin ciki a gidan duniya da lahira…. Matan bariki suna da illa kuma suna tattare da masifun dasu ma kansu basu san suna dasu ba , bariki wuta ce mai azabar raɗaɗi da wahala , zina halakace kuma babbar cutace , me matan barike suke dashi wanda baku dashi ne ? Komai iri ɗaya ne abu ɗaya suke dashi wanda matan aure suka rasa , kuma suma matan auren suna da abu ɗaya wanda matan bariki basu da irinshi ! Wannan abu ba komai bane sai sakaci , shine abinda matan aure garesu , matan bariki kuma basu dashi , matan bariki basu da sakaci abinda matan aure suka rasa kenan… Ummu Afsar ta saki baki ga wacce bata sani ba taci gaba da buɗemin sirrin mijinta wanda haka ba daidai bane ga duk macen data san abinda takeyi , ɗakinta da tsore inta babu inda bata kaini ba dan in gani da idona tana da komai na rayuwa tsaftarce da haƙƙin Alaji bazata bayar ba , tunzura ta nayi tare da cewa Eyy ki barshi gaskiya gaki ma yadda kike kyakkyawarki ko kun rabu sai kin samu wanda yafi shi , murmushin jin daɗi tayi tare da cewa ai cewa ma akeyi nafi ƙarfin shi , kallonta nayi tare da cewa gaskiya keɗin duniya ce da matsayin gidan sarauta… Sallama mukayi da ita tayomin rakiya har ƙofar gida inda nayi parking in motana , saida na fara tafiya sannan nasa Wane Yaro ya kiramin wayar Alaji , bayan ya ɗauka nace masa ina san ganinshi amma ya faɗamin sirrintaccen wurin da zamu haɗu , bayani yamin sannan nace masa na gode tare da kashe wayata… Kai tsaye gida muka nufa a bakin hanya na ajiye Wane Yaro ni kuma na wuce gida , a ƙofar gida nayi parking in mota ta na shige ciki , sallama nayi kamar yadda na saba na wuce ɗakina , ruwa na zubo a boket naje na watsa sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata dan hutama rayuwata…. Bayan sati biyu , abubuwa da dama sun faru , ga lamarin iskanci na kuma yanzu na zuƙa hannu na , Babana kuma ya samu mage kamar yadda malam yace kuma ya aiwatar da aikin kamar yadda akace yayi , Na samu Alaji munyi magana dashi kuma ya faɗamin cewa yana san wayayyar mace “yar gayu wacce zata biya masa buƙatarshi a duk lokacin daya so , ba laifi yana da wanka kuma yana gayu kuɗinshi a sake yake ga mata , dan haka na ɗaura dashi cewa ya saurareni ina san na haɗa gidanmu sannan naci gaba da harkar bariki na, Da alkairi na nake shiga cikin ahalinmu , nakan basu kwance kaya , in siya musu kayan kwalliya idan na samu kuɗi , ina aika musu da kayan abinci kuma ina zuwa lokaci ² ina basu sha’awa kuma cikin hikima na fara musu tallar bariki , Duk wata hidimata yanzu Alaji shike ɗauke da ita , babu abinda na nema na rasa fanni abinci kuɗin kashewa da kuma suturu ya kwacemin duk wani abinda zaizo ya dameni , yauma ƙaton rago ya kawomin dan haka na sakashi a napep na tura Wane Yaro yakai gidan Baba ƙarani da 100k nace ya sayi icce… Babana kenan , ɗan duniya abin alfahirin uwar ɗakin kwarata , cikakken namiji mai dogon zamani , namijin duniya gatan mata , ka gansu ka ƙyasa ko ba sisinka su bika , baka gada ba haye kayi Sultana tai gado ɗan gado kuma saiya zarta….. Uhum Baba kenan , Amisty ce kwance a saman Baban Sultana suna ɓalgacewa bayan sun gama ɓalɓalewa yake tambayarta ya Uwar masu gida ? Tace tana nan cikin ƙoshin lafiya , Amisty itace take kaiwa Baban Sultana labarin halin da Sultana take ciki , kuma shine ya tirsasawa Amisty ta kwashe kayanta ta dawo zamani dan kawai ya riƙa jin halin da nake ciki , abin kunya Baba ka rasa macen da zaka huta da ita sai abokiyar “yar ka , dakai da Amisty duk ranar da Sultana ta gano ku zaku fuskanci babbar matsala…. Lokacin da Baba ƙarami yaga rago abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba dan babu biki ba suna kuma ba sallah kawai an bashi kyautar rago , yaji daɗi sosai a lokacin da Wane Yaro yaje kai rago ya samu Zainab da Farida a gidan dan haka daya tashi zai dawo suka biyoshi zuwa wurina… Nayi farin ciki da ganin “yan uwana , muka rungume juna cikin soyayya irin ta “yan uwan da suka daɗe basu haɗu ba , sannan muka shiga jajantawa juna yaushe rabo ? Bayan an gama suka tambayeni ko na fara kasuwanci ne ? Dariya nayi tare da ce musu sosai ma , me kike siyarwa ne ? Suka tambayeni kai tsaye nace *Karuwanci* shine sana’ar da nakeyi… Zasu fara wani mamaki nace karku wani damu kuma kar kuyi mamaki nayi amfani da huɗubar da Baba yake baku ku tashi ku nemi kuɗi domin ku kare mutunci kanku , huɗubar ce na ɗauka kuma da ita zanyi amfani kuma ma babu laifi an samu nasara tunda na siya gida ga mota kuma ina da “yan canjina , ku kun samu gida da mota ne ? Na tambayesu , shiru sukayi , murmushi nayi tare da cewa karku damu ƙanwarku ta kasa kuma ta samu masu siya nayi ciniki sosai dan haka kawai ku dawo nan muci gaba da zama dan tunda na siyi gidan na fitar da ɗakunan matan Baba shima Baban zan dawo dashi dan kasuwa bata yuwuwa babu shugaban ƙungiya…. Gaba ɗaya wutarsu ta ɗauke musu basu da zaɓin daya wuce su dawo zama tare dani tunda inda suke a raɓe suke , koda suka tashi tafiya na basu kuɗi na basu kayan sakawa , sunyi godiya sosai tare dacemin insha Allah zuwa jibi zasu dawo , rakiya nayi musu suka tafi… Baba ƙarami da jama’ar dake da sauran mutunci a idon Babana sune suka sameshi suka bashi magana cewa ƙauracemin bashi ne zaisa nayi halayen kirki ba , ya dawo kusa dani wani abun ma a gaban idonshi bazanyi ba , Baba yace shi ba wani abu yakeji ba kawai kunyata yakeji ya zama sokon uban daya kasa ceton “yarshi daga shiga wata baƙuwar rayuwa ! Magana suka ba Baba harya amince zai dawo gidana , kuma yaje wurin Maman Fa’iza suka ce zasu dawo suma jibi idan Allah ya kaimu dan haka gida zai dawo kamar yanda yake da , su Nana Karima da suke zaune a gidan kuma bazan tada su ba saidai idan sune suka tashi da kansu… Da marece ina kwance Amisty ta shigo ɗaki babu sallama , jakarta ta ajiye ta ɗauki buta ta nufi bayan gida , tana fita na tashi da sauri naje na ɗauko jakarta na buɗe , kuɗine masu yawan gaske a ciki dan haka na tattarasu gaba ɗaya na kwashe su na ɓoye sannan na koma saman katifa nayi kwanciyata kamar yanda nake daga farko… Ban daɗe da kwanciya ba ta shigo tare da cewa tashi gidansu Hafsa zamuje bata da lafiya , subahanallah na faɗa tare da tashi zaune nace meya sameta haka ? Ƙonewa tayi ta faɗi maganar tare da ɗaukar jakarta , nima tashi nayi banko ɗauki gyale ba makullin mota kawai na ɗauka tare da cewa muje , tunda nake ban taɓa zuwa gidansu Hafsa ba sai yau zan fara , a tsakar gida nayiwa su Nana saina dawo sannan mukayi waje dani da Amisty… Daga ni sai Amisty muka tafi ni naja motar har muka isa gidansu Hafsa , har zanyi parking a waje Amisty tace inyi horn za’a buɗe , banyi musu ba na dannan horn mai gadi ya kwashe mana get muka shige , kusa da motar Hafsa anan nayi parking in mota ta sannan muka shige ciki… Har muka isa ɗakin Hafsa bamu haɗu da kowa ba , palon ɗakinta ma ba kowa dan haka bedroom muka shiga kai tsaye , Hafsa tana kwance a saman gado an naɗe ƙafarta da farin bandeji , idonta a rufe kila tanayin bacci ne , zanyi mata magana Amisty tace karki tasheta bacci takeyi , banyi magana ba na samu gefen gado na zauna , palo Amisty ta koma babu jimawa ta dawo ɗauke da wata ƙatuwar roba bansan ko miye a ciki ba , wurin ƙoƙarin ta hawo saman gado ta ɓareminshi kaf a jikina , tsakiyar idonta kaɗai na kalla na gane wannan abun shiri ne , Kallon kokon data makomin a jiki nayi sannan na sake kallonta , kiyi haƙuri Amisty ta faɗa , ba koma nace cikin sanyi jiki dan Amisty tsoro take bani , cikin sigar lallashi tace ki shiga toilet saiki wanke , banyi magana ba na miƙe na nufi inda Amisty ta nunamin da ɗan yatsanta , kokon gaskiya baya wankuwa gefe² dole sai na cire kayan nayi wanka gaba ɗaya dan babu inda bai kai ba ,Cire kayana nayi nai wanka , bayan na gama na wanke kayana na ɗauro towel na fito da kayan a hannuna da niyar ince a ina zan shanya ? Ina fitowa naga Hafsa tana rufe ƙofa da makulli bayan ta gama ta tillashi can saman waldrop , bayan ta tilla ta warware bandejin sannan tace hausawa sunce mai haƙuri mawadaci nasha haƙuri kuma na daɗe ina dakon yunwa da ƙishirwa , yau zanci insha zan kore duk wata tsohuwar yunwar dake cikin hanjina… Dariya sukayi tare da tafawa ita da Amisty….Amisty ta ansa da cewa lallai zamuga wasan kura ga uwar kwarata gata lesbian , Hafsa tace tabbas yau zan koya mata irin namu salon tunda muma ta koya mana irin nata , a’uziyya naja tare da ƙara riƙe towel in jikina gam , murmushi Hafsa tayi tare da cire rigar jikinta tace kinga sheɗan baya tafiya gashi ma ya fara cire rigar jikina , kin gani ta faɗa yayin da ta ɓalle bireziyarta , ja baya na farayi da niyar komawa toilet ina ihu a kawo min ɗauki *kwarata* sun rufeni a ɗaki ,Dariya Hafsa tayi tare da shan gabana tace ina zakije ne ? Kuma babu mai cetonki dan gidan ma babu kowa , shi yasa nace Amisty ta kawomin ke kwana biyu zakiyi kawai kafin nan nasan kema kin zama “yar hannu… A saman bedsite naga kwalbar mai mai gurguwa dan haka da sauri na yada kayana na ɗauka na kwaɗawa Hafsa a kai harsai da jini ya fita , ajiyar zuciya ta sauke tare da fizgoni tace nagode ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin haɗa bakina da nata , da ƙarfi na tureta naci gaba daba da ihu ina kai mata duka , kwata ² bataji dan haka ta janye towel in jikina , ita da Amisty suka kamani mukaci gaba da kokowa da ƙarfin bala’e suka ɗorani saman gado….. 11/09/2019 💅🏻 *MEELAT MUSA NE….*⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 30*_Ina miƙa saƙon ta’aziyya ga “yar uwar aikinmu Halima Yahya 20 Allah ya bada haƙurin rashi ubangiji yasa ta huta Allah ya kyautata namu ƙarshen idan ajaliyyarmu tazo…._* Amisty ta danneni da ƙarfin tsiya Hafsa ta sauka dan ɗauko igiyar da zasu ɗaureni da ita , murmushi nayi tare da kallon Amisty sannan na nunata da yatsa na juya na kalli Hafsa itama na nunata da yatsa sannan na gaggaɓe da wata irin dariyar dani kaina bansan na iyata ba , Lokaci guda kuma na ɗaure fuska kamar bani nayi dariyar ba , da sauri Amisty ta kalli Hafsa suka kalloni a lokaci ɗaya , hawo saman gadon Hafsa tayi tana ƙoƙarin riƙe hannuna ta ɗaure , kallonta nayi kamar wata sakara sannan nace dake da Amina ku tabbata idan har kuka min wani abu kasheni shine kawai mafita a rayuwarku , amma na rantse da girman Allah wanda ya halicceni ya halicceku dani daku dukanmu shi muke bautama , mutuwa ta ko taku zata iya zuwa ko wane lokaci yanzu ko anjima , ko kuyi ko ku bari yanda kuka buɗemin sirri saina buɗe sirrin uban kowa a cikinki , Bayan buɗewa saina tona musu asirin da ku kanku sai kunsha fiya² kun mutu saboda baƙin ciki , kar wacce ta ɗauremin hannu ko ƙafa kuyi duk iyakar iskanci da kuka iya , bashi ne kuma bazaiyi kyau ba a lokacin da zan biyashi akan iyayenku , Muni , baƙin ciki , firgici , tashin hankali gaba ɗayanku zaku fuskance su yayin dana shigo rayuwarku , ina da illa kuma ina da bala’en haɗari haka nake dasa baƙin cikin da baya mantuwa a zuciyar duk wanda ya nemi ya dasa baƙin ciki a rayuwata , ciwo gareni haka nake da ɗaci kuka akemin kamar mutuwa yayin da na shigo gida dan ruguza farin ciki zuri’a ɗaya , ku lasa ku maida miyanku tunda kun buɗa ni kuma nayi alƙawari daga yanzu rayuwar farin ciki ta ƙare gareku , Kallan kallo suka tsaya yi kowa da abinda take saƙawa a zuciyarta , tsoki nayi tare da cewa kuna ɓatamin lokaci domin ni ruwan ƙorama ce zuwa nake da ƙarfi na tafi idan kuma na tashi tafiya nakan tafi da abu mafi soyuwa ga al’ummar gari za’ayi ta tunani na har shekara ta zagayo ba’a gama wani kukan ba zan sake caɓar wani abun inyi gaba dashi haka mutane zasuyi ta kuka dani har ranar da mutuwarsu zata riskesu , dake da dake duk wanda na bari a cikinku ya huta ban yafewa kaina ba… Dukan ƙofa akayi da ƙarfi tare da cewa Hafsa me kukeyi kuma ? A shagwaɓa tace Mom ya akayi kuka dawo ne ? Ƙara dukan ƙofar tayi tare da cewa ni banje ba tunda na shigo nakeji ana ihu *kwarata* wai me ke faruwa ne …? Dukansu shiru sukayi , ci gaba tayi da dukan ƙofar tana cewa wallahi idan kika bari na buɗe ƙofar nan da kaina zaki ci ubanki…. Cikin yanayin ɗacin rai Hafsa ta kalleni sannan ta sauka ta fara ƙoƙarin saka rigarta a lokacin har Mom inta ta zuro makulli ta waje ta fara buɗe ƙofa… Murmushi nayi da gefen bakina nima na sauka daga saman gadon na ɗauka towel in na ɗaura , ban gama ɗaurawa ba ta shigo ɗakin , kayana na ɗauka da makullin motar na raɓa ta gefenta zan fita , riƙoni tayi tare da cewa ke daga gidan ubanwa kika zo nan ke kuma….? Ko kallonta banyi ba da nace mata daga gidan ubanta nake , bakiji ina miki magana ? Kema nan dako haihuwarki ba’a gama ba har kin iya iskanci haka ? Kallonta nayi sannan na faɗa mata kaf abinda ya faru na ɗaura da cewa kuma na rantse da girman Allah saina rama ,Haƙuri ta fara bani , niko nace dama kin adana kalmomin haƙurinki kila zasuyi tasiri a lokacin da “yarki ta fara halbe²n mutuwa , ina faɗin haka nayi gaba , a palo naga wata ƙatuwar hijabi dan haka na ɗauketa nayi gaba , a ƙofar palo na saka sannan na wuce inda na ajiye mota ta , ina zuwa na shiga naja cikin gudun tashin hankali nabar gidan kamar babu rai a cikin motar… Tuƙi nake bansan inda nake bi ba , domin idona cike yake da hawaye yayin da hankalina da zuciyata suka tafi tunanin hanyar da zan samo iyayensu Amisty dan babu hanya mafi muni da zan saka musu inba inyi iskanci da iyayensu ba kuma in ɗauka vidio in tura musu… Wani irin wawan burki na taka dan ban lura ba traffic ta riƙeni , tsayawa nayi tare da sauke gilashin mota ta ina kallon wata mace data bugawa wata mota itama dai masiffiyace itace take da laifi amma sai rashin kunya takeyi , Kyawawan motoci ne masu tsada kuma ta kashe musu fitilar baya kuma sai zagi takeyi tana cewa idan sunajin su wasu shegune itace maganin “yan iska sai an biyata motar ta data goge , tunda sune sukayo baya , duk wanda ya bata haƙuri sai tace batayin haƙuri uban waye ma ake tuƙawa a motar ? Daga ciki aka sauke gilashin motar ya sauka a hankali , Dikko na faɗa tare da ƙarasa sauƙe gilashin mota ta dukanshi , matsawa matar tayi taci gaba da zazzagawa Dikko rashin mutunci , kuma ya hana kowa yayi mata magana , murmushi nayi tare da ɗaga kaina na kalli danja har yanzu ba’a sakemu ba , amma waccan wawiya ce da tasan Dikko da bata shiga rayuwarshi ba Allah dai yasa ba a gidan haya suke zama ba suma… Ina tunani naga ta juyo tana kuka kome Dikko yace mata Oho su kuma an sakesu sun wuce , ɗaga gilashin motar nayi nima ana sakinmu nabi bayan motar matar da gudu dan ina so inji abinda Dikko yace mata take kuka , Itama gudu takeyi sosai nima na take tawa sosai , muna samun sarari na shiga gabanta , dole ta tsaya har yanzu tana cikin ɓacin rai , fitowa nayi daga cikin mota ta ko takalmi ban tsaya sakawa ba , na nufo motar matar har yanzu kuka takeyi , gidan gaba na buɗe na zauna , kallona tayi tare da cewa lafiya ? Cikin yanayin damuwa nace abinda aka miki ne baimin daɗi ba shi yasa na biyoki in baki haƙuri me ya haɗaki dashi ne ? Cikin ɓacin rai tace ɗan iskan yaro ne gashi da siffar mutanen kirki amma baida mutunci , kuma baida kunya ko kaɗan , driver inshi ne yayo baya ya gogi motana ni kuma na kasa haƙuri na fita nayi musu magana shine duk sukamin shiru , ni kuma nace uban waye ma ake tuƙawa a motar ashe yana ji yana sauke gilashi ni kuma naje wurinshi da niyar ce masa bai kyauta ba shine yace min…Wai kar inmi mishi rashin kunya bayan yasan komai , cukwui da nonon raƙumi nasha aka bani kyautar motar na taho kan titi ina ma mutane ganganci ko an faɗa min titi ɗakin mijina ne ? Ban tsaya naji sauran bayanin shi ba na taho saboda yaci min mutunci da yawa… Lallai Dikko cikakken ɗan iska ne , haƙuri na bata tare da fita daga cikin motarta na nufi mota ta , wato ya yazo gari kuma hali na nan bai canja ba , mota na koma na shiga naja nayi gida , Tun kafin inyi parking naga Nana zaune a saman dakali sai kuka takeyi , ko inda take ban kalla ba na wuce cikin gida , dan har Nana haushinta nakeji saboda abinda su Amisty sukamin…. Wanka nayi tare da sake wanke kayana na bazasu a saman igiya , ɗaki na koma na shirya bayan na gama abinda nake na ɗauko kuɗin Amisty dana sace na fara irgawa , ban gama irgawa ba naji A ` i tana kwalamin kiran cewa kizo ana kiranki a ƙofar gida , Abinda raina ya bani Babana ne dan haka na ajiye kuɗin na fito , a tsakar gida Karima ke ƙyanƙyasa min cewa an saki Nana , idanuwa na zaro tare da cewa innalillahi garin ya ? Nayi maganar a sirrance tare da natsawa kusa da Karima ! Karima tace ai labarin sai kin dawo kije kiji kiran da ake miki , har ga Allah banji daɗin mutuwar auren Nana ba kuma na lashi takobin gyara aurenta da gaskiya , A ` i ta ƙara cewa jiranki akeyi , cema Karima nayi ki jirani ina dawowa , bayan na fito ƙofar gida nacewa A ` i waye yake nema na ? Filin da aka rushe gidaje ta nunamin kallon motar da akayi parking nayi sannan na kalli A ` i nace waye ? A ` i tace wani dattijo ne , wane kala ne ? Fari ne ! Ya yanayinshi yake ? A ` i tace wallahi ban lura dashi sosai ba yaro dai ya turo yace Sultana taje… Kai tsaye na nufi wurin , tunda mu “yan kasuwa ne ina zuwa na buɗe mota na shige naja na rufe garam , shi kuma ya sanyawa motar lock , ko faɗuwa gabana baiyi ba domin dama raina ya bani za’ayi haka , Waye kai ? Na tambayashi domin duhu ya shiga , ni ne , ya bani amsa , kaine wa ? Na sake tambayarshi , *Shekara biyu…* ne ya bani amsa , dama ana ganin shekaru ? Umm idan bakya ganinsu zaki wuce su ? Ɗan gajeran tsoki yayi tare da cewa yanzu ba wannan ba me yasa kike san yawan yin kuka ? Ni banda isashiyar lafiya sai kiyi ta kuka kina taramin damuwa ! Me akayi miki ɗazu ne ? Tou sai yanzu na gane ko waye , murya nabi na ganoshi , me kuma ya sake dawo dakai cikin rayuwata ? Na tambayeshi , bai bani amsa ba ya fara gangarawa da motar yana saukowa , riƙe sitiyarin nayi nace ina zaka kaini ne kuma ? Janye hannuna yayi daga saman sitiyarin baiyi magana ba a daidai lokacin daya sauko ya juya kan mota ta kalli titi… Haba wai ina zakaje dani ne haka ? Ba tare daya kalleni ba yace yi haƙuri An mata yanzu zan dawo dake bazan daɗe ba , shiru nayi , kinyi haƙurin ko ? Ya tambayeni cikin sigar lallashi murya mai kwantar da hankali dasa natsuwa , shiru nayi ban sake magana ba , a hankali yayi tuƙi har muka fita bakin hanya , yana hawa titi kuma ya fara falfala gudu kamar yanda ya saba. Tafiya mai nisa mukayi , sannan Dikko ya sauka daga saman titi yaci gaba da gurzar burji , ganin ɓoyayyar hanya yasa na fara kuka , kallona yayi tare da cewa wai miye ne ? Kina tunanin zanyi miki wani abu ? Ɗan soɓaro baki yayi sannan yace wannan hanyar tafi sauri ne bara mu koma titi tunda kinajin tsoro.. Nidai bana so ka mayar dani gida, kwaikwayo na yayi tare da cewa idan naƙi mayar dake kuma fa ? Sai in barka da Allah…. , murmushi yace An mata kenan waike bakijin kunyar min rashin kunya ? Banaji kai har abunda za’aji ma kunya ne , murmushi yayi bai sake magana ba , Wayarshi ya fiddo yayi latse² sannan ya kara a kunne , bayan an ɗauka yace fito na iso , kashe wayar yayi ya faka motarshi gefen wani gida , Duk dani dashi babu wanda ya sake magana har mutumin ya fito daga gidanshi , saitin Dikko ya tsaya ya gaisheshi cikin girmamawa nima ya gaisheni cikin mutuntawa , ko kallonshi banyi ba ban kuma ansa ba , gyara zama Dikko yayi sannan ya kalleni fuska a ɗaure yace bakiji ana gaisheki , gabana ya faɗi yanayin kallon da yayi min nace ai nace lafiya lau bakaji ba , kauda kanshi yayi sannan yace ya kukayi dashi ne ? Yake tambayar mutumin , Eh babu damuwa amma sai an koma hutu ,Dikko yace har yaushe ne hutun zai ƙare ? Mutumin yace saura sati biyar , tsoki Dikko yayi yace ko na barta yanzu ? Cikin girmamawa yace ai matan gidan dukansu basa nan idan dai sun dawo zan kiraka insha Allah , Ba komai sai ka kira ɗin , inji Dikko godiya mutumin yayi sosai cewa yaga saƙo yafa gode sannan ya matsa , Dikko yaja mota muka dawo gida , A ƙofar gida yayi parking sannan yace ki kiyayi dawowa ta iskanci da rashin kunya cike da kai amma babu ilimi ni bana san zama wuri ɗaya da jahili kina ɗawainiya da fankon kai a haka kike tunanin zaki hareni shakaru biyu masu zuwa ? Dan dai zan fita katsina a daren nan amma wallahi dana zaune dake har tsawon sati biyar saina koya miki hankali bakauya dake kina fitowa ko hijabi babu ke ba ɗiyar kafirawa ba , zama saman dakali yawon banza fira da maza rashin kunya da tara “yan daba duk ranar dana waiwayoki jikinki zai baki labari fice ki ban wuri kafin in fara miki rashin mutunci , ya ƙarasa maganar tare da buɗemin motar na fice…Fita nayi daga cikin motar jiki a sanyaye dan duk duniya babu abinda na tsana irin inji an danganta ni da kalmar jahila , kuma ba ƙarya bane jahilarce ni , fita katsina kuma da zaiyi yanzu zaije jigawa saboda an fara shagalin bikinshi ne naji ana ta faɗa , Banda tsoki babu abinda Dikko keyi da ana canja hali daya canjawa Sultana hali , duk duniya babu abinda baya so irin mutumin da baya ganewa , wallahi idan har Allah yasa ya dawo lafiya sai an nemi An mata an rasa idan zata shekara dubu saita ta wadata da ilimi , baida inda zai ajiyeta daya tafi da ita , kuma yana so kusanci mai girma da shaƙuwa ta shiga tsakaninshi da ita , Rayuwarshi da ita ya fara kuma yana so ya kulle da ita , farin ciki da duk wani jin daɗin shi yana hannun Sultana bai taɓa tunani zaiji soyayyarta ko kaɗan ba a zuciyarshi , daya san wannan ranar zata zo da baiyi mata abinda yayi mata a baya ba , Bai ɗauki mace komai ba amma ƙaramar yarinya ta hana mishi sukuni , da girmanshi waishi soyayya zata zo ta dama , kamarshi soyayya zata hana bacci abubuwa suyi ta masa yawo a zuciya , idan An mata tayi fushi ko kuka duk yanaji wannan bala’e kamar asiri….. A ƙofar gida na samu Nana har yanzu bata daina kuka ba da takardar sakinta a hannu , wurinta na nufa dan jajanta ma…… Dikko kuwa yana komawa gida ya ɗauki abinda zai ɗauka suka kama hanyar jigawa……12/09/2019 Jamila Musa….⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 31 *_Gaisuwa ta musamman gareki “yar uwa ta gari fatan alkairi da addu’ar Allah ya ƙara zaman lafiya da ƙauna mai girma tsakaninki da mai gidan ki , RABI MUSA …_* A damuwance na zauna kusa da Nana dan ina tattare da ɓacin rai da damuwa , ansar takaddar nayi da cewa saki nawa akayi miki ne ? Cikin kuka Nana tace saki ɗaya , tou ina shi mijin naki yake ? Cikin shashshekar kuka tace yanzu ya shiga cikin gida… Tsoki nayi nace tou me yayi zafi haka har ya sakeki ? Ƙara fashewa da kuka Nana tayi saida tasha kukanta har ta godewa Allah nidai ban bata haƙuri ba kuma bance tayi shiru ba saida ta gaji ta rufe bakinta da kanta na kuma sake tambayarta abinda ya haɗa har akayi mata saki ! Aure zaiyi ! Ba tare dana kalli Nana ba nace tou ke ina ruwanki da auren banzarshi da zaiyi ? Saida Nana ta ƙara goge hawaye sannan tace ba auren ya dameni ba matar da zai aura itace ciwona , wace alaƙace tsakaninki da ita da har bakyaso ta zama abokiyar zamanki ne ? Rumtse ido Nana tayi tare da ƙara rurewa da kuka tace *A ` I* zai aura fa , ɗan gajeren tsoki nayi tare da miƙewa nace A ` in banza A ` in wofi ! Da saboda A ` i har kika kashe aurenki ? Kiyi haƙuri Nana gaskiya baki da wayau kuma lokacin dana so na farkar dake daga baccin asarar da kikayi dake dasu A ` i kuka haɗu kuka riƙa cimin mutunci , kin watsa mutuncin aurenki kin lalata rayuwarki kika biye musu suka koya miki maɗigo ,{ Lesbian } ta koya miki kika koya kuma kika iya , gashi yanzu zata aure miki mijin kinga zaki tashi a tutar babu , ba abokiyar iskanci babu mijin aure.. Idan kuma zawarcin kika fuskanta ga “yan mata tsalala sabbin zubi suna yawo a gari suma basu samu sun shige ba , idan maza suna kallon lutsa²n zawarawa wankakki “yan gayu masu ƙamshi da gogewar zaman takewar aure , Nana gaki muguwar ƙaza babu sallah babu salati babu biyayyar aure ki faɗamin wane sakaran namiji zai kalleki bare yayi tunanin jajibar ki ya kaiki gidanshi , Ke kanki baki wanke kanki ba bare namiji yayi tunanin idan ya aureki zaki wanke mishi gidanshi , mazan yanzu sunfi san kwankwashshin mata , masu gogewa wanda zasu gyara masu gida ba su kashe musu gidaje ba , dan mazan yanzu suna kashe kuɗaɗe su gina gida na fita idon duniya , tou yau dake da A ` i wa gari ya waya Nana …? Kin san zawarci kuwa ? Kai lallai kin tafka babban kuskure aradu… Juyawa nayi zan shige gida Nana ta riƙoni cikin kuka tace ki taimaki rayuwata wallahi ko naje gidanmu korata zasuyi Baba baya san *Zawarci* shi yasa ban tafi ba , tou idan kuma na bashi haƙuri ya mayar dake kika sake jawo matsala fa ? Bazan jawo ba Mother kuma zan ɗauki duk shawarar da kika bani bazan sake tsallakewa ba ,Tou zan baki shawara idan har kika ɗauka ba A ` i ba ko uwar A ` i mijinki bazai sake kallo ba bare ya sha’awar aure tunda sun zama maciya amana , Nana tace ngode sosai…., Muje cikin gidan , lokacin da muka shiga har mijin Nana ya gama tattara kayanshi ya fito zai bar gidan , Gabanshi nasha tare da cewa Audu ina so zamuyi magana dakai don Allah , kallona yayi ƙasa da sama yace idan har maganar Nana zaki min bana so , ko Nana autar matace duniya na haƙura da ita , cikin sigar lallashi nace don girman Allah kayi haƙuri ka saurareni , ka bani dama nayi magana dakai na minti biyar kaɗai dan Allah badan halina ba , Tsoki yayi ya koma da baya ya jingina da bango sai haɗe rai yakeyi shi mai gida , murmushi nayi sannan na matsa kusa dashi nace Audu meya haɗaka da Nana ka saketa ne ? Banza yayi ya ƙaleni , ban damu da shirunshi ba naci gaba da cewa tou nidai don girman Allah ina neman alfarma kuma wannan alfarmar ba kowa zaka ma ita ba saini , na roƙeka da girman Allahn daya halicceka ya baka aron numfashi da lafiya , ya baka ji ya baka gani yayi maka hankali , idan har kaji daɗin wannan ni’imomi da ubangiji yai maka kayi haƙuri ka mayar da Nana …Cikin damuwa Audu yace Sultana Nana bata da mutunci kwata² ina ce duk abinda Nana kemin a gaban idonki , Nana ta rainani itace dakamin tsawa fita ba izini na magana da mazan waje duk wanda nace bana so tanayin tarayya dashi sai ta kafe tayi , rabon da inyi kwanciyar aure da Nana tun muna tsohon gida , na rabata da A ` i taƙi ta rabu da ita , A ` i tana so na kuma tana tausayamin sai in aurota dan ta kwantarmin da hankali na , kuma nace zan auri A ` i sai tacemin bata yadda ba ? Bayan tana san A ` i ta kasa rabuwa da ita tou idan na auro ta ta zama abokiyar zamanta ai duk wata ƙauna ya kare ko ? Duk cikin ɓacin rai yakeyin maganar har wata maganar ma bata fita , haƙuri na bashi saida na tabbatar ya sauka sannan nace tou aurenka da A ` i fa babu fashi kayi aurenka bama hanaka , amma kayi haƙuri ka mayar da Nana dan soyayyar da kake ma manzan rahma S. A. W , Jinjina kai yayi yace in zauna da ita da baƙin halin nata da ƙazantar da duk iskancin da takemin a haka ? Karka damu mayar da ita sauran gyaran duk nawa ne idan bata gyara ba ni da kaina zan ƙaro maka mata sadaki da lefe duk ni zan bayar kuma zan baka jari , tou shikenan na mayar da ita… Godiya nayi mishi sannan nasa Nana ta anshi kayanshi ta mayar cikin ɗaki , nayi musu saida safe , na wuce ɗakina , ina shiga Karima ta shigo tana cewa wallahi banso kika sa aka maida ita ba , banza nayi bance da ita komai ba , ta ƙari kilbibinta naji babu ansa ta fice…. A ɓangaren su Amisty kuwa ina fita Momyn Hafsa ta cire wayar wuta taci gaba da dukansu babu ji babu gani , tana dukansu tana cewa wato na hanaki wannan iskancin bakya bari ko ? Tou wallahi yau saina kashe ki , dama tunda nabar gidan nan na kasa samun natsuwa zuciyata tana saƙamin tunda bana nan nan zaki kawo “yan iska su tarar min a gida , Amisty ganin hankalin Mom ya fita jikinta tana dukan Hafsa har ta daina motsi yasa ta biyo ta bayanta ta fice da gudun tashin hankali , A bakin get ta faɗawa mai gadi Momy ta kashe Hafsa , da gudu ya nufi ɗakin Hafsa , ita kuma ta fice daga gidan , saman Hafsa ya samu Momy tana dukanta tana yaginta duk tayi mata kaca² jini saibin jikinta yakeyi , da sauri ya ciro wayarshi ya kira Yayan Hafsa ya faɗa mishi duk abinda ake ciki dan babu yanda za,ayi ya ɗauke Momy , babu ɓata lokaci ya iso , dakel ya ɓanɓare Momy sannan mai gadi ya kama mishi Hafsa suka tafi asibiti da ita…. A asibiti kuwa likitoci sun tabbatar cewa Hafsa bata mutu ba , dan haka suka shiga bata taimakon gaggawa dan ceto rayuwarta….Amisty kuwa a gidan Asma’u ta yada zango , tana zuwa wanka tayi Asma’u ta kawo mata abinci taci sannan suka ɗora iskancinsu daga inda suka tsaya ! Tunda safe almajirai suka fara kawo kayan “yan gidanmu a cikin baro , sahu ɗaya yaran sukayi nace idan sun koma suce a samu mota a zubo kayan zan bada kuɗin , Nana na kira ɗakina nayi mata nasiha , cewa ki rufawa kanki asiri ki gyara halayenki , ki zama mai tsabta ki fita daga harkar zaman majalisa kija mijinki jikinki , ki zama mai biyayya da haƙuri a rayuwarki , karki kuskura mijinki ya sake neman haƙƙinshi a wurinki ki hanashi , ko inuwar Audu kika gani ki bashi natsuwa , Tsafta a rayuwar aure itace jigo , kamar yanda baki shiga makaranta dole saida uniform , bazai fa yuwu ba ki gama duk wata fangila taki kisha yawo cikin rana ga kaurin zufa ga warin rana gana haƙi , zaninki na zarnin fitsarin yara ga ƙarnin tunbiɗi babu wanka babu wanke jiki ba sake kaya a haka zakije kice namiji ya kwanta dake ? Wace natsuwa zai samu ? Taya zai samun natsuwar da zai biya buƙatarshi….? To idan zaki gyara ki gyara , ki nemi ruwa da turare sabulun wanka da man shafawa ki fara wanka , ki zama mai biyayyar aure kima mijinki sannu da zuwa idan ya dawo ki masa rakiya idan zai fita tare da addu’ar Allah ya bashi halal inshi , ki gode masa akan abinda ya kawo miki ki kuma yi haƙuri idan bai kawo miki ba , ba kullum ake nema a samu ba , dole wata rana a samu wata rana kuma a rasa , kin dai ga yanda rayuwar take tafiya dan haka ki tashi ki miƙe da gaske ki janye tunanin mijinki daga kan A ` i idan kuwa ba haka ba ta shigo to aradu sai tayi waje dake… Jiki a sanyaye Nana tayi godiya tare da cewa bara in tashi nace da dai kin kyauta ki kuma zuƙe jikinki daga sabgar matan banza , insha Allah Mother ngode sosai , yayi kyau na faɗa tare da cewa zan fita saina dawo , addu’ar a dawo lafiya tamin , ni kuma na irga kuɗi 20K na bata idan an kawo kaya ta sallami masu motar , in an rage canji ta ajiyemin , insha Allah ta amsa min sannan ta fita , nima na shirya na fice ! Anguwar su Amisty na nufa , kafin inkai ƙofar gidansu nayi parking jikin wani shago , amma ina hangen gidansu Amisty , wayata na kallo da take kuka , lambar Amisty ce keta tsalle saman screen in wayata , kamar bazan ɗauka ba na ɗauka dan inje me zatace ! Ina ɗauka ta fara ,Tauraruwa mai wutsiya ganinki ba alkairi ba , ciwon tsakar dare mai hana bacci , ance kinje anguwarmu bayan kin sacemin kuɗi me kuma kikaje yini ? Murmushi nayi tare da gyara zamana sannan nace tsauni da ƙaya da tsawon zango maibi da ƙafa sai ya daure , yaro bai ɗaukar yaro dan kansu matsa sai sun faɗi , guguwar tsakar dare ga tsoro ga ban al’ajabi , kura bata cin damisa saidai taci zaki , ki saurari kaidina zuwa gobe kamar yanzu , kashe wayata nayi dan ganin mahaifin Amisty ya fito , Yana wucewa da motarshi nima nabi bayanshi da tawa motar , a hankali yake tuƙi nima a hankali nake binsa saf da ƙafa har ya isa wurin aikinshi , inda yayi parking nima a wurin nayi yana fitowa nima na fita murmushi ɗauke da fuska na nufi wurinshi , Da sallama na isa wurinshi tare da cewa sannu , yawwa ya ansa yana kallona , murmushi nayi tare da cewa naga kamar baka ganeni ba ma ko ? Cikin muryar dattijantaka yace Eh ban gane ba gaskiya , ajiyar zuciya na sauke tare da cewa me yasa baka gane mutane haka ? Murmushi yayi sannan yace to bani sani mana , nace tou sakamin numberka mayi waya dai zuwa dare , babu musu ya ansa ya gwagwaɗamin lambar shi nayi ajiyeta da Lamba shidda , bayan na gama ajiyewa na kirashi yaga tawa sannan nayi masa sallama na wuce , Daga nan ban zame ko ina ba sai Office in Babansu Hafsa , suna da dokoki masu tsaurin gaske dan haka aka hanani shiga , nayi ² aka hanani , lambarshi na tambaya itama dai ban samu ba , dan haka na haƙura na nufi gidansu Hafsa , A wurin mai gadi na samu number bayan na bashi cin hancin 5K , ina ansa na nufi gida , cikin farin ciki nayi sallama dan har “yan gidanmu sun dawo dukansu , amma Inna bata dawo ba , Babana kuma saida dare zaizo ,Cikin kulawa nake gaishesu amma kowa sai ya ansa min a wani dusasar , haka nan dai na haƙura na wuce ɗaki na , saida nayo wanka na fito Nana ta shigo ta bani cikon kuɗina tace ta bayar da kuɗin ta sallamesu , godiya nayi mata sannan tace bara ta sharemin ɗakina , nace babu damuwa ta share… Satin “yan gidanmu ɗaya da dawowa amma Babana baizo ba kuma Inna bata dawo ba itama , Baban Amisty da Baban Hafsa munayin waya dasu , kowa ya damu yaushe zamu haɗu dan wayar babu abinda ke cikinta banda zallar sakin layi , har yanzu badai mu haɗu ba kuma sati biyar ya ragemin a lissafin satikan da Dikko yake lissafi…. Mijin Zalifa ma ya matso lamba mu haɗu amma yanzu bashi ne gabana ba , Alaji wato Abbu Afsar shi kuma yana min hidima sosai wacce ta wuce hankali ma , maganar wani abu har yanzu babu wani abu daya shiga tsakaninmu yadai cemin yana so muyi aure na zama abokiyar rayuwarshi niko ba auren ne gabana ba , Zalifa kuma tazo min da labarin mutuwar ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita a station Fadeela wacce tayi cikin shege da aurenta kuma itace ta kawomin Zalifa gidana , ta mutu sanadiyar rataye kanta da tayi bayan tasha gwagwar maya wurin zubar da ciki bai zubu ba , kuma sunje wurin bokaye anyi asiri anyi tsafin amma cikin bai fita ba , kuma anyi ƙoƙarin ɓatar da hankalin mijin dan ya yadda cikinsa ne shima ba’a samu nasara ba , dan haka ta kashe kanta , … A ɓangaren ango D K yau akayi walima amarya ta tare a gidan angonta Dikko dake G R A { karkara road } , an gina gida na faɗi a faɗin birnin garin katsina , an kashe kuɗi kuma anyi hidima ta kece raini , gida ya tsaru iyakar tsaruwa , iyayen amarya suma sun kashe kuɗi wurin ƙayata ɗakunan amarya da palukanta tunda kuɗi da kuɗi ne suka haɗu abindai sai wanda ya gani , duk inda ka nufa a gari maganar auren Dikko akeyi da gidanshi , gaskiya Dikko mai sa’a ne… Cikin farin ciki ango ya shiga ɗakinshi danshi babu wani abokin daya rakoshi cewa yayi baya so , bayan yayi wanka ya saka jallabi ya nufi ɗakin amarya , itama tayi wanka ta shirya cikin shiga mai kyau da burgewa , a ɗakin amarya yayi alwalla suka gabatar da nafila raka’a biyu dan miƙa godiya ga mai duka , Bayan sun gama sukayi addu’o’in neman zaman lafiya da wanzuwar arziƙi mai ɗorewa tare da addu’ar Allah ya basu zuri’a masu albarka ya kuma kauda sharri da fitina a zaman aurensu , bayan sun gama ya dafa kanta yayi mata addu’a , Bayan ya gama ya koma palo dan ɗaukoma amarya ɗan abinda ya shigo mata dashi kamar dai yanda kowa ya sani anayi , sama ² Sadiyya taɗan lallasa tace ta ƙoshi , shine ya tattara sauran yaje ya zubarwa da karnuka , bayan ya dawo ya wanke hannunshi da bakinshi ɗakinshi ya koma ya sake ciwo ɗama dan shima ya nuna tashi jarumtar a daren farkonshi da matarshi…Itama amarya fitar ango ta ƙara gyarawa ta cuscusa na cusawa ta shafa na shafawa ta kukƙurɓa na ƙurɓawa ta ɗaga katifa ta jera layunta , ango na dawowa itace ta taroshi dan a halin yanzu sha’awar Dikko ta rufe soyayyar da take mishi , Cike da bariki taja Dikko suka sauka saman gado , daga nan labari ya fara canja salo , kowa dai gwanine wurin ganin ya nuna shi wani shege ne , Dikko kuwa a zuciyarshi yake mamakin Sadiyya dan yasan duk macen da bata goge ba a harkar maza tana tsoron namiji bare kuma a daren farkon ta , Yayin da Sadiya kejin daɗin salon Dikko ta yaba mishi ko a haka aka tsaya tasan Dikko namijin duniya ne gaskiya Dikko ya karanci mace yasan duk wasu salo na burge da saka nishaɗi , ya iya sirrika masu tsayawa a zuciya , duk mazan da tayi mu’amula dasu tasan Dikko zakara ne a cikinsu , Soyayya tai nisa ango ya tunkari gidan sarauta , amma me zai samu ? Labari yasha banban domin dai wani ya rigashi hayewa saman kujerar mulki , la’ilaha illa anta sub’hanaka innee kuntu minazzalimeena , lahaula wala kquwwata illa billahi aliyyil azeem , Dikko ya faɗa tare ci gaba da cewa Allah na tuba , Allah ka yafemin , kukan makirci Sadiyya ta fara wani irin kallon tsana Dikko yabita dashi yayin da yake kallonta kamar an mata a daren daya kacaccala mata rayuwa , Yaya DK don Allah ka rufamin asiri yanda Allah ya rufa maka , ka rufe wannan sirrin don girman Allah karka tona min asiri…. Wani irin tashin hankali yazo a zuciyar Dikko ya tsaya yayi ² yayi control in zuciyarshi ya kasa yana ƙoƙarin sauka daga saman Sadiyya matsalarshi tazo , wani iri ihu yayi ya tafi gaba ɗayanshi kafin kace mi ? Tuni lumfashin shi ya tsaya cak….. Wannan itace babbar matsalar dake damunshi da ranshi ya ɓaci sai kawai numfashin shi ya ɗauke….Cikin ruɗewa ta ɗauki wayarta ta fara kiran Momyn Dikko , babu ɓata lokaci ta ɗauka Sadiyya ta karanta mata halin da Dikko yake ciki , jikin Momy na ƙyarma ta miƙe “ya “yanta suka riƙeta saboda karta faɗi ta samu matsala , kuka ta farayi tana Allah ka tausawa rayuwata idan har Dikko ya samu matsala mijina ya shiga tashin hankali ubangiji ka dafamin a dukkan lamurarra na , meya faɗawa Dikko rai a wannan dare ….? Kai ku sakeni ta faɗi maganar tare da kwacewa ta shiga ɗakinta ta nemo wani magani da ake mishi amfani dashi idan lalurarshi tazo , ko Dadyn bata faɗamawa ba driver ya ɗaukota tayo gidan Dikko dan tasan idan har Dady yaji to idan dai Dikkon bai mutu ba kilashi yana iya mutuwa… Sadiya kuwa tana gama waya da Momy ta sakama Dikko gajeren wando dakel , sannan ta lulluɓeshi da bargo , Babu ɓata lokaci Momy ta iso , Sadiyya ta buɗe mata ƙofa kuma itace tayi mata jagora har zuwa ciki , a ɗakin Sadiyya ta samu ɗanta kwance cikin tausayawa tace meya haɗaku ne ? Sadiyya cikin daburcewa tace ba komai wallahi , Momy tace bazai yuwuwu ba me kikai masa ne ? Fashewa da kuka Sadiyya tayi tana cewa wallahi ba komai Momy , Hmm shine abinda Momy ta faɗa tare da matsawa kusa da Dikko ta buɗe bakinshi ta zuba mishi magani , kamar mai ciwon aljannu haka ya tashi kamar babu abinda ya taɓa faruwa dashi , kallon Momy yayi tare da cewa lafiya kika zo ? Ya ƙarasa maganar yana ma Sadiyya kallon tuhuma , Cikin so da ƙauna Momy tace ba komai yanzu ma zan tafi , zaiyi magana Momy tace ba komai , tana faɗin haka ta fice daga ɗakin da maganinta bata barshi ba , Sadiyya kuma gefe ta koma ta zauna ta rasa inda zata saka ranta dan Dikko ya tsareta da ido…. Tsoki yayi bayan wani lokaci sannan ya gyara kwanciyarshi , idonshi na kallon sama ya rasa abinda ke mishi daɗi , amma yayi alƙawari kamar yanda Sadiya ta nemi ya rufa mata asiri wannan maganar duk duniya babu wanda zaiji kuma babu wanda zai sani , kuma ya zamarshi dole ya zauna da Sadiyya abin family a saketa zuminci zai samu damuwa….. Saukowa yayi daga saman gadon ya nufi ɗakinshi , Sadiyya kuma abun duniya duk ya dameta , sai yanzu take nadamar da bata da rana….. 13/09/2019 Meelat Musa….💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 32 Dikko kuwa yana komawa ɗakinshi wanka yayi , a gaggauce ya shirya bayan ya fito cikin ƙananan kaya , blue in riga da upwhite in wando shima takalmin irin wando ne amma rufaffi ne takalmin , ya naɗe hannun rigar daidai guiwar hannu , turare ya fesa sannan ya ɗauki makullin motarshi ya nufo ɗakin Sadiyya , a bakin ƙofa ya tsaya har yanzu tana nan zaune inda ya barta kamar asara , Kamar ba abinda ya faru dashi ɗazu kuma babu wata damuwa a tattare dashi yace zanje in dawo yanzu ! Cikin jin kunya da kama kai tace ina zakaje yanzu ? Naga har 11:05pm shima kallon agogon yayi sannan yace Ey ai na sani juyawa yayi tare cewa saina dawo bai jira yaji abinda zata ce ba… A wannan dare kai tsaye gidanmu Dikko ya taho ni kuma a lokacin ina zaune saman dakali dani da Alaji muna fira , tun kafin ya fito nasan shine dan tuƙishin yasha banban dana kowa , cikin filinshi yayi parking sannan ya juyo motar ya haskemu da hasken fitila , Alaji dake da matsalar ido ya fara kauce² yana burza idanuwanshi dan gani ke barazanar ƙare mishi… Fitowa Dikko yayi ya zauna saman mota , Alaji kuma miƙewa yayi ya fara laluben hanya dan gaucewa haske , cikin damuwa na kalli Alaji ina gilashin ka ne ? Ba tare da yayi magana ba ya miƙomin makullin mota , da sauri na ansa na nufi motar dan ɗauko masa gilashi , Da sauri na dawo da gilashin a hannuna nace tou saka , bawan Allah hannunshi yana kyarma ya ansa ya saka , ajiyar zuciya ya sauke cewa waye ne ya haska ? Baiga mutane zaune a wurin ba ? Banji daɗi ba gaskiya , haƙuri naba Alaji tare da cewa idan akace kayi hukunci wa mutumin daya haska maka ido me zaka mishi ? Alaji yace wallahi da fitulun motar zan kashe…Shiru nayi ina nazari dan nasan idan har na faso fitulun motar Dikko na sake tarowa kaina fitina , tou amma ai ba gidan haye muke zaune ba , zuciyata ta ingizani in koma cikin gida kawai in ɗauko taɓarya na rusa fitulun kamar yanda Alaji yake sha’awar gani…Kallo Dikko nayi dake zaune a saman mota yana kallonmu tas , gaskiya bana iyawa idan ya riƙeni a wurin can jakin duka zaimin babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani , ya dakeni ya daki banza , kallon Alaji nayi tare da cewa barshi ya samu daidai dashi muje ka tafi gida , Rakiya nayi ma Alaji har wurin mota ya shiga , addu’a nayi masa Allah ya tsare hanya Allah ya fisheshi dare , ina tsaye a wurin harya tafi , buzum² na nufi gida dan anguwar ta ɗinke da duhu sosai gashi babu wasu “yan gayu da zasu kunna gen bare su bamu sadakar fitila ɗaya a cikin anguwa muga haske , yanda baki baya ɓace maka a cikin duhu haka ƙofar gidanmu bata ɓacemin dan haka na tunkari gidanmu cikin sauri… Ina ƙoƙarin shiga Dikko ya fizgoni tare da cewa yawwa kwanakin baya kince zaki gauraya dani nine abokin wasar ki yarinya ? Ya faɗi maganar cikin neman fitina idan yaji haushi mi yasa tun a lokacin baiyi magana ba ? Sai yanzu ? Da nayi tunanin babbaka mishi ashariya amma sai zuciyata tace karki biye mishi so yake ya jagula miki lissafi , idan har kika zageshi ko kika faɗa masa baƙar magan akwai wani abu a zuciyarshi , kawai kice masa yayi haƙuri , kinga idan baiba kinsan masifa yakeji… Cike da rashin kunya nace kayi haƙuri amma hakan baya na nuna inajin tsoronka bane a , a , dan ɗan dambe yaja baya ba yana nuni ya tsorata bane gyaran tako ne , a haka zaki gyara takon kina tarayya da makafi ? Baki ba kwalwarki natsuwa ba zance har 11:49pm a haka kike tunanin zaki gyara tako ? Duk macen da tasan abinda take tana cikin gidansu kamar yanzu amma ke kina nan kina balbaɗewa a santa , kindai ji kunya ! Cikin jin haushi nace kaine kaji kunya ƙato dakai kana faɗa da mace , murmushi yayi tare da cewa kindai gane baki iya gauraya da Dikko kenan ? Tunda dai kinji tsorona kin fanshi kanki a daren nan amma dasai na hanaki baccin dare… Jana yayi tare da cewa nima muje kimin rakiya , tirjewa na farayi bazan je ba , kallona yayi sannan yace kifa wuce muje idan ba haka ba kinsan Allah ɗaukarki zanyi , tashi nayi na daina tirje² cikin murya mai saukar da kasala yace muje ya faɗi maganar tare da sakin hannuna , gaba nayi yana bina a baya har wurin mota , buɗewa yayi ya shiga ni kuma na juyo da sauri , shima cin taya yayi ya biyoni da sauri tare da cewa An mata zo zo zo banza nayi na shige gida , saida safe ya faɗa , ko inda yake ban sake kallo ba na shige abu na… 12:20am Dikko ya isa gidanshi zuciyarshi na ƙara azabtuwa da soyayyar Sultana , addu’arshi a daren yau itace yanda yakejin kishin Sultana ubangiji ya sanya mata kishinshi a zuciyarta , yanda yakeji soyayyar ta itama Allah ya saka mata soyayyarshi , yasan dama babu ranar da zata ga girman shi tunda ya gama ɓareshi a wurinta , amma yasan idan dai tana mishi soyayya zatasan girmanshi dan darajar wannan son nashi dake zuciyarta…. Da sallama ya shiga ɗakin Sadiyya har yanzu tana nan inda ya barta tasha kuka har ta godewa Allah , cikin tausayawa ya kalleta yace har yanzu baki kwanta ba ? Dakel ta sauke ajiyar zuciya cikin kuka tace ina kaje ? Kusa da ita ya duƙa ya ɗagota cikin sigar lallashi yace meye ? Ki daina kuka kinji ya ƙarasa maganar tare da rumgumeta , cikin shashshekar kuka tace ina kaje ? Shine ka tafi ka barni , Shiru Dikko yayi , Sadiyya taci gaba da cewa nasan da ciwo a rayuwarka yau kaji babu daɗi kuma nasan duk lokacin daka kalleni zakaji baka ƙauna na , murmushin ƙarfin hali yayi cewa haba keko waye yace miki haka ? Sadiya tace ka daina ɓoyewa Yaya DK nasan babu daɗi kuma akwai ɗaci kayi haƙuri ka rufemin wannan sirri ko bayan babu ni…Lallashin ta Dikko yayi saida ya tabbatar ta samu natsuwa har tayi wanka sannan suka kwanta , har Dikko yayi bacci Sadiyya ta kasa bacci baƙin ciki yazo ta taru a zuciyarta sai kukan zuci takeyi tare da nadamar biyewa soyayyar zuciya… Tunda safe na farajin hayaniyar “yan gidanmu masu abun kuɗi suna ɓoyewa , masu wayoyi na kashewa suna adana abunsu , muryar Naja yayata naji tana cewa wallahi gashi nan yayi parking fa , zai fito , zai fito ya fito , gashi nan zai shigo zai shigo…. Sai kuma naji gidan ya natsu yayi shiru kamar babu masu rayuwa a cikin gidan , tashi nayi na leƙo ta jikin window dan ganin wanda yake shigowa , Babana duniya kenan , kai ina san Babana wallahi dan nafi sanshi fiye da Inna , Da sauri na buɗe ƙofa na nufi wurinshi da gudu ina mai farin ciki da ganinshi , cikin soyayyar da ya saba nunamin ya riƙeni tare da cewa bi sannu Uwar masu gida karki faɗi , yayi maganar cikin jin kunyata ya kasa haɗa ido dani tsaɓanin yadda yakemin a baya , rumgume Babana nayi tare da fashewa da kuka nace me yasa ka tafi ka barni Babana ? Kasan ina sanka banajin daɗin rashinka a kusa dani ? Me nayi maka kayi nisa da rayuwata ? Shiru yayi baice komai ba , naci gaba da cewa idan har akwai sauran wata soyayya bayan wacce nake maka Babana itama na baka ita dan jaddada soyayya da ƙauna a gareka , ina alfahari dakai daka zama uba a gareni , kuma ina addu’a na kasance dakai har numfashin ƙarshena a duniya , kuma ina roƙon Allah yasa kar na wayi gari babu kai a duniyar nan , ɗagowa nayi cikin kuka na kalli cikin idon Babana nace karka sake tafiya ka barni ka kasance dani dan nima na samu duk irin soyayyar da ko wane mai Baba yake samu a duniya Babana… Baiyi magana ba yaja hannuna muka fita ƙofar gida , motarshi ya buɗe muka shiga muka zauna , cike da soyayya Babana ya kalleni yace Uwar masu gida duk wata soyayya ta duniya wacce Allah ya halitta ta bayan soyayyar shi da manzansa da nake a duniya soyayyarki ke ɗaya tak ta goge soyayyar kowa a faɗin duniyar nan , idanuwana basa kallon kowa haka kuma zuciyata bata nunanin wani a duniyar nan idan bake ba ,tun daga ranar dana sameki ubangiji ya ɗoramin jarabtar soyayyarki a zuciyata , ni Allah bai ɗoramin ciwon son “ya “ya ba , wallahi bansan yanda akejin soyayya ɗiya ba saida Allah ya kawo zamaninki…Nayi kukan baƙin ciki nayi nadama da har na kasa samar miki farin ciki , tunda nake a duniya ban taɓa nema na rasa ba , haka kuma babu wani abu na rayuwa daya taɓa kubcemin matsawar inajin soyayyarsa a zuciyata , an cuceni an kuma yaudareni da har aka samu nasarar rusamin farin cikin rayuwata , nayi tir da Allah wadai dana zama sokon uban da ya kasa ceto rayuwar “yar sa…. Mamana ki yafemin ni ban cancanci na zama uba a gareki ba , banso kika zo cikin rayuwar wahala ba , banso ba kuma banji daɗin haka ba , da ana canja uba dana zaɓar miki mafi girma da matsayi a duniya ya zama shine mahaifinki domin kiyi rayuwa mai inganci ba rayuwar dana sani ba , Uba ɗan caca bashi ne ya dace da rayuwarki ba , ba nine ya dace na zama uba a gareki ba bayan ni na kasance bana cikin mutanen kirki , idona ya rufe da duniya bansan duniya bata da daɗi ba saida na kasa magance duk wata damuwa taki , saboda haka ki daina alfahari dani nasan ke da kanki zaki gogeni daga lissafin rayuwarki matsawar kika gane wane irin mahaifi gareki a duniya… Girgiza kaina nayi tare da cewa duk rayuwa sunanta rayuwa , jin daɗi ko rayuwar baƙin ciki baya sa a gane mai rabo a duniya , girman zunubi da saɓo baya sa kakai mutun jahanma domin rabon rahama wannan daga Allah ne , ɗan caca da ɓarawo duk matsayin su iri ɗaya ne a idon al’umma amma a wurin ubangiji azabarsu ta rabauta , manta da abinda ya faru baya kawai mu fuskanci rayuwa , amma waye Bello ? Meye tsakaninka dashi ? Me ka mishi wanda har ya zaɓi nice zaka saka a wasan caca…..? Hawaye ya gangaro daga idanuwan Babana , murmushi nayi tare da riƙe hannunshi ina masa kallo mai tattare da soyayya….. Cikin soyayya shima ya kalleni sannan yace ki jirani ina dawowa yanzu zan mayar da mutane motarsu , idan na dawo zan faɗa miki asalin waye Aliyu Binna , haɗuwata da Bello abinda ke tsakaninmu saka ki a wasan caca duk zakiji , sakin hannunsa nayi ba tare da nayi magana ba na fice daga motar , shi kuma yaci sitiyari yabar anguwar , cikin gida na koma ban damu da hararar da akemin ba naci gaba da sabgogin gabana…. Har yanzu Sadiyya bata daina kuka ba , kuma Dikko yayi lallashin duniya taƙi ta daina kuka kuma taƙi taci abinci , daga jiya zuwa yau ta rame idanuwanta sun kumbura , Dikko ya gaji yace mata kode shine bata so ? Sadiyya tace duniya da tasan zata zama matarshi kwata² da bata ɓata rayuwarta ba , gajiya yai ya fita sabgarta yaci gaba da huɗɗoɗin gabanshi zai bar gari ana rantsar dashi idan Allah ya kaimu gobe… Cikin ƙananan kaya ya fito yayi kyau sosai a cikin coppie brown in riga, da wando ash mai haske , rufaffin takalma brown mai haske yayi stocking yafa ɗauku iyakar ɗaukuwa yayi kyau sosai , ɗakin Sadiyya ya nufa yana ɗaura baƙar agogo a tsintsiyar hannunshi yana cin cigom cikin salo mai ɗaukar hankali… Da sallama ya shiga tana kwance saman gado cikin bargo ƙasa² kakejin sautin kukanta , yaye bargon yayi fuska a haɗe yace waike baza ki daina kukan banzar nan ba ,? Nifa bana san iskanci bana so inyi ta magana abu ɗaya , zan tafi idan kinga dama kiyi shiru idan kinga haggu kiyi ta kuka har masu kuka suzo su sameki…. Murmushi Sadiyya tayi tare da cewa Allah yasa ka sauka lafiya , kuma kayi haƙuri idan har kazo ka samu na mutu to ka yafemin , tsoki Dikko yayi ya fita ba tare daya sake mata magana ba , Al ‘ Ameen shine yaja su , Dikko ne a gaba mutane biyu kuma a bayan mota , su huɗu kenan , kuma saida suka biyo ta anguwarmu amma yau bamu samu haɗuwa da Dikko ba , kuma ya aiko kirana har gidanmu akace masa bana nan , bayan kuma ina nan , amma banji lokacin daya aiko kirana ba…. , Dikko yaso ya ganni amma haka ta gagara , dole ya haƙura suka ibi hanyar Abuja……. 14/09/2019 Jamila Musa….💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 33 Tafiyar Dikko babu jimawa Nana ta shigo take faɗamin mai gidan dokuna yazo nema na amma ance bana nan… Tsoki nayi ban bata ansa ba , tsintsiya ta ɗauka taci gaba da share ɗaki , ni kuma jakata na ɗauko na buɗe ina kallon abinda nake fesawa mutum ya tafi bacci , jijjigashi nayi bayan naji sauran abinda ya rage na mayar a jaka ina mai addu’ar haɗuwa na da iyayen su Hafsa… Maganar Babana naji a tsakar gida yana cewa duk iya ƙwarewa munafircinku na gano ku baƙaƙen munafikai , wato duk lokacin da kukaji motsina sai ku kashe wayoyi ku ɓoye kar nace ku bani kuɗi kuce babu , idan naji babu zansa wayoyi suci kasuwa , dan ku bani kuɗaɗen , lissafo duk yayuna yayi masu waya cewa kowa ta kawomin wayarta dukanku ancemin har face buk kukeyi , kuma na gani da idona dan babu wacce banga hotonta a cikinku ba… Cike da damuwa suka fara fitowa Babana yana zaune a saman kujera kowa sai ta bashi ta koma ɗaki cike da ɓacin rai , bayan ya gama tattare wayoyin kaf ya kira babban yayanmu yace maza kasuwar tsaitsaye ka siyar min dasu , da guda² yake bashi wayoyin tare da faɗa masa adadin farashin da yake so a siyar da ko wace waya…Shima Yayanmu cikin fargaba yace Baba ai duk kuɗin daka faɗa baza’a siya a haka ba , wata irin harara ya zabgaga mishi tare da cewa wannan kuma damuwarka ne , kai tunani ya rage ma yadda zaka siyar danni duk kuɗin dana faɗa su zaka kawomin a ko wace waya na faɗa maka , yana faɗin haka ya miƙe ya nufo ɗakina… Da sauri Nana ta ajiye tsintsiya saida tayi masa sannu da zuwa ta fice daga ɗakin , bayanta yabi da kallo zuciyarshi tana ƙisima mishi wasu abubuwa , amma bai ansa sannu da ta masa ba… Gefen katifa ya zauna kusa dani cike da soyayya irinta mahaifa yabini da kallona mai tattare da tsantsayar soyayya , murmushi nayi nima ina kallonshi nace Babana baka da kuɗine ? Murmushi yayi bai bani amsa ba , nima murmushin na sakeyi kamar yanda yayi sannan na jawo jakata ina cewa ni ina da kuɗi bara na baka… Ansar jakar yayi tare da rufeta yana mai cewa nifa ina da kuɗi Mamana kinsan mage kota ƙoshi sai ta hari ƙwari , ajiye kuɗinki anjima zan ƙaro miki wasu , ajiye jakar yayi a gefena sannan yace Mamana tun kuna ku hamsin da bakwai har yau an wayi gari kun zama ku sittin ciff,Tsoki yayi tare da kauda kanshi gefe yace tirr , wallahi da za’a tambayeni abinda nake so a musanya min da tulin “ya “yan nan ke kaɗai zan cire a cikinsu sauran a mayar min dasu daga motocin hawa sai ƙayataccin gidaje , ita kuma matar malam bahaushe ita dai burin ta kawai ta tara taron “ya “ya ita dai a mutu kawai taci gado , tou ban ajiye ba kuma bazan ajiye ba duk wacce ta haifi “ya “yanta taji da abunta ni babu ruwana… Uhum Babana kenan mugunta kamar mai tsaron gidan yari , wato karya nema ya ajiye idan baya duniya a ci gado , hmm halin Babana saishi kallo nabi shi dashi ga wayyen mutum kisan boko ɗan gayu mai buɗewar ido yana da ilimin boko mai zurfi amma saboda tsabar baƙin ciki ko aikin gwamnati bayayi , tunda yaga ana ruguwar haifar mishi “ya “ya ya daina aiki ya koma caca…Kallona yayi yace ki ɓoye sirrin mahaifinki koda bana faɗin duniyar nan , ki zama maimin addu’a bayan mutuwa ta ɗaukeni daga kusa dake , ki nunamin soyayya irin wacce nake nuna miki Mamana , ina miki soyayyar da duk duniya bana ma kowa irinta , banajin kunyar kowa idan nayi abinda ban kyauta ba amma Allah ya sani inajin kunyarki Mamana , babu wanda ya isa yasa nayi ko na bari amma idan har kika hanani na hanu , labarin waye Binna kuwa zan faɗa miki ne saboda abinda ya faru dake wanda ba’a san raina hakan ta faru ba , kuma ki yafemin na roƙeki ya haɗa hannayensa biyu tare da ci gaba da cewa kuma bazan sake tafiya na barki ba , ya ƙarasa maganar yana mai min kyakyawan murmushi …. Riƙe hannunshi nayi tare da cewa kayi alƙawari ? Jinjina kai yayi yana murmushi yace nayi miki alƙawari , nima murmushin nayi tare da cewa nima nayi maka alƙawari Babana bazan taɓa tafiya na barka ba , yayi Allah ya albarkaci rayuwarki Uwar masu gida , da amin na ansa tare da gyara zamana , shima gyara zamanshi yayi sannan ya fara…. *ALIYU MUHAMMAD BINNA…* Shine cikakken sunan da kowa ya sanni dashi , *BINNA* laƙani ne dana sakawa kaina shi bayan na shiga harkar wasan caca , dalilin binna kuwa saboda tsabagen neman asiri irin nawa , *BINNA* a binne kenan , dan da anyi magana kaza bazai yuwu ba , zance a binne shi kawai , tou idan nace a binne sai mutane suka fara ankara da abinda nakeyi dan haka sai nayi waiwayen damisa na zama Binna kawai dan ɓatar da mutane lissafinsu , sunan yana firgita kowa haka kuma yake bawa kowa tsoro duk wanda yaji ance *BINNA….* tou binna abin tsoro ne abun firgici tashin hankali ne ga duk wanda yasan Binna da irin rayuwar da nakeyi…! Malam Muhammad shine mahaifina , Maryam wacce ƙauye yasa ake kiranta da mero itace mahaifiyata , matan malam 2 mero da sahura , mahaiyarmu itace ƙarama kuma dake ta daɗe bata samu aihuwa ba , ita kuma Sahura dama tuni ta kwankwatso ɗiyanta goma sha shidda , hmmm Babana yayi tare da cije haƙorashin na gefen dama ya karkace leɓunansa sukayi sama , jinjina kai yayi sannan yaci gaba da cewa “ya “ya sha shidda saboda haɗama sai kace wata kaza , dan tun kafin a auro Mero tuni Sahura tayi haihuwarta ta gama…Mu talakawa ne na abin musali , kaf zuri’armu ba’a taɓa samun mutumin daya mallaki kaza biyar ba , kaf kauyen Ƙarara babu mutane masu talaucinmu , bamu gaji arziƙi ba kuma babu wanda yayi shi , kowa dai yanashan azabar talauci yadda ya kamata , Malam kuwa wutar talauci data isheshi ya rasa inda zai saka ransa saiya fara aikin tsubbanci , kuma sai Allah ya tallafa mishi domin idan yayi aiki kamar yankan wuƙa wuyar dai kafin yayi ne kawai , cikin ƙanƙanin lokaci sunansa ya fara ketawa yana zagawa kunnen jama’an duniya , yayin da mutane suka fara kiransa mai gobe da nisa… Nanfa harka ta buɗe dan Allahn yace masa zama , tun abun bai fita ba har mutane suka fara shigowa daga cikin birni suna zuwa wurinshi , a tsabibincin nasa fa yakai maƙura kuma shekarar arziƙin nasa ya tsaya kalmar zama da Allah ya yaddar masa taci gaba da tabbata akanshi…. Malam fa ya fara tara abun duniya , liƙafa taci uban ta da , dan malam ba mutum bane mai rowa dan haka jama’a suka fara saɗaɗowa zuwa gidanmu cin arziƙi , cin nan 3 a yini tou fa idan mutum yazo zaici ya ɗinke har yayi guziri , shi yasa gidan namu kullum ya koma kamar wani gidan biki ko suna…A lokacin da Mero ta samu cikin farko Sahura kuwa tace ina wuta ta jefata , nan ballin asiri ya fara tashi jefe² tahana mahaifiyarmu zaman lafiya , da ta samu ciki sai ya ɓare , ciwon yau daban na gobe daban , abun dai babu daɗi , Su kuwa malam ba abinda ya damesu da harkar da iyalinsu ke ciki burinsu kawai sudai a kawo musu , kullum matan malam basu da aiki sai wanke alluna , ana haka dai har Allah yasa Mero ta samu cikina , tunda Sahura ta lura Mero tana da ciki taci gaba da wurgago subbancinta , haba ina harta isa ? Allah yace saina zo asiri baya tasiri a wannan lokaci sai hukuncin Allah… Har Mero ta haifeni cikin wahala take da musibar rayuwa , tunda na sako ƙafa duniya dama azababbena aka haifoni , da rana zansha baccina har in gode Allah , amma da zaran an kira sallah magrib na fara kwarara ihu har garin Allah ya waye babu wanda ya isa ya runtsa idonshi kona second a gidan nan saboda kuka na , a haka akayi suna Allah ya cidani da Aliyu , ina wannan masifafen kuka da an kira asubahi kuma zanyi bacci , malam kuwa saida ya rubuce yace abani insha maganin kuka duk ranar da aka bani rubutu kukana sai yafi na jiya , har malam ya haƙura ya daina rubutu ana bani… Haka Mero ta haƙura taci gaba da rainona duk wanda ya ganta yasan tana tattare da damuwa , tabi ta soye tayi baƙiƙƙirin saboda tsabar rashin kwanciyar hankali , dana fara zama kuwa idan ta zaunar dani zan fashe da wani irin ihu mai firgici wanda dole saita ɗaukeni ta goyani , nadai zama fitinanne ta ko wane sashi , Dana fara rai rafe kuma ɓarna harta ƙeta , duk abinda yake na Mero bana ɓatawa amma daga ba ita ba duk abinda na gani saina tadashi aiki , Sahura tace iskanci kesa nakeyi ɓarnar tunda nasan abun uwata bana ɓatawa , da nayi mata ɓarna sai tayita dukana maimakon inyi kuka sai inyi ta dariya… Abun fa ya fara tayar da kowa hankali , har aka yayeni a nono , iskancina kuma sai abinda yayi gaba , tun ina ɗan firiri na , na iya tsakalo fitina saidai idan ban fita ba , masu kawo ƙara kuwa haka zasu jero layi , wasu a biyasu wasu kuma a basu haƙuri… Shekarata 3 Mero ta sake samun ciki , amma har ta haifeshi Allah bai sanar da Sahura ba , tashin hankali wanda tayi ba kaɗan ba , amma bata da yanda zatayi dan duk wanda yazo baya komawa sai idan Allah yaso… Ranar suna data zagayo aka sakawa jariri suna Muhammad , wanda ake kiranshi da ƙarami , ku kuma kuna ce masa Baba ƙarami , haka dai akaci gaba da cakwakiyar rayuwa , har Allah ya kawo wata mace matar wani attajiri malam yayi mata aiki , bayan buƙata ta biya shine ta siyawa malam gida anan cikin garin birnin katsina , a anguwar ƙofan marusa , daga nan muka tattaro mukayo birni ! Shekarar mu biyu da dawowa birni Mero ta ansa kiran mahaliccinta babu jinya haka kuma babu ciwon kai bare na hannu , nasha kuka kamar zan mutu na rashin mahaifiyata , wanda Sahura ko a kwalar rigarta , Bayan anyi kwana 3 da rasuwar Mero Sahura ta samu malam ta kitsifa masa ita bata iya zama dani ga iskanci ga rashin kunya ta taɓani ace dan uwata bata raye take azabatar dani , saidai ya raba mana wurin zama ,Ba tare da nazarin komai ko tunani ba , yace in bar mishi gidanshi dani da ƙarami , haƙuri na bawa malam akan ya bari saiya kamani da laifi , amma fur ya ƙeƙashe idanuwanshi saina bar mishi gida , ina ƙoƙarin barin ɗakin malam Sahura tace sai inzo in tafi da ɗan uwana dan so take gaba ɗaya fitina ta fitar masu daga gida , a lokacin shakarar ƙaramin 2 da wattanni , ni kuma ina da shekara biyar da “yan watanni , haka malam yayi mana korar karnuka , ina kuka na ɗauki ƙarami muka fita daga gidan ,Ina ɗauke da ƙarami na shiga cikin gari , duk wanda ya ganni ɗauke dashi zaice na mayar da yaron nan bana iya ɗaukarshi , ko sauraron mutane banayi bare na basu ansa , tafiya nakeyi har aka kira magrib , ni kuma a lokacin na isa wata anguwa ita Gambarawa…. Bakin wani shago na zauna na sauke ƙarami dake ta zabgaga kukan gajiya da yunwa , bayan na zaunar dashi naje na ɗauko buta da wani ya gama alwallah ya ajiye na bashi sauran ruwan daya rage yasha , bayan yasha na matsa wurin mai shagon da yake ƙoƙarin buɗewa ya dawo daga sallah nace Baba da Allah ka taimakamin da sadaƙa zan siyawa yaro abinci yaci , Cikin hargowa yace ai sai ka buɗe ka ɗauka mishi ɗan barauniya , dama irinku ne masu sacewa mutane abu idan basa nan , wata irin kwanya yaimin tsakiyar kaina harsai da nayi tunanin kaina ya huje , dariya nayi tare ce masa ka nunamin inda zan ɗauka , kuɗi ya fiddo daga cikin aljihunshi kwaci ² shege ɓarawon banza , kallonshi nayi sannan na duma ma kuɗin wawa , kaf kuɗin na kwace na ruga na cicciɓi karami nabi lunguna ba tare da nasan gari ba , Biyoni yayi da gudu yana a tara ɓarowa , ƙarami kuma sai kuka yakeyi saboda ya wahala , ganin jama’a na ketowa daga hanyoyi da dama yasa na samu wani zauren gida na sake na rufe bakin ƙarami sautin kukanshi ya daina fita… Dube ²n su sukayi basu sameni ba saboda haka suka hakura kowa ya kama gabanshi , saida na tabbatar babu kowa sannan na fito naje na samawa ƙarami abinci yaci muka bar anguwar Gambarawa a daren na dawo Qerau da zama…. Haka rayuwa taci gaba da tafiya , ni na saka kaina makarantar allo kuma na samu gidan aiki , gidan aikin suka sakani makarantar boko , haka dai na haɗa abu goma da ishirin , ga karatun allo ga boko ga gidan aiki ga rainon ƙarami , A daddafe dai nayi ta dafa rayuwar kuma ban sake zuwa wurin malam ba kuma daga Qerau zuwa Ƙofar marusa babu wani nisa , Shima ƙarami daya isa sakawa makaranta boko gidan aiki na suka sakashi , kuma tare dashi mukaci gaba da aikin gidan , daga baya ma suka bamu wurin zama a cikin gidan , Na gama secondry sch Bello ya shigo cikin rayuwata , gidan ƙawar matar da muke zaune gidanta itace take aikena gidan ƙawarta gidan kuma a maƙotan gidansu Bello ina zuwa idan aka aikeni nan ya ganni ya liƙemin , yana zuwa gidan da muke zaune yana yini wani lokaci ma har kwana yakeyi , ya shigeni sosai abota mai girma , Makarantar gaba da secondry tare da Bello muka fara nidai nayi karatu kuma na fito da sakamo mai kyau yayin da Bello ya faɗa harkar mata , a lokacin kuma ƙarami yana secondry sch aji biyar , bayan na gama degree aka fara neman min aiki , yayin da ni kuma nake neman ƙara faɗaɗa ilimin nawa… Har wannan lokaci banje wurin malam ba , kuma malam bai nemeni ba ni kuma naƙi nemansa dan dama ni nasan inda yake , saida naci gaba da karatu na , na faɗa harkar wasan caca daga nan duk lissafi ya jagulemin , dan duk wannan kangarar da nayi a baya tana da dalilinta kuma a gaba zaki ji ta , dan bayan na baro gida naɗan samu natsuwa , amma shigowar Bello rayuwata yasa na ida ƙwacewa…… 16/09/2019Jamila Musa…..💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 34*_Fatan na samu kowa lafiya ? Kuyi haƙuri na jina shiru kwana biyu banajin daɗi ne amma na samu sauƙi alhamdulillah ngode da addu’o’in ku a gareni masoyana , gaskiya naga soyayya kuma ngode sosai , na warware zamu ɗaura daga inda muka tsaya , fatan alkairi a gareku masoyana kuyi farin ciki…_* Shiru Babana yayi ya zubamin idanuwa yana min kallo mai tattare da bayaso ya faɗamin , nima ƙureshi nayi da idanuwa amma bance masa komai ba , shiru yayi yana nazari zuwa can ya ɗago ya kalleni , nima kallonshi nake har yanzu zuciyata dai ta bani kila zai ɓoyemin wani abu ne…Gyara zama yayi yaci gaba da cewa , zuwan Bello rayuwata yazo min da al’ajabi mai girma , wanda ya kasance bana iya ƙetare maganarsa , idan yacemin inyi zanyi idan yace na bari zan bari ya rabani da ko wane aboki shi ɗaya ne abokina , Bello shi ɗayane iyayenshi suka aifa , kuma attajirai ne na gaske , soyayyar duniya sun ɗorawa Bello sun sangartashi yadda ya kamata , saidai ya kashe waccan mota ya ɗauka waccan , ba mazaunin gida bane ba , domin duk kayanshi na sakawa yana cikin motarshi , tafiya yake jira kawai yayi gaba , gashi cikakken ɓarawo domin duk ƙarfin arziƙi mahaifinshi saida ya duƙar dashi ƙasa.Tun wancan lokacin Bello ya mallaki bantan baƙin biri , daya ɗaurashi duk inda ya shiga idan dai akwai kuɗi hayaƙi ne zai riƙa tashi , da yaga yahaƙi yasan kuɗi ne a wurin zai buɗe kawai ya kwashe yayi gaba , Bello mashayi ne , ɓarawo ne , ɗan caca ne sannan tantirin mazinaci ne , idan har ya zuƙawa mace masifa tou duk irin kamun kanta da natsuwarta sai Bello ya keta mata mutunci , baya neman zawara baya neman matar aure sai “yan yara ƙasa da shekarunki , shekaruna kenan ni Sultana , kuma daya biya buƙatarsa ya gama da ita wata zai nema… Da nayima Bello magana sai yacemin sa’ar caca malaminshi ya bashi , gabana Bello ke zuƙewa kuma gabana yake kwalbewa , ma’ana a gabana yake shawuwa yasha sigarinshi yasha giya da sauran kayan shaye ²n shi… Ni kuma a lokacin na koma makaranta naci gaba da karatu na , dan zurfafa ilimina dan na fahimci rayuwar idan baka da ilimin zamani mai zurfi tou ka zamo an maido wuta an ɗauke… Banda isashshen lokaci bansan abinda gida yake ciki ba idan na tafi makaranta , gidan da ake riƙemu akwai ɗiyar mai gidan itama yarinya ce ƙarama lokacin tana js3 ashe itama Bello ya ɗora mata alƙalamin kudirinshi akanta wanda ya fake da soyayya ne ni kuma duk ban sani ba , Wallahi babu abinda na sani tunda bana nan , ƙarami ma baya zama gida shima makaranta , Bello idan yazo bama nan zai buɗe ɗaki kawai ya shiga babu mai hanashi tunda abokina ne , Wata rana kwatsam ina makaranta “yan sanda suka zo suka tafi dani , tambayarsu na farayi lafiya ? Babu mai lokacina , haka suka sarkafeni da sarƙa suka tafi dani ofishinsu… Suna zuwa office sukaci gaba da dukana babu ji babu gani , sunma hanani nayi magana bare naji laifina ? Saida suka min lullusar fitar hayacci sannan aka wurgani cikin cell aka rufeni , Saida na dawo hayyacina naga Bello gefena yana kyalkyalamin dariya , ƙarami na gefe sai kuka yakeyi , goge hawaye nayi tare da cewa me mukayi haka abu babu mutunci ? Dariya Bello yaci gaba dayi yana shan lolypop inshi…Ƙarami na kalla nace meye wai ? Cikin kuka yace wai rafe naji dai suna cewa , cikin ɓacin rai nace rafe me ? Miye rafe kuma ? Ƙarami yace nima ban sani ba kawai dai haka naji suna cewa , tsoki nayi zuwa can nace waye yayi rafe ɗin ? Cikin kuka yace mu duka naji suna cewa , har yanzu Bello dariya yakeyi yana shan lolypop , raina naji ya ɓaci na tashi nayi kan Bello naci gaba da dukanshi babu ji babu gani ina cewa me mukayi ne …? Dariya Bello yakeyi yana cewa wallahi hauka yasa suka kawoku , ni kaɗai nayi kuma yarinyar da kanta tacemin tana so in rantsar da ita , itama ta zama cikakkiyar mace kamar kowa , tou dan nayi abinda takeso sai azo a rufemu , ai godemin ma ya kamata suyi , shaƙe Bello nayi sosai tare da cewa itama ka zuƙe…….? Bushewa yayi da dariya to me ake jira da abun kwaɗayi…. ? Yau taji abinda uwarta keji , da sauri na rumtse idanuwana dan naji kaushin maganar Bello a raina , murmushi yayi tare da cewa kaji babu daɗi ko ? Tou ai itama uwar ta tuni na bata alƙalamin daraja kuma yanzu nan zata zo ta fitar damu dan nace idan har ta bari muka kwana sirrinta a buɗe yake dan ina da babbar sheda , Kallon Bello nayi idona cike da hawaye nace hajiya ma …..? Murmushi Bello yayi yace harda tukwuici take bani ma , kuka naci gaba dayi dan banji daɗin abun ba , daga haka nayi shiru na samu wuri na natsu muna jiran tsammani… Hajiya itace tayi cuku² dan Alhaji shine yasa aka kamo Bello kuma Bellon yace tare mukayi kowa saida ya zagaya sau biyu domin ya buɗe mutuntakar a yarinyar yadda ya kamata ! Saida Hajiya ta saki kuɗi sosai tare da ƙaryata zance mijinta cewa ba Bello ne yayi wannan aika ² ba wasu daban ne sukayi kuma suka gudu haka nan aka ɗaura alhakin tuhuma akansu yara marayu basuji suka gani ba sai Allah ya saka musu… Saida aka kai ruwa rana sannan muka fito , Bello yace mena faɗa muku nace muku zamu fito babu ɓata lokaci , haushin sa kawai nakeji domin naji ciwon wulaƙantawar da yayiwa yarinyar da nake ma kallon ƙanwata , kuma naji ciwon keta mutunci mahaifiyata Hajiya da ta ɗaukeni matsayin ɗa , kuma nima daga wannan lokaci na ɗaura ɗamarar saina masa yaji idan da daɗi ! Alhaji kuwa korar kare yayi mana daga gidanshi bayan yayi maganganu masu zafi da ɓatanci akanmu , kayanmu muka kwashe daga gidan Bello ya bamu mazauni a gidansu… Duk lokacin dana kalli Bello sai naji kamar in haɗiye zuciya in mutu saboda tsabar baƙin cikin abinda yayiwa mutane masu mutunci , koda zai fita da daddare binsa nayi domin na fara harin rayuwarsa ,Gidan caca muka nufa dashi , shine zuwana na farko dan kallon wasan da Bello zai buga , bayan yayi “yan al’adunshi ya binne ya ɗaura , hankalina ya tashi ganin tulin kuɗi da aka zuba , cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gabatar da wasa , an ɗauki lokaci mai tsayi ana gwabzawa bayan wasan yayi zafi Bello ya lashe wannan makudan kuɗaɗe , Bayan ya kwashe kuɗinshi aka fara shagali , kwalaben giya suka fara wali da dai duk wani mai ɓatar da hankali , ina cikin ɓacin rai dan haka bansha ba , amma Bello yace idan nasha zan rage damuwa , dan haka na ansa nasha cikin ƙanƙanin lokaci na nemi damuwa na rasa ! Uwar masu gida labarin dai bazai buɗu duka ba , dan wasu labaran bai kamata na faɗa miki ba , mu tsaya haka nan , domin nima na zama atsabibin matsafi dan ko magana nayi bata faɗuwa ƙasa na koma kamar wani mai kambun baka saboda tsabar neman asiri irin nawa !Daga nan na shiga wasan caca nima , naci gaba da harkar mata , shaye² da duk wani abunda ya zama zunubi , nayi nisa banajin kira , sheɗan yaci gaba da busamin sarewar halaka na shi , ga Bello bashi da ƙanne , Bayan ƙarami ya gama secondry sch yacemin bazai ci gaba da karatu ba , nayi juyin duniya yacemin daga haka ya tsaya , to ni na bashi gidan zama wanda a caca na ciwoshi , kuma ni na bashi kuɗi yaci gaba da kasuwanci , kuma duk matan daya aura nine na kashe kuɗi nayi masa hidima ,Ƙarami bai daɗe da aure ba Malam ya saki wasan , wato ya mutu , bayan yasha doguwar jinya an girbi abinda aka shuka domin aikin tsubbu ɓata ce , ya lalata maka zuri’arka ga dakon zunubi , wasu an ɓatar an raba an haɗa dan dole an talauta wasu an raba aure an raba uba da ɗa anyi an gama dai duk an tafi an iske Allah…. Bayan ƙarami yayi aure aka barni daga ni sai Bello mukaci gaba da gurza rayuwa , har Allah yasa ya samu yarinyar da yake mugun so , kyakkyawar yarinya mai hankali da biyayya Bello ya mutu akan yarinyar nan , sukaci gaba da soyayya , na tambayeshi ko itama dai kamar sauran ? Yacemin a , a wannan ta aurece gaskiya , naji daɗi sukaci gaba da zuba soyayya sun shaƙu sosai tarayyarsu abun burgewa , Basu wani daɗe suna soyayya ba sukayi aure , lumshe ido Babana yayi sannan yaci gaba da cewa ango na shirin shiga ya angonce Binna ya anshi budurcin matar Bello , Bello yayi kuka saida yayi jinya gashi kuma yana mata san da baya iya rabuwa da ita , uhum tafasha azaba yarinyar nan , bayan Bello ya samu sauƙi akaci gaba da abota , Nima yana nan zai rama ashe , to yanda kasar suri bata cuwuwa ga bakin duk wani bil’adama haka Uwar masu gida tafi ƙarfin Bello dan yasan idan yace akanki zai ɗauki fansa tabbas nima zan rama akan “yar sa , shi yasa ya matsamin na sakaki a caca , hawaye ya cikawa Babana ido , Yaci gaba da cewa yasan duk duniya ya cire soyayyar Allah da manzan sa babu wanda nake so a faɗin duniyar nan bayan ke , tabbas yasan zanci caca shine suka juyarmin da hankali ta hanyar bani asiri cikin abunsha , bayan sunyi galaba a kaina suka rasa abunyi , shawarar abokinmu ya nema shine yace yasan wani da yasan Dikko , yace idan aka kaiki a wurin bazan iya ja da hukuma ba , hankalina ya kwanta da naji wurinshi kike nasan babu abinda zai faru ,Ashe shima sun shirya mishi gadar zare , ɗan masu aikin gidansu shine yayi jagoranci , cikin kuka Babana yace aka ciwa “ya ta mutunci , haka na gudu na ɓuya kamar ƙolo na boye saboda kunyarki , duk da nayi haƙuri ban ɗauki fansa akan abinda Bello yayi ba duk da haka bai faru ba , Amma dana biyewa sharrin zuciya gani takaini ta baro ni , murmushi nayi nace ba komai Babana na yafe maka , kuma wannan abun ka ƙaddara babu abinda ya faru , ! Amma me yasa ka bar iyalinka cikin wahala ? Tsoki yayi sannan yace nima haka aka barni a saman titi bansan mai kyau ba bansan mara kyau ba , banda mai nunamin kyakkyawa ko mummuna , babu wanda ya kula dani shi yasa nima na saki kowa yayi rayuwarshi , Baba Allah fa yana kallonka , ka karanta kuma kaji ka gani kuma kasan abinda Allah yace akan iyali , girgiza kai yayi tare da cewa kar muyi haka dake Mamana , banasan maganar su , tou Babana amma me yasa baka aiki ne ? Wannan ra’ayina ne , caca na zaɓa kuma zanci gaba bazan daina caca ba sai numfashina ya ƙare , cike da damuwa nace ko kana da dalili ne ? Uwar masu gida mubar maganar nan ,Tou Babana ina Sahura ? Kuma me yasa kayi kangara kana ƙarami ? Murmushi Baba yayi tare da cewa wannan kangara wani aiki ne malam yayi akan wani yaro dan ya lalace , matar Babanshi tazo ayi mata aiki ne , sai abun ya dawo kaina , Matar ta dawo ta faɗawa malam buƙata bata biya ba , can wurin binci kenshi ya gano inda aiki ya sauka kuma ya warware komai , idan dai kayi mugunta tou ka daina saurin rufe ƙofa domin dawowa takeyi , Sahura kuma tana can gidanta bana dai zuwa gaskiya… Tou ita Inna baza ta dawo ba ? Manta da ita gani nan na isheki taje can tayi ta zuciyarta , kallon agogon hannunshi yayi ya miƙe yana cewa bani makullin motarki , miƙa mishi nayi ya fita yana mita ba’a kawo mishi kuɗin wayoyinshi ba , gaskiya Babana bansan irin halinshi ba , dandai yaƙi yadda ya faɗamin komai duk haka ya bani labari nidai a duƙunƙune…. A ƙofar gida ya anshi kuɗin wayoyinshi yayi gaba , “yan gida kuma cewa sukeyi da wani yake da motar nan sai Baba ya siyar da ita amma da yake ta Sultana ce komai daren daɗewa zai dawo mata da abinta , saboda kar yamin faɗa raina ya baci shi yasa baiji a ina na samu mota ko yamin faɗa ina hawa mota ba , Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , Babana yake amfani da mota ta , Bello ya fita harkata nima na fita harkashi , d c o babu ruwana dashi , Hafsa da Amisty banda labarinsu , su A ` i ma bana shiga sabgarsu , mijin Zalifa da Zalifar duk na daina jinsu , Alaji kaɗai yake zuwa fira danshi ya matsa aurena zaiyi… Haka nan na tsira yin bedday babu gaira babu dalili , nayi i v nasa akaci gaba da rabawa , har a gidan radio nasa Alaji yakai sanarwa , manyan baƙi a wurin Baban Amisty mai yanka cake kuma Baban Hafsa , wurin taron kuma wani zuƙeƙen gidan Baban Hafsa , nayi gayya duk wani lungu da saƙo na zaƙulo manya ² karuwai nakai musu gayyata wanda duk ba ƙawaye na bane nasu Amisty ne , Al’amarin wannan taro ya karkato da hankalin jama’ar gari a kaina dan ban ibo abun da wasa ba , kowa da abinda yake faɗa akai na yayin da wasu mutane suka cewa taron iskanci ne ba wani taron birthday ba , Hafsa kuwa Amisty tayi mata waya ta faɗa mata cewa zanyi birthday amma taga venue gidan shaƙatawar Dady inta ne , yaushe ne ake taron Hafsa ta tambaya ? Amisty tace mata ranar laraba , Hafsa tace tou Allah ya kaimu zata ga yanda zan wulaƙanta ta …. Nima da Nana ta bani labari dariya nayi tare da cewa Nana nima zan wulaƙanta ta yayin da taga Dad inta ya yanko cake ya rungumeni yana bani a baki na , itama Nanar dariya tayi tare da cewa Allah ya kaimu zanje idan har Audu ya barni , Lokacin da Dikko ya samu labarin wannan taro da zanyi zuciyarshi tayi mishi ɗaci domin yasa ana biyayyar mishi rayuwata duk wani motsina da komai nawa babu wanda Dikko bai sani ba , Tsoki yayi tare da kallon agogon hannunshi jinjina kanshi yayi ya cusa “yan yatsun sa ko wane yana gogar ɗan uwansa , laraba , ya faɗa a bayyane tare da sake jinjina kanshi , litinin kuma ya faɗa a bayayyane Allah ya bamu aron rayuwar muje larabar dani dake…….. 19/09/2019Jamila Musa 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 35 Har yaci gaba da cin abinci kuma yaji gaba ɗaya moƙoshin nashi abincin baya wucewa , tsananin ɓacin rai da damuwa suke ta kartar masa zuciya , dakel ya haɗiye yawu mai ɗacin gaske , kallon Al ‘ ameen yayi yace kiramin Umar…. Wayar ya ɗauka da sauri ya fara kiran wayar Umar , saida Umar ya ɗauki wayar ya miƙawa Dikko cikin ladabi , ansa Dikko yayi cike da ɓacin rai yace har yanzu kana anguwar ko ka fita ne … ? Magana Umar ɗin yayi , Dikko yace tou kaje ka kaima An mata waya zanyi magana da ita yanzu ² yi sauri karka ɓatamin lokaci , saida ya jira abinda Umar zai faɗa sannan Dikko ya kashe waya ,Ina zaune ƙofar gida dani da Alajina muna fira Umar ya faka da machine inshi , kallo ɗaya nayi masa na kauda kaina yayin da na ciro wayana na fara ƙoƙarin kiran Wane Yaro , Sallama yayi suka gaisa da Alaji nima ya gaisheni , ansawa nayi babu yabo ba fallasa , ɗan gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa dan girman Allah saƙo aka bani wurinki , daina kiran wayar Wane Yaro nayi na tattara hankalina kaf wurin Umar nace waye ya baka saƙon ne …? Cike da ladabi ya miƙomin waya bayan ya kira number ya miƙomin yana cewa kiyi magana an ɗauka , cike da wasi² na kara wayar a kunne na tare da cewa Assalamu Alaikum…. Ansa sallamar yayi yana mai ci gaba da cewa An mata kinaso in saka ƙafar wando ɗaya dake ne ? Shiru nayi banyi magana ba , Dikko yaci gaba da cewa na rantse da Allah ki kama kanki wannan iskanci birthday in da kika taro ki warwareshi tun kafin inzo wurinki ina fushi , banda kyau idan na ɓata rai ki roƙi Allah ya rabaki da ganin fushi na amma na rantse da Allah…. Saida yayi rantsuwa mai sa faɗuwar gaba sannan yace idan kunne yaji …. Sai kuma yayi shiru bai ida faɗar maganar ba , ni kuma na ɗaura da cewa idan ka barni na huta baka ƙaunar Allah , tsoki nayi tare da miƙawa Umar wayarshi naci gaba da magana na da Alaji ,Cike da masifa Dikko yace Umar ya maidomin wayar , bani yayi nima kuma na ansa , cikin sigar lallashi yace An mata nine bana ƙaunar Allah ? Wai mi yasa kike min magana haka babu ɗa’a , ai kasan gidanmu ba’a koyamin ɗa’a ba shi yasa ma har nayi rashin ɗa’ar a cikin gidan ubana , Dikko yace idan kinajin rashin kunya ki fita daga cikin mutane ki zageni idan kin isa , ni nasan baki isa kimin rashin kunya inda babu kowa ba , dama kin tsaya a gaban waɗanda ko naso nayi miki hukunci zanyi haƙuri a haka kike tunanin bakyajin tsoro na ne ? Idan dai bakijin tsoron Dikko maza ki tashi daga inda kike kice Dikko ƙarya kakeyi nafi ƙarfin ka takuramin ki faɗi haka kiga yadda zanyi wasan kura dake wallahi …. Kamar wata sakara na miƙe na matsa daga inda su Umar suke , ashe shi kuma yayi wayau ne dan kar in riƙa wulaƙantashi ne a gaban yaronshi , saida na matsa sannan nace ƙarya kake ni nafi ƙarfinka kuma nafi ƙarfin ka takurani dan banajin tsoronka kayi duk abinda kakejin zaka iya yi na matsa daga cikin mutanen…. Dikko yace tou babu komai dani dake aga fasashshe , ni zanzo katsina insha Allah gobe talata , ke kuma zakiyi birthday ranar laraba sai nazo , kuma karki sake kiyi mafarkin gemuna na faɗa miki…. Gemun banzar ka gemun wofi , Allah ya sawaƙe min in ganka a barci na , cikin murya mai saukar da kasala yace nifa bana san cika baki bayan nasan komai , kawai yarinyar kirki taga ustaz ta maƙale mishi aidai kina so na ko…. ? Tsoki nayi ban bashi ansa ba na kashe wayar naje na bawa Umar ko sallama banma Alaji ba na shige gida raina a ɓace , Murmushi Dikko yayi bayan na kashe waya tare da cewa An mata rigima , zaki zo kusa dani kuma inaji a jikina wata rana zaki rumgumeni ki kalli cikin idanuwana kice Dikko ina sanka , yana maganar yana nuna yanda Sultana zatayi , cikin farin ciki yaci gaba da cin abinshi bai sake kiran Umar ba , kuma koda Umar ya kira dan ya faɗa masa cewa Sultana ta tafi bai ɗauka ba , Shima Alaji kiran wayana yayi tayi naƙi ɗauka , ya gaji ya tashi yayi tafiyarshi , shima Umar tafiyarshi yayi gida ,Ni kuma ina shiga ɗaki saman katifa na faɗa nayi ruf da ciki bansan dalili ba , maganar Dikko yake dawo min a zuciyana , karki sake kiyi mafarkin gemuna , cike da fargaba zuciyata ke cewa kodai Dikko ya gane ina kallon masa gemu ne …. ? Tsoki nayi na gyara kwanciyata ina tuno kyakkyawar fuska Dikko , tunani dai barka tai a zuciyata har bacci ya ɗaukeni…. Da safe Alaji yazo ya kaini kasuwa dan Babana baya nan kuma motana tana wurinshi , siyayya na bada mamaki nayo domin fa Alaji yana da hidima kuma yana da gabata , ya kashe kuɗi duk yanda tunani baya tunani , ko kayan da zan saka wurin partyn zagayowar shekarar aihuwata wallahi masu masifar kyau da tsada ya siyo min abun dai zabburgewa sai wanda ya gani , Bayan mun gama siyayya nace masa ya tafi zanyi kitso idan na gama zan kirashi ya ɗaukeni , Alaji yace to saida ya ƙaramin kuɗi ya tafi ni kuma na shige shagon “yan arna da basa gane yare na , na fara faɗa musu abinda nake so amma dan ubansu wai basu gane ba , saida wata rantsatstsar karuwa maiji da iskanci har iskanci yayi mata sign tayi musu bayani , girar ido za’a sakamin akaifa da kuma atach duk gashina saida nasa aka yimin ƙari saboda tsabagen wawanci irin nawa , A ƙofar gidanmu kuwa 5:00pm Dikko suka kafe motocinsu , aikawa yayi a kirani amma sai akace masa na tafi kasuwa , maimakon ya tafi sai yace zai jirani har na dawo , Duk lokacin da minti ɗaya ya wuce sai Dikko ya kalli agogo ranshi ya ƙara ɓaci , shiru ² babu ni har aka kira magrif , cikin damuwa yace ma Al ‘ ameen muje zan dawo anjima , Tashin motocinsu sukayi gaba ɗaya suka taho , suna fita anguwar mu kuma muna shigowa hannun riga mukayi dasu wato suna fitowa mu kuma muna shigowa , Babu abinda na sauko daga mota nace ma Alaji ya tafi sai Allah ya kaimu , sallama mukayi dashi ya tafi ni kuma na shige gida , ina shiga na shirya a gaggauce domin Baban Amisty zaizo , naje kasuwa har nayo kawalcin mace zan haɗasu , itace karuwar da muka haɗu ta tambayeni sana’ar da nakeyi nace mata karuwanci nakeyi , tace ashe tafiyar ɗaya ce ? Nace mata Eh musayar number mukayi har na bata labarin iyayensu Amisty tace suna da mai ne ? { kuɗi } nace sosai ma , shine tace a cikin daren nan in bata aron kowa a cikinsu ita kuma tamin alƙawarin zata ɗaukomin su dukansu a cikin yanayi mara kyau tou shine zan haɗasu , duk da dai malami da mawaƙi da karuwa basu da amana amma zuciyata ta yadda da ita 100% , Har ƙofar gida Baban Amisty ya ɗaukeni kuma yanzu ma muna fita Dikko yana shigowa , akace masa yanzun nan muka fita ko bakin titi bamu kai ba , da sauri ya biyo bayanmu ko zai sameni amma bai iskomu ba , ganin baisan ta ina zai samoni ba yasa ya haƙura ya koma ƙofar gidanmu a ranshi yayi alƙawari ko zankai yaushe ban dawo ba zai jirani ,Daga gidanmu ƙofar soro muka nufa gidansu Mamy ƙarfe 8:18pm mukayi parking a ƙofar gidansu kamar yanda tayimin kwantance , bayan mun tsaya na kirata a waya , babu jimawa ta fito cikin shiga mai ɓatar da hankali , tana isowa ta kama mota ta buɗe ta kashe a gidan baya , shi kuma yaja mota muka tafi , shegen tsoho kenan yace ina muka nufa ne ? Yayi maganar yana kallona , Murmushi nayi tare da cewa nifa guzirin dare nayo maka itace zaka tambaya bani ba , kaga ni kullum muna saka rana amma abun bai yuwu ba shine dana ga mai buƙatar ruwa a tsakar rana nace tazo ina da ƙatuwar randa { tukunya } a gidana har yoyo takeyi { ɗiga } kaga kuwa idan har ta riƙe babban kofi a tausayawa ruwan nan domin saita ƙare shi kaf hankalinta zai kwanta , juyawa nayi na kalli Mamy sannan nace a ina zakisha ruwan ne …. ? Cike da bariki tace aishi ruwa ko a tsakiyar hanya shanshi akeyi saidai idan ba ƙishirwar ke damunka ba , amma tunda ni mace ce dole zan matse ƙishirwa har mu isa gida , amma ka daure kar kayi tafiya mai tazara dan lumfashina gaf yake da ɗaukewa , ! Karkata mota yayi ya ibi hanya , muka nufi kwaɗo , har muka isa babu wanda ya sake magana , a ƙofar gida yayi parking shida ita suka shiga aka barni a cikin mota , shigarsu babu jimawa na fara kiran Baban Hafsa inda zamu sameshi ya faɗa mana nace muna zuwa babu ɓata lokaci , Mamy kuma da Baban Amisty bansan abinda ya faru ba , sundai share awa da rabi sannan suka fito… Bayan sun fito ta buɗe inda nake zaune tace fito mana haka nan , nace kidai shigo muje , Mamy tace nan zamu sauka , fitowa nayi mukayi sallama dashi tare da ƙara tuna mishi sai mun haɗu wurin party yace in Allah ya yadda , yana tafiya muka samu wuri muka zauna , wayata ta ansa ta tura min vidion data ɗauko nashi abundai babu kyan gani ko ya akayi tayi masa dibara ta ɗaukoshi tasa shi sai iskanci yakeyi , a wayana ta tura bayan ta tura ta shiga whatsapp ta turawa Amisty abinda zata faɗa nake faɗa tana rubutawa… _Salam aminiyata Amisty , Sultana ce ban sani ba ko kin goge lambana shi yasa na baki sani dan kar ki shiga dogon nazari da tunani , kinsan mage bata cin bushiya , idan kuma maciji ya raɓi bushiya noƙe kanta takeyi yana tahowa da ƙarfinshi dan niyar mugunta sai ta noƙe kanta ya soki ƙayoyinta , maciji baya san tabo daga nan sai ya sari kanshi ya mutu , bushiya sai ta fito taci gaba walinta a duniya , tou haka tsaka take mage kaɗai ke cinta ta rayu amma ke in kakaci ta sai sheƙawa lahira , ganin aljanni a siffarshi akwai tsoro da firgitarwa masana ɓoyayyan sirri suna cewa idan kaga aljani a siffarshi kwanakin mutuwar ka ne yazo , nidai naga aljani ban mutu ba kuma naci tsaka ban mutu ba shi yasa na turo miki kema ki gani shin kina da yawancin kwana ko daga yau kwananki ya ƙare ne….?_ Turawa tayi ni kuma na ɗora da voice note cewa kiyi haƙuri kuma kibi sannu ki warware maganganuna kinsan tsarƙesu nakeyi idan kin gani kiba Hafsa ta tayaki gani….Bayan na tura muka hau napep muka doshi barhim estate acan Baban Hafsa ke jiranmu , shima dai sun shana yadda ya kamata kuma Allah ya bata nasarar ɗauko min mugu , itama Hafsa tura mata nayi da voice note cewa… Duk gudun kare idan yaga kura ɓoyewa yake domin tsira da rayuwarshi , haka mutum idan yaga abun tsoro kuka yakeyi ya rumtse idanuwanshi , irin haka kikaji a lokacin da kika cire towul in dake jikina….. ? Ina gama faɗa na sakeshi ya tafi…. , Napep muka hau muka nufo gidanmu , saida aka fara saukeni aka wuce da ita bayan ta shedamin zasu zo wurin shagalin ita da zugar tata ƙawayen , godiya nayi ina ɗaga mata hannu har suka tafi , Kallon agogon hannunshi yayi yaga 11:35pm , daga ina nake a wannan daren shine tambayar daya fara ma kanshi kuma bashi da mai bashi ansar tambayar , ni kuma cike da farin ciki na tunkari ƙofar gidanmu sai tsalle² nakeyi na jin ɗaɗi na shige gida abu na , Jiki a sanyaye DK yaja motarshi ya nufi gida zuciyarshi tana mishi babu daɗi , amma yayi addu’a gobe tazo mishi lafiya , Yau laraba kuma itace ranar da nake wannan gagarumin taro wanda na samu damar gayyato mutane daga sasoshi da dama , tunda safe ake shiga da fice a gidanmu duk inda ka buɗe idonka zunzurutun karuwai ne kawai suke kai koma , wane yaji ga wane waccen taji ga wance , taron motoci ne burjik a ƙofar gidanmu duk wanda ya wuce sai yayi tir da irin matan da dake ƙofar gidanmu ! Shi kuma Dikko a safiyar nan tayi mishi babu daɗi dan matarshi aka kai asibiti bata da lafiya sosai , kuma taƙi cin abinci ta rame tayi duhu saboda ciwo da damuwa , hankalin Dikko idan yayi dubu ya tashi da guda ² kallo ɗaya zaka mishi ka gane yana cikin damuwa , ga damuwata ga ciwon matarshi …. Taruwa akaci gaba dayi duk yaran Baba Ƙarami sunzo gida ya cika taf kuma na duba har yanzu daga Amisty har Hafsa babu wanda ya hau online dan suma suna can suna shirya tasu gadar zaren , Komai fa anyi kowa ka gani a wurin shima yakai wani babban shege , sai 6:00 aka fara tafiya wurin partyn , Nana dai bata samu zuwa ba mijinta ya hanata kuma ta hanu , Karima itama bataje ba amma A ` i da Saude tare dasu aka tafi duk yayuna maza da mata sunje ,Dikko yana duƙe gaban gadon Sadiya riƙe hannunta yayi cike da damuwa yace Sadiya karki kashe kanki don Allah idan baki so na ki faɗamin sai in sahale miki auren nan ki huta , ni ina da damuwa idan naga kina cikin damuwa ko nayi miki wani abu bai miki daɗi ba ne ? Karkata kanta tayi gefe hawaye suna ci gaba da gangaro mata , zama Dikko yayi gefen gado ya tattaro natsuwarshi fuskar Sadiya ya tallafo da duka hannayenshi yace mene ne ? Ki faɗamin wai meke damunki ne ? Dakel ta ɗaga bakinta zatayi magana a daidai lokacin da wayarshi ta fara ringing , cirowa yayi ya duba , Umar ne dan haka ya ɗauka tare da cewa ina ne….. ? Bayani Umar ɗin yayi masa , bayan ya gama Dikko ya kashe wayarshi , shafa gefen fuskar Sadiya yayi ina zuwa , yana faɗin haka ya miƙe ya fito daga ɗakin , ita kuma taci gaba da kuka , bayan ya fito yacewa Mom insha zaije ya dawo yanzu , Allah ya tsare tayi masa Al ‘ Ameen da sauran tawagarshi suka rufa mishi baya…. ! A bakin get suka ɗauki Umar suka nufo inda muke taro , a lokacin anci rabin shagali itama Hafsa ta taho dan ta wulaƙantani tunda gidan Babanta ne , amma tana zuwa labari yasha banban duk wannan taron jama’ar bai hana uban Hafsa rungumeni ba ya yanko cake yana bani a baki , gaba ɗaya wurin aka ɗauki sowa da ihu shi dama Alaji tunda ya ajiye kayan party nace kawai yaje tunda taron mata ne babu maza , kuma yayi tafiyarshi… Lallaɓawa tayi ta koma da baya ba tare data bari wani yaji koya ganta ba , ihu akaci gaba dayi sakin sauti akayi yadda ya kamata mata sukaci gaba da farantawa sheɗan , Hafsa tana fita taci karo da Dikko ya fito daga mota , da gudu ta nufi wurinshi tana kuka cikin kuka ta fara faɗa mishi abinda Sultana tayi mata niko nace danma baki ga vidio ba , number wayar Sultana Dikko ya ansa a hannun Hafsa ya fara kiranta , Muna ta cashewa wayata ta fara zurzur dan ba ƙara takeyi ba murzawa takeyi sai kaji sautinta yana shiga maka hannu burbur , ɗauka nayi naci gaba da kwantace ba tare dana jira naji ko waye ba ,Cikin wata irin murya yace fito gani nan na kasa gane gidan , wallahi banyi tunanin Dikko bane nayo waje , ina fitowa naga Hafsa tsaye da wanda bansan ko waye ba domin ya juya bana ganin fuskarshi sai bayanshi , cike da mugunta nayo wurinta dan a tunani na taga vidio zamu cashe rashin mutunci , Saida nazo gabansu na gane Dikko buɗe baki nayi da zumar nayi magana ya wanka min wani irin gigitaccen mari harsai dana juya kamar ranfa saboda karfin mari kafin in dawo hayyacina ya sake wankamin wani firgitacce wanda saida nayi ɗimuwar tunani na dan wallahi a daidai lokacin da zaka tambayeni suna na bansan abinda zan faɗa maka ba , Ƙara ɗaga hannunshi yayi zai kaimin wani marin a gigice na riƙe hannun cikin kuka nace yi haƙuri don Allah , a tsawace yace tou shiga mota , har yanzu dafe nake da inda ya mareni na nufi wurin motar da kanshi ya buɗemin na shiga sannan shima ya shigo dani dashi ne a baya , rufe murfin motar yayi Al’ Ameen yaja sauran motocin suka biyo bayanmu… Duƙar da kaina ƙasa nayi ina kuka cikin sauti mara hayani jikina sai kyarma yake dan har yanzu marin shiga jikina yakeyi ,20/09/2019 Jamila Musa ….. 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 36 Duƙiyar ta isheni na ɗago hannuwana na rumgume kujerar da ake kira da mai zaman banza , ta kusa da Al ‘Ameen babu kowa akai dan haka na rumgumeta kawai naci gaba kuka , Kallon hannuna Dikko yayi idonshi ya sauka akan wayata kawai ya miƙa hannunshi da zumar cirota daga wurina , da sauri na ƙara riƙe wayar gam tunda bana saka ma waya wasu malatsan sirri wanda saini na buɗe da kaina zata buɗe a buɗe take zaka iya shiga duk inda kake so… Da ƙarfinshi ya fizgi wayar kafin yayi mata kyakkyawan riƙo na fizgeta a hannunshi dan bai kamata ace anga wannan ɗaukar ba bai kamata ba , miƙo hannunshi yayi tare da kauda kanshi gefe yace bani , Girgiza kaina nayi alamar a , a , cikin tausassar murya ya matso da fuskarshi kusa dani yace bani wayarki nace , matsawa nayi tare da ƙara saƙe wayar a bayana , shima matsowa yayi kusa dani yace zaki bani ko sai kinci cingom ne … ? Cikin kuka nace dan Allah ka shafamin lafiya , kallona yayi gefe da gefe sannan yace ta ina zan shafa miki inyi sauri dan nafi so kiyi lafiya da nisan kwana ya ƙarasa maganar yanamin kallo mai nuni da rainin hankali , nima kallon raini hankali nayi masa amma banyi magana ba ,Shima shiru yayi bai sake magana ba kuma ya daina maganar in bashi waya , daga haka dukanmu babu wanda ya sake magana har muka zo inda zamuzo , duk sauran motocin a waje suka tsaya tamu kaɗai ce aka buɗe ma get muka shiga , bayan Al ‘ Ameen yayi parking ya fita daga cikin motar aka barni daga ni sai Dikko ! Al ‘ Ameen na fita Dikko ya sake taro hannu in bashi waya , cikin kalar ban tausayi na maida hannuwana baya tare da cewa dan Allah kayi haƙuri , ni nace kinyimin laifi ne ? Wayarki kawai zaki bani nace ya ƙarasa maganar cikin kausasa murya yana zazzaro idanuwa , Tsoro naji ya kamani sosai dan haka da sauri na miƙawa Dikko wayar , ansa yayi yana mai min ƙwafa tare tare da latso wayar haske ya bayyana , kafin ya shiga inda yake so kiran Amisty ya shigo cikin wayar , badai serving nake da sunan mutum ba lamba ce kawai , dan haka kiran sunan lambar dana ajiye number Amisty yayi sannan ya shafa wayar ya kara a kunnenshi , Dafe kaina kawai nayi lokacin da Amisty ta fara watso kalamai masu zafi da ɓatanci akaina sai ta ciko bakinta da ashariya sannan ta luƙaƙamin tare da furta wallahi idonta idona sai takaini kiyama ta dawo , maganganun dai babu daɗi dan har mahaifina ta saka duka dai abun gwananin ban takaici , tana zurara zagin wayar Hafsa ta shigo , amma bai ɗauka ba saida Amisty ta sauka ta kashe wayar , har ya gama waya da Amisty kiran Hafsa daya tsinke sai ta sake kira…. Itama Hafsa ta tata nata rashin mutunci itama a kalaman nata maganganu tayi masu kyaushi itama dai abun babu daɗin ji , idan tayi magana taji Dikko baice uhum ba , sai tace kina jina ko ? Sai yace Umm itama itace ta gaji ta kashe wayarta…Cikin takaici Dikko ya kalleni tare da cewa fita , ina zanje ? Rumtse idanuwanshi yayi tare da sake cewa fita bana san ganin ki wallahi komai zai iya faruwa ki fita kafin naji miki ciwo , ƙaruwa hawaye na sukayi nace da Allah wai ina zanje ? Ki fita…….. Ya faɗa cikin murya maisa firgici babu shiri na buɗe mota na fito , sai yaita yin abun kamar wani shafar aljannu , Ina fita Al ‘ Ameen yace muje ciki yayi gaba babu musu na bishi muka matsa , makulli yasa ya buɗe ƙofa sannan ya shiga , nima shiga nayi palo ne mai girman gaske sai wasu ƙoƙofofi biyu da bansan ko ina ne ba , makullin ya ajiyemin a saman hannun kujera yamin saida safe…. Banyi magana ba na saki baki kamar lefen wawiya ina kallonsu suka fice daga gidan , dan daga cikin palon zuwa bakin get ba wani nisa kuma daga cikin palon kana hange duk wanda yake bakin get , wuri na samu na zauna ina maijin takaicin rashin kasancewar wayana a kusa dani , A ɓangaren masu party kuwa saidai shagali yayi nisa sannan aka gane bani a wurin , nemana aka farayi amma ina mutane basu ankara ba Dikko yayi layar ɓata dani , wasa ² abu ya zama gaske yayin da wasu ke cewa sunga anmin waya na fita , nemana aka shiga yi amma babu ni kuma babu labarina…. Dikko kuwa asibiti suka fara zuwa ya ƙara duba Sadiya da jiki yayi mata nasiha ya lallasheta , saidai tayi murmushi mai tattare da ƙuna da baƙin ciki tabi Dikko da kallo mai ban tausayi , duk da yawan murmushi ba ɗabi’arshi bane idan tayi murmushi shima sai yayi mata dan ta samu natsuwa domin shi kanshi yasan murmushin shi wani sirrintaccen sirri ne da Allah yayi masa baiwa dashi badan halinshi ba , murmushi yana ma Dikko kyau sosai kuma murmushin shi yana da ɗaukar hankali da burge duk wanda ya gani , Saida Sadiya ta samu bacci Dikko yayi sallama da wanda zasu kwana da ita ya wuce gida , yana zuwa wanka yayi bayan ya fito ya saka riga da gajeran wando na jersey palo ya dawo ya zauna zuciyar shi na mishi babu daɗi , gaskiya tunda yake a shakarunshi bai taɓa cin karo da yarinya mai taurinka da rashin ji kanta cike da iskanci ba irin Sultana , a shekarunta har tasan taje ta ɗauko vidion tsiraicin uban wani ta tura ma ɗiyarshi , Shi kuma Babanta shima dai anyi tsohon banza ka rasa wacce zakayi lalata da ita sai ƙawar ɗiyar daka haifa , kai abu yayi muni gaskiya , jinjina kanshi yayi shi idan shine duk su Sultana ba mata bane a wurinshi , ko iskanci zakayi da sakarci ai ka samu macen da ta cika mace ta ansa sunanta takai mace ta ko ina da ko ina mai cikakkiyar zarra ba wannan jagwalgwalon yaran ba , Ya daɗe yana zaune palo yana tsaƙawa yana kuncewa wallahi zai tsaya saman ƙafafuwan shi ya cusa wa An mata soyayyarshi a zuciyarta idan ya riƙo ragamar rayuwata wato zuciya yasha da ita kuma ya gama da ita har abadan duniya , zata ga girmanshi tasan darajarshi saboda wannan kamun da yayiwa rayuwarta , Wayarta ya buɗe yayi binciken duk da zaiyi bayan ya gama ya rufe wayar gaba ɗaya tare da zamewa saman kujera yaci gaba da bacci ! A ɓangaren Babana kuma yana can gidan caca baisan wainar da ake toyawa ba a gidan , yana can ya shawu an zinatu kuma akaci gaba da caca , baya tunanin komai na ɓacin rai bare kuma halin da iyalinshi suke ciki , sabgar gabanshi ya saka a gaba kuma ita yakeyi baiji duk faɗin duniyar nan ba akwai mai iya dakatar dashi akan abinda ya saka kanshi ba…. Gajiya nayi da tsayuwa na tunkari ƙoƙofin biyu da na gani a jere , ƙofa ɗaya a rufe take ɗaya kuma a buɗe , turawa nayi na shiga da sallama a baki na , ɗan madaidaicin palo ne da kujeru masu kyan gaske na leda , sai labulaye masu kyau da tsada wanda suka dace da kujerun , a gefe kuma ga ƙatuwar talabijin girke a tebirin ajiyarta kamar zata ɓaro ƙasa saboda girman ta , abundai zabburgewa , ciki na shiga wato ɗakin bacci babu gado sai ƙatuwar katifa da “yar ƙaramar talabijin liƙe a bango , labulayen suma irin na palo ne , toilet na leƙa sannan na fito daga ɗakin duka nayo waje inga ko ni ɗaya ce a gidan ! Wasu irin murɗaɗin ƙattin mutane na gani marasa kyan gani yanayin duk ko wane ɗaya kamar ɗan rastilin amma su wanɗan nan baƙaƙe ne , suna gani suka yo kaina suna wata irin magana mai tada hankali wallahi saboda tsoro saida na saki fitsari a wurin , saboda wallahi siffar su bata da kyan gani abun tsoro ce abun firgici ce idan kuma sukayi magana sai kaji kamar ba duniya kake ba , tsaye nayi wurin saboda tsoro na kasa gaba na kasa baya , ruɗewa tasa na manta da ina da ƙafafuwa … Tunzura babbansu yayi yanayin shi ya nuna yana cikin ɓacin rai dan haka yayi wani irin kuka mai motsa tunani ya ƙara takowa dan ya samu damar matsowa kusa dani , nidai bansan ya akayi na ruga ba saidai kawai na ganni saman katifa har na lulluɓe da bargo ina kuka ! Bansan lokacin da bacci ya ɗaukeni ba , Da safe Dikko daga masallaci asibiti suka nufa daga shi sai Al ‘ Ameen , har yaje ya dawo Sadiya bacci takeyi , bayan ya dawo gida ne ya kira danjin ita kuma An mata ko ta kwana lafiya , lafiyanta qalau suka faɗa tare da bashi labarin abinda ya faru , mugu yaji mugunta , dariya Dikko yayi sosai tare da cewa zaizo anjima ai , Ba’a mugun sarki sai mugun bafade , Al ‘ Ameen bayan Dikko ya gama waya yace mai gida dan girman Allah ka kyale yarinyar nan tayi tafiyarta , sai kace dai itace kaɗai mace a duniya ? Yarinya mara kunya mara tarbiyya mara ɗa’a masu gajeren asali wallahi mutuncin gidanku da nasabarku da kai kanka taka mutuntakar ta wuce ace kana sauraren yarinyar nan wallahi , kana da zarrar da duk macen data ganka duniya sai tayi addu’a ta sameka a matsayin abokin rayuwarta. Kana babban asali ga cikar zati ga kyau ga kwarjini me zakayi da yarinya mara tarbiyar ? A hankali Dikko ya lumshe idanuwanshi dan duk duniya idan akwai kalma mafi muni da ɗaci a wurin shi bata wuce ace An mata bata da tarbiyya ba , Al ‘ Ameen yaci gaba da cewa uwa uba kuɗi kana da cikar arziƙin da zaka iya auro mace ko wace iri ce kai ko babu kuɗin sai ta so ka dan kyan ka , abin kunya daci baya ne ka auri ɗiyar ɗan caca mashayin giya manemin mat…. Hannu Dikko ya ɗaga alamar dakatar dashi , shiru yayi bayan yayi shiru yayi masa nuni da ya fita kawai , Allah ya baka haƙuri mai gida ya faɗa cikin girmamawa sannan yabar ɗakin , Fitar Al ‘ Ameen Dikko ya fara nazarin maganganun shi tabbas duk abinda ya faɗa ba ƙarya bane ba , ko wane mai asali yana so ya auro mai asali gidan tarbiyar da mutunci amma miye aibun An mata ? Duk dai haɗa jini da mutane banza bashi da wani amfani dan ba’a gane matsalar hakan sai zuri’a sunzo dan iskanci jini yake bi , tou amma mi yasa ita An mata batajin magana ne ? Wani sashe na zuciyarshi yace ba komai wata rana zata daina , idan har mace tana shakkun namiji idan dai ya shata mata doka tou fa tabbas ba zata karyata ba , wani sashe kuma cewa yayi matsalar ba’a nan take ba , tsoki Dikko yayi tare da cewa da Allah ku barni… A ɓangare na kuma , da asuba ina farkawa kayan jikina na cire na wanke su saboda na ɓatasu da fitsari na goge katifar dake da leda a jikinta kila ma sabuwa ce , labule ɗaya na ciro na ɗaura , bayan na gama wanke kayan a palo na shanya saman kujera na kunna fanka , ɗaki na koma na shiga nayi wanka tare da ɗauro alwalla , bayan na fito na sake ciro wani labilen na rufa dashi naci gaba da sallah…. 🤔 Bayan na gama na koma na kwanta , ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni , dan banda wata damuwa saidai kaiwai ina so in tafi gida , Ina bacci Dikko yazo kuma tun a palo na fara jin faɗashi wai waye yace kujera wurin shanya ne ? Da sauri na tashi na ɗauki bargo na ƙara lullube jikina a dai² lokacin da naji Dikko yace maza cire wannan tsumman kaje ka jefar dashi a waje , kutumelesi ? 😭 rigata mai tsada itace za,a yadar ? Amma dai wallahi Dikko ɗan iska ne , kuɗi fa masu yawan gaske Alajina ya siyamin ita shine zaisa a yado ta , Ina cikin kuka naji ƙarar takalminshi yana tahowa ɗakin da nake , ci gaba nayi da kuka ko zai tausayamin yasa a dawo min da rigata , kwance nake cikin bargo fuskata kaɗaice a waje ina kuka , ƙamshin turarenshi ya ƙara matsowa kusa dani haka ya tabbatarmin yana gab dani dan haka na buɗe idona ina kallonshi , Murmushi yayi cikin natsuwa sannan ya fara magana cikin kamun kai da aji , gaba ɗaya jiya da daddare tunaninki nai tayi , da sauri nace me ? Murmushi ya sakeyi sannan yaci gaba da cewa tunanin da nayi tayi cikin dare shine nayi kuskure , sam bai kamata ace na ɗaga hannu na mari mace ba , kiyi haƙuri don Allah idan ma baki gamsu ba zaki iya rama marikin kamar yadda na mareki , ƙoƙarin tashi na farayi dan rama marina , cikin magana mai kama da raɗa yaɗan fiddo kyawawan idanuwanshi yace a haba keko ba’a nan ba kinsan babu kaya a jikinki koma kawai ki kwanta , Babu gardama na haƙura na koma na kwanta , fita yayi bai daɗe ba ya shigo da wani haɗaɗɗen kwando ya ajiye a can gefe cikin magana mai laushi da kalamai masu burgewa yace kiyi kalaci ya faɗi maganar tare da nunamin inda kwandon yake , zai fita nace am da Allah idan babu damuwa rigar nan kada a yadar da ita anjima idan zan tafi ita zan saka , Ba tare daya kalleni ba yace bama buƙatar ita rigar kayanki yanzu zansa a shigo miki dasu palo , wai ance jibi hutun ku zai ƙare idan zan wuce zan ajiyeki makaranta , kallo ni yayi tare daci gaba da cewa kyakkyawar fuska da kyawawan idanuwa irin naki gararin gari ba nasu bane da ilimi suka dace bada taron murnar zagayowar shekarar aihuwarki ba , yana faɗin haka yayi gaba abinshi , ni kuma nace wallahi aiko babu sakaran da ya isa yakaini makaranta tunda ba cewa nayi ina so ba , dawowa yayi tare da cewa kina magana ne ? Banza nayi dashi naci gaba da hararar ƙasa , Murmushi yayi da gefen bakinshi ya fita , yana fita na ƙara cewa kuma ko ka kaini saina dawo dan kaga na kwana nan gidan nan ko an faɗa maka ni ina tsoron waɗanda ka ajiye ne ? Sake dawowa yayi yace kina so ki madani kamar wani sa’ar wasanki ko ? Tou idan kinje makarantar ki gudo mu gani , Dikko ya kaiki saboda haka Dikko zaici gaba da ɗauko ki , ke ɗaya na bayar kuma ke ɗaya za’a bani a ko wane hutu , kuma ko hutu akayi idan ba nine naje ba ko waye wallahi yarinya bazaki dawo gida ba gara ma ki fara kamun ƙafa tun yanzu ko zan riƙa ziyartarki lokaci ² idan kuma kika nunamin yarinta sai ina barki kisha baƙar wahala babu abinci babu kuɗin kashewa , yana faɗin haka ya fice abunshi ,Ni kuma ƙasa² nace sai inyi ta iskanci da malam su sa fiddoni , in dawo gida , kuɗinkan banza kuɗinkan wofi ko an faɗa maka ni matsiyaciya ce ? Hahaha niko nace da kanki ma zaki riƙa cewa ya baki bari dai kisha azaba yarinya …. A palon ɗaki na Dikko yasa aka ajiyemin kayana saman kujera , shi kuma yayi tafiyarshi , saida naji fitar motarshi na tashi naje na ɗauko kayan na saka ina sakawa ina mita ni za’a bawa kwance kila ma kayan matarshi ne ya ɗibomin , kona ƙannenshi , niko nace kedai kika sani… Ɗaki na dawo ina cewa shikenan an yado rigar Alajina daya ji kuɗin rigar shi kanshi nasan sai gabanshi ya faɗi , Allah yasa ya dawo yanzu yace in rama marina saina ci abinci na ƙoshi zan zabgaga mishi mari sai yayi fitsari saboda azaba , Gaban kwandon na durƙusa ina ci gaba da surutu babu kai babu misali , kwalin makilin da burosh a gefe da sauri na fara buɗewa dan inga abinda aka kawomin inyi kalacin safe dashi ….. 21/09/2019 *JAMILA MUSA…*💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 37 Gayu mutanen Allah shine abinda na furta a lokacin da naga shagalin dake cikin food flarks , murmushin jin daɗi nayi wai duk ni ɗaya zanji daɗi na , miƙewa nayi tare da komawa da baya cikin farin ciki na faɗa saman katifa zanci daɗi yau zanyi kalaci da farfesu , ga doya ga farfesun “yan ciki , wannan daɗi da hawa tsaunin rayuwa har haka ? Ɗaga ƙafafuwana nayi sama ina musu shangululu tare da rumgume duka hannaye na a ƙirjina cikin farin ciki nace wallahi madarar ma duka zan juyeta… Wani irin ihun farin ciki na kurma wanda har na waje saida sukaji ni , da sauri na sauko daga saman katifata naci gaba da aiki dan gani nake idan na tsaya wanke baki a iya shigowa aga kamar na gama a fita dasu , ina ci ina kaɗai kai tare da addu’ar rayuwa ta ɗauremin da irin wannan daddaɗan kalaci , naci komai kuma komai nasha nayi hamdala ga ubangiji da ya bani aron lumfashi ya bani baki da ciki da lafiya kuma ya ruboto min wannan babban rabo da alƙamin kudarar shi… Ina gamawa na tattara komai na fitar palo , labulayen dana ciro na ɗaura na mayar dasu mazauninsu na gyara , saman katifa na dawo tunda dama nayi wanka cike da farin ciki na lumshe idona na tafi duniyar bacci………! Tashin hankali a gidan su Sultana , cike da farin ciki Baba ya shigo gida ya dawo da kuɗin shi cike da aljihu domin a daren jiya shi ya lashe maƙudan kukaɗaɗen da aka zuwa a wasan caca , ƙofar ɗakin Sultana ya nufa kai tsaye yana cewa Mamana kin ganni sai yanzu ? Kowa yayi cirko² domin “yan gidansu Sultana tun jiya suka dawo da labarin ɓatanta , kowa dai yana cikin jimami da tashin hankali , Baba kuwa bayan ya shiga ɗaki shiru² bai fito ba dan a tunaninshi Uwar masu gida tana bayi ne… Zama yayi har ya gode Allah , komi Uwar masu gida takeyi ai ta isa ta gama ta fito gajiya yayi da zama ya fito tsakar gida yana cewa ina Mamana taje ne ? Shiru kowa yayi ya kasa magana , bin kowa yayi da kallo yanayin fuskar su ta nuna akwai wani abu daya faru , bayan ya gama kallon kowa yayi magana cikin karyewar zuciya cewa ina Mamana…… Take ? Ya ƙarasa maganar yana mai bin bango ya sulale ya zauna ƙasa a hankali , Maman Fa’iza ce tace mu saka Sultana a addu’a domin yanzu ba abinda take buƙata sai addu’armu mu dage da roƙon Allah har ubangiji ya bayyana mana ita domin Sultana dai ta ɓata , lokaci guda zufa ta ɓarkewa Baba ya tsurama wuri guda ido kamar mage ta ɗana tarko , bayan wani lokaci kuma yace haka zakimin Mamana ? Haka mukayi dake ? Wannan shine sakamakon alƙawarin ? Ina kika tafi ne ? Inajin babu jimawa mukayi magana dake baza ki taɓa tafiya ki barni ba , shine kika tafi kika barni….. ? 😭 hawaye ya gangaro mishi daga cikin idonshi , daga nan yayi na wani mawaƙi da yace ayye mata a ƙame ƙam , tou Baba shima ya ƙame kamar wayar da tayi hucking….Tunda na kwanta bacci babu abinda ya dameni kuma bana wani tunanin komai haka kuma banga komai ba a cikin mafarki na , bacci na nakeyi cikin natsuwa da kwanciyar hankali , sai da aka kira azahar na farka nayi sallah bayan na gama na watsa ruwa na koma nayi kwanciyata amma ba bacci nake ba ! Gidan shiru kamar babu kowa ciki sai ƙarar iska irin mai tahowa da ƙasa , a hankali sanyi ya fara saukowa irin mai shiga ƙashin nan , zuwa bayan la’asar sanyi ya sauko sosai wanda yasa mutane suka fara saka rigunan sanyi, Ni kuma da banda rigar sanyi ina cikin bargo na duƙunƙune , ga azabar yunwa da nakeji na rasa inda zan saka rayuwata , har akayi magrif babu wani labarin abincin rana bare in saka ran na dare zaizo , nasha ruwa har nayi fitsari bansan adadi ba , tun ina daurewa har na fara Allah ya isa a zuciyata… Tunda nayi magrif ban tashi daga inda nayi sallah ba ina zaune na zabga tagumi kuma ni ba addu’a nakeyi ba , ina cikin wannan tunani naji ƙarar buɗe get murmushin jin daɗi nayi nasan Dikko ne kuma yazo da abinci , tabbas abinci yazo ya kawomin , cike da murna na leƙa ta window kuma wallahi shiɗin ne , sanye da tsadajjiyar baƙar rigar sanyi mai kyan gaske da burgewa tana da farin zif daga gaba , an zageye wuyan rigar da farin ado amma ba irin na mata ba ina ganin dibara ce dan kar rigar ta lalace daga saman wuya , sanye da shuɗin wando da takalmi baƙi amma ba rufaffu bane maɗauri gare su kamar sandals , hannun rigar ya ɗan naɗeshi zuwa guiwar hannu , kanshi babu hula kuma fa gaskiya yayi kyau dake baida ƙiba ko kaɗan amma yana da tsayi daidai burgewa bana zarce misali ba… Al ‘ Ameen ke ɗauke da kulolin abinci shi kuma waya yakeyi , ina ganin sun tun karo ƙofar shigowa palon nayi sauri na kowa saman abin sallah na kalli gabas , Suna shigowa shi Al ‘ Ameen ya kunna musu kallo , maimakon ya kawomin abinci sai kawai suka zauna sukaci gaba da kallon kwallo , har akayi isha’e suna zaune kamar asara suna kallon kwallo , inajin maganar Dikko lokacin daya shiga ɗaki mai kallon wanda nake ciki yana cewa bari inyi sallah dai , tsoki nayi tare da cewa andai ji kunya sallah a gida , nima tashi nayi nai sallah dan ina da alwallah … Har na gama sallah banji Dikko ya fito ba , kuma naji palon ya fara cika da maza ga dukkan alamu kila gidan dai matattara ce ta maza , tunani na farayi karfa su cinye abinci ban samu ba , tashi nayi na fita ɗan madaidaicin palon na zauna ina jiran fitowar Dikko idan ya manta da ina nan tou ya ganni ya gane ina nan , Tunda na zauna ƙarar motoci ke shigowa , hayaniyar sai ƙara sama takeyi maza surutu ga magana babu natsuwa , nafa daɗe ina zaman jiran Dikko bai fito ba , kuma bana so na leƙa babban palon bansan ko su waye a wurin ba , na haƙura da niyar komawa ɗakin da aka ajiyeni naji dai bazan iya kwana banci komai ba yunwa nakeji kamar zan mutu wallahi , dawowa nayi kai tsaye na shiga ɗakin , Da sauri ya kallo ƙofar dan yaga waye yake shigowa yana zaune saman abin sallah , murmushi yayi ganina tare da cewa An mata miye ? Ɗan suɓaro baki nayi ina wasa da yatsun hannuna nace dama , sai kuma nayi shiru , ɗauke kallonshi yayi daga gareni yace dama me ? Shiru nayi na kasa magana , shima bai sake magana ba yaci gaba da latsa counter , naci uwar mintuna sha biyar Dikko bai sake kallona ba kuma bai sake magana ba , Saida ya gama abinda yake ya ɗauke abin sallar daga inda yayi sallah ya ɗora gefen gado , zuwa yayi zai wuce ya fita dan yayi kamar ma babu ni a wurin , Ya kusa fita nace yunwa nakeji , yi yayi kamar baiji abinda nace ba ya fice abunshi , biyoshi nayi a lokacin har ya kusa fita daga palon ya shiga babban palon , nace da Allah nace maka yunwa nakeji nayi maganar a tsiwace , naji ya faɗa tare dayin gaba abunshi , Tsoki nayi cikin ɓacin rai na koma ɗaki ina gunguni , shi kuma daya koma kallonshi yaci gaba dayi , sai ihu sukeyi “yan iska kamar mahaukata , amma bana tunanin Dikko yana wurin dan har yanzu ban jiyo maganarshi ba , duk wanda aka ci su sai kuji hayani ta ƙara sama , sai gaddama da magana cikin faɗa² , Sai yanzu naji dariyar Dikko yana shigowa cewa ko gobe da fansar kura saidai garin da babu awaki , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya nace ashe kaima ka iya karin magana ? A dai² lokacin daya shigo yana dariya , Ɗaure fuska nayi kamar ina cikin yanayi damuwa , ko kallonshi banyi ba ya ɓatamin rai ni zai zubowa abinci a gaban bainannasi hmm , ga abinci ya faɗi maganar a daidai lokacin da yake ajiyewa a gabana , kauda kaina nayi na tura abincin na ƙoshi … Murmushi yayi tare da ɗaukar abinci zai fita , nace kai nifa wasa nakeyi bani nan nayi maganar tare da nuna mishi ya maidoshi gabana , banza yayi ya fice daga ɗakin da sauri na tashi nabi bayanshi amma kafin in fito harya fice ya koma cikin abokanshi yana dariyar mugunta , a ranshi yace daga yau sai kiyi hankali ni ban iya wasa ba kuma ba’amin wasa ,Wannan rana saidai na kwana da yunwa nasha kukana har bacci ya ɗaukeni bansan lokacin da suka tafi ba , Koda safe dakel nayi sallah saboda yunwa duk jikina ciwo yakeyi kamar nayi aikin ƙarfi , bayan na gama sallah na daddafa nayi wanka , na canja kaya sannan na koma bacci , Yauma da asibiti ya fara , ya lallashi matarshi kamar yanda ya saba , yau ya samu ya lallaɓata tasha ruwan tea , ya kuma sake tambayarta damuwarta dai tayi masa zurfin ciki har yanzu , dan haka bai wani damu ba ya wuto wurina , Yau shi ɗaya yazo babu Al ‘ Ameen kuma kai tsaye ya shigo ɗakin , bayan ya ajiye kayan da yazo dasu ya kunna fitila yana cewa anya ma kinyi sallah ? Tashi ya faɗi maganar tare da yaye bargon dana lulluɓe , juyawa nayi na kifa kaina saman katifa saboda haushi ya bani jiya sosai , Yauma bakijin yunwa bara in tafi , ya faɗi maganar tare da ɗaukar kwandon , cikin fushi nace abinci banza gare ka , ko an faɗa maka yunwarshi nakeyi muma gidanmu sau 3 a rana akeci ka tafi na ƙoshi nasan yunwa baza ta kasheni ba an girma ba’asan an girma ba , Dariya yayi tare da zama gefen katifa yace wai nima irin wasan jiya nake miki amma ke naji kalaman naki zafi garesu ai kema da sai kiyi shiru kamar yanda nayi shiru jiya , sai kace dai kina jirana ? Cike da jin haushi na tashi zaune ina cewa jiranka nakeyi kamar yadda ka zanemin rayuwata haka zan zane taka rayuwar babu gudu babu ja da baya ba abinda ke cikin zuciyata face ɗaukar fansa akan ka , Murmushi yayi tare da gyara zamanshi sannan ya ɗaure fuskarshi babu wasa a tare da ita ya fiddo siffofinshi masu tayar da tsikar jiki da saka fargaba yace ke har gobe yarinya ce , amma ki sani ya nuna ni tare da ci gaba da cewa wannan tsarin tamkar sautin radio na ne , na ƙarashi na rageshi yadda nake so , kiyi haƙuri burina kaɗan ne amma sanin ya kamata na yana da ƙarfi , ban iya ba kece kika koyamin kinsa na zama kamar wani sakarai sai biye miki nake ina ƙananan maganganu kamar mace , dakamin tsawa yayi tare da zaro idanuwa sannan ya sassauta maganar shi zuwa sauti mai kama da raɗa yace ki kiyayeni kafin na baki hukunci a karo na biyu , azabar yau sai tafi ta jiya zafi , ina nan kuma namijin ne …. 🤫 ya ƙarasa maganar tare da ɗora ɗan yatsanshi a saman bakinshi yace shitt ya rufe maganar da fiddo idanuwanshi da suka ɗanyi ja… Jiki a sanyaye na koma na kwanta , ba tare daya kalleni ba yace tashi muyi break , da sauri na tashi naje na wanko bakina da fuskata nazo na zauna kusa dashi cikin ladabi , shine da kanshi ya zuba komai amma tea ɗin a kofi ɗaya ya haɗa kuma da kofi ɗayan mukayi amfani yana sha ya bani insha in miƙa mishi , cokali ma ɗaya mukayi amfani dashi , Ba wani damuwa a tare dashi ko kunya ko irin yaji babu daɗi haka dai , tsakaninshi da Allah hankalinshi a natse yake , har muka gama da kanshi ya tattara komai ya mayar a kwandon ya ɗauka kwandon ya fita , ya daɗe sannan ya dawo ya kwanta a gefen katifa , Wayarshi ya ciro yace zo kiga in nuna miki “yan uwana , matsawa nayi kusa dashi amma ni ba kwanciya nayi ba zama nayi , ɗago kanshi yayi tare da bani wayar na riƙe a hannuna yana wuce hotuna , wannan itace wance wannan kaza ce dad ina ne kinga momy kinga wannan itace nake bi mawa , tana aure a gari kaza , haka dai yayi ta wucewa har yazo kan Sadiya yace wannan kuma matata ce…. Kai kalmar namiji yace matata kalmar tana da girma da matsayi , matata saida na maimaita a zuciyata sannan nace ban ƙaunarta har abadan duniya na faɗa a zuciyata , kallona Dikko yayi tare da cewa tayi kyau ko ? Ban sani ba nace masa , baiyi murmushi ba kuma baiyi dariya ba yace kada Allah yasa ki sani “yar rainin hankali , Cike da ɓacin rai nace dakai da matarka duk kune “yan rainin hankali munafikai dukanku , tsareni yayi da ido tare da cewa kishi ko ? Ya ƙarasa maganar yana nunani da san yayi murmushi amma ya haɗeshi , tsoki nayi tare da cewa hmmm Allah ya sawaƙe min niko waye zanji kishin a cikinku kai ne ko ita ? Miƙewa yayi tare da cewa tunda baki son na tayaki fira zan tafi , bazan dawo anjima ba Al ‘ Ameen zai kawo miki abinci , idan Allah ya kaimu gobe lafiya ki shirya da wuri dan bana san tafiyar rana , yana faɗin haka yayi gaba abunshi…. Abinci rana da dare duk Al ‘ Ameen ya kawo min , yau babu wanda yazo kallon kwallo ni ɗaya a gida bayan naci nasha na koma na kwanta tare da addu’ar Allah ya kaimu gobe lafiya ! Da safe tun kafin in tashi bacci Dikko yazo , shi ya tasheni tare da ajiye uniform a gefen kati yace maza jiranki nakeyi , kallon kayan nayi sannan na kalli Dikko da yasha manyan kaya hada babbar riga hular kanshi kuwa sai sheƙi takeyi saboda sabinta ko wanki ne ? Koma dai miye sai ka kalli kanka a ciki kayi sakace , kallon ƙafarshi nayi nan ma komai yaji gemu ma dai yasha gyara yana nan dai da jan hankali da yakeyi , gaskiya Dikko haɗaɗɗen namiji ne mai tafiya daidai da zamani , ga kyau ya gayu uwa uba iya saka sutura , Dikko nada burgewa … Katse min tunani yayi da cewa kin tsaya kina kallona ! Kiyi maza jiranki nakeyi , yana faɗi maganar yabar ɗakin , cikin kuka na nufi toilet nayo wanka sannan nayo alwalla nazo na fara gafatar da sallah asuba da banyi ba akan lokaci , bayan na gama na shirya cikin kayan makaranta ina kallon kaina a madubi na fashe da wani irin kuka wanda har sai da gaban Dikko ya faɗi… Da sauri ya shigo ɗakin fuskarshi ɗauke da damuwa yace a mota zakiyi kalaci , shi a tunaninshi yunwa nakeji , cikin kuka nace ni wallahi bana san makaranta haba Yaya Dikko me yasa zakamin haka abin kunya a ganin a makatanta yanzu , Wani irin kallon rainin hankali yayi min daga sama zuwa tsakiya ta yace lallai yarinyar nan kin rainani nine Yayan naki…. ? Baki da hankali ma da Allah ni wuce mu tafi munatane na jirana , hannu na ɗora saman kai ina cewa dan girman Allah ka kyaleni wallahi bazan sake ba , cikin kwantar da murya yace muje tun kafin kiji babu daɗi , 😭 hijabi na saka nabar kallabin a katifa nayi waje , abun kunya shi ya ɗaukomin kallabin wai hada jakkar makaranta saboda ci baya , waini zan koma makaranta , ina gaba yana bayana har cikin mota , ni kaɗai na shiga baya ya wurgomin jakar da kallabina ya rufe ƙofar ya shiga gaba , Al ‘ Ameen yaja muka fita daga gidan , kuka naci gaba dayi ina ma katsina kallon ƙauna , tafiya akeyi sosai dan Al ‘ Ameen yakai mota maleji wurin gudu , kuka na ya ƙaru lokacin da naga an ibi hanya tafiya da gaske babu fashi……. ! 22/09/2019 *JAMILA MUSA CE…* 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 38 Ƙuramin idanuwa yayi yana kallona ta cikin madubin gaban mota , sai kuka nake ina fyace majina da gefen hijabina , tissue ya wurgomin bai juyo ba kuma bai kalleni ba yace zaki ma mutane shiru haka nan ko kuma dai…. ? Harararshi nayi cikin muryar kuka nace mara zuciya ko mutum baya harkar ka sai ka shiga nashi mutum ba dangin uwa ba na uba kawai ka shigomin rayuwa , kyakyawan murmushi yayi da gefen bakinshi amma baiyi magana ba , kallonshi Al ‘ Ameen yayi bakinshi ɗauke da magana , murmushi Dikko yayi tare da cewa manta da labarinta ka ƙaddara ma bama nan bare kayi tunanin munji abinda tace , makaranta dai zuwa babu fashi ! Shiru sukayi su dukansu babu wanda ya sake magana , saidai shi Dikko yana kallona ta cikin madubi idan akayi sa’a muka haɗa ido sai yayi murmushi mai tattare da mugunta , matsawa nayi daga saitinshi dan ya daina kallona , ƙara gyara saitin madubin yayi yaci gaba da kallona , kwanciya nayi na lulluɓe da hijabi naci gaba da baccin dole… Har nayi bacci na farka bamu isa ba , kuma tafiya Al ‘ Ameen yake bata wasa ba dan shima kusan irin tuƙin Dikko yakeyi kamar basa san rayuwarsu , ganin har yanzu a hanya muke yasa na sake komawa na kwanta ina mai ci gaba da kuka , jin kukana yasa Dikko juyowa tare da cewa ke miƙomin kunun nan tunda baza kisha ba , Cikin kuka nace ina sha , Al ‘ Ameen yasa ya faka a gefen titi da kanshi ya fita ya ɗauko ruwa a but sannan yazo ya buɗe inda nake ya bani ruwan , yana nufi in kuskure baki na , fita nayi na kuskure bakina na wanke fuskata na koma mota na zauna ,Ɗan ƙaramin flaks ne na sulba mai kyau cike da kunun gyaɗa tun kafin in fara sha Al ‘ Ameen ya tada mota ya hau titi yadda ta kamata yaci gaba da gudu , cike da baƙin ciki nake shan kunun , yayi min daɗi sosai ɗan kaɗan na rage na miƙawa Dikko flarks in dan ya ajiye , ansa yayi ya shanye sauran dana rage, a raina kuma tunani nake Dikko ko ƙyamata bayayi yanda yake ɗan gayu mai aji har zansha abu in rage yasha saura na , Har muka isa bakin get in makaranta babu wanda ya sake magana , a bakin get Al ‘ Ameen yayi parking , muna zaune a mota ga dukkan alamu akwai wanda ake jira , bamu wane daɗe ba , wata irin shareriyar mota tayi parking kusa da tamu , wani matashi ne ya fito daga motar yayo wurin motarmu , Al ‘ Ameen ya sauke gilashin kusa da Dikko , yana isowa Dikko ya miƙa mishi hannu suka kashe , Sai kuma aka shiga gaisawa bayan sun gaisa yace ina An matan take ne ? Murmushi Dikko yayi yace gata can baya kuka takeyi , dariya matashin yayi tare da cewa tun daga katsina har bakori tana kuka ? Dikko yace ai bata da aikin yi , dariya matashin ya sakeyi tare da cewa sannu dai za’ayi mata , Ba tare da Dikko ya juyo ba yace An mata dani dake waye ya kamata ayi ma sannu ? Banza nayi dashi ban bashi amsa ba , dariya yayi tare da cewa muje sauri nakeyi yayi maganar yana kallon agogon hannunshi , komawa matashin yayi cikin motarshi ya tada , mu mukayi gaba shi kuma yana bayanmu har muka isa bakin ofishin principal , a bakin ofishin mukayi fakin sannan muka fita gaba ɗayanmu muka nufi cikin office in… Bayan gaisuwa akaci gaba da abinda za,ayi duk wani abinda ya kamata ayi anyi , kuma Dikko yace wa principal ko hutu akayi idan bashi yazo ba kar wani ya ɗaukeni , ya ƙara da cewa ko wannan ya nuna Al ‘ Ameen yace koshi yazo a , a, niɗin dai , tace insha Allah , saboda Dikko ya ɗaukeni ƙarshen kidahuma JS 1 yasa aka ajiyeni , inajin aji ɗaya na ƙara fashe wa da kuka duk da dama kukan nakeyi tun safe har yanzu , Bayan an gama aka ciro kayana daga bayan motar Dikko , a bayan motar abokinshi aka fiddomin katifa , bayan an gama sauke kaya Dikko ya bulale Prcp da kuɗi wanda Al ‘ Ameen ya miƙa mata su , tayi ta zabga godiya Dikko yace tasa min ido sosai a riƙa zaneni idan nayi abinda bai kamata ba , tace insha Allah ! Ina tsugunne a gefe sai kuka nakeyi , bayan sun gama abinda suke Dikko ya kallo inda nake yace taso ki biyoni , jiki a lalace nabi bayan shi har cikin mota , dukanmu a baya muka zauna , da yanayin tausayi a fuskarshi yace idan kina san wani abu ki faɗawa principal zatamin waya kinji ko ? Nace to , karkiyi rashin ji kiyi karatu kuma ki zama mai haƙuri karki sake ki biyewa abokan banza kinji ko ? Saida na goge hawaye sannan nace tou , Shiru yayi zuwa wani lokaci yace tou kalloni kiga , ba musu na ɗaga idona na kalleshi , murmushin shi mai burgewa yayi tare da cewa idan kuma kikayi , uhum ? Ya nuna idanuwanshi da hannunshi , bansan abinda hakan da yayi yake nufi ba , banyi magana ba ina kallonshi dai , yace to nan ? Ya nuna , girgiza kaina nayi alamar a , a tou zakiyi tunani na ko ? Da kai na bashi ansa Eh , tou idan dai kin tunoni kar kiyi kuka kinji An mata zan riƙa zuwa da wuri ina ganinki ai zaki ji daɗi idan kika ganni ko ? Nace Eh , Bandir in “yan 1k ya bani guda biyu yana cewa karki yi damuwa sosai kiyi farin ciki kullum don Allah kar kiyi kuka da yawa inaji a jikina idan kina cikin damuwa kinji ko ? Jinjina kaina nayi alamar gamsuwa , godiya yayi tare da cewa tou kya iya tafiya , godiya nayi sannan na fita daga motar , ina fita Al ‘ Ameen ya shiga yaja suka tafi abokinshi yabi bayan su shima cikin motarshi… Aji Principal tasa aka rakani tare da cemin idan an tashi makaranta inzo da “yan ajinmu su tayani ɗaukar kayana , nace tou , kamar wata geliya haka nake ji na , na koma kamar wata sakara , haka na zauna ina bin “yan ajin da kallo , kowa sabgar gabanshi yakeyi babu wani da ya damu da wani , Koda aka tashi ban nemi kowa ya tayani ɗaukar kaya ba na koma ofishin principal , tou Dikko dai ya nemomin mutunci na tunda yayi mata wanka da kuɗi mutane basa abu dan Allah sai dan hatimin nasara , da kanta ta samu yara suka tayani ɗaukar kayana har zuwa ɗakinmu… Bayan munje mun ajiye kayan na samu wuri na zauna ina kallon yanda kowa yake rayuwarshi domin ina so na fahimci yanda rayuwar makarantar take tafiya ! Tunda Baba ya sulale ƙasa ya tsaya cak ya daina aiki , yana da rai amma dashi da matacce basu da banbanci ɗagowar da cikin shi keyi kawai zaka gani ka tabbatar da ranshi , wannnan abu yayi ƙololuwar ɗagawa kowa hankali dan haka aka kwashe shi akayi asibiti dashi… A ɓangaren Sadiyya kuma tanajin jiki sosai dan haka iyayenta suka buƙaci ta koma gida suyi jinyarta , amma daga inda Dikko yake ya murje idonshi tas yace idan dai shine yake aurenta a barta kar wanda ya tafar mishi da mata ko yace ya kasa kula da itane ? Dole suka haƙura suka barta , Amisty kuwa da Hafsa lingu da saƙo sun nemi Sultana basu samu ba , kuma wayarta ma idan sun kira a kashe take dan tuni Dikko ya ƙarya layin , kuma sunje wurin Alaji sun tambayeshi ko yana da labarin Sultana yace shima kanshi nemanta yakeyi , yaje gidansu ance an saceta wurin partyn birthday inta Babanta ma yana asibiti baida lafiya , bawan Allah Alaji shine ke kula da Baba duk wani aune ² da magunguna shine yake biya… Sati na ɗaya a makaranta banda damuwar komai kuma banda wani tunani daya dameni sai Babana da nakejin kewarshi kullum rana , bana tunanin Inna kwata² dan na tabbata itama duk inda take bana rayuwarta kuma bata tunani na amma nasan duk inda Babana yake yana can yanajin damuwa na rashina a kusa dashi ! Har yanzu banyi abokiya ko ɗaya ba kuma bana shiga sabgar kowa tunda babu abinda na nema na rasa , ni ɗaya nake rayuwata idan kuma naje aji idan malami ya shigo zan samu natsuwa na tattara hankali na , rubutu ma ni nakeyin abuna da ɗaiɗaya nake ɗauko ko wane harafi , bana surutu a aji dan ba’a magana da hausa idan kuma mutum yayi za,aci shi tara ne , Tun ranar da nazo ban sake zuwa wurin principal ba , kuma ta aiko a kirani banje ba , harkar gabana kawai nakeyi dan gaskiya naji ciwo da Dikko yasa aka ajiyeni JS 1 kuma naci ɗamara saina nuna mishi ni ba jahila ba ce ba , Dikko kuwa tunda ya ajiye Sultana a makaranta yaci gaba huɗɗoɗin gabanshi , baiyi waya yaji ya Sultana ba kuma baizo makaranta ba da sunan ziyara , duk juma’a yana katsina yana komawa monday tunda safe yana ta zirga² a hanya saboda rashin lafiyar matarshi amma ko so ɗaya bai biyo wurin Sultana ba , Haka dai rayuwa ta taci gaba da tafiya a makaranta , mutane suna ta shigowa rayuwata amma banda lokacin kowa ina so in tsula iskancina amma ba yanzu ba saina san abinda nakeyi , saboda ko magana nayi ma mutum sai kawai inji suna wani min turanci banza shi yasa na fita sabgar kowa nake tawa sabgar.. Wallahi kwata² banajin daɗin zaman makarantar nan a daddafe dai muka fara jarabawa dan hutu za’ayi mana kuma har yanzu Dikko bai zo ba bai aiko ba , kuma kuɗin daya bani har yanzu akwai su kayan provision ina ma akwai sosai dan gaskiya ba ƙananan kuɗaɗe ya kashe ba dan dai kawai inyi farin ciki ! Tunda naga hutu ya fara gabatowa nake neman “yan katsina dan in turasu gidanmu su faɗawa Babana ina FGC nasan zaizo idan muka dawo hutu , na samu “yan katsina amma duk wanda na faɗa masa anguwarmu sai yace bai sani ba dan abinda na lura duk “ya “yan masu kuɗi ne irin wanda basa zuwa yawo kamar yanda mu “ya “yan talakawa keyi… Dole na haƙura gashi ban riƙe number kowa ba dana riƙe tabbas dana samu aron waya na kira nace a faɗawa Babana yazo ya tafi dani , tou ban riƙe ba banda yanda zanyi inba haƙuri ba dan ban samu yanda nake so ba , duk ɗalibai suna farin cikin hutu kowa yana cike dajin daɗi zaije yaga iyayenshi saɓanin ni da bazan samu ganin Babana ba , Anyi jarabawa an gama kuma an bada report ga ko wane ɗalibi nima an bani na saka a jakata na adana abuna , Ranar hutu kowa yana cikin farin ciki ko wane ɗalibi ya samu “yanci kamar sakakken tsuntsu kowa na wali sakamakon ni da principal ta tsare a ofishinta , motoci kuwa sai ɗaukar dalibai sukeyi suna tafiya abin dai gwanin burgewa ina ta kallon ikon Allah har ɗalibai suka ƙare kaf dan principal tacemin tun satin hutu ta faɗawa Yayana za’ayi hutu , kuma jiya ta kirashi tace mishi yau ake hutu yace zaizo insha Allah ! Saida kowa ya watse babu sauran ɓishi²n ɗaliba ko ɗaya saini ina jiran zuwan shi , Dikko baizo ɗaukata ba sai bayan azahar bayan ya iso ya kira principal ya sanar da ita zuwanshi , dan dama lokaci ² tana kiranshi ya kawo ina tana mishi sannu da hanya , tare muka fito da ita har wurin mota muna tare da ita , bayan mun isa suka shiga gaisawa da Dikko tare dajanshi da fira dan kilbibi an fara magana da hausa sai a wani jefo turanci dan munafirci , gajiya nayi da tsayuwa na buɗe mota na shiga na zauna , Yauma ya tunbiza mata kuɗi masu yawa , gaskiya Dikko yana da kyauta sosai zaiyi wuya ka ganshi bai baka ba , ya ganka yanzu ya baka anjima ma idan kuka sake haɗuwa saiya ƙara maka , godiya tayi sosai tare da mana addu’ar sauka lafiya ta wuce…, Saida Al ‘ Ameen ya fara tafiya Dikko ya juyo dukanshi yana kallona , bayan wani lokaci yace An mata kin rame me ya sameki ne ? Gyara baki na nayi tare da cewa ina yini , na gaishe shi dan kauda waccan maganar , murmushi yayi tare da cewa lafiya qalau , gaishe da Al ‘ Ameen nayi shima ya ansa , Cike da tausayi Dikko yace kodai baki san wannan makarantar ne ? Dama saida nace bazan kawoki boarding ba kowa yace min wai in kaiki makarantar kwana , a raina nace wato saida kayi shawara kenan , kallon Al ‘ Ameen yayi tare da cewa ji yarinyar nan ta rame ni gaskiya banji daɗin haka ba wallahi ya ƙarasa maganar yana mai dawo da kallonshi wurina yace An mata ko bakicin abinci ? Murmushi nayi nace ina ci , to baki da kuɗi ? Nace ina da , to meke damunki ? Ko baki lafiya ne ? Yayi maganar tare da nunamin in matso kusa dashi , Matsawa nayi kamar yanda yake so , ƙasa² yayi da murya yace meke damunki ne ? Ba komai nace , tsoki yayi tare cema Al ‘ Ameen ya tsaya zai dawo kusa dani , parking Al ‘ Ameen in yayi Dikko ya fito ya dawo baya kusa dani , ansar jakata yayi bayan ya rufe ƙofa yana cewa matso kusa dani , juyar da kaina nayi ina cewa nidai ka gyaleni a dai² lokacin da motar taci gaba da tafiya ,Buɗe jakar yayi yana cewa ni wallahi naga duk kin koma “yar ƙarama Allah dai yasa ba masonyo min ke akayi ba , shiru nayi kamar banji ba , kalloni yayi da kallo maisa natsuwa , magana yayi cikin riƙe haruffa yace umm ya nunamin nayi shiru da kanshi , murmushi nayi shima murmushin yayi yace tou kice wani abu mana , Sake maimaita maganar yayi , girgiza kai nayi cewa nice , yace ai banji kin fara kuka ba yau naji kinyi shiru , a daidai lokacin daya fara duba littafai na , haka yayi ta cirosu ɗaya baya ɗaya yana dubawa har yazo kan report ina , warwareshi yayi ya duba , gaba ɗaya annurin fuskarshi ya ɗauke ya ƙurawa report in ido , cikin muryar ɓacin rai yace tsaya , tsayawa Al ‘ Ameen yayi Dikko yace fita ki koma gaba ki zauna , da sauri na fita na koma gaba na zauna , ina ta mazurai kamar nayi wa sarki ƙarya duk yanda akayi a cikin waccan takarda yaga ɓacin rai… Shiru yayi tun daga nan ba saike magana ba har muka iso katsina , ko waya aka kirashi baya ɗauka , lokacin da muka iso har an fara sallah magrib , Al ‘ Ameen na tsayawa na fita da sauri zan wuce cike Dikko yace ke zo nan , da sauri na dawo shi kuma Al ‘ Ameen fita yayi ya ɗauki buta ya zagaya can bayan gida dan yayi alwallah , Buɗe murfin motar yayi ya fiddo ƙafar ɗaya ɗayar kuma tana ciki , tsareni yayi da idanuwa dan haka na sauke kaina ƙasa shiru yayi na wasu mintuna sannan ya ɗago report in yace dan kin ɗaukeni sakarai ni zaki kawo ma wannan abun ? Shiru nayi banyi magana ba , tsawa ya daka min yace baki ji ina miki magana ne ? Cikin rawar murya nace yi haƙuri , fitowa yayi daga cikin motar da sauri nayi baya , shima takowa yayi ya matso kusa dani , da sauri na sake ja baya , ya sake biyoni , yana sake matsowa na ƙara ja baya , idan na sake matsowa kika matsa wallahi saina zaneki , tsayawa nayi jikina ya fara kyarma ina kallonshi , Cike da ɓacin rai yace wannan iskanci zaki kawomin ? Girgiza kaina nayi ba tare da nayi magana ba , cikin tsawa yace shin kinyi rantsuwar magana ne ina miki magana kina girgizamin kai , da sauri nace a , a , jinjina kai yayi tare da tillomin report in yace ɗaukarshi ki shiga gani nan zuwa zaki faɗamin iskanci da kikeyi makaranta har kika ɗaukomin na 20 , na ƙarshe ke jakar da baki kishin kanki ya ƙarasa maganar tare da nannaɗe hannun rigarshi dan Al ‘ Ameen ya kawo mishi ruwa zaiyi alwallah… Duƙawa nayi na ɗauki report in zan shiga ciki yace kije ki fiddo min jakar banzarki daga mota , da sauri naje na ɗauko jakar na wuce ciki a lokacin shi kuma har ya gama alwalla ya biyo bayana yana ci gaba da faɗa , Ɗakin da yake shiga ya wuce ni kuma na shige ɗakin da nake zama , yana nan kamar dai da babu wani ci gaba a cikin ɗakin , alwallah nayo nayi sallah ina roƙon Allah ya bani mafita Babana kaɗai nake ciwon san gani , Har nayi sallah isha’e Dikko bai fito ba , su kuma uwayen ƙwa² har sun cika gidan sun fara gardamar kwallo , gajiya nayi na kwanta a inda nayi sallah gaskiya rashin ahali masu mutunci bai ba , duk wanda ya rasa iyaye masu daraja ya zama sai a hankali , ita kuma Inna ko wane irin ahalin suka raine ta ? Soyayya tana rufewa mata ido dasan duniya har su kasa gane aibun namiji , irin wannan rayuwar bata dace dani ba , da na fito daga zuri’a masu mutunci da duk haka bata faru dani ba , Inayin rayuwa irin ta dabbobi kuma ni ba dabbar ba , mahaifi ya haifi zuri’a wai ya barsu da cida kansu wannan ba komai bane sai rashin tsoron Allah , caca neman mata shaye² shine wanda na samu a matsayin ubana , rayuwata tazo a garari zata ƙare a raɓe² , na ɓarar da mutuncin da yasa har wani namiji yake da damar shigowa rayuwata ya ɗaukoni daga cikin ahalina ya maidoni cikin rayuwarshi , wannan wace irin rayuwace na samu kaina a cikin ta… ? Dariyar Dikko na jiyo sai kyalkyatawa yakeyi duk yadda akayi waccan dariyar wallahi mugunta yaji , palon yayi shiru sai salati akeyi ƙasa² amma Dikko sai dariya yakeyi yana ƙarawa , maganar Al ‘ Ameen naji yana cewa mai gida tou ya za,ayi , miƙewa Dikkon yayi yana dariyar mugunta yayo ɗakin da nake kwance , Cikin dariya yace ya miƙo hannunshi yana cewa An mata taso mu tafi , da sauri na taso kallona yayi yace wai duk me kikeyi baki cire kaya ba , ba tare dana kalleshi ba nace ba komai , tou zo mu tafi kina zuwa ? Ya tambayeni , girgiza kai nayi alamar a , a dan Dikko baida saiti abinda na fahimta idan dai yana cikin mugunta zaiso yayi ta zalinci yana dariyar cuta , Dariya ya sakeyi cikin sigar cuta yace da Allah kizo mu tafi , kyaleshi nayi na koma na kwanta , murmushi yayi sannan yace to tunda baza ki ba karki bacci ki jirani yanzu zan dawo kinji ko ? Nace tou , kallona yayi cikin wani irin yanayi sannan yace kinsan yau zan hanaki baccin dare sai kin faɗamin abinda yasa kika je kikayo na 20 , nace tou , har ya fita kuma ya dawo yace kiyi wanka kafin in dawo ga kayanki nan palo ki kwashe su ki dawo dasu ciki naga ma duk sunyi ƙura , yana faɗin haka yayi gaba abunshi , ina kallonsu ta window kowa ya shiga mota amma ba’a fita da motar Dikko ba kuma ba’a tafi da Al ‘ Ameen ba , saida suka gama fita na wuce bayi dan inyi wanka…..23/09/2019 *JAMILA MUSA …* 💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 39 Ina fitowa daga wanka na wuce palo inda kayana suke ajiye , ɗagasu nayi ɗaya bayan ɗaya naga babu wata ƙura da kayan sukayi nidai a gani na dan an lulluɓe su da towel , zani da hijabi kawai na ɗauka na koma ciki , Zanin na ɗaura wato ɗaurin ƙirji , na saka hijabin na nufi palo dan naga Al ‘ Ameen yana waje har yanzu bai shigo ciki ba , inda kulolin abinci suke naje na buɗe na zuba abinci naci na ƙoshi sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata ! Babana ne yazo ya tsayamin a rai gaskiya ina cike da kewarshi soyayyarshi ta hanamin zaman lafiya , duk duniya ban haɗa soyayyar Baba da kowa ba , ko ina yake ? Ko a wane hali yake yanzu ? Yana tunani na ko shima bayayi… ? Haka nan naji hawaye sun cikamin ido cike da rauni nayi magana a bayyane ina kake … ? Murmushi nayi mai cike da ɓacin rai zuciyata cike da kudurirrika akan Dikko duk runtsi duk wahala komai daren daɗewa sai Dikko yayi nadamar sani na , yanda ya takura ma rayuwata nima saina takura ma tashi rayuwar saina mishi zargen da bazai iya warware kanshi ba , da wannan tunanin bacci ya ɗaukeni. Su Dikko kuwa sai 12:30am suka dawo hayaniyar shigowar motocinsu ta tasheni daga bacci , tunda suka fara fitowa daga cikin mota suke gaddama har suka shigo palo , bayan kuma sun shigo haya² ƙarar filets da cokula kowa yana zuba abinci amma har yanzu banji maganar Dikko ba danshi baya da ƙoƙari wurin magana saidai dariya itama sai yaji mugunta yakeyi… Zuwa wani lokaci kuma palon yayi shiru bakajin maganar kowa sai ƙarar tv dan sun fara cin abinci , bayan wasu mintuna kuma naji wani yana cewa kai ubangiji ya fishshemu tsaka mai wuya , gaskiya na tausayawa kaina na tausayawa Saminu wallahi , Dariyar Dikko naji yana cewa niko wallahi bai bani tausayi ba aishi ya siya tsautsayi da kanshi maganin ganganci da rayuwa kenan kaga garin neman gira an rasa ido , anso ayi suna sai aka samu matsala… Hayani taci gaba da tashi , yayin da wasu ke cewa wannan tashin hankali da suka gani yau basu iya bacci , Dikko yace badai anan gidan ba ku gama cin abinci kowa ya kama gabanshi wallahi yau babu mai kwana a gidan nan , dariyar wani daban naji yana cewa sai An mata , Dikko yace koma “yar tsohuwa ce sai kunbar gidan nan , Kusan mutum biyu suka haɗa baki wurin cewa wai da gaske akwai mace yanzu haka a gidan nan ? Dikko yace mai maganar zaka tambaya dan nima dai ban sani ba , wai wace ce ita An matan nan ni na daɗe wallahi inaji Dikko yana kiran An mata ko itace ɗiyar ɗan… Sai naji kuma yayi shiru , murmushi nayi nace ɗiyar ɗan caca , Duk yanda akayi wani ya dakatar dashi ta hanyar hanashi yayi maganar shi , gaba ɗaya kuma palon yayi shiru har suka gama cin abincinsu babu wanda ya sake magana , bayan sun gama suka fara saɓewa ɗaya bayan ɗaya , bayan kowa ya gama fita naji Al ‘ Ameen yana ma Dikko sai da safe , banji abinda Dikkon yace mishi ba , ya fice kuma da motar Dikkon ya fita , Bayan Al ‘ Ameen ya fita daga gidan Dikko ya fara kirana , ban ansa ba na taso na fito palon daga bayanshi na tsaya nace gani , shima bai juyo ba yace kinajin yunwa ne ? Nace a , a me kikaci ne ? Nace ba komai , a , a ƙarya kike yarinya me kikaci dai ? Nace maka ba komai , tou zo nan yayi maganar a daidai lokacin da yake kwanciya saman kujera , Gabanshi naje na durƙusa cike dajin haushin shi , bai kalleni ba dan hankalin shi nakan tv amma dan tsabar ya ɗaukeni kidahuma yace kinmin kyau fa , zanyi magana ya tsareni da idanuwanshi tare da cewa bafa ina nufin kina da kyau ba ko kin birge ba kawai dai dan bakyajin yunwa nace da kyau , kallonshi nayi amma yanayin fuskata ya nuna banji daɗi ba , murmushi yayi tare da taɓe bakinshi ya kauda kanshi gefe guda yana ci gaba da cewa ni mace mai kyau haushi take bani , dan mafiya yawansu jakuna sunyi yawa a cikinsu kalloni yayi yana tambayata ko nayi ƙarya ? Kallon da yayi mani yasa nace a , a , murmushi yayi yace ɗaukomin report inki , tashi nayi jiki suku² na fara tafiya , tallabo kanshi yayi da duka hannayen shi yana kallona , zuwa can kuma yayi tsoki wai ji mace na tafiya , babu wani tsari mai jan hankali babu wata zarra mai burgewa a tattare dake , shi sakaran waccan rana kome ya gani a tattare dake zance har 12ndare , ya gane sarai banji daɗin abinda yake faɗa a kaina ba , naje na ɗauko report in na kawo mishi , Ansa yayi tare da tashi zaune yana kallona , yace wallahi kina burgeni sosai saboda kina da kyau , murmushi nayi tare da kallonshi , gyara zama yayi yaci gaba da cewa kyawawan idanuwan ki inajin natsuwa yayin da kika kallene ni dasu saboda kyawunsu da sheƙinsu ko a duhu kikayi kallo dasu abun ɗaukar hankali ne , ƙarajin daɗi nayi tare da ɗanyin wasa da idanuwana dan ina so inji an yaba surar da Allah yayi min , kyakkyawan murmushinki yana tafiya da hankali na a duk lokacin da naga kina cikin nishaɗi dan yanayin yana sakani cikin wani irin shauƙi mai wahalar misultuwa , ƙara yashe bakina nayi inajin daɗi , hankalinshi nakan report in yace kike ta wani kwashe baki da ita fa nake ba ke ba , ɗan kama kaina nayi sannan nace wace ce ? Matata mana dan tafi ki haɗuwa yayi maganar tare da ɗaure fuska yaci gaba da kallon report in.. A dibarance na kalleshi shi kuma hankalinshi yana kan report yana kallo ko kyaftawa bayayi sai gemunshi dake motsawa a hankali saboda taunar cingom in da yakeyi cikin kwarewa da salon ɗaukar hankali… Naɗe takardar yayi tare ɗago ƙafarshi ya takamin kafaɗa yana wasa da report in yace tunanin me kike a makaranta ? Kin rame , kuma cikin ku 20 kika yo na 20 , tunanin me kike ? Duƙar da kaina nayi ƙasa ina wasa da kafet banyi magana ba , jijjigani yayi da ƙafarshi yace baki ji wai ina magana ne ? Cikin ladabi nace babu komai , to ko aure kike so ne ? 😳 aure kuma ? na tambayeshi tare da zaro idanuwana ina kallonshi , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya wanda saida tsikar jikina ta tashi naji wani irin yanayi mai wahalar fassarawa na kasa daina kallon idonshi , Ɗan kauda kanshi yayi cewa tou daina kallona haka nan , gyara bakina nayi na sauke idona daga fuskarshi , yaci gaba da cewa zan miki haƙuri na yau saboda bance miki kar kiyomin na 20 ba , ban faɗa miki irin position in da nake so ki kawomin ba , amma zan faɗa yanzu.. Kalloni yayi sannan yace wallahi ׳ nayi rantsuwa kuma bazanyi kaffara ba , idan har kika sake kawomin 20 bazan dakeki ba , kuma bazan zageki ba haka bazan sakeyin fushi ba , kinga gidan nan dagani sai ke , sassauta muryarshi yayi ƙasa² yaci gaba da cewa babu wanda zaiji kuma babu wanda zai gani , duk lokacin da kika zo min da na 20 nasan abinda kike tunani , duk lokacin da naga 20 ni kuma zan sakaki a ɗaki irin abinda nayi miki a gidanmu ai kin tuna ko ? Ba tare da ya jira na bashi amsa ba yace tou wallahil azim irinshi zan ƙara miki , Kinga idan baki so in miki sai ki dage kiyi karatu , idan kuma kina so sai ki sake kawomin na 20 ni kuma ina ganin 20 tou sai mu shige daga ciki in rufo ƙofa in baki abinda kike tunani kuma ince karki sake ki faɗawa kowa… Lallai Dikko digirarran ɗan iska ne kuma baida kunya ko kaɗan , kasa haɗa ido ma nayi dashi naci gaba da kallon kafet , komawa yayi ya kwanta tare da cewa kashe tv n can kije ki kwanta , simi² na tashi naje na kashe tv in na wuce ciki , Tun daga wannan rana Dikko ya zama siriki na , nafi sati ɗaya ban yadda mun sake haɗuwa dashi ba , idan basu nan zanje in zuba abinci inci , idan kuma yana nan saidai in yini kuma in kwana da yunwa , da kuma naji maganarshi ya shigo ƙaramin palo zan gudu bayi in zamana , idan kuma akayi sa’a ya shigo ɗakin dan ya jira in fito ya ganni to shi da kanshi zai gaji da zaman jirana ya fita , ni kuma idan zasu fita daga gidan zan laɓe jikin window inyi ta kallonshi wallahi bana gajiya da kallonshi kwata² Gidan kuma kullum sai ya cika da maza suci su asha suyi ta gaddama mara amfani , amma zaiyi wahala kaji bakin Dikko , idan sun gama sun tafi kuma zaiyi kwanciyarshi ne kawai a palo , dan yanzu gidan yake kwana tun ranar da abokinshi yace wai da gaske akwai macen dake zama a gidan nan ? Amma naji ranar nan yana waya da wata wai yaushe zata dawo zai kawo mata amanar wata ɗiyar tsintuwa , nidai haka naji daga nan ban sake jin maganarshi ba , shin nice ɗiyar tsintuwar ko kuma wata ce daban oho… Kwance nake saman katifa sai juyi nakeyi saboda azabar yunwa , na rasa inda zansa kaina cikina sai zafi yakemin har na gaji da kwanciya kuma gashi duk yau Dikko bai fita , yanzu haka palon ya cika da mutane kuma wallahi ko jiya babu abinda naci tun daga kalacin safe. Na rasa inda zan tsoma rayuwata inji sanyi , sai hamma nakeyi ga bacci inaji amma yunwa ta hana inyi bacci duk jikina ya mutu bana iya tsinana uwar komai sai kwanciya nake kamar ruwa , Ta dubu nasha na fita ƙaramin palo na zauna ko Allah zai kawo min Dikko , amma mi har 11:30 bai shigo ba kuma babu wanda ya fara tafiya har yanzu dan naji sun tashi daga firar kwallo sun dawo labarin “yan danbe , har yanzu banji maganar Dikko ba kila baya gidan gaskiya , Daga firar “yan danbe suka faɗa maganar Saminu , wani ne yace bawan Allah Saminu wallahi ana maganar danben nan shi ya faɗo min a rai , me ya sameshi ne ? Wani daban ya tambaya , cikin muryar jimami yace bakaji ba ? Yace wallahi banji ba kuma ban sani ba miya faru ? Yace wallahi tsautsayi da rabon ayi , yaje kallon danbe . Dariyar Dikko naji yana cewa babu wani tsautsayi kuma babu rabon ayi , kawai ka faɗa mishi matar wani ya nema , kuma dan hauka ya tashi ya bita har gidanta , Allah yasa mijinta ya ritsasu shine yayi ma Saminu shegen duka har saida idonshi ɗaya ya fita , innalillahi wa’inna ilaihir raji’un wannan masifar Dikko kema dariya ranar da na dawo daga makaranta kenan ? Shima mutumin da ake ba labari salati yakeyi , Dikko yace wato mu mutane muna da wani hali na daban , kai da kanka zaka siyawa kanka matsala sai kace wai Allah ya kawo maka ? Ko ƙaddara ne ko meye ne , kaje ido ya fita wurin zina , kuma abin takaici ma Saminu matanshi biyu amma saboda masifa sai ya nemi mata , waye ya aike shi ? Wa ya saka shi ? Waye ya sashi neman matan aure ni wannan masifa da ta samu mutane bansan irinta ba , wannan tsautsayin dai Saminu shine ya kawo ma kanshi abunshi ba wani ba , Mai tambayar yace wa Dikko ina suka haɗu da matar tou ? Dikko yace an faɗa maka kallon danbe yaje , dariya sukayi dukansu , yace nifa ban gane kallon danbe ba , dariya Dikko yayi yace nanfa aka tsaya , wurin kallon danbe suka haɗu , Shima naci gareshi mai tambayar yace don Allah wai ya wurin danbe suka haɗu ? Tasowa Dikko yayi ya taho ciki , yana shigowa ya ganni zaune saman kujera yace baki bacci ba kenan ? Yayin da naji “yan palo sun ɗauki ihu duk yanda akayi an fassara kalmar dambe , Ba tare dana kalleshi ba nace Eh , zama yayi kusa dani yace mene ne tou ? Nace yunwa nakeji , kallon agogon hannunshi yayi sannan yace kuma wallahi banajin sun rage abinci amma bari su fita mu gani , nace to , wayarshi ya ciro daga aljihu ya ƙura mata ido yana danne ² yayin da nakejin kamar in tambayi Dikko miye dambe ? Dan ina so naji yanda labarin yake tiryan² kuma gashi palo labarin suke amma zuwan Dikko yasa banaji , Haka dai rayuwata taci gaba da tafiya zamana tare da Dikko , kullum da tunanin Babana nake kwana dashi nake tashi , bani da wata damuwa ta rayuwa dan Dikko ya shigo cikin rayuwata sosai kuma babu abinda na nema na rasa , Daren yau kuwa da kanshi yake tayani haɗa kaya saboda gobe zan koma makaranta idan Allah ya kaimu , sai nasiha yakemin cikin lallashi cike da tausayina da kuma nuna tsantsar soyayyar a gareni , kamar ya buɗe kaina ya zubamin ilimi haka yakeji bawan Allah , saida muka gama haɗa kayan muka fitar dasu ƙaramin palo , duk yanayin Dikko yana nuna bayajin daɗi zai rabu dani , duk inda na motsa zai tsareni da kallo mai tattare da tsantsar ƙauna da shaƙuwa. Murmushi yayi yace idan kika koma makaranta zaki riƙa tunani na kuwa ? Ya mutsa fuska nayi tare da taɓe baki nace wai ni ? Na nuna kaina ! Yace Eh , nace Allah ya sawaƙamin mema zaija min nayi tunanin yin tunaninka ma ? So ya bani ansa , murmushi nayi tare da cewa tirr Allah ya sawaƙamin in faɗa Soyayyarka , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya harsai da naji jikina ya mutu sannan yace ke komai sai kinyi wasa ni banajin daɗin haka , Jan hannuna yayi muka zauna saman kujera ya tattaro duka natsuwarshi sannan yaci gaba da cewe , ni ina sanki , da sauri na tashi tsaye nace me ? Dikko yace ƙwarai ina sanki kuma kema kina so na wannan shine gaskiya ina ta ɓoyewa kwarai , ya faɗi maganar tare da kauda idonshi daga kaina , dariya nayi tare da cewa wasa kakeyi ne ? Yace a , a da gaske ne fa , ba yanzu na faɗa soyayya dake ba tsawon lokaci , duk lokacin da nazo kusa dake sai inyi ta zuba miki ido wannan ai soyayya ce , Idan kina magana ni kuma kawai sai nayi shiru natsaya nayi ta kallonki inajin daɗi wannan shima ai soyayya ne , dakatar dashi nayi ta hanyar ɗaga mishi hannu ya isa , ya isa haka :• Abinda ka bayyana wannan shine ƙimar matashi kamar ka ? Ba shi bane ba , tsawon wane lokaci muka ɗauka da zamu fuskanci juna ? Fari yaro da yarinya ko wannen su yasan damuwar ɗan uwanshi wannan shine so , sannan fahimtar juna , Dikko yace sani da kuma fahimta da kike san ko bakya so kina da damuwa ko bakya da , yayin da kika samu wannan sannan ki so ni ? Wannan shine so ? Soyayya fa ita ba tsarata akeyi ba kawai faruwa takeyi , kinyi waya kuma kina saka mata kati ki siya data sai ta baki duk abinda kike buƙata kinga faruwa hakan yakeyi ba shiryawa akeyi ba , tou wannan shine so , bana so na rasa damata yayin da nace kece sarauniyar mafarkina , kina da damuwa kuma kina da riƙe abu a ranki , Duk da haka inayinki , ina sanki , tsoki nayi tare da cewa kayi haƙuri Dikko ba kamar yadda kake tunani bane ni banma yadda da soyayya ba tun daga farko ma kenan , soyayya tana faruwa ne cikin wani lokaci mai gushewa da wurwuri wannan shine tabbataccen hasashen da babu irin shi , ina kaiwa nan na juya na shige ɗakina , Murmushi Dikko yayi bayan tafiyar Sultana yace yanzu ta gayamun abinda zanyi kenan , duk da abinda na faɗa mata saida tayimin gaddama ta yarinta na faɗa soyayyarta yawancin abubuwa sukan zo da aibi ku tsaya ku gani zata faɗa soyayya ta da wurwuri……. 24/09/2019 *JAMILA MUSA …*💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 40 Miƙewa yayi bayan ya gama surutanshi ya fita babban palo maƙulin motarshi ya ɗauka ya fita , ina tsaye a jikin window ina kallonshi har ya shiga mota ya bar gidan da gudu bansan inda zaije ba , kuma ga dukkan alamu bazai kwana gidan ba , murmushi nayi tare dayin magana ƙasa² nace sauka lafiya. Yana fita na dawo na kwanta saman katifa naja bargo na lulluɓe na rufe idanuwana ina jinjina irin wulaƙancin da Dikko yayi mana shi mai kuɗi , “yar madara dabbace amma duk lokacin da naji an kira sunan mage ko na ganta sai magena ta faɗon min a rai da Dikko yabi ta kanta da mota bataji bata gani ba , Wulaƙancin da yayi ma Babana a ranar daya wankemin ubanda yafi ko wane uba a wurina da ruwan taɓo , lokacin daya bugamin kanshi har na suma , uwa uba ƙarshen wulaƙanci daya keta min mutuntaka ta , idan ma har zuciyata ta bari ƙiyayyar Dikko ta goge a cikinta ban yafewa kaina , ɗaukar fansa ƙudirina ne kuma muradi nane ko ba daɗe ko ba jima saina kafawa Dikko tarihin da bazai taɓa gogowa a rayuwarshi ba , Maganar cewa idan na kawo mishi na 20 zai rufe ƙofa dani nayi masa rata har abada nayi masa nisan da bazai iya kamoni ba , yanda Annabi ya gagari arna haka na gagareka Dikko sa’a ɗaya kawai nake nema fita daga hannunka amma da zaran na zare tou kwankin hararka sun soma… Dukan sitiyarin mota Dikko yayi a daidai wannan lokacin yace wallahi ƙarya kike , dan tunda ya fito daga gidan zuciyarshi tana faɗa mishi Sultana tana sanshi tabbas kuma akwai wannan soyayya domin yaga soyayyashi kwance a cikin idanuwanta ! Da safe tunda nayi sallah asuba nayi wanka na shirya cikin kayan makaranta , jakata na ɗauka da sauran kuɗina da ban kashe ba nayo babban palo , Na daɗe dan nafi ƙarfin awa ɗaya amma babu Dikko babu alamarshi kuma babu mota ko ɗaya a gidan , tun ina zama na marmari har na fara gajiya na kwanta saidai na kalli agogo nayi tsoki dan gani ma nake lokutan basa sauri , raina fa ya gama ɓaci sosai dan har nayi tunanin kila bayau zan koma ba , Ƙarfe 9:46am ya shigo gidan , a kasalance ya fito daga cikin motar ya nufo palo , kallo 3 nayi mishi kafin ya iso na kauda kaina , kamar yayi kuka dan yanayin fuskarshi ya nuna rai a haɗe kamar hadarin tsakar dare , Da sallama ya shigo palon bai ko kalli inda nake ba ya wuce ciki , na ansa sallamar na gaishe shi bai ansa ba ya wuce , murmushi nayi a zuciyata nace kila matarshi taci ƙaniyarshi , mugu kenan sai lahira a gane halinshi… Yayi fata² da awowi biyu sannan ya fito tunda ya fito ƙaramin palon ƙamshin turarunshi ya fara zagaye cikin gidan nan lungu da saƙo bana tunanin akwai inda ƙamshin bai kai ba , ƙamshin turare mai daɗi mai jefa mutum cikin wani irin baƙon yanayi mai wahalar mantawa , Bayan kamar minti biyu ya iso cikin babban palo , wallahi dole tasa na juya dan yanda naji ƙamshi inga wace shiga yayi haka ? Dan nasan bazaiyi wannan ƙamshin a banza ba , yanayin ƙamshin nasan yanayin haɗuwar da zaiyi kuma ba’a magana , dan duk yanda zan musulta muku kyawun Dikko zakuga kamar shiri ne abun , gaskiya Dikko yana da kyau fiye da duk yanda mutum yake zato , tunda nake a rayuwa ban taɓa ganin wayayyen namiji ɗan gayu mai saurin shiga rai kamar Dikko ba , ko ta ina babu inda mutum ya isa ya kushe shi saidai wani halin daban dan ɗan adam 9 yake bai cika 10 ba , Dikko yana da aji yana da natsuwar da ko mace tayi natsuwarshi taci Allah buɗa , Baida yawan dariya haka kuma bai cika murmushi ba , idan kuma yaji mugunta ya fara dariya kai kanka sai abun ya burge ka domin dariya tana mishi kyau , haka kuma murmushi ke ƙara ƙawata kawunshi , kuma yanayin ɗaure fuska ma dai yana mishi kyau gaskiya ! Idona na sauka kan idonshi gabana ya yanke ya faɗi , yasha ƙananan kaya abunshi yayi kyau cikar zatinsa da ƙwarjinsa ya ƙara fitowa sosai , bai kalleni ba ya yayi kamar ma bana nan saida yazo dai² inda nake zaune yace muje , Ajiyar zuciya na sauke na ɗauka jakata nabi bayanshi dan shi tuni ya fice daga palon , lokacin dana fito harya shiga mota , ina buɗe murfin motar zan shiga baya zaune naga shine zauna , fuska a haɗe kamar an aiko mishi da sauƙon mutuwa , Kawai dai naji babu daɗi yanayin yanda yake ta haɗe rai duk na kama kaina haka nan naji duk na takura , jakata na fara sakawa sannan na shiga na rufe na kalli wani gefe daban ba na driver ba kuma bana Dikko ba , yau an sako Al ‘ Ameen wani mai girman kan bala’e ne , kamar jira yake na rufe ƙofa ya bige mota kamar zai tashi sama , Saida muka fara biyawa Alheri clinic acan matar Dikko take shi kaɗai ya fita yaje ya dubota bai wani daɗe ba ya dawo yana gaba wata kyakkyawar budurwa tana biyoshi baya har suka iso wurin mota , Buɗe motar yayi ya ɗauki wayoyinshi daya bari lokacin da zaije wurin Sadiya , gaba ya koma ya zauna ita kuma ta shigo baya , kallona tayi ƙasa da sama sannan tayi tsoki tare da faɗin wata kalma da turanci amma ko miye tanayin maganar da zafi ne , Ɗaga kaina nayi na kalli cikin madubi inda Dikko yake kallona , sam yau idonshi hankalin shi da tunaninshi baya wuri na , da gudu driver ya sauko daga inda aka tanada dan ajiye motoci ya ibi hanya yaci gaba da falfala gudu babu ji babu gani , Saida mukayi tafiya sosai sannan ta sake faɗar irin kalmar data faɗa daga farko tana hararata , shiru nayi banyi magana ba , bayan wani lokaci tace au na manta ashe da daƙiƙiya nake magana jahila karuwar banza karuwar wofi , wani irin ɓacin rai na haɗeye dakel lumfashina ya fara yawo tsakanin duniya da lahira , taci gaba da cewa karya wacce iyayenki suka kasa baki tarbiya balbaɗaɗɗiya dake ɗiyar ɗan caca , Murmushi nayi mai cin zuciya amma banyi magana ba dan na fahimci tana da sauran magana , ci gaba tayi da cewa ni sweetheart baya ɓoyemin komai ni nace yayimin rainonki zuwa ranar da za’a ɗaura mana aure zaki dawo gidana kuma gidan mijina da zama a nan zan fara baki azabar tausayin da yasa kika shigo rayuwata Sadiya ma da tamin hawan ƙawara ya kikaga lamarinta ya ƙare ? Zata tafi duniyar mutuwa babu jimawa , Murmushi nayi tare da gyara zamana na kalleta sosai sannan nace idan kin isa ki sake maimaita abinda kika faɗa daga farko ! Nace jahila , nace ni ba jahila bace dan abinda na sani ko uwarki bata sanshi ba , ina da ilimin addini sittin ce a kaina sakara izihinki nawa ke ? Tayi shiru nace tou kinga ɗan caca tun nan ya nuna tarbiyarshi tafi irin wacce babanki ya baki , Da kika cemin karuwa tabbas ni karuwa ce bazaki shaida hakan ba saina kasa tallata a bakin titi uban naki idan ya gani zai kwasa , ni da kika gani kamar ɗan silif nake ko mutum baici ba saina burgeshi idan kuma harya taɓa kwanon zai taɓo cikin idan baici ba saiya lashe hannu , tabbas zan nuna miki kaidina da kuma illar kirana da karuwa da kikayi , Matsalarki da Sadiya ba tawa bace amma tabbas sai ubanki ya taɓa nan da nan ya kuma maida miyanshi , na faɗi maganar tare da nuna mata wuraren da idonta ke iya gani sannan nace dake da Dikko duk nafi ƙarfinku kuma kinyi ganganci shigowa rayuwata abun harina ya koma biyu daga yanzun nan zanci gaba da hararki kuma in hari Dikko , mari takaimin , nima na rama daga nan muma cakume da kokowa daga zaune , Da sauri Dikko ya juyo yace miye haka kuma ? Cikin ɓacin rai nace ban sani ba baƙin munafiki dakai , zaro ido yayi yace ai bake nake tambaya ba , cike da masifa nace nima ai bakai nake ba ansa ba , Ashiru yi parking inji Dikko , da sauri ya gurji gefen titi ƙayyyyy yayi parking har lokacin bamu daina bige² ba , Ni Dikko ya fara fiddowa tunda ni nake saitin daya buɗe murfin motar yana fizgoni ya mareni yace nine munafikin An mata ? Kafin ya sauke hannunshi nima na zabgaga mishi mari nace kaine mana munafiki dama akwai wani bayan kai ? Da sauri Ashiru ya kauda kanshi , murmushi Dikko yayi yace An mata ni kika mara ? Nace waye kai ? Dikkon banza Dikko wofi , fitowa tayi daga cikin motar ta kamani da kokowa duk da banda ƙarfi na firgice sosai dan na tsani inji an aibata Babana , kokowa mukaci gaba dayi Dikko ya riƙeni na sake fizgewa mukaci gaba da faɗa , ya ƙara riƙeni sosai hannun damarshi ya riƙo min ƙuguna dashi hannun haggunshi kuma ya ɗagomin fuskata kowa yana kallon kwayar idon kowa , Cikin maganarshi maisa natsuwa yace An mata yau kuma Dikkon ne na banza da wofi ? Ni An mata ? Kinmin adalci kenan ? A gaban mutanen dake ganin girmana zaki tozarni ? Mi yasa bakimin jiya ba ? Me yayi zafi haka haba An matana…. Ya ƙarasa maganar kamar zaiyi kuka , cikin kuka nace cewa fa tayi Babana ɗan caca kuma kaine kace mata ni karuwa ce kuma karya fa 😭 jahila fa 😭daƙiƙiya balbaɗaɗɗiya fa wai Babana bai bani tarbiya ba irin wannan shedar zakuyi ma Baba ? Tsareni yayi da idanuwanshi masu ɗaukar hankali sannan yace tou kiyi haƙuri , rufe idanuwana nayi nace inyi haƙuri a aibata min Babana ? Dikko ya ƙara cewa kiyi haƙuri , buɗe idanuwa na nayi tare da cewa wallahi Babana bai kasa bani tarbiyya ba kuma kai zaka sheda haka wata rana sakeni , sakina yayi baiyi kaddama ba mota na koma na ɗauko jakata nazo gabanshi na zazzageta nace ga jakar ka nan ga sauran kuɗinka nan idan naje gida zan bada cikonka a kawo maka , Ina faɗin haka nayi gaba , Dikko yace ina zaki je ? Juyowa nayi cike da ɓacin rai nace zanje gidan ubanda ya hafeni ne , nasan darajar ɗan caca kuma nasan mutuncinshi , kallon inda budurwar take nayi nace sunana MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA { Sultana } ki fara kuka tun daga yanzu domin kwanakin baƙin cikinki sun soma daga yau , mafita ɗaya kawai shine ki mutu ki huta amma tabbas bazan goge kuɗina akanki ba wallahi ׳ , Kamar sakarai haka Dikko ya tsaya yana kallona , nunasu nayi dukansu da ɗan yatsa nace gata nan gatanan ku , goge hawaye nayi nai gaba cikin ɓacin rai , Dikko ya sake cewa wai An mata miye kikeyi haka ? Tsayawa nayi amma ban juyo ba nace idan ka sakemin magana saina tona maka asiri……. 25/09/2019 Kuyi haƙuri don Allah wallahi banajin daɗi wannan ma dakel nayi shi , *JAMILA MUSA…*💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 41 Dariya Dikko yayi mai shiga zuciya yace tou miye ribarki idan kin tunamin asiri ? Ai asirina da naki a haɗe yake ki tona tunda ban riƙe miki baki ba , amma ki sani idan kin tonashi sai ki fara neman hanyar da zaki rufeshi saboda tabbas wata rana zaki zama ni , ni kuma zan zama ke , kije abunki amma duk abinda zaki kiyi na hankali da tunani , cikon kuɗi kuma da kike magana bake ba da wani abu ya shiga tsakani dake nake ganin mutunciki da ƙimarki saboda kina da wani matsayi na musamma a rayuwata da zuciyata wanda ta dalilinshi kuma nake ɗaga miki ƙafa , duk abinda ya fita hannuna na gama dashi har abadan abada , Kuma zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne , idan akacemin An mata ta mutu ina da yaƙini zuciyata tacemin a , a tou tabbas idan nazo zan ganki kina numfashi , sauka lafiya amma banda kukan dare dan ina buƙatar bacci a wannan lokacin kiyi kuka da safe kiyi da rana amma idan har kikayi kukan dare gani nan zan dawo , Kallon budurwar yayi ya nuna mata da hannu ke koma mota muje , shiga tayi mota shi kuma ya biyo bayana , gabana yasha yace An mata karki zo kiyi abunda zai zama matsala a rayuwarmu , ki manta da abinda ya faru baya mu fuskanci sabuwar rayuwa , Cikin kuka na kalleshi nace har ƙarshen numfashi na bana fatan na sake kasancewa dakai wallahi , kuma zuciyarka ta faɗa maka gaskiya tabbas zan dawo amma ɗaukar fansa zata dawo dani , Murmushi yayi tare da cewa haba yarinya , Dikko ne fa ! Kin manta nine na koya miki ? Nine nayi kuma nine na fara baki idan daɗi kikaji ko zafi duk nine dai , ruwa idan da rabonka cikin sa ko ka zuba a kwando bai maka yoyo , ni ba abin farautarki bane zaki duk jarumtatai yana ganin ƙimar mafarauci a wancan karon suma kikayi , wannan karon ma haka zata sake faruwa dake ba suma ba har jinya sai kinyi , idan kin dawo ɗauka fansa zaki gane Dikko ba sa’ar wasanki bane domin saina baki azabar da sai kinyi fitsarin wahala bayan kin dawo daga duniyar suma , tsoro na zai shigeki a lokacin da kika kasance dani a shifimɗa ɗaya , idan kuma Dikko baya nan zakiyi kuka bacci ya gagareki gidan biki ko suna Dikko yana tare dake a zuciyarki domin zan zame miki garkuwa , da hannun damarshi ya daki na haggu yace wallahi jarumi ɗaya ake a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma ke da kanki zaki faɗa keje ki dawo ina nan ina jiranki , Idan kuma soyayya ta dawo dake , ƙasa ya kalla yana nazari bayan wani lokaci ya kalloni yace tabbas zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , nace wa ni ? Yace tabbas ranar zata zo , nuna kaina nayi tare daci gaba da cewa yi haƙuri Dikko ka manta da wannan wasan kwaikwayon naka har abadan duniya hakan bazai yuwu ba , murmushi yayi tare da taɓa daidai saitin zuciyarshi yace ina da tabbacin zaki soni kamar dai yadda na faɗa , ko kina da tabbacin cewa baza ki taɓa so na ba ? Nace Eh har abadan abada , murmushi yayi yace ƙarya kikeyi , nace da gaske nake , yace zaki gani nima nace zaka gani , girgiza kanshi yayi yace jeki abunki , Ci gaba nayi da tafiya har yanzu yana tsaye a wurin dana barshi , motoci masu komawa katsina nayi ta ɗagawa hannu har Allah yasa na samu masu ragemin hanya shiga nayi na nufo katsina yayin da Dikko ya shiga suka kama hanyar abuja , Budurwar Dikko kuma ga wayarta a hannuna , domin dana koma mota dama ba jaka na koma ɗaukowa ba waya na ɗauko abinda yasa na fito da jaka dan karsu zargi ni na sace kuma nasan idan sukayi gaba zasuyi tunanin wurin fitowa ta yada ita , Baba da Mama da kowa nata yana cikin waya… Tunda Dikko suka tafi yake kukan zuci daren jiya da An mata tasan irin matsalar daya fuskanta akanta da bata baɗa mishi ƙura ba , abinda ya faru tsakaninsu sirri ne babu wanda ya sani sai shi sai ita sai Allah , yana bata mutuntukar mutuncinta daya ɗauka amma yarinta ta hanata kusantowa gareshi ! Abinda ya faru jiya , bayan Dikko ya faɗawa An mata yana santa tafiyarta kawai tayi ta barshi palo zaune kamar wani sakarai , bata daɗe da shiga ɗaki ba Dady yace yana nemanshi duk abinda yakeyi ya barshi yazo , shine ya tashi ya fita babban palo ya ɗauki makullin mota ya fita kuma a gaban idon Sultana yabar gidan…Bayan yaje gida a palon Dady ya samu Al ‘ Ameen gurfane a gaban Dady , kallo ɗaya yayi mishi ya ɗauke kanshi tare da samun wuri shima ya zauna can nesa da Dady , bayan ya zauna ya gaishe da Dady ya ansa shima Al ‘ Ameen ya gaishe da Dikko , Dikko bai ansa gaisuwar ba , kallon Al ‘ Ameen Dady yace ya kira mishi Ummar , Miƙewa Al ‘ Ameen yayi kafin ma ya fita daga palon Umar ya shigo saboda dama tuni an kirashi bai samu isowa da wuri bane , bayan kowa ya zauna Dady ya kalli Al ‘ Ameen yace ga Babana nan ka sake faɗar abinda ka faɗa , shiru Al ‘ Ameen yayi , Dady kuma ya kalli Umar bayan Al ‘ Ameen yaƙi magana yace Umar wace yarinya ce take zaune da Baba ? Da sauri Umar ya kalli Dikko amma shi basu yake kallo ba yana kallon wani wuri daban , cike da fargaba Umar yace wallahi Dady nidai ban sani ba , Dady yace tou aini Al ‘ Ameen yace min ya ajiye mace gidanshi na goroba road bayan ni nasan Babana baya huɗɗa mata shi yasa hankalina ya tashi , Umar sake kallon Dikko yayi amma har yanzu Dikko fuskar nan tashi dai kamar yadda take kullum kuma har yanzu baya kallonsu kawai dai yana saurarensu. Dady yace ƙarya zakamin ne ? Ya tambayi Umar , Umar yayi shiru , Dady yace ma Al ‘ Ameen yanzu ina yarinyar take ? Tana gidan har yanzu ? Al ‘ Ameen yayi shiru , gyara zama Dikko yayi yace tana gidan Dady , amma lokacin dana fito na barta tayi bacci , nayi kuskuren rashin sanar dakai amma da Allah kayi haƙuri nayi amfani da maganar ka ne da kace na zama mai kyautatawa duk wanda naga rayuwarshi tana buƙatar taimako , Yarinya ce ƙarama shekarunta bazai wuce 18 ba kuma na baka labarinta kwanakin baya itace yarinyar da mukeyin faɗa tou yanzu mun daina faɗan ne , a tsawace Dady yace ɗiyar ɗan caca ? Karuwar Babana ? Cikin ladabi Dikko ya sauke kanshi ƙasa tare da rufe idanuwanshi , Dady yaci gaba da cewa duk ƙoƙarin kare martabar ka da nake maka ni zaka ɓatawa siyasa ka ɓatamin suna har cikin jahata ? Ni zaka zubarwa da mutunci ? Ka ɗauko karuwa ka ajiye a gidanka ka bar matarka kaje ka kwana da “yar iska mara tarbiya wacce tafi ƙarfin iyayenta itace wacce kake ganin kaine zaka gyara mata rayuwa ? Masifar da tasa iyayenta suka yada ita ba ƙarama bace kai shine kaje ka ɗauko ka dawo da ita rayuwarka kai sarkin imani da tsoron Allah ? Kana siyasa zaka ɓatawa kanka suna , ka zubar da mutuncinka a idon duniya ina amfanin mu’amula da karuwa ? Ko zaka dafa Al ‘ Qur’ani kayi rantsuwa kace baka neman yarinyar nan babu wanda zai yadda , da yarintar ka baka bi mata ba sai yanzu da shekaru suka fara hawanka ? Tou idan dan rashin lafiyar matar ka ne Momynka ta nemo maka auren ɗiyar yayarta shikenan na kashe maganar… Murmushi Dikko yayi tare da cewa gaskiya Dady ban tsara zama da mace 3 ba a rayuwata itama Sadiyar haƙuri nayi kawai na ansa amma ni gaskiya mata 3 sunmin yawa wannan karon bazan ansa ba kuyi haƙuri , ciki ɓacin rai Dady yace wallahi idan dai ina lumfashi a duniyar nan baza ka auri karuwa ba sakaran banza da baka san macen da ya kamata ka aura ba , shi aure daka ganshi yana buƙatar cancanta mutuntaka asali da nasabar mace , banda kake sakarai ka rasa wacce zaka so sai karuwa ? Karuwar kake tunanin zata zama uwar “ya “yan ka ? Ni wallahi ko jirgi zan siya bana buƙatar na hannu sai sabo shi yasa bazan iya auren zawara ba amma kai dan baka kishin kanka har kake tunanin auren karuwa , wallahi da kasan kanka ko mace baka nema ,na tsani wani yayi amfani da abu nayi amfani dashi saboda tsanar da nayi ma abun yasa bana sauka hotel , duk jahar daka gani babu inda banda gida babu ƙasar da ban mallaki gida ba dan na tsani wani ya shiga a wuri na shiga sakarai wawa dakai idan baka fita harkar yarinyar nan ba zaka haɗu da fushi na , Dady kayi haƙuri kasan…. Tsawa Dady yayi masa yace nasan me ? Ko zaka mutu banajin komai Babana , Dikko zai sake magana Dady yace fita bana san ganinka , jiki a sanyaye Dikko ya miƙe ya fita , ɗakin mom inshi ya nufa itama faɗa ta mishi sosai domin Allah kaɗai yasan abinda Al ‘ Ameen ya faɗa akan Sultana , Itama wata yayarshi da isowarta kenan nigeria tazo ganin Sadiya ta sako bakinta tayi ta ma Dikko faɗa tare da cewa kadaiji kunya wallahi kuma kayi asara ka rasa wacce zaka so sai ɗiyar ɗan caca , abun kunya duk nasabarka da mutunci gidanku kaje ka auro mana ɗiyar marasa asali , jiƙar matsafi ɗiyar ɗan caca karuwa tou ka faɗamin ita me zata haifa ? Kalli yadda tazo ji yadda take tata rayuwa wace irin tarbiya zata ba “ya “yanta ? Gaskiya Dikko ka bani kunya da ina alfahari dakai amma , Dikko ya tareta da cewa amma yanzu kin daina ko ? Tou kije kiyi ta daina warki kuma ki fitar da bakinki idan ba haka ba kuma duk abinda nayi miki ke kika jawa kanki , Momy tace rufemin baki mara kunya ko itama halin karuwanci zaka nuna mata ? Dikko yace tou ta ƙara aibata ta kiga yanda zanyi da ita ! Wallahi saina zane mata jiki tas idan kuma tana ganin zaki hana na daketa ta fito waje wallahi saina bi ta kanta da mota na wuce , wani irin mari Momy taimishi dan tasan halin Dikko da kafiya idan dai yace zaiyi sai yayi idan kuma ya rantse akan abu ko za,a mutu baya kaffara saiya aikata wallahi , Kallon Yayarshi yayi yace akanki aka mareni ko ? Jinjina kanshi yayi tare da miƙewa yace zan haɗu dake , tace ni ba’a kaina aka mareka ba akan karuwa dai , cikin ɓacin rai Dikko ya nufi wurinta Momy tace idan ka taɓata ban yafe maka ba shanyayye , dariya yayar tashi tayi tare da cewa aikin san karuwa koba asiri akwai bariki mai wahalar goguwa a zuciya , wallahi Dikko ka daiji kunya ɗiyar daka isa ka haifa ai ko baka haihu ba ka kalli ɗan abokinka , fita Dikko yayi daga ɗakin dan idan ya tsaya komai zai iya faruwa , Wurin motarshi ya samu Umar , kuma Umar shine ya faɗawa Dikko cewa Al ‘ Ameen yazo ya faɗawa Dady komai kuma ya ɗora da cewa idanma aure mai gida zaiyi ga ɗiyar yayarshi , shine ya kawota gidansu Dikko kuma tayi sati tunda tazo Dikko bai taɓa ganinta ba sai yau , kuma Dady shine ta tursasa Dikko yaje asibiti ya ɗauketa ya tafi da ita ya ajiyeta kaduna , tunda tazo itace take kula da Sadiya , tana kyautatawa kowa na gidan , Ita kuma Momy ta riga data yanke shawara kawai Dikko zai auri autar ɗiyar yayarta , kuma duk zagin da yarinyar nan tayiwa Sultana wallahi Dikko baiji ba , baisan sunayi ba dan hankalin shi baya wurinsu yana can ya tafi duniyar tunani , bige²nsu kawai yaji , amma wallahi baiji zage²nsu ba , Al ‘ Ameen shi yasan komai akan Sultana kuma shine ya bawa ɗiyar labari yace ta faɗawa Sultana tace Dikko ne ya bata labari , amma tayama Dikko zai fara wannan sakin layi ? Bayan bai haɗa Sultana da kowa ba , A gajiye na iso anguwarmu tafiyata babu jimawa anguwar ta samu ci gaba sosai , tun daga farkon layin hannun da Dikko ya sissiye har zuwa gidan dawankashi an bugeshi anyi wani irin zuƙeƙen gini babu wani maƙoci daya raɓeshi baya tare da kowa sai gidajen dake kallon gidanshi , waje kawai aka gyara aka ciccina mishi fulawowi ciki kuma aka watsa dawakuna da wasu irin lafiyayun karnukan turawa masu kama da kuraye , an ƙawata gidan da wasu irin fitulu wanda idan dare yayi aka kunnasu haskensu zai gauraye ko ina da ko ina , Gidanmu na shiga da sallama , Nana tana gani na ta tashi da gudu ta shige ɗaki , Babana na gani kwance saman tabarma yanajin magana na ya karkato da kanshi dakel ya kalleni , Kowa ya tsaya yana kallona babu wanda ya ansa min sallamar da nayi , wurin Babana na nufa na durƙusa na kamo hannayenshi nace meke damunka ? Kallona yayi cike da tsantsar ƙauna sannan ya buɗe baki dakel idonshi ya cika da hawa yace shine kika tafi kika barni….? 😭Murmushi nayi tare da goge mishi hawayen nace ai gani na dawo ? Kana tunanin zan tafi na barka ne ? Bayan bana iya rayuwa saida kai ! Dare da rana safe da yamma yanayin farin ciki da damuwa halin yunwa ko ƙoshi babu kowa a zuciyata sai kai , farin ciki ya dawo rayuwar kunci da damuwa zata kama gabanta , Har yanzu babu wanda yayi mana magana ga gida cike da jama’a yayin mutane suka fara janye “ya “yansu , matar Baba ƙarami ta kira “yarta gefe tace ki wuce ki tafi gida annoba ta dawo , Wane yaro ne ya shigo gidan cikin farin ciki yana barka da dawo uwar ɗakinmu , ban kalleshi ba kuma ban saurareshi ba ina kallon yadda jama’a suke tsame “ya “yansu saboda zuwana , jinjina kai na nayi tare da cewa wane yaro a kawomin abinci da Allah , saida ya saramin caucau Allah dai ya kare miki sharri yayi maganar cikin muryar dabanci , nace Amin shi kuma ya fice… Fitar wane yaro nabi duk wanda ke gidan da kallo , sannan nace duk sannun ku ? Na dawo ya mai jiki ? Babu wanda ya bani ansa , murmushi nayi na zauna gefen Babana , ban gama zama ba Amisty ta shigo , fitowar Nana daga ɗaki shigowar wane yaro da kwanon abinci , Hafsa A ‘ i Saude Zalifa Karima sai kuma wata daban wacce nake tunanin itace suke zuwa gidanta wato Asma’u , Murmushi nayi tare da miƙewa tsaye nace dama nasan ranar nan tana zuwa shi yasa na taho gida na dawo kuma a tafe nake da sabon salo na baya ba komai bane ba , ga Sultana ga Amisty ga kuma Hafsa ku kaɗai nake da damuwa daku sauran kuma banma sansu ba , …. 26/09/2019 *JAMILA MUSA….*💅🏻⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }__Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻*ASMA’U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ &*RABI’ATU AMINU MAMMAN DEE*🅿 —— 42 *_AHUMAGGAH yadda kika fara lafiya ubangiji yasa ki kammala lafiya , ku nemi naku karku bari ya wuceku daga alƙamin SURAYYAHMS haziƙar marubuciya mai tafiya dai² da zamani yana nan yazo…_* Kallon wane yaro nayi nace kai muje ƙofar gida kaji , na faɗi maganar ina nufar hanyar fita , riƙoni Amisty tay ta baya tana cewa babu wani wajen da zakije anan zamu ci uwarki , ban kalleta ba na kalli inda ta riƙeni nace sakemin hijabi , Hafsa tace baza’a saki ba kina nufin mu zaki ɗauka wasu ƙolaye mu barki kuma , murmushi nayi na kalli Hafsa nace sakarar banza ba ƙolaye ake cewa ba kuzo muje ƙofar gida , saboda bana so ayi wulaƙancin a gaban Babana da kuma sauran jama’ar dake gidan gani na ma kawai yasa sun kora “ya “yansu ina kuma ga anyi wannan maganar a gabansu , duk a zuciyata nayi wannan nazarin …. Babana ya karkato cikin yanayin jin jiki yace Uwar masu gida me ya faru ne ? Nace ba komai Babana , a kadarance Amisty ta kalleshi tace ai kasani , a wahalce ya kalleta yace me na sani ne Amina ? Nace Baba da Allah ya isa haka kayi bacci abun ka kada a ruwa ai sarki ne kaja bakinka kawai kayi shiru domin ni wutar kara ce ba’a kwana dani ba saidai idan ba bacci ake ba ! Mamana….. Ya faɗa tare da lumshe idanuwan shi yace mene ne ? Kallonshi nayi cikin ɓacin rai nace wutar da aka daɗe da kashewa ni kuma nake so yanzu ta ruru , cikin hayaga ga , nace ɗaukar fansa da ramuwar gayya a cikin jininka yake Babana , baka gada ba ni kuma na gada ɗan koyo da ɗan gado dukansu idan suka tashi sai sun zarta , Na rantse da ubangiji da ya bani aron lumfashi da rayuwa dawowa ta sai ta zame ma kowa tashin hankali saina firgita kowa saina jinyata duk wanda ya shigo rayuwata , wallahi ׳ Amisty da Hafsa kun sake toƙalowa kanku masifa idan baku kiyayeni ba uwar kowa a cikinkun nan , na nuna su da ɗan yatsa na jinjinashi nace kuma nayi rantsuwa…Da sauri Hafsa ta kalli Amisty suka kalli juna cikin firgici , komawa nayi na zauna tare da cewa har kun firgita kenan ko ? Jinjina kaina nayi tare da cewa baku ga komai ba furtawa kaɗai nayi kuma ban faɗa muku abinda zan aikata ba amma tabbas wani abu zai faru , kallon wane yaro nayi nace kai bani abinci kaji , gabana ya ajiye abinci nace muci shi tare , babu ɓata lokaci yasa hannu mukaci gaba dacin abinci , Kallo Babana ya bini dashi na wani lokaci sannan ya kalli Amisty yace mi ya haɗaku da Uwar masu gida ? Amisty tayi shiru tou maganar dai bata faɗuwa da kunya tace tsiraicin Babanta na ɗauko , tayi shiru ta kasa magana , lashe hannuna nayi tare da cewa bara kaji abinda ya haɗamu Babana , Kafin in ɗago su Amisty sunyi layar ɓata domin dai bansan ta inda sukabi suka fice ba , murmushi Babana yayi mai nuni da yana alfahari dani , kallon wane yaro nayi nace jeka idan Allah ya kaimu jibi ka dawo ina neman ka , godiya yayi ya fice daga gidan , ni kuma ɗakina na nufa ina zuwa na cire kayana , alwallah nayo nazo nayi sallah azahar har saida nayi la’asar sannan na tashi , Komai na ɗakina yana nan yanda yake babu abinda aka taɓa har kuɗin dana sata a jakar Amisty duk suna nan , wanka nayi na saka kaya na fice daga gidan , a napep naje gidan su Mamy wacce muka haɗu da ita a wurin saloon , ban sameta gida ba , saidai nabar saƙo idan ta dawo ace mata Sultana tazo mu haɗu gidanmu jibi idan Allah ya kaimu , Kasuwa na shiga nayi “yan hidimomi na har katifa na siyowa Babana da sabbin zannuwan gado 3 sabuwar ledar tsakar ɗaki sai ƙaton bargo saboda yanayin sanyi ² dake shigowa da labulaye masu kyau , bayan na gama da kasuwa naje na siya sabon sim card na wuto gida… Ɗakin kusa da ɗakina na share na shinfiɗa leda na saka katifar na rataya labululluka na shinfiɗa zanin gado mai kyau a saman katifa , ɗakina na koma na ɗauko fulaluwa nazo na saka musu rigarsu irin na zanin dake saman katifar , ruwan zafi na dafa na kaiwa Babana bayi yaje yayi wanka , Kafin ya fito na ɗauko mishi kayan da zai saka dan naga kayan a gefen katifar ɗakina , ɗakinshi nakai mishi da turare shima a kusa da kayanshi na gani turare mai shegen tsada da ƙamshi , yana fitowa ya saka kayanshi ya shafa turare sannan yayi alwallah dan magrib ta gabato , abin sallah na shinfiɗa mishi ya hau sama , nima na fito nayi alwallah na wuce ɗakina… Duƙe yake saman bayan kujera ya ƙurawa waya ido yana kallon hotunan Sultana , murmushi yayi a bayyane yace da wannan kyakkyawar zan kere sa’a na kasace na daban abina , amma dai ya kamata na bata shawara ta daina ciki baki akan cewa baza ta taɓa so na … Zagayawa yayi ya zauna saman kujera yana cewa dani dake yau zanga waye tunani zai hana bacci , kwanciya yayi saman kujera ni na kwanta kuma bacci zanyi ya ƙarasa maganar yana murmushi , saida ya lumshe idanuwanshi yace ki kasance cikin farin ciki na barki lafiya…. Saida na gama duk abinda nakeyi na kwanta saman katifa a gajiye , a hankali naja bargo na lulluɓe tare da ƙurawa wayar dana ɗauko ido kira sai shigowa yakeyi babu ƙaƙƙautawa , uhum murmushi nayi tare da kashe wayar gaba ɗaya na rufe idonuwana danyin bacci…. _Ƙarya kike…_ Wannan kalmar itace ta fara zomin a cikin kwalwar kaina , ɗan jujjuya kaina nayi a hankali na gyara kwanciya ta , _Zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo , bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne_ Murmushi nayi har yanzu idanuwana a rufe nace tou ya akayi ban dawo ba ? _Zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , tabbas ranar zata zo , murmushin shi yazo ya tsayamin a rai kalmar ƙarya ta sake dawomin a zuciyata…_ Da sauri na tashi zaune nace wallahi ƙarya kakeyi na tsaneka…. Murmushi yayi ya gyara kwanciya , nasan baki tsaneni ba ɓacin rai yasa kike faɗar wannan kalmar , idonshi a rufe yayi magana … Wallahi a daren ranar banyi bacci ba , tun daga ranar dana fara ganin Dikko har zuwa yau da muka rabu ko ta ina Dikko ya zargemin zuciya , nayi juye² wallahi bai fita ba , ganin dai baccin bazai zo ba yasa na haƙura na fita nayo alwallah naci gaba da sallah ! *** Yau laraba kuma itace jibin da nake jiran zuwanta , bayan hantsi ya ɗaga na dafa ruwan wanka wa Babana , kafin ya fito na gyara mishi ɗakinshi na share na goge fess na zuba mishi turaren wuta , bayan ya fito wanka ya shirya cikin shiga ta kamala ya baɗa ƙamshi , Sama ² ya yagi abin kalacin dana kawo mishi , bayan ya gama ya umurceni dana fitar dashi ƙofar gida saman dakali , ɗakina na koma na ɗauko kafet na naje na shinfiɗa mishi sannan na dawo na kamashi dan har yanzu yanayin abu irin na wanda yasha jiya harya gaji , A hankali muka fito dani da Babana muna lallaɓawa , saman dakalin na samu Amisty zaune ita da Hafsa , ko inda suke ban kallaba na taimakawa Baba ya zauna , a dai² lokacin da Umar yake tsugunniya a gaban Baba yana gaishe shi cikin girmamawa tare dayi masa sannu da jiki ,Naji daɗi sosai dan haka nima na gaishe shi , ya ansa cikin kulawa tare da cewa wurina yazo ya faɗi maganar yana miƙewa , bayanshi nabi mukayi nisa da Baba , bayan mun samu madakata yace mai gida ya aikoni wurinki , kallonshi nayi banyi magana ba , wayarshi ya ciro daga aljihu ya kira Dikko bayan ya ɗauka yace mai gida gata , ya faɗi maganar tare da miƙomin wayar , Cikin jin daɗi na ansa na kara a kunne na tare dayin sallama , ansawa yayi cewa ya kike ? Lafiya qalau kaima kana lafiya ? Alhamdulillah , tun shekaran jiya nake so nai miki ya hanya Umar yace yazo ² bakyanan ina kike zuwa ne ? Banje ko ina ba , tou da kyau , na sake cewa banje ko ina ba , yace ai shine nace hakan yayi kyau sai anjima , shiru nayi dan bana so wayar ta tsaya hakanan , shi kuma kashe wayar yayi abunshi… Miƙa mishi wayarshi nayi , shi kuma yace min yana zuwa , mota ya koma ya ɗaukomin wata “yar ƙarama leda mai tambarin waya a jiki yace gashi yace a kawo miki kuma akwai layi a ciki anyi mata caji , Uhum ni da zanma Dikko cikon kuɗi saina ɓige da ansar waya , cikin farin ciki mukayi sallama da Umar , ban koma wurin Babana ba nayi cikin gida ina zuwa na shige ɗakina na zazzage ledar na ciro “yar kyakkyawar wayata na dudduba bansan sunan wayar ba anma an rubuta a jikin wayar , ban damu da sanin sunanta ba nidai tamin kyau kuma ta burgeni sosai , ajiyewa nayi na koma ƙofar gida wurin Babana dasu Amisty dana baro waje , Ina fitowa a daidai lokacin da Mamy ta faka da tsadajjiyar motar ta , tasha wani irin dakeken gilashi wanda ya cinye kaf rabin fuskata , karuwa ce data ansa sunanta karuwa , ba karuwar muje mu dawo ba , ba karuwar wahala ba , ba karuwar ya zanyi ba ? Kana ganin zubin iskancinta kasan karuwanci takeyi mai aji kuma mai matsayi ba iskanci cini inci tuwo ba , Tana fitowa ta fara bi bi biyyy 👍🏻 cikin yanayi mai nuni da “yar hannun ce , murmushi Babana yayi cikin jattako da gogewa , wata alama yayi mata da ido irin tasu ta “yan bariki , dariya tayi tare da cire gilashinta tace *BINNA* 👍🏻 , Binna kaci dubu ka binne dubu , binna zaki binna kura binnan ƙarshen ƙarni binna ka taushe ….. Sai kuma ta fasa ƙarasawa ! Dariyar “yan duniya Babana yayi tare da ɗan kauda kanshi gefe cikin jin kunyata , Mamy ta sake cewa Binna wuta , wuta na wurina…. Ba tare daya kalleta ba yace ga Mamana nan da nake baki labari ku gaisa , gaba ɗaya tabi mu da kallo dani da Amisty da Hafsa a wani irin yanayi tace wace ce Uwar masu gida ? Kakkaɓe idanuwa na nayi nace nice , ƙwalalo idanuwa tayi tana kallona sannan ta sake kallon Babana tace Binna Sultana ɗiyarka ce ? Jinjina kai Babana yayi alamar Eh , ƙara kallona tayi sannan ta sake kallon Baba ta juyo ta tsareni da ido…. Kusa da ita na matsa na duƙa ƙasa² nace matsayin kura daban amfanin labule sirri , huɗɗakir da Babana daban nima tawa dake daban , Murmushi tayi tare da kallon Amisty tace Amina kuma tsaf ta kira sunan Hafsa , tace ke kuma Sultana ? Nace sosai suma mu’amular ki dasu daban nima har yanzu nawa daban da nasu….. Kallon Babana tayi shi kuma yayi murmushi tare da cewa mijinki ya dawo ne ? Miji kuma ? 😳 wane irin miji na tambaya a bayyane , kallona Mamy tayi tare da cewa ya dawo ya koma ta ƙarasa maganar tana murmushi , Babana yace sai kuma yaushe zai dawo ? Har yanzu ni take kallo tace harsai na kirashi…. ! Dama kina da aure ne ? Na tambayeta tace Eh amma auren jeka nayi ka kawai idan yazo miji idan baizo ba sauka lafiya , ƙara duƙawa nayi nace ina kika san Amisty da Hafsa ? Wurin Babanki na sansu , Babana kuma kamar ya ….? Dariya tayi tare da cewa amfanin labule sirri yanzun nan kika faɗa Sultana , saboda haka a sake labulen muje ciki inji neman da kike min , Amisty tace Aunty Mamy amana don Allah , cikin rashin fahimta na kalli Amisty nace amanar uwarki …. Dariya Mamy tay tare da cewa ai kinsan ba haka nake ba , kowa da wurinshi , Murmushi nayi na nuna mata da “yan yatsuna biyu manuni da mai bi mishi 🤞🏻 kamar ina datsa abu nace kema …? { lesbian } Tace ina yaran wata ƙawata ne , nace baƙar magana kika faɗamin kenan kikace wurin Babana kika sansu ko ? Tace wallahi tare da Babanki nake ganensu kullum rana , Kallon idonta nayi tare da cewa kuma fa da gaske kike ba ƙarya kika faɗa ba , tou amma idan na gano akwai wani abu tsakaninsu da Babana tabbas zaune da tsaye bata ƙare ba , murmushi Mamy tayi tare da cewa ki kiyayi Binna duk macen da kika ga tana manneshi ki mata uziri idan ya gaji da kanshi zai wulaƙansu wallahi babu asiri ba komai idan dai kika faɗa tarkonshi fitarki sai Allah , matan yanzu da kansu suke bibiyarshi , kuma duk mutanen da kika sa nayi musu vidio kwanaki kinsan ko su wayen Babanki ne ? Nace sai kin faɗa , jinjina kanta tayi tare da cewa gaba zaki sani amma Allah yasa dai wani abu bai shiga tsakaninki da Baban Hafsa ba , ni babu abinda ya taɓa haɗani dashi saidai munayi waya ana maganganu dai irin na gyaran kasuwa , so ɗaya kawai ya taɓa rungumeni ya bani cake a bakin partyn birthday ina , Mamy tace gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA…* Cikin rashin fahimta nace su waye ahali ɗayan ? Murmushi tayi tare da cewa wai dani da mijina shima neman matan bariki yakeyi , murmushi nayi nima dan ban taɓa daukar akwai wani abu ba , saidai tacemin da Baban Amisty da Baban Hafsa na fita hanyarsu tsohuwar motace su koda mai sai an tura , na gane karatunta kalami ne na matan bariki , Kallon inda su Amisty suke suna fira da Babana cikin tsantsar soyayya akwai soyayyar Babana mai zafi a cikin kwayar idon ko waccensu , sun tsareshi da ido daga gani sunajin daɗin kallonshi dan Babana yana kyau sosai gaskiya kuma ɗan gayu ne ƙirƙirar farko yana da aji kuma yanayin komai nasa cikin tsari da burgewa , tabbas saboda Babana su Amisty suka ƙyaleni amma da ba haka ba idan duk katsina dangina ne babu wanda ya isa ya kwaceni a hannun su Amisty… Cikin gida muka nufa da Mamy amma zuciyata tana tamin tariya akan maganar Mamy , _Gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA…*_ Juyawa naji kaina nayi kwalwata na zakuɗawa wasu abubuwa sunamin yawo a cikin kai da sauri na rufe idanuwana jikina ya fara kyarma lokaci guda zufa ta ketomin kaina da tunanin da nake dashi da wani sauran sani ya juye kwalwata ta sake toshewa , na sake tashi wata kidahuma ta karfi da yaji….. Gaba ɗaya saina manta maganar da nayi da Mamy nayi ² na tuno amma sai zuciyata tacemin bamuyi wata magana ba , duk yanda naso na tuno wallahi gaba ɗaya komai ya goce daga cikin kaina , amma ban manta na fitar da Babana waje ba kuma na riƙe nabar su Amisty kuma na tuna nayi waya da Dikko amma sauran maganganun sun ɓacemin , Ina ƙofar ɗaki tsaye Mamy ta miƙomin waya cewa ana kiranki , da sauri na ansa na ɗauka , An mata Dikko ya kirani a cikin wata irin murya yace meke damunki ne ? Ba komai na bashi ansa , yace karki min ƙarya meke damunki ne ? Tunani na fara yi , sassauta murya yayi yace me kikeyi yanzu ? Ba komai , kina yanayin tsayuwa ko zama ? Nace tsaye nake , An mata zaki iya faɗamin ko wane iri ne Dikko ? Shiru nayi ina tunani , yace tuna ² An matana , har yanzu kaina juyawa yakeyi , yace kin tuno ko wane iri ne Dikko ko ? Wallahi Dikkon ma ya ɓacemin , An mata tsaya kiji kin tuna nine mukayi fada dake har kika mareni , kin tuna ? Eh na ganeka , amma me yasa kamin wannan bayanin ne ? Murmushi yayi tare da cewa kawai mafarki nayi wai kin manta dani shine nayi sauri na tashi a baccin na kiraki dan Allah kimin adalici karki manta dani kinji An mata , nace tou yawwa An matana….. Muah yai sumbata , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya na kashe wayar…. Ɗaki na shiga na ɗauko wayar budurwar Dikko ina zama kusa da Mamy nace ciro layin ciki ki saka a wayar nan….. 27/09/2019*JAMILA MUSA….* 💅🏻Download Kwarata Littafi Na Ɗaya Complete Hausa Novel