kuruciya complete hausa novel
kuruciya complete hausa novel
‘Rayuwa sirrice iya magana Baiwace, Hikima Jigo ce Hankali ma’auni ne Hak’uri Gurbi ne, Fushi Kuma Dana sani ne. Kowa kagani Yanada rana, Zama na kowa Yawan Fushi Bana bane, Duk rintsi ka Kyauta_ta wa Mahaifan ka Zasuji Dadi, Duk wanda ya iya zama da mutane ko a ina zakagan shi daban Na.
‘‘Ruwa Ake zubgawa kamar da bakin k’warya, yara subiyu mace Da namiji kyawa_wa Macen tafi namijin itace rik’e da Leda ta rufe musu jikin su Kafafuwan su ko takalmi babu.
Bayan ruwa ya dauke Ta bude Su, tace ‘‘Ismail” Yaya naga kayi shiru maiya same ka ya girgiza kai tace Haba Kayi magana mana kodai yunwa kake ji yayi murmushi ta girgiza kai, tayi murmushi tace To Ga ragowar Abunda yake jikina Jirani bari na siyu maka Kosai Kaji?.
Ya girgiza kai yace to yaya ta tashi ta ruga da gudu Ta tafi gurin wata Mata mai tuyar ‘‘KOSAI” ta tsaya A gefe ta mik’a kudinta matar Tace Koma gefe zan Sakamiki karki kashe min kasuwa Tace To ta koma gefe tana ta kar_kar wa rawar d’ari, Tana kallo tana ta sallamar mutane Chan ta saka mata A takar da tace zoki karba, Ta mik’a mata ta karba ta ce na gode, ta ruga da gudu, Mata mai tuyar k’osan ita da kanta ta ce Allah sarki Gata kya_kyawa Ga kyan hali Ban kyauta mata ba, ta tsallako titi da sauri.
Ta Kari so gun k’anin ta harya fara bacci tace ‘‘Isma’il” ya bude ido tace ga kosan bayawa kaji Ya k’arba tana kallon shi ya raba k’osan biyu Dama guda hudu ne, yace Yaya ganaki nima ganawa tace A’a kaci nibana jin yunwa kaji?, yace to kici d’aya ta dauki guda d’aya ta ci sauran ra gowar ‘‘isma’il” ya cinye sauran.
Yace Yaya nikam yaushe Baba zaizo nam ya dauke mu ne? Tayi murmushi tace Ai baba da mama suntafi gurin da ba’a dawowa Sai dai muyi musu A’du’a kaji ‘‘ISMA’IL” yace to yaya Tace tashi Mutafi kaji Yace to ta rik’e hanun sa Sukaci gaba da tafiya k’afar su ko takalmi babu Sunacikin Tafiya Wata mata ta yiyo siyayya a kasuwa ta gansu ta tsayar dasu taje ta nema musu kaya da takalma ta basu tace maza kukoma gida kukoma makaranta kudena yawo Akan titi kunji, Macen ta ce to Suka saka kayan gwanin burgewa ‘‘ISMA’IL” yace Yaya kayan nam sun miki kyau, tayi murmushi Tace Kai ko ismail surutun ka yayi yawa Yayi dariya ta ja shi suka cigaba da tafiyar su idan ka gan su Kamar yan biyu.
Suna cikin tafiya Sai ga motar Sojoji tazo wucewa Ta gefen su isma’il yana ganin su ya fizge daga hanun yayar sa Birki Aka taka Kowa dayake gurin yagama zata An taka yaron Wani sojane, captin 3 sters, yafito daga motar Isma’il ya nufi gunda yake, Da gudu Yace Soja.
Capting din sojannam Yayi mamaki sosai yayi murmushi yace Kai K’anina bakajin Magana ko?.
“ISMAIL” ya dafa kafadar sa yace Nima ina son soja, Yace To fa kanason soja Yace A yayi murmushi yace To kabari Sai ka girma zan zo na dauke ka da kaina kaji ko ismail yace To ya juya yayi tafiyar sa Yana zuwa gun yayar sa harta d’aga hanu zata mare shi, sai sojan ya daka mata tsawa yace Zo nam ta taho yace Karki taba shi kinji Tace Yaya baya jine.
Captin na sojannam yace Yana son soja Inane Gidan ku tayi shiru, Abunka da yaro yace ta ho kusa dashi yace Yaya itace take min komai Bamuda kowa.
Sojannam yayi shiru Yace Ina iyayen ku suke tace Gabad’ayan su sun rasu Kuma bamuda kowa Sojan nam yace A’a tana hawaye yace zaku bini mutafi tare tayi shiru, ‘‘ISM’IL” yace yaya zamuje gida ne, Tausayin ismail ne yasata tace A ya saka su A mota Yatafi dasu.
Tafiya suke yana tamabayar su zasu iya gane Garin su macen tace A’a yace Allah sarki, Karkuda mu Zan Aje ku A guna Kaikuma zan saka A makaranta Bakace kanason Ai kin soja ba?.
Ya na isowa Gida ya faka motar sa Awaje Ya shiga yna rik’e da hannayen su, yayi sallamah Ta amsa Yana shiga dasu Ta bata rai, Yace, ‘‘Khadija” ta amsa Yace Zomana zamu dan tattauna dake tace toh ta taho ta zauna Yace khadija Wa dan nam yaran Inason Ki rik’e mini su marayu ne basuda kuwa zasu zauna Anam tashi tayi tace Bazai taba yuwuwa ba nazama baiwar su Kaje chan dasu amma nikam karkayi tinanin Zan lura dasu kanaji ko?.
Ya kalleta yace marayune fa, ta tintsire dadariya tace, A’a “ya”yan hauwai niya ne su karshen marai ci Ya daka mata tsawa tace A’a kazaba kawai koni kosu?.
Rek’e kai yayi yace Shikenam ‘‘Amarya” kisani fa A idon su kike furta wa ‘yan nam munanam magan ganun ta yi tsaki, tace to sai me ta kallesu tace tabbas wahala zakusha Idan har Kunzabi zama agidannam, Cikin bacin rai ya fusata zai daketa yaji an k’an kame kamar sa yarinyar tace A’a yaya (Balaifin bane), Kabar mu kawai Daman munsaba da fadi tashi Ahaka ta kama hanun‘‘Isma’il” tace zo mutafi yace To yaya taja k’anin ta suka fice, daga gidan Ismail yace Yaya kowa baya son mu Yayi murmushi, Tace A’a ismail Kadaina damuwa Ai ganinam zan share maka hawayen ka kaji, yace to yaya!.
Ismail shekarun sa bakwai dawatani Ne Amma bai kai shekara takwas ba, ita kuma yayar tashi Shekarun ta tara ne tana cikin na shiga na goma.
Ahaka sukacigaba da rayuwar su, Duk Dan Abunda wani Daga cikin su yasamu Baya ci sai ya ragewa d’an uwan sa Abun tausayi! Har Ismail ya cika shekara 12 da haihuwa, ita kuma Addar tashi Ta cika shikara 15 da hai huwa.
Ismail Abunda yake yafara Damun Yayar tashi, Watarana Suna zaune Ismail yace Yaya tace na’am ismail Meyasa bakaji Nekam Yakamata Ka fara nituwa Yayi dariya yace yaya kenam Ai ni Zan iya komai dan ganin ki cikin farin ciki, Bazan juri ganin Kina cikin damuwaba tayi murmushi tace Haba Kai kuwa Ni ai yanzu Abunda kake ne Bana so naji labarin Kwanaki Kaje kayi fada dawani Daya daga cikin Abokan ai kina kaga dan wankin nam danake agidan hajiya Ai yana rufa mana asiri, Ahaka mukeci muke sha Kadaina Rikici da muta Idan harkana ganina cikin farinciki Yace Shikenam Addata nadaina, Tace yauwa daman inaso Zan maka rijister yakamata kashiga makaran ta Ya juya ya kalli gefe yace A’a ni yaya bana so, Ta lallabeshi sannam yace to tace To zan koma nacigaba da aikin da Tajuya zata tafi, Yace Yaya kibani Kudi yunwa nakeji Ta biyu shi da gudu yace ya ranta da gudu Ya yi tafiyar sa.
Tana shiga cikin gida ta tatar da hajiya Tana ganin ta tace, ‘‘AISHA” kinsam akwai aiyuka da yawa a gaban ki kika tafi shashan cinki ko?.
Tace A a Hajiya Daman Ismail naje na duba kwana biyu banaganin sa tace to daga yau duk abunda zakiyi sai da sanini kinji tace to Hajiya Ta tashi ta ta kinkimo dilar wanki, Ta fara tafito Cikin rana tanata Wanki Gaba d’aya ta jike jagab Da gumi Tanata wankin Ta jitayi Anyi Sallamah ta Amsa Wani Matashin saurayi ne ya shigo, Sanye sa wa’yan masu kyan gaske, har wani shek’i suke, Yazo yawuce ta kusa da zainaba, Ta durk’usa ta ce sannu da zuwa ya bita da kallo yace yauwa.
Yaja Jakarsa yashige cikin gida yanazuwa, Yace mama ta fito Tace A’a An samu hutu kenam yace A mama yace mama nikam Wacece A waje kitake miki wanki, tayi tsaki tace maza kaje Ka aje kayanka Kahuta, kaji yace to mama, Ya tafi Amma hankalin sa gabaday’a nakan ‘‘AISHA”, Yanazuwa daya aje kayan sa ya zagayo ta baya yataho yace da ita sunnu cikin rawar jiki tace yauwa, Yace Maiya faru nagan ki A tsorace tace A’a bakomai, yace yaya sunam ki?.
Tace ‘‘Aisha” yace Gaskiya zanyiwa mama magana a na rage miki Aiki za’a nemo mai tayaki, ya sa hanu ya fara wankin shima bai wuce kala biyu ya wankeba yace kai Aisha gaskiya naggaji Gaskiya kina k’ok’ari sosai Allah sarki dazan iya dana taya ki, Tace ba komai Ka tafi kar hajiya tazo nam tasa meka Kaji, yace A’a zan tayaki hira Zuwa kigama wankin kinyi k’ok’ari sosai ai tayi murmushi, tana cikin wankin Tafara jin hajijiya tace wallahi Hajijiya ma nakeji, Ta nemi gu ta zauna take ta fara gyan gyadi, Bacci ya fara daukar ta shikuma tashi yacigaba da shan ya mata wa ‘yan da ta wanke.
Hajiya ta fito ta rik’e baki Ta dau ko ruwa a bokati Ta shek’a mata take ta farka daga baccin da take, tace Ok dan nawa kika mayar Bawan ki ko?.
Tace A’a hajiya kiyi hakuri, Yana tahowa yace haba mama kina tausaya mata Aikin yamata yawa ta hararre shi Yasan bacin ranta ya sshige cikin gida. ta taho da dinga rankwashin ‘‘Aisha” tanacewa kekam Ba naga alama koranki zanyi daga gidan nam Ta kukkun bura mata fuska.
Ta window ya lek’o ya girgiza kai yace gaskiya mama bata kyau tawa, Tana juyowa suka hada ido, Tace ‘‘HASSAN” bakajin magana ta ko, Ya koma ciki Ta cigaba da wanki, Ta kammala baki daya, Ta koma gefe ta zauna, Tayi tagumi! Awannam rana hajiya Ko lomar Abinci D’aya bata bataba, ‘‘HASSAN” daya fahimci haka ya Raba Abincin sa gida biyu A plate Ya taho tana zaune, Yace Aisha tace na’am ta share hawayen Fuskar ta yace Kiyi hak’uri kinji?.
Ya mik’a mata Abin ci Taci rabi Ta rage Yace kicin ye mana, duka tace A’a yace saboda me to naga a bin in madam me?.
Tace Inada k’ani Sunam shi, ‘‘ISMA’IL” shi naragewa Yakalleta yace Allah sarki! Sunacikin maganar Sai tace Ana buga k’ofa tace to gashinam Ma ya zo tatashi da sauri, Ta bude K’ofa Tace gashi bayawa Abincin Yau take yaci ya cinye Abincin Yana daga kai ya kalleta yaga gaba d’aya fuskar ta a kuk_kun bure!.
Yace Yaya Mai ya same ki A fuska?.
Ta Shafa fusrkar tace ba komai, kawai nad’an buge ne, Yayi murmushi yace Adda kenam Wannam Ai dukane, Bazan iya jurar ganin Abun da Ake miki A gidan nam Ba, Yaya Insha Allah zan saya mana gida namu Na kan mu, Ta kalleshi ta yi murmushi tace Ismail kenam Tayaya zaka saya mana gida Bayan Bakada sana’a Nikam banga ta inda zaka saya mana ba?.
Yace Yaya daman Akwai Wani Abokina Dayace Zamuna tafiya Aiki tare dashi, Gashi Ma yasaya mini waya harda Layi, Ya mik’omata yace gashi Ki rik’e ta In munje chan zanna k’iran ki insha Allah Zan saya mana gida kinji yaya ta tace to bazan hanaka ba Amma ka kiyaye, Sukayi bankwana ya yi tafiyar Sa.
Coming Soon, Yananam Tafe.
Page 3 – 4 of kuruciya complete hausa novel
Sukayi bankwana ya yi tafiyar Shi, Har ta juya tafara k’ok’arin Rufe (Gate), ya juyo ta sake bude Masa tace Yaya naga kadawo ismail? Ya girgiza kai Yace Yaya jinake Kamar Karna tafi Na barki Tayi murmushi, tace Haba d’an k’anina Insha allah Zakayi Nasara Kokatafi Ai gawaya Zamu na gaisawa Karkadamu kaji ko?.
Yace To yaya ‘‘Hassan” ya taho Yana zuwa Yace, wannam shine k’anin Naki Tace A yace Yaya kake?, ‘‘Ismail” yace lafiya k’alau yace Dan Allah ga yayata Kadinga kulamin da ita Har zuwa lokacin Da allah yayi Tawowa ta, Yayi murmushi yace ba komai Allah yabada sa’a ismail yace Amin yajuya zai tafi, ‘‘AISHA” ta dakatar dashi ta ciro wasu ‘yan kudade a ak’ulle Gefen (ZANINTA),ta mik’ama ismail tace Gawannam zasu yima amfani ko a hanya kaga abunda kake so sai ka saya kace, yayi murmushi hawaye ne suka fara zubuwa daga idon sa, Ta saka Hanun ta ta goge masa, tace Bana son ganin Wannam hawayen Yimaza katafi kaji, yace to Shikenam tace katafi nace yace A’a saidai ku juya bayan ki muddin ina ganin fuskar ki bazan iya tafiya ba.
Tayi murmushi ta juya baya sannam yayi tafiyar shi, ta juyo ta duba taga har yayi nisa, saita maida k’ofar ta rufe ‘‘Hasan” Irin yadda yaga Suke Ma’a malar su ta burgeshi, yace Aisha wannam Abun naku najima banga shak’uwa irin wanna ba tayi murmushi, tace Ai koda kaine dole kasa d’an uwanka wanda duk fadin duniyar nam bakada kowa sai shi ‘‘HASAN” yace hakane kinyi gaskiya.
Tace hasan kagadai abunda ya faru dazu karhajiya tazo tasake tarar dakai Anam kaga kayan nam yanzu Sun kusam bushewa tana tattabasu tace Ai harma sungama bushewa ta tattaro su ta Nufi d’akin ta Ta rubesu kan latsatsiyar katafar ta, Shikuma ‘‘HASSAN” yayi ficewar sa yawo gurin Abokan shi.
Ta taho k’ofar hajiya tayi Sallamah, ko Amsawa batayi ba Cikin fushi ta hantare ta, tace Uwar me kikazo yi nam kuma yanzu?, cikin rawar jiki ‘‘AISHA” tace hajiya daman kayan naki ne Sun bushe ‘‘DUTSEN GUGA” nazo k’arba Tace Ok to shigo kizo kidauka gashi nam A gefen (TV) ‘‘AISHA” ta shigo kanta a sunkuye ta dauko dutsen, Ta juya kenam k’afar ta ta harde ta taho yif! Sai kan k’afar hajiya Ta tashi dasauri tace Hajiya kiyi Hak’uri Ta ciza baki Ta saka k’afa ta harbeta ta Kai mata mari, ‘‘AISHA” tana durkushe Harta rufe idon ta sai taji marin bai iso fuskar taba tana bude idonta bawanda ta gani face ‘‘HASSAN” yace mama kiyi hak’uri yace ‘‘AISHA” Tashi kije tatashi tayi tafiyar ta.
‘‘HASSAN” yabawa hajiya hak’uri sannam ta hak’ura, ya taho ta bayan ‘‘AISHA” a hankali tana guga.
Ya sauna, tana k’ok’arin Jona (DUTSEN), a soket Tana share hawayen Fuskar ta tace Ba laifin mu bane, Allah yaka yaso ya ganmu, ‘‘HASAN” yayi magana yace Kik’ara hak’uri da hajiya kinji, Ta juyo tayi murmushi tace Bakomai, Yana Gyara mata kayan ita kuma tana ta goge su Sukacigaba Da tad’i tamkar Ba itaba, Harta gama Goge kayan Baki Dayan Su, Ta ninke su ta tafi Bangaren Hajiya tayi Sallamah hajiya tana harara ta Ta jera kayan Kowanne A inda yadace.
Ta juya zata fice hajiya tace Duk abunda yasameni Kisani bazan barkiba, Batace komai ba ta fito Tana zaune wayar Ta tafara ringin, tana dauka ‘‘Tace ismail” yace na’am Tace dafatan kun kama hanya ismail yace A’a tukunna tafiyar dazamuyi Sai dare saboda Hanyar Da rana ana yawan tare mutane, Tace to Indai kasan Da matsala kawai kadawo yayi dariya yace haba Yaya ta Ai insha allah Sai nacika burina, Tace to Allah ya shige mana gaba, Yace Amin Ya kashe wayar Sa.
Washe gari;
DA safe, ‘‘Aisha” ta na zaune Tana Goge_Gage A falon hajiya, Ta goge komai ya fita tass, Tana murna Wata ya k’are zata Samu Albashi Tana gamawa Ta zo gefen Hajiya tatsugu na, Hajiya ta kalleta tace kin gama Aikin naki ne? Tace A nakammala komai Hajiya ta bude jakar ta ta ciro kudi, Ta lissafa su ta raba biyu ta mik’awa ‘‘Aisha” ita kuma ka karba ta lissafa Tace Hajiya dubu Bakwai ne, (7000), Hararar tayi tace A haka naga daman Baki, naraba kudin ki biyu (2), dashi nake zuwa gun doctor Ko kinada wata magana ne, ‘‘AISHA” ta girgiza kai tace A’a hajiya, Ta nuna mata k’ofa da yatsar ta tace Kifice min Daga Dakin nam, kafin ranki ya baci.
‘‘AISHA” Ta tashi ta yi fitowar ta waje Taji zafin Abunda hajiya ta mata ta daga kanta sama tana hawaye tace Bakomai, Nadan Wani lokaci ne insha Allah, ji tayi Ta bayan ta Hajiya tace zagina ma kike ko ‘‘AISHA” dan bakida mutumci ko?.
‘‘idon ta ya cic_ciko da k’walla tace A’a hajiya Kiyi hak’uri Ta ciza baki hajiya tace Allah yasoki, Dana babbalaki Agidannam Naga kamar ‘‘HASSAN” ne yake D’aure miki gindi ko? To shima shima baifi k’arfin na gindaya mar dokaba, tafi kibani gu kar Raina yabaci.
Tafito tana share Hawayen Fuskar ta,jeta Gindin ‘‘Fanfon ruwa” ta kunna yana zuba shaaa… Ta sa fuskar ta ta kama wankewa, ‘‘HASSAN” ne yashigo cikin gida Yana ta dariya, Harya kwanta k’asa ‘‘Aisha” ta tsaya kallon shi Ta kashe Fan fon tace To lafiya kai kuma nagan ka kana dariya?.
Ya ce lafiya, ‘‘AISHA” wata ce Taci kwalliya tana tafiya Kawai wani Mai mota ya wanketa da ruwan kwata, Kawai ta fashe da kuka nayi nayi Na danne dariyar amma hakan ya k’agara gaskiya taban tausayi.
‘‘AISHA” tace oh! Shine kake mata dariya yatashi kenam San tsi ya debeshi ya zame, Yafad’i kasa fuskar sa duk Toka, kamar dodo ‘‘Aisha” tatasam lokacin data tintsire da dariya ba, Shima ya kama dariya Sai kuma ‘‘AISHA” taji kunya ta juya tayi tafiyar ta.
‘‘HASSAN” yashiga cikin ‘‘GIDA” yana ta dariya Hajiya tafito tace Hassan mai zangani Haka ta tintsire dadariya Shigewa Fanin sa, yayi ya Watsa ruwa Yafito, yayi Dresing na kayan wasan kwallo, Yafito Yace Mama sai na dawo tace to Adawo lafiya, Ya fito wajen gida da kwallon sa yana dan bubbugawa.
Dukan tambalar yayi da k’arfi, ‘‘AISHA” ta shawo kwana kenam sai A fuskar ta Gau! Ta tsala wani irin I hu ta fadi, K’asa hancin ta ya fara zubda jini, Taken Hankalin ‘‘HASSAN” ya tashi ya taho da gudu, ya dagata Jini na zuba ta hancinta, Tana murmushi, Ta tashi Tana tafiya Ta yanki jiki tafadi, K’asa.
‘‘HAJIYA” tafito dasauri ta ce Kai ‘‘HASSAN” meya faruda ‘‘AISHA” tazo ta d’aga hanunta ta tab’a ta ko motsi batayi, ida nun ‘‘HASAN” suka k’ara girma suka zazzaro, Yace Mama kodai mutuwa tayi ne kam?.
Too been continue….
*BISMILLAHIRRAH MANURRAHIM*
K’irk’irar_ren labari ne, a kan Wasu k’ananam yara guda biyu ‘‘Marayu”, akwai Darusa Acikin sa, Sun tashi basuda kowa basusan kowaba Sannam Bawanda Yake kuladasu Ta dalilin haka Aka samu akasi kash!.
Page 5 – 6 kuruciya complete hausa novel
ida nun ‘‘HASAN” suka k’ara girma suka zazzaro, Yace Mama kodai mutuwa tayi ne kam?.
Dora ha nun ta tayi Akai, Tace A’a suma tayi, ‘‘Hassan” Hankalin sa gaba d’aya yatashi, Yace haba mama Yanzu Mukaita Asibiti Mana, ta ha rare shi, Tayi tsaki, tace Ta mutu mana, Daman fa batada kowa! ‘‘Tsayawa kan lonta yayi, yace Mama kenam, Koda batada kowa ai gamunam Baikamata muna wulakanta ‘‘AISHA” ba k’anin ta kafin yatafi, yacemin Murik’e masa ita Amana, mama karkiyi haka tatashi, tace Ok! Na fahimceka Gabadaya Bakada tinani, So kake Tasamana guba ta kashe mu gaba d’ayan mu ta mallake mana dukiyar ko?.
Yayi murmushi, Ya tafi bakin Fanfo, ya kunna ya taro ruwa a hanun sa ya yayyafa mata afuska, Hanun ta ya fara motsi, Daga bisani, ta bude idon ta sai, ta kama hawaye, Ganin ta farfad’o ‘‘HASSAN” yaji dadi sosai, yace Aisha sannu ta girgiza kai, ta mik’e ta zauna, hajiya kallonta tayi tace Dakin yi niyyar tafka mana sharri ko, Ace mumuka kasheki, Zakiji da munafurcin ki, tayi tsaki Tayi komawar ta cikin gida.
‘‘takalli hasan tace Hassan hajiya Batason zamana agidannam kaikadai ne kake nunamin kulawa agidannam, nagode sosai ya girgiza kai yace A’a Aisha kiyi hak’uri da abunda mama take miki, insha allah komai zai wuce.
Wayar hassan tafara ringin, Yana dubawa yaga, ‘‘SARDAUNA” yayi murmushi yadaga yace saudauna, Kunga bansamu halattar ball ba ko? Yace A kasan wannam wasan dazamuyi wasa ne mai mahimmanci, idan bakazoba Komai zai iya faruwa Bamutaba zuwa wannam matakin na (final) ba ka k’okarta kazo Dan allah, Yayi murmushi ya kalli ‘‘AISHA” ta kallishi itama tace wannam wasan nada mahimmanci, kadai ji Abunda sardauna ya fada Yakamata ka k’okarta kaje ka hassan?.
Ya kalleta yace A’a yanzudai kizo nakaiki karamin Asibiti na bayan mu abaki maganai, na hak’ura da wasan namu, ta kalleshi tace A’a jeka inyaso inkadawo ka siyo min maganin bakomai Tatashi ta zauna, taje bakin fanfo ta cika bokati daruwa Tace Dan allah katafi Inaso kuci kofin nam Idan har kukaci Nikaina zanyi farinciki sodai Saikadawo.
‘‘HASSAN” yayi mamaki sosai yayi murmushi, Ya shiga ya fito da mashin, d’in sa yahau, Betsaya ko inaba sai, Babban filin kwallon ‘‘GARIN MAIDUGURI” yana zuwa yasamu kocin su zaune yatabashi, Yamasa magana yna ganin ‘‘HASSAN” yace haba kazo a k’urerren lokaci gashi harsun saka mana kwallo 3 a ragar mu, Amma bakomai ayayi chanji, Hassan nashiga, Ya zura kwallo daya a ragar Abokan karawar tasu, daga bisani ya kara tabiyu, Aka tafi hutun tak’aitaccen lokaci na minti shabiyar, Aka dawo ‘‘HASSAN” ya kara samusu kallo a ragar su yazamana ana kunen doki,.3=3 uku da uku.
Saura minti Biyu A hura tashi, ‘‘HASSAN” ya k’ara saka musu kwallo ta hudu, Fili yacika da masu murna, Aka tashi Hassan aka masa kyauta ta musamman, Ya natahowa yanata murna, Yanazuwa ya wuce Wani babban asibiti, ya karbawa ‘‘AISHA” ma gun_gu na.
Ya nadawowa gida ya tarar da ‘‘Aisha” zaune tana kuka, Yayi shiru ya taho da sauri, yace Aisha maiyafaru Ta nuna masa hanun ta Ta k’one gun yayi yajuya yasiyo mata wani maganin, ya dawo tamika masa hanunta ya saka mata magani, Ya bare mata magun gunam ya kuma diba mata ruwa yabata tasha.
Yace Agarin yaya naga hanun ki ya kone tace Nazo girkine Abincin ya zubemin A hanu, ‘‘HASSAN” ya kalleta tace yaya ina fatan kunyi Nasara kam ko?.
Ya gyara zama yace Tabbas munyi nasara ‘‘AISHA” tace to alhamdulillah, Yaciro Wani kyauta na musamman da aka bashi, Yace gashi na baki kyauta, tace A’a nikam ai ba abunda zai min koda na karbi wanna Abun nagode.
Maida Kayan shi yayi Aljihu, Yana juyawa Suka had’a ido da mahaifiyar sa, tace hassan inason magana dakai, Yace to mama Yana zuwa tace hassan Nayanke Shawarar Goben nam zaka koma makaranta, Yace Haba mama saura 2weeks fa, Take yaji mari tasssss a fuskar, yasa hanu yana shafa gurin yace to mama naji amma saboda me bazaki bari na k’ara miki koda 1 week bane?.
Tace banaso banason ganinka tareda wannam yarinyar tukunna ma kai bakada tinani ne, Naga tanason rabani dakai ne, ‘‘HASSAN” yace to mama naga batada kowa ne shiyasa nakeson tazauna A gidan nam Zatana miki duk wasu ayyuka muddin muka bar ‘‘AISHA” mama bazamu samu madadin ta ba, kiyi tinani.
Sallamah sukaji, Tace to kaje ka lek’omin Kaga suwaye ne, ‘‘HASSAN” na sako kai ya hanngi wata Hadaddiyar ‘‘YARINYA” tace sannu yace yauwa Tace ‘‘HASSAN” ko? Yace A ta miko masa jaka tace Maza kashiga min da ita kafin nanuna maka fushi na, yayi murmushi yadauka suna shigowa Tatafi da gudu, Ta rungumi hajiya Tace yaukam dai gani nazo miki Hajiya tayi murmushi, tace Yaya hanya Tace lafiya k’alau ta haye kujera ta zauna, ‘‘HASSAN” na kallonta yace mama wannam fa wacece ta kalli hasan tace ‘yar uwar kace tazo nam ne ma saboda kai, Hassan yace saboda ni kuma mama to ai ni bansan da zuwanta ba, zaraf tasa baki tace A nazo ko dawata magana ce, ya girgiza kai yace A’a.
Tace Brother ‘‘HASSAN” inason zamuyi yawo da kai idan Allah ya kaimu gobe, Yace tab to ai kin makara nidazan koma school gobe, tace tab! Ai dasauran kwanaki, Ba inda zaka koma yace to fa kekike da iko dani ko mama, yace to mama ce tace zan koma, tace mama wai haka akayi tace A amma andaga tinda Bak’uwa tazo musamman dakai.
‘‘HASSAN” ya ce to ni kinganni banida kudi, tace to ai dakudina nazo dan haka Duk abunda nake buk’ata shi za’a yi da kudina yayi murmushi yace to Allah ya kaimu goben Yayi tafiyar sa yayi Alwala yatafi masallaci, Yaje yayi sallah yadawo Bayan Anyi sallar isha’i Sun hadu za’a ci Abinci yace Au mama ni kirabamin nawa biyu, Zan bawa ‘‘AISHA” tace to fa bayaddaba yace Mama kidinga tausaya mata, mana ta k’one Ahanunta bazata iya girkiba pls mama, Bak’uwar dasukayi ne ta ce A’a mama ya san mata Yadibi Abincin yatafi ya buga mata k’ofa tana budewa ya mik’a mata taja k’ofar ta ta rufe, yadawo suka ci abincin su, aka kunna kallo kowa daya gaji yatafi fanin sa washe gari.
DA safe misalin k’arfe 10:30 am nasafe.
‘‘HASSAN” ya fesha wanka, ya saka turare na musamman, Ya fito da babur din shi, ‘‘AISHA” tafito ta ga yana goge ta tace Inazuwa yau koma hassan?.
Yace Zani Wani guri ne Wallahi, Tace Allah yatsare, Tayi komawar ta tacigaba da Aikace_aikacen goge_gogen ta, Ta, wayar ta ne, tafara ringin Tana dubawa, Taga ‘‘ISMA’IL” ne cikin fara’a tadau wayar suka gaisa, Yace Yaya Alhamdulillah Komai sun Fara Dafiya daidai, Ta daga hanu ‘‘AISHA” tace Alhamdulillah.
Hajiya ne take tahowa tace zankiraka anjima yace to Takashe, wayar Hajiya nazuwa tace Au Aiki zaki tsaya yi ko Waya, Wannam yarinyar kunen ki na k’ashi ne ko?.
‘‘AISHA” tace A’a hajiya cikin zafin nama tacigaba da goge gogen ta, Bak’uwar budurwar nam ce ta fito tana tafiya kamar bazata taka k’asa ba, ‘‘AISHA” ta bita da kallo tazo ta wuce ta kusa da ita ‘‘AISHA” tace sannu ta sauk’e Tabarun fuskar ta tayi tsaki, tace Ke ni Sa’ar kice Ni bana son Haka, ‘‘AISHA” tace Allah yabaki hak’uri, Laifi nane, harta juya zata tafi ta dawo tace ke ta kai hanu Ta mare ta tass, ‘‘A idon hassan, yataho A fusace Ya kai hanu Zai Mare ta ya fasa yace Meyasa zaki Mare ta.
Budan bakinta tace Oh! Haba dan na mare ta wani Abune Nifa Ban son raini ne, Yayi murmushi, Yace ‘‘AISHA” kiyi hak’uri, tace Bakomai Yadawo kanta yace Kibata hak’uri, Tace Hmmm Ni Hakan bazai taba yuwuwa ba, ‘‘HASSAN” yace to nikuma idan baki Bata Hak’uri ba nafasa fita dake ‘‘AISHA” tace Aa hassan Karkayi haka bakomai, dan allah Kuyi tafiyar ku, Kaji Hassan, Ya fusata yace to kinci Albarkacin Tasa baki, natafi Idan kinga dama Kizo mutafi?.
Ranta ya baci, tace Dakata Hassan Dalilinka nazo gidan nam amma Abunda zaka sakamin dashi kenam A idon wannam k’azamar zaka ci mutuncina to tafiyar ma na fasa ta, ta juya taje Ta zauna Kan babbar wata kujerar( 3sitter), Tana ta ciza yatsa Hasan ya zauna gefe ya kunna kallo ‘‘AISHA” na gefe tana goge,gogen ta, Yasaka tashar (HAUSA) sun saka wani film yanacikin kallo.
Kawai yaji An zauna agefen sa Ta dau remote ta saka Music wak’ar ’‘koredo Bello” Takama mamin Ta koma gaban tv tacigaba da rawanta Gogan naka ko kallon ta beyiba, Ta matso sitin shi taci gaba da rawanta, ‘‘AISHA” data gama mofin ta yi tafiyar ta.
Tayita tik’ar rawar ta harta gaji ta wuce ta dauko drinks dinta ta bude tasha tasha ta k’oshi, Tace ‘‘HASSAN” rawar ya burgeka ko, ya kalleta yak’ara hade fuskar sa, tace Ai nasan ta burgeka, Ta zauna gefen shi tace dan uwana pls ka saurare ni dan Allah, Ya ce to ina sauraron ko, Tayi murmishi Tace nazo garin nam badan komai ba sai dan kai Hassan d’ina Yayi dariya yace hassan dinki kuma, Tace yes kwarai da gaske Ai mutu karaba Nidakai, Tashi yayi zunbur yace tab, Ni karatu ne Agabana kinji Danasan Zkizo. Da kuwa bazan dawo gidan nam nam kusa ba.
Ta yi murmushi, Tace Ai aikin gama yagama Ni banida wanda ya kwanta min A raina kaf duniyar na Face Mumtum, d’aya Ba kowa bane sai kai, Masoyi na ‘‘Tayi murmushi ta nuna shi da d’an yatsa, yace Tab! To ai kin makara Ni Inada wacce na keso, Tatashi tace Wht…. Tana girgiza kai tace Wacece Haka, Ai kuwa Ta tara wa kanta bala’i Inka isa kafada min ko wacece ita, Ta juya tasake juya tace Kakalleni sama da k’asa ba A yi macen dazata hada nema dani ba, ya yi murmushi yace to na yaushe kuma Ai aikin gama yagama.
Tsabar kishi Jikinta karkarwa ya fara yi, take Aljanunta suka tashi, Hankalin hassan yatashi Ya tafi da bibo ruwa a k’aramin kofi yayi adu’o’i Ya tafo mata A ruwa Ya fesa mata Take Ta zube Kan kujera Ta zauna, Tayi shiru Yazauna gefen ta yace sannu Tayi shiru batace komai ba, Hassan Tace ki dan kwanta ki huta, kinji ta kishi gide bacci ya dauke ta Shi kuma ya koma cikin d’akin sa ya zauna yayi shiru yayi ta gumi Abun tausayi !.
To bee continue……
Page 7 – 8 of kuruciya complete hausa novel
Tsabar kishi Jikinta karkarwa ya fara yi, take Aljanunta suka tashi, Hankalin hassan yatashi Ya tafi da bibo ruwa a k’aramin kofi yayi adu’o’i Ya tafo mata A ruwa Ya fesa mata Take Ta zube Kan kujera Ta zauna, Tayi shiru Yazauna gefen ta yace sannu Tayi shiru batace komai ba, Hassan yace ki dan kwanta ki huta, kinji ta kishi gide bacci ya dauke ta Shi kuma ya koma cikin d’akin sa ya zauna yayi shiru yayi ta gumi Abun tausayi !.
Sak’e_sak’e yake A cikin ‘‘ZUCIYAR SA” shin wannam yarinyar mai takeso danine kam?, A firgice Ya juya Boka k’ofar sa Akayi Yataso Ya bude, Yaga mahaifiyar sace, Tace ‘‘HASSAN” lafiya naga ‘yar uwar taka kabarta ita kadai A falo tana bacci, ya girgiza kai mama lafiya k’alau wallahi, Tace to Kazo daman inada magana dakai, cikin ladabi da biyayya yace to mama, Yabiyota abaya suna tafe Har suka k’ariso falo ta zauna shikuma na zauna ya durk’usa A gaban ta Yayi shiru, Ta ce to Kaganta nam yar uwar kace Dan kai tazo gidan nam dan haka ka kula da ita sosai, Ina fatan ka fahim ceni yace to mama, Sunacikin tadin su, tafar ka daga bacci tayi mik’a ta bude idon ta tace A mama yaushe kika dawo?.
‘‘HASAN” kuwa ya sunkuyar da kansa K’asa ta kallishi tace Marar gaskiya dole ka sunkuyar da kanka ai, Tatashi tayi shigiwar ta bayi tafesa wanka tafito tana kamshi.
Tace Mama Zan d’an fita nazaga gari, tunda yaya ‘‘HASSAN” yak’i yawo dani, Zafar yayi yace Allah yakiyaye Hanya, Tace Amin Ai kamin Komai dakace Allah yakiyaye Hanya, Mahaifiyar sa tayi murmushi tace to Kikula karkiyi Nisa fa kinga garin namu Balafiya sosai yanzu kinji ko?.
Tace to Mama, ta yi ficewar ta ta barsu agurin suna ta hirar su.
‘‘AISHA” kuma tana komawa bangaren ta tacika alk’awarin da tadauka ta kira numbar d’an uwanta, ‘”ISMA’L” tanashiga yace tab! Sai yanzu zaki k’irani Ko nayi fushi Tace a’a yi hak’uri ina sauraron ka bani labarin gurin Aikin naku?.
‘‘HASSAN” yace Ai alhamdulillah komai na tafiya yanzuhaka Nasamu alheri sosai, Zan turo miki da kudi, Tace A’a kabarshi kawai bana buk’ata kaidai shawarar dazan baka karage rigimar kannam Yace To shikenam Yaya Insha allah bazan baki kunya ba, Kota wace hanya indai zaki ji dadi koda ni zansha wahala bandamu ba tace a’a gaskiya kana ji da yayar kannam to Allah ya kiyaye min k’anina yace amin, Wani ne ya kwala masa k’ira kai hassan kazo mana kacigaba da aikin da kake yi yace to ganinam ina zuwa tace ana k’iran ka ko yace A tace to sai anjima ya tafi cikin sauri, yace Maigida Kayi hak’uri Nayi waya da gida ne.
Ya Kama kwale_kwale ya haye sukacigaba da tafiya, Har suka iso wani K’asur gumin daji, suka tsaya ya fito dawani k’aramin akwati yace gashi Kana zuwa kan wannam Dutsen ka jefa shi k’asa kayi maza_maza ka dawo kaji kam idan kuma ka bata lokaci duk abunda ya faru dakai to nifa baruwana.
‘‘HASSAN” yadauka yayi tafiya mai nisa yajefa akwatin Kamar yadda maigidan nashi ya umurcesa Ya juyo yana tafiya Sai ya hangi jikin wata bishiya kamar mutumne Yake d’aga masa hanu yace kai Karkuma naje Maigida yatafi yabar ni, Yace kai sainaje naga ko menene, Yatin karo gurin Sai yaga wata Kya_kyawar mace ce, Tana ganin shi tace Dan allah ka taimakeni na maka alkwarin Ko nawa kake buk’ata nikuma zan baka.
‘‘ISMA’IL” yayi shiru ta sake maimaita abunda take fad’a yace Naji Zan tai makeki amma saikin fadamin Dalilin Zuwan ki wannam dajin.
Tace naji zan fad’a maka amma ka tafi dani daganam idan har sukazo dagani harkai bawanda zasubari, Yace suwaye ne haka, tace Kaidai bakasan suba Amma kayi Abunda na umurceka, Yace to tashi mutafi Ta mik’e Sai ta fadi tace bazan iya ba sai ka talkafamin yataho tadafa kafadar sa, Ya cigaba da tafiya da ita yana zuwa dai_dai inda Maigidan shi yake, ya tarar ba kowa yace Shikenam kin ruguzamin lissafina nayiwa yaya ta Alk’awari Amma gashi zata daukeni Mak’ar yace Kuma duk kekika jawo, Tace nawa yake biyanka nizan biyaka fiye danashi idan har kafitar dani dawannam dajin, yace Ta ina zaki iya biyana tace Kai kam bana maka alk’awariba Yace to naji zakai zubanyamini kudin da suke biya na sau biyu tace A yace suna biyana Naira dubu d’aya ne duk Bayan kwana d’aya, Tace naci nikuma zan baka dubo goma duk Kwana d’aya, take ‘‘ISMA’IL” yace shikenam Namiki alk’awarin Zanyi iya ka k’ok’arina amma ina so kibani Labarin Abunda ya jawo zuwanki wannam dajin?, tayi murmushi tace Aikin kud’i zakayi Idan kudin bemakaba nizan k’ara maka sannam zanbaka labarin zuwana nam wajen Amma sai munbar yankin Dajin nam.
‘‘HASSAN” yace to Naji Amma nima bansam hanyar dazata bulle mana zuwa Inda kikeson zuwa ba, tayi shiru tace Gama ga Allah Kaodai mubar Gunnam, sukacigaba da tafiya sunyi Tafiya mai Nisan gaske wanda hassan ya lura yarinyar nam bata saba wahala ba gashi kafafunta duk sun Far_fashe da kyar take tafiya, Sunacikin tafiya Wanta iska mai k’arfin gaske ce take tin karo su hassan yace kidaga k’afa kafin iskar nam ta cin mana, tace toh suna tafiya tana yamutsa fuska, Har zuka iso Daidai wata k’atuwar bishiya wacce gefen ta akwai wani K’aramin kogo, Hassan yace dakata Barin duba mana nam kila ma pake A nam, tace to ta nemi gu tazauna Hassan yaciro wayar sa ya haska gurin daga bisani yasaka hanun sa yashare ciki tass ya karyo wasu itatuwa ya had’a Abun kwanciya guda d’aya da kuma na zama yataho gunta yace zamu iya fake wa, ta tashi ya tallafa mata Ta zauna kan gadon daya hada na karare Ta mik’e kafafun ta Hassan ya kalli k’afafuwan ta suna jini, Yace Sannu tace yauwa Ya hada itatuwa Ya dauko duwatsu guda biyu yayi ta gurzasu har saida yasamu wuta ta kama, Tayi mama kin hassan sosai, Suna cikin wannam yanayin ne Wata iska tazo ta tirnik’e sannam aka sake ruwa anyi Awanni Ana zabga ruwa, Har bacci Yadauketa, shikuma hassan yana zaune, Ahaka ya kwana cir da idon sa batare da ya rintsa ba.
Ta na tshi ta nemeshi, bata jishiba saita farajin takun sawu, tayi shiru Ganin mutum tayi yashigo Da Wani katon tsun_tsu a Hanun sa, Taga Abokin tafiyar ta ne sannam hankalinta ya kwanta Ta ce Ina kaje haka yace Abinci naje ne mo miki, Tayi murmushi, Ya fige Tsun_tsun tas..
Sannam Yaciro Wata wuk’a ya fede shi ya gyara ya sake hada wuta ya gasashi ya gasu sosai, Ya mik’a mata tace ai ni banacin naman nam, yayi murmushi yace To ya yaga naman biyu yasa abakinsa yanaci, yace mata kice mana Kar yunwa ta galabaitar dake, Bataso hakadai ta karba tafara ci dataji dadin naman tacinye tass ta koshi, Yace Ya sa hanun sa ya dibo mata ruwa tak’afa kai tashi yanazuwa yana dawowa harta koshi, Tace Na gode Yayi murmushi yace Ba komai, Yanzu zamutafi kokuma tace duk yanda kace, Yace Yanzu dai k’afar kinnam Barin nemo wani magani Yakama mu zauna anam har kidan samu sauk’i naga kafar taki duk ta farfashe, tace Karsuzo su samemu nake tsoro yace A a kikwantar da hankalin ki insha allah ba yadda za’a yi susame mu.
Ya ta shi ya fice ta dinga ballo ganyayen ”ya”yan itatuwa har kusan kala goma sha, Sannam ya taho dazu Yasamu wani itace yayita rarake sa har saidayiyi gurbi inda zaka zuba ruwa sannam yayita murza ganyayen har saita suka fitta ruwa yasa ta mik’e kafafun ta ya zuba mata ruwan tace wayyo allah akwai zafi yace Daman dole zakoji zafi allah yabaki lafiya.
Akwana na a tashi sukayi kwana hudu, Kafar ta ta dazo ragas kamar bata taba jin wani kunburi Ba, Tayi mamaki sosai, Tace Gobe in allah ya kaimu da rai da lafiya zamu bar nam gurin kaji, Yace to Ai ni sai yadda kikace, tayi murmushi ta e meyasa Kakeson tara kudi, ne kam?.
Yayi murmushi yace‘‘BALAIFIN MU BANE” dolece ta sa mu Sonake Zan ginawa yayata gida Tazauna itama kotasamu sawaba a rayuwar ta Tayi murmishi tace lallai Kanason yayar kannam zan so nima na ganta, Yace dagaske tace A yace to shikenam zan nuna miki ita, Tayi murmushi.
Washe Gari DA safe suka sake shiga cikin Daji Tsundum, suna cikin tafi sukaji wani wari Na dosusu, suka toshe hanci, suna k’arisowa suka tarar da gawar wakin mutanene Ankashesu Har sun rube, Hankalin ‘‘ISMA’IL” ya tashi, suka wuce gurin sunyi tafiya mai nisa sun zauna suna hutawa yace mata kai ni hankalina baitaba tashiba irin wannam yawan gawar wakin danagani an koshesu, to wana laifi sukayi haka dan allah kai Duniya abun tsoro ce?.
Murmushi tayi tace Hmm ai ni nasaba da hakan, Nima kaina bansam dalilin dakkoni wannam dajin ba, Haka suke kashe mutane ba gaira babu dalili, tafashe da kuka.
‘‘ISMA’IL” ya rarrashe ta yace Shin maiya kawo ki wannam dajin yakamata yau kam ki sanar dani kadam dagacikin labarin ki? gaskiya tace to shi kenam.
Nakasan ce ‘yar gata mahaifina mutum ne mai tarin Arzik’i yanada dukiya sosai, wacce shi kansa bai san adadin ta ba.
‘‘ISMA’IL” Yace allah sarki ina sauraron ki? Gaskiya Amma dai shikenam.
Tgirgiza kai tace, Natashi cikin gata Sannam mahaifina Bayason yaga Kana rena na gaba dakai, sannam kullum cikin taimakon talakawa yake, watara yana zaune Al’umma sukayi gangami sukace, Suna son yashiga harkar siyasa dan taimakon marar sa k’arfi, ‘‘TALAKAWA”yace A’a bazai shiga harkar siyasa ba saboda Siyasa tana zubar wa da mutum kimar sa da darajar sa, sannam kuma duk yanda kayi bazaka iyama mutane ba, Yak’ara dacewa tabbas dazan shiga siyasa watarana kuzaku fara zagina Ni kubarni banason shiga harkar siyasa, sukayi sukayi Yak’i Amincewa.
Bayan yadawo gida ya Zauna gani gashi ga mahaifiya ta yanemi shawara Agunmu muma mukace, A’a bamason yashiga siyasa Abukamar wasa Wasu sukayita sukan mahaifina Abun yana matuk’ar bata masa rai sosai Amma shi mutum ne mai Hak’urin gaske.
Saboda kullum idan muna zaune dashi yakan cemana nida mahaifiyata muzama masu hak’uri Zamuga cigaba sosai A rayuwar mu.
Tafashe dakuka! ‘‘ISMA’IL” ya rarrashe ta tayi shiru, Yace mata baya ganam kuma sai me ya faru?.
Tayi murmushi! Tacigaba da bashi labari, Tace Watarana ‘‘FAMILY” namu mun hadu Manya da yara daman munsaba duk Bayan wata muna Shirya Zama na musamman Duka dangin mu Mukan hadu manya da yara Mutattauna Abubuwa Na musamman Dangane Da abunda ya shafemu, Akan tara kudi Kodan gaba buk’atar wani ko Rashin lafiya Acikikin wannam Gidauniya ta ajeyar Ake komai, mahaifina shine Babba, Kowa yana bashi girman sa dai_dai misali, Bayan Angama Taro Munyi rakiyar Masu Tafiya Muna dawowa Kawai Aka tare mu Ahanya Mahaifina yanaji Yana gani Akaciro ni a mota mahaifiyata tana kuka shima yana kuka, Sukace Yana yunkirin wani Abu sai sun kashe ni.
Haka suka rabanidashi Kuma suka karbe wayata Sannam suka yi awun gama da mu bani kadai bace munada yawa Mutanen nam basuda imani kisan killa suke wa mutane Suba kudi suke bukata ba Nina gaga fahimtar wa’yanna irin mutanene su.
‘‘ISMA’IL” ya kalleta ya girgiza kai yace Gaskiya natausaya miki Ta girgiza kai tace Ko, ‘‘ISMA’IL” yace yanzudai to sai kitashi mu kama tafiya nasan lallai suna nam suna bibiyar mu, Begama rufe bakiba yace Ance ai gata chan, Idanun ta suka zazzaro, Suka Kama gudu, kafin kace Mai Antare su tako ina, Rik’e kai tayi tazauna a k’asa tafara kuka tace Wayyo Allah Bakasan komai ba gashi na jefa ka cikin damuwa.
‘‘ISMA’IL” yadaga Kansas ya k’are musu kalla shima ya durk’usa yace K’addarace Bayanda muka iya hakan Dole sai ya faru, Karkiji komai Allah Natare damu….
Page 9 – 10 of kuruciya complete hausa novel
‘‘ISMA’IL” yadaga Kansa ya k’are musu kallo shima ya durk’usa! yace K’addarace Bayanda muka iya hakan Dole sai ta faru, Karkiji komai Allah Natare damu….
Fuskokin su gaba d’aya a rufe, Da kagan su kasam Ba imani A tattare Dasu, wani bushe_she ne Ya taho ko wanne daga cikin su ya yakoma gefe ‘‘ISMA’IL”, yaka kallon sa, ya daka masa tsawa, Kai yaga ko gizau beyiba, ya tuntsire da dariya yace lallai wannam Hatsabibi ne kai Har Ka isa Ka dauke wannam (YARINYAR)?.
lallai ka aikata babban kuskure Ita wannam dakake gani ‘yace Gawani Attajirin mutum kuma shi mutumne mai taimakon Al’umma, Munbi duk wata hanya Domin Nakasar dashi, Amma shidin Mutum ne me tsananin k’wazo, Yagagare mu, ‘‘ISMA’IL” cikin tsaurin ido da rashin tsoro Yace, Maizai hana Ku karbi dukiya Ku rabu da ita?.
Cikin mamaki, yace Ai muba dukiyar bane Abun daya dame mu, ‘‘ISMA’IL” yace to me ya dameku Naga duk wani Mutum a duniyar nam bawanda za’a masa tayin zunzurutun k’udade wanda yasan idan har Yasamesu zai koma cikin mutane yacigaba da yaruwar sa cikin kwanciyar hankali, Shugaban tsagerun nam yace wannam kai ya dama kagan ninam wannam yarin yar Kawai burina, Ganin ta bata numfashi a doron k’asa.
Dajin wannam Batun nashi, sai ta fashe dakuka, tace Dan allah karkukashe ni, Kufadi duk Abunda kuke so na muku Alk’awarin zan baku.
Murmushi, yayi yace Ai badaga ni bane nima umur ni Aka bani Dan haka dole Zan zartar da kukunci Lokaci kawai nake jira Ana bani umur ni Tabbas Zan ai watar, ya daga bindiga sama yayita Harbata har Sai da harsashin da suke cikinta suka k’are tass!.
Sake fashewa da kuka tayi, ’‘ISMA’IL” yace haba kidaina kuka, ya share waye fuskar ta tace, Dole na nayi kuka saboda yanzukam nasan tawa ta k’are, ‘‘ISMA’IL” yayi murmushi ta kalle shi tace kai gaba d’aya naga hankalin ka kwance, Isma’il yace ai ni nasaba dan Wani namin barazanar mutuwa Abun bai damuna, saboda ni natashi cikin k’uncin rayuwa Bawanda yake tallafamini sai ‘yar uwa ta guda d’aya tilo, Nayi Alkawarin fuskantar duk wani k’alubane Idan har ita zata kasan ce cikin jin dad’i da kwanciyar hankali, Ta share ragowar hawayen fuskar ta tace Allah sarki!.
‘‘ISMA’IL” ya k’ara gyara zama yace mata ki kwantar da hankalin ki idan har kina tare dani Insha Allah, zamu samu mafita, Kinji kidaina Tada hankalin ki, Nam da wa ‘yan su yan kwanaki tace to shenam.
‘‘AISHA” kuma tanachan ta shiga damiwa yau kimanin Sati biyu kenam, babu labarin k’aninta ‘‘ISMA’IL” tana zaune tayi tagumi, Abakin gate Da yamma liss! ‘‘HASSAN” yafito yayi shiru yatar da ‘‘AISHA”tayi tagumi ya zauna agefen ta yana kallon ta ya k’ura mata ido yace ‘‘AISHA”tinanin me kike haka?.
Tayi murmushi tace kade bari kawai, Yau sati biyu kenam lambar ‘‘ISMA’IL” ko na k’ira bata tafiya shine gaba d’aya nashiga cikin damuwa saboda shikadai ya ragemini Bana so na rashi banason wani abu ya sameshi amma baya jin magana haka yayi nisa dani, ‘‘wani mirmushi ‘‘HASSAN”yayi yace haba kidaina wani sama kanki damuwa insha allah yana nam lafiya kinji Aisha.
Gyad’a kai tayi tace Amin, turo gate Akayi da karfi Sanadin hakan, Yagauce daga inda yake, ‘‘ISMA’IL” yace ‘‘AISHA” maza ki gudu gate, Ina kafin ta yun k’ura Ya jubgo Akanta, inda take ya nufa da gudu ya tura gate din gefe da karfin tsiya, Ya samu ya jawo ‘‘AISHA” ko motsi batayi, Yana juyawa ya dan ganin waye ya tab’a gate dinnam har hakan tafaru, Ganin mitumiyar sa yayi Agefe yace dama kece kika taba abunnnam Amma ke gaba d’aya banga amfanin zuwanki Gidan nam ba, Take ya daga wayar sa ya k’irawo Abokin sa yataho da mota sukadauke ta Abun tausayi suka sak’ata amota Suka wuce da ita Asibitin (Fravet) suna zuwa aka karbe su hanu bibbiyu, Likita na zuwa ya ce, Za’a mata aiki Amma lallai sai kun biya kudi kafin A fara, ‘‘HASSAN” yace nawa ne, Likita yace Su nemo naira Dubu Dari Da hamsin, Dajin wannam kudaden sai k’irjin Shi ya buga yace to likita zandawo yanzunnam.
Kama hangar Vida yayi yshigo A gigice, ya durk’usa a gaban mahaifiyar sa yace Mama ki bada kudi Za’a yiwa ‘‘AISHA” ai ki wani irin kallo ta masa tace nikuma ina ruwana tunda ba’a bunda yasameka To ai Alhamdulillah, Ni banida kidi, ‘‘HASSAN” yace A’a mama karkice haka, itannam fa mareniya ce mama tace dakata Ba’a bunda zanbaka saidai tamutu ni baruwana, Rik’e kai yayi ya tashi, Ya fice waje Ya tura mashin Din sa, Waje Ya yi buga buga ya sayar da ita naira dubu d’ari, ya koma asibiti yace likita gawannam dan allah a fara mata aiki dan allah likita take yanke, Suka shiga da ita d’akin Taimakon gaggawa,(imagency), sun bata fiye da awad’aya ‘‘HASSAN” Kuma yanata sintiri yaje yadawo yaje ya dawo, likitocin ne suka tafito babban likitan yace, An samu Nasara, Amma saidai Kanta ya dan bugu, Amma zata samu lafiya, farinciki ya kama ‘‘HASSAN” aka chanja mata d’aki hassan yana gefen ta tana ta bacci bata far kaba.
‘‘ISMA’IL” yaji wani Abu a jikin sa, Yace to kodai wani Abu yafaru Da ‘yar uwa tane Dole yaukam insha allah zamu nemi mafita A daren yau ko mu tsira kokuma sukashe, Tabbas acikin biyu za’a yi d’aya.
‘‘ISMA’IL” yaji wani Abu a jikin sa, Yace to kodai wani Abu yafaru Da ‘yar uwa tane Dole yaukam insha allah zamu nemi mafita A daren yau ko mu tsira kokuma sukashe, Tabbas acikin biyu za’a yi d’aya.
Murmushi, Tayi tace Haba kaiko, Nikam banga wata hanyar dazamu tserawa wannam gun_gun ‘yan tadddan ba, Kasan sun ‘kara saura komai.
murmushi ! ‘‘ISMA’IL” yayi yace Idan harkin amince shikenam, ta girgiza kai tace Na amince Dare ya raba, Misalin k’arfe, 12:17am Tana bacci ‘‘ISMA’L” ya tatta ba ta ta farka, Ya ce gawannam Ki wanke fuskar ki, Ta karbi ruwa ta wanke fuskar ta Ahankali Suka Fita Suka yita gundun tsira sun dau sa’o’i suna gudu, Ta kama Haka, tace ‘‘ISMA’IL” zan mutu bazan iya guduba na gaji, Ya tsa Sukayi ‘yan mintoci, Sannam sukacigaba da tafiya, suna cikin tafiya ‘‘ISMA’IL” yace lokacin Sallah yakusan k’aratowa gare ya kusan wayewa, koda sun taho bazasu cinmana ba saboda mun musu nisa, sa hanun shi yayi A aljihun sa, Yajire yayi shiru, Tace yaya naga kayi shiru, ‘‘ISMA’IL” yace Wallahi Na manata wayata A baya amma bakomai damuwata daya ne, ‘‘AISHA” amma bakomai sukaciga da tafiya Suna tafiya “ISMA’L”, yadaga gansa yace (ALFIJIR) ya fara ketowa muk’ara sauri, Suka cigaba da tafiya, Hamma tafara yi, Tace ‘‘ISMA’IL” yumwa nakeji, ‘‘isma’il” yace Ai yazama dole na nemo miki Abunda zaki sa Acikin ki amma mudan k’ara gaba tukunna.
Sunacikin tafiya, ya hango wata bishiyar (TUFA), Yace jirani Anam ya na k’arisawa ya hau ya tsinko, Ya taho Ya bata gaba d’aya guda biyu taci taji to k’oshi, Suka tashi sukacigaba da tafiya tafiya suke har gari ya gama Waye wa, Suna isowa Wani kogine, Iya ganin ka, Tsayawa sukayi, ‘‘ISMA’IL” yace to fa, Yanzu yaya zamuyi kenam, Wannam ruwan Kodai zamu shiga ne, Ta girgiza kai tace a’a gaskiya Mu dakata ko Allah zai Kawo mana mafita, ’’ISMA’IL” ya kalleta yace to shikenam, Suka nemi gu suka zauna, Isma’il yace Nikam Inane Garin nam Naku haka?.
Tace, (ADAMAWA), Mubi yayi murmushi yace insha allah kamar kin koma gida Amma dan Allah Kicika min Alk’awarin da kika dauka, Karki Karya zuciyar Maraya, tayi murmishi, Tace Ai nina maka Alk’awari, karkaji komai.
Sunacikin Maganar Saiga wani Yataho da ‘‘KWALE_KWALE” isma’il yawota yayi harta yunk’ura zatayi magana janta gefe yayi suka labe, kwale_kwalen Yana isowa Mutumin ya fito ya jawo kwale_kealen, yayi fito sau uku, Ya sauk’e wani Akwati, isma’il ya rufo da gudu yana ganin isma’il ya tsaya yace kai Meya kawo ku wannam gurin Isma’il yace Ka tai makemu Akwai Masu bibiyar mu, Yayi mirmishi, Yace Nima ina musu Aiki Amma idan Har kunada kudi Ba’abunda bazan mukuba, Isma’l suka kalli juna, Isma’il yace Bamuda kudi gaskiya, Mutumin Ya fara kunce kwale_kwalen shi, Harya hau zai tafi, yayi murmushi yace kozo kushiga wani farin ciki Isma’il besan lokacin da ya taho ya rungumi mutuminnan ba tsabar murna, Yashiga ta taho ya rike hanun ta mutumin ya tada ingin girgin ruwan nashi, Sukayi ta tsula gudu, Sai da sukayi Kwana uku akan ruwa suna tafi, Sannam sukazo wani giri na musanman, A tsakiyar ruwan.
Ya umurci su da su buya inda baza’a gansuba, yafita bewuce ‘yan mintoci ba, Ya dawo ya tada ingin nashi, suka cigaba da tafiya, Wuni sukayi kass! Sannam suka iso bakin ruwan suna sauk’a isma’il yadinga masa godiya, Mutumin yace bakomai karkudamu Allah ya k’iyaye hanya har sun Kama hanya isma’il ya jiyo yace Malam karkagaji dani, samu A hanyar dazata kaimu Adamawa, Mutumin yayi shiru yak’irawo wani yace ciri wasu kudade yace Inaso sai ka ke bodar ADAMAWA, ka nuna musu kabar su, Anam kaji cikin girmamawa, yace to Sukajuya Yasaka su Awani kwale_kwalen, Sunata tafiya Har dare ya musu Suna tafiya ga sanyin tsiya, ‘‘ISMA’IL” yacire rigar sa ya lulluba mata, duk da haka tanata kar_karwa.
Kwanwa sukayi, Gadari ya waye Yana zuwa daidai_wani Guri ya Ajesu ya nuna musu, Yace Daganam Zanbar ku akwai jami’in tsaro A gunnam, Isma’il suna tafiya Daga nesa wani soja ya daka musu tsawa, Isma’il yadakata yanazuwa yace ina katin dan kasar ka, Isma’il yace Katsaya zan maka bayani, Kafin kace me yayi wani yare sojoji suka dawo kan isma’il tare da yarin yar nam Sukace bamu yadda dakaiba sato ta kayi, dan ta’adda ne kai.
Ita kuma gasanyi ga cizon sauro ga wahalar da tasha, ‘‘ISMA’IL” yana kallonta kawai ta zube ta fadi k’asa maza maza aka dauketa Shikuma isma’il Suka kamashi, Aka daure shi suka masa dukan tsiya sai ya fada musu Yanda yayi yasato Yarinyar nam Yace, nima Kawai tsautsayi ne ya had’ani da ita, duk abunda isma’il ya fad’a basa yadda.
Daga karshe Aka juya kan isma’il Aka sa mar Bindiga Akayi Daya dagacikin sojojin Yace Zamukashe ka tinda ka k’i fada mana gaskiya bakin isma’il yana murmushi Bakin sa najini Yace Gaskiya ta kenam, Wannam zalincin da mai yayi kama, ‘‘AISHA” nagaza cika miki burinki Ya fashe da kuka, sojojin suka tin tsire da dariya sukace dan soyayya kenam.
Tau! Tau!! Tau!!! k’arar harbe kakeji, sau uku, Cikin firgici ‘‘ZUBAINA” ta farka, Tana bude ido ta kama hawaye, Tace A ina nake, Wani soja ne A gefen ta yace kikwantar da hakalinki, Azzalumin War haka ya shek’a kiya farat tayi tace ! Kar ku aikata kisan kai ‘‘ISMA’IL” Ba dan ta adda bane. Sojon yace Ai war haka ya mutu harbin nam daya tashe ki Ai shi A ka harbe, Dur k’usawa k’asa tayi takama kuka, Tana cewa Da nasan haka zata faru dashi Da tun A baya nina mik’a kaina sun kashe ni, Yanzushikennam ai kun kyauata, Ta tashi tana kuka ta fito.
Tace Wayyo ni ‘‘ZUBAINA” dawana ido zankalli ‘yar uwar ‘‘ISMA’IL”. Na jawo An kashe mata dan uwa.
Fitowa ‘‘ZUBAINA” tayi A gigice Tace Wayyo ni ‘‘ZUBAINA” dawana ido zankalli ‘yar uwar ‘‘ISMA’IL”. Na jawo An kashe mata dan uwa Tanata famar rusa kuka, Jim kadam, Sojan dayake kusa da ita ya daka mata tsaya, Ta firgita Ta tashi zata gudu ya dakatar da ita, yace Hak’uri zakiyi ki dau dan gana ba kuka zaki tsaya yimana anam ba, Ya sakota a gaba sukazo har wajen da Ragowar sojojin suke, Kyalla ido tayi taga Ba ko gawar isma’il ta kama bude_dube tamkar wata mahaukaciya, Chan ta hango shi A kwance yana numfashi sama_sama.
Tahowa tayi dagudu ta juya shi, ya kallita yace, kibani ruwa k’ishin ruwa nakeji Hankalinta ya kara tashi, Ta hango wani Rowa A kan wani tiburi, ta ruga aguje Ta dauko, Ta fara bashi yana sha kenam wani fusataccen soja yayi boll, da robar ruwan,‘‘ISMA’IL” yace kinga yanda rayuwa ta kasance dani ko?, (BALAIFIN MU BANE) bamuda kowa Allah ne kadai gatan Mu, Burina koda na mutu bana so kisanar da ‘yar uwata hakan, ‘‘ZUBAINA” tafashi da kuka!.
Wani Soja ne, Ya sauk’o a wata motar yak’i Suna ganin shi, gaba d’ayan su suka k’ame, ‘‘ZUBAINA” tata ho da gudu, ta durkusa, Harwani soja ya kai hanu zai dakatar da ita Ya nuna mar yatsa, ya koma gefe Ta ce, Ka taimakeni Yanda allah ya taimake ka, Dan uwanane Bashida laifin komai, yayi murmushi ya kalleta, Yace kekuma to meya biyo daku nam hanyar?, ta ke ‘‘ZUBAINA” tafara bashi labari sai da yayi kwalla, Yace maza maza A na baku umurni A kula da yaronnam take yanke, Su kauko ‘‘ISMA’L” zubaina tayi mamaki sosai, tace yallaboi nagode sosai, Banzaci akwai wanda zai taimake muba sai gashi Allah ya kawo ka, ‘‘ISMA’IL” shi mutum ne mai tausayi bashida kowa marayane kaga duk abunda ya faru dashi nice sila, Bayan Wasu ‘yan Sa’o’i gaba d’aya dakarun sojojin suka taru, Kowa ya tsume, Shi babban nasu ya dinga musu fada, Daga bisani ya umurci kowa ya koma bakin Aikin sa, Ya dawo inda zubaina take ya zauna gefen ta ya tam baye ta ke ‘yar wana garine, ‘‘ZUBAINA” tace ni yar Ada mawace Nida mahaifina da mahaifiyata muna zaune a garin (MUBI), yace Allah sarki Muje wajen d’an uwan naki, tace to sukakama hanya, suna tafe tare da ita Duk wajen daya wuce k’ananam sojoji sai sun rasa masa, kai Gidan soja Akwai Biyayya, Shiga sukayi ‘‘ISMA’IL” yana bacci harda munshari ‘‘ZUBAINA” tana ganin shi taji sanyi A ranta tayi murmushi ta koma gefe tayi zaman ta a kusa da ‘‘ISMA’L”, Haka suka yita samun kulawa a wajen babban sojannam har na tsahon kwana bakwai(7), ‘‘ISMA’IL” yayi garau kamar bashi ba.
‘‘ZUBAINA” tana zaune tayi tagumi! ‘‘ISMA’IL” ya hangota suna hira dawani, jami’in (SOJA), Yataho wajen ta, ya zauna gefen ta, yadau k’ananam duwatsu guda biyar zuwa shida, yana d’an jefa su nesa, yace me ke damun ki ne kam?.
Tajuyo tace o ‘‘ISMA’IL” kenam abunda kedamu kawai, dai bazai wuce nagani Gani ga mahaifina ba, ga Mamana ‘‘ISMA’IL” yayi murmushi yace karkida mu ai zamu tafi nam bada dad’ewa ba kinji?, ta gyada kai tace shikenam.
Suna zaune suna ta hirar su, suna ha go shugaban sojojin sukatashi.yace a’a kiyi zamku nazo nima tataku hirar ne.
”ISMA’IL” Yace bakomai. Suna zauna hira takai hira sojan nam yace,Abokina ”isma’il” kake dasuna ita kuma,”ZUBAINA” ko?. murmushi yayi yace Gaskiya da jarumine yanzu, Kai baka tsoron Yar uwar taka ta rasaka?, murmushi ismail yayi yace haba yallabai… Idan har zata kasance kikin farinciki tabbas ba komai burina yacika, murmushi, sojannam yayi ta tafa wa isma’il, yace wannam shk’uwar ta ku bazata misal tuba, na jinjina maka haka akeson dan uwa yabamu da ahalin sa, bawai ya watsar da suba ‘‘ZUBAINA” wani murmushi tayi tace nima sonake naga wannam ‘yar uwar tashi dayake ta bamu labarinta gaskiya.
Wata motar sojojine ta taho ta faka, wasu sojojine na musamman suka fito suka tinkaro inda babban maigidan nasu nake zaune, cikin girmama wa suka sara masa sukayi wani yare wanda bakowa bane yasan abunda suke nufi ba sai su ya su, Rungumar juna sukayi, Ya gabatar da isma’il tare da ‘‘ZABUAINA” yace dasu yaukam yakamata ashiga daku cikin garin (ADAMAWA) mubi, take wani farinciki ya lullube zubaina, tace isma’il gaskiya ina cikin farin ciki, kallonta yayi kawai yayi murmushi, Sukayi bankwana, Gafe da gefen su, Sojojine Akamusu rakiya har izuwa cikin garin (ADAMAWA), aka sauk’e su Anam kuwa suka zama abun kallo, isma’il yace ‘‘ZUBAINA” kinga bamuda kudin motar da zamu tafi izuwa garin mubi, yanzu yaya zamuyi kenam, gashi wayata tana chan ta salwanta, Yana tinani yataba aljuhun rigar sa futu_futu, Yaji nauyi kamar kudi, yaciro yace la ikon allah duba kiga kudi ya lissafa su naira dubu goma sha d’aya, yayita tinanin a ina yasamu k’udaden nam, sai yayi murmushi, zubaina tace fadamin naga kayi murmushi yace bawanda zai mana wannam abun fa ce, sojan nam kai Allah ya masa albar ka, isma’il yace yanzu ya kamata mu sayi kaya dazamu saka kafin nam nushiga motar dazata kaimu zuwa garin ku daganam ni sai kisallame ni nakama gabana, shiru tayi tace yanzu shikenam muna zuwa garin mu mun rabu kenam, isma’il yace A mana ta gyada kai tace to shikenam, take suka sayi kaya kala biyu, Na naira, dubu uku da d’ari biyar.
‘‘ZUBAINA” tafito tayi kyau sosai, tace da isma’il kayan nam basumin kyau ba gaskiya ko, yayi murmushi yace In ba keba ina mukaga lokacin wani Gaye nima kayan gwanjo nasaya riga da wando, Kingan su zasujima ina saka kayana ni baruwana dawani kyale_kyale tayi murmushi tace to shikenam, suka kama hanya Suka shiga mota, Sunata tafiya sunyi tafiya mai nisa sosai Anzo wani waje ‘‘ZUBAINA” tatiwa matuk’in motar magana tace Sauke mu Nam ALHAMDULILLAH, ‘‘ISMA’AL” yace kai garin nam Naku Gaskiya Ya burgeni sosai, murmushi Zubaina tayi tace(MUBI) garin Dadi kenam ta nuna Masa wata hanya tace idan muka bi nam Har Gidan mu, Tana murmushi suka kama tafiya Wani gida suka iso Kaf Illahirin Ayarin jerin Gidajen Wajen Ba gida kamar Wannam Kuma Cikin TALAKAWA, mamaki ‘‘ISMA’IL” yake yace zubaina Gaskiya Dazan ce wani Abu amma na fasa, murmushi tayi tace Kaiba Ko.
Suna zuwa dai_dai (Gate) na gidan Ta kwan_kwasa, Ta juya furkarta Tace Nasam Mom dina ce zata fara fitowa Tana zuwa zan rungume ta, Murmushi isma’il yayi Ta juya Wata mata tazo tana bude (gate), Ta juyo Isma’il gani yayi ta tsaya yace ‘‘ZAINABA” yaya naga kin tsaya tayi shiru tace Tabbas Basa gidan nam Ta fashe da kuka isma’il ya rarrashe ta suka zauna A k’ofar gidan, Isma’il yace to Mezai hana ki neme su Awaya Tace A’a so nake sai dai kawai suganni A gida Amma gashi kuma basanam To meya faru, Duk wanda yazo wucewa sai ta ce yar alhaji Lafiya kuwa yau a anguwar nam Tabbas Basu kyauta wa Mahaifin kiba, Ko ina ya shiga sai Allah.
‘‘Duk wanda yazo wucewa sai yayi mamaki ya ce yar alhaji Lafiya kuwa yau a anguwar nam Tabbas Basu kyauta wa Mahaifin kiba.
‘‘ISMA’IL, kallon Zainaba yayi ya gyada kai, Yace Hmmm to Mahifin ku kuma mai ya faru dashi, Gashi kuma Shi mutum ne Mai Taimako, hmm Allah sarki Daman A rayuwa Duk Abunda za’a kiwa Mutane Wani Lokacin Basa yiwa mutum uzuri Tabbas Akwai Abunda Ya faru, ‘‘ZUBAINA, murmushi tayi Tace Nidai fatana Allah yasa Mahaifina Nacikin kwanciyar Hankali Koma me suka Masa Allah Zai saka mana, Ta fashe da kuka!!.
‘‘ISMA’IL, ya rarrashe ta yace zubaina Mezai hana Ki nemi lambar Mahaifin naki, ki ji Ina ya koma, ta yi murmushi ta ce Shikenam yanzudai Mu k’arisa ‘Kofar gidan su, ‘‘AINA’U, tana tafiya isma’il na biye da ita K’ofar wani Gida suka zo Wacce ko k’ofa babu A mashigar gidan Wani Buhu a ka saka mai makon k’ofar suna zuwa isma’il yana tsaye Awaje Tayi sallama, Isma’il yana daga waje ji yayi Gidan ya rude da shewa yayi murmushi.
‘‘AINA’U, ta ce zubaina Ashe da rabon zamu sake ganin guna, ikon Allah, suka sake rungumar juna, ‘‘ZUBAINA, tace Muje waje Suka fito ta nunawa aina’u ‘‘ISMA’IL, Ta ce wannam dakike gani ya taimake ni sosai suka gaisa, sunacikin tad’i zubaina tace Nikam k’awata mahaifina tashi sukayi daga anguwan nam ne?.
Murmushi ‘‘AINA’U, tayi tace Allah sarki Alhaji Ya kwan biyu da Barin anguwar Nam sai da yatafi Daga baya Kowa Ya gane kuren sa, A yankinnam Gaskiya Ba a kyau ta wa mahaifin ki ba, Murmushi zubaina tayi tace Nikam meya faru k’awata ki fadamin gaskiya karki boye min komai duk da nasam mahaifina shi mutum ne mai hak’uri da kawai ci.
Murmushi ‘‘AINA’U, tayi ta ce Watarana mahaifin ki yana zaune A k’ofar gida yana karatun, (ALQUR’ANI) mai girma Wata mata ta ho da gudu Tafad’i Gaban shi tace ALhaji Katai makamin kamar Yanda ALLAH ya taimake ka, Yata ce Gata chan Na Kowa ya k’i kulata A garin nam, Kuma haihuwa ce tazo kowa ya guje mu, Dukda ta gane kuren da tayi Bekamata A juya mata baya ba, Bawanda ya fi k’arfin hakan ta faru dashi, Take yace jirani ina zuwa, Ya shiga cikin gida ya ajiye ALQUR’ANI, mai girma shida mahaifi yar ki suka fito, Ya umurci matar ina ‘yar tata take, suna zuwa ya kalleta cikin tausayi yace Maza Mahaifiyar ki ta sakata A mota shikuma ya shiga mota, Suka kai ta (ASIBITI), cikin ikon Allah ta sauk’a lafiya ta samu d’an ta namiji Ya musu tara ta Arzik’i.
Bayan Sati d’aya da faruwar hakan matar tazo da d’an nata tare da mahaifiyar ta, Sukayi sallamah Mahaifinki Ya musu iso suka shigo Suka zauna k’asa suka gai she da Alhaji, Nam ma ya musu tara ta arzik’i matar tace Alhaji Kai tayiwa ta kwara, farin ciki Ya kashi Ya ji dadin hakan harya karbi, Yaron Ya rik’e A hanun sa ya nuna wa mahaifiyar ki, Ta kalli yaron ta fashe da kuka, tace Idan na kalli Jariri Sai hawaye yazomin ina tinawa da ‘yar mu guda d’aya tilo mun rasata ita muke gani Tana saka mu farin ciki.
Dajin wannam Batun, Mahaifiyar yaro tace Alhaji Idan kuna bukatar shi Bakomai zan baku shi, Dan zaman shi A gurin ku zaifi samun kulawa fiye da gun mu, Da jin wannam, batun Alhaji yace to idan har Uwar gida ta amince ba komai, Murmushi tayi tace Na amince Amma sai ya isa yaye idan kin yaye shi, Sai kikawo min shi, ta ta shi tashiga dakinta ta dun k’ulo kudade ta mik’a musu sunkak’i karba tace A’a kodai kunre nane sukace A’a hajiya.
Hakadai Alhaji yasa aka ginawa matar nam gida mai kyau, Suka tare ciki, To tindaga wannam lokacin mutanen garinnam sukafara jifan mahaifin ki da munanam maganganu akan Shine asalin mahaifin Wannam yaron Amma angagara samun wanda zai fadawa alhaji ido da ido, Watarana Yafito ya tarar da manyan anguwa a k’ofar gidan sa, yana fitowa ya musu sallamah suka k’i amsawa wani daga cikin su yace haba Alhaji Abunda kayi a matsayin ka na mai fada aji Kana aikata irin wannam Abun to yaya kake tsanmanin sauran al’ummar ka na wannam gari?.
Murmushi yayi yace ba laifi bane, Dan ka taimaki wanda yake buk’atar taimako. agaji a kan gab’a, kukan ta ta kawomin nikuma na share musu hawayen su, shin hakan danayi laifi ne?.
Sukayi shiru, Daga bisani Wani yace Alhaji wai ace kaine da aikata (ZINA) a boye hartakai ga ka dauki nauyin magaifiyar yaro da mahaifiyar yarinyar girma yafadi, dagin wannam maganar alhaji yaji zafin maganar sosai Amma ya danne zuciyar sa yace Abunda zaku saka min dashi kenam na gode ya juya zai shiga gida suka mar ihu!.
Yajuya ya shiga gida yasanar da mahaifiyar ki, Daga k’arshe ya yanke shawarin barin garin (ADAMAWA) baki d’aya, Washe gari da safe Ya tattara duk wasu abubuwan sa masu mahimman ci, ya shiga motar shi ya fito zai tafi matar nam tataho da gudu tace Alhaji Meyasa baka fahimtar dasuba, yayi murmushi yace Ba komai yasake murmushi yace kukula min da mai sunana, ya sake dunkulan wasu kud’ade ya bata.
Yaja motar shi sukayi tafiyar su, Bawanda yasan taka mamai inda alhaji yake, ‘‘ZUBAINA, ta sunkuyar da kanta tace Bakomai tabbas watarana gaskiya zata fito, Sukayi bankwana da k’awar ta tace To nabar ki lafiya mukam zamutafi, suka rungumi juna tace K’awata zan kawo miki ziyara watarana amma Badan naso ba saboda garinnam Inaganin sa tam kar Wuta bazan iya zama na wasu minto ciba, Ta umurci ‘‘ISMA”IL, da su bar garin haka kuwa akayi sukakama hanya tana kallon garin tana girgiza kai har suka bar cikin garin (MUBI) adamawa.
‘‘ZUBAINA, ida nunta duk sin cic_ciko DA hawaye, suna tafiya isma’il ya lura DA hakan yayi murmushi yace Dan Allah kidaina bana son ganin ki cikin damuwa kinji zubaina, ta goge hawayen ta ta ce shikenam, Yanzu ina zamu nu fa gashi bansam ta inda zamu Fara Neman mahaifina Ba, ta yi murmushi tace nasamo mana mafita, kasam yaya za’a yi kuwa isma’il?.
Gyada kai yayi yace sai abunda Kika ce, wani kallo ta mishi ta yi murmushi tace munemi wayar wani sai mu k’ira lambar su, Haka kuwa akayi wani bawan Allah yabasu waya, ‘‘Zubaina, sau hudu ta k’ira amma ba’a gada wayar Ba tsumewa tayi ta mikawa me wayar kayan shi, tace Malam mungode. Ya juya zai tafi akabiyo shi ya daga yace, ke ga shi ank’ira dasauri ‘‘ZAINABA, ta haho ta karbi wayar ta Kara A kunen ta.
‘‘kara wayar tayi A kunne, tayi magana tayi magana taji shiru tace To wata’kila dai mama bata gane Zainaban ta bace ke magana, Ta kashe wayar tana hawaye aka sake kira ta daga tace mama ki daga murya bana jinki zainaban kice mama na, shiru kawai ta kashe wayar aka sake ‘kira kawai ta mi’kawa mai wayar tace mun gode Malam Ya karbi wayar sa ya sakata a aljihun sa.
‘‘ISMA’IL, kallon fuskar ta yayi yai murmushi! Ta juyo suka had’a ido yace bata jinki ne gyada kai tayi tace A mutafi kawai, kama hanyar su suna tafiya Isma’il yace gaskiya, Ni abunda yake damuna ‘‘Farinci kina ma’ana yaya ta kowana hali take ciki se allah.
Mai sauroro Shin Aisha yayar ‘‘isma’il, dai mun barta a baya tana gadon Asibiti muje zuwa dan jin yadda zata kasance?.
‘‘AISHA tana zaune tayi tagumi tayi shiru, ‘‘HASSAN, Ya taho yace yaya yace wai ke haryanzu baki daina wannam tinanin nakiba,?. Adu’a zakiyi Allah ya bayyana manashi, Gashi gobe zan koma makaranta Amma naji Labarin kamar wai An kwara mana Hutun (SATI BIYU), juyowa Aisha tayi ta ce saida na fada masa karya je gunnam amma yak’i to ai gashinam Abunda ya faru, Wayar sa ma ta daina shiga.
Tagama rufe bakinta kenam hassan Yaga inuwa ta bayan sa, yana juyawa Yayi murmushi ya ce haba malama Ni bayadda za’a yi na zauna da ke kiyi hak’uri Inafatan kingane tsaki tayi tace Malam kokaso koka k’i dani za’ayi Kasani Ita kuma wannam Korar kare zan mata Agidannam Matsiyaciyar Banza Marar asali, Juyowa ‘‘AISHA tayi ta ce Allah baki Hak’uri Insha Allah duk lakocin Da nima yayana yasoko k’afa cikin gidannam Insha Allah zan barmiki gidan ku kinji?.
Hassan kallonta yayi yayi murmushi yace Ba laifin mu bane, Haka itama ba laifin ta bane, Ke meyasa ba kya gane wa ne kam, Tin tsirewa tayi dadariya ta ce, ni ‘‘SAUDAT” ina da tsananin kishi Zan iya Abunda baka tsammani Akan Abunda nake so, Daka mata tsawa yayi yace malama barkai na ta juya tayi tafiyar ta.
‘‘ISMA’IL tare da zainaba sukayi landin cikin garin barno, Da yamma Kai tsaye isma’il ya kwan_kwasa (gate), zainaba tana zaune ta taho dan ganin waye yake buga gate tana hada ido da isma’il, A fusace ta tafka mar mari Tasss sai da yatsun ta suka fiffito a kumatun sa, Daga bisani ta rungumeshi, zainaba kuma kallon ikon allah kawai take ta sake Baki, Aisha ta Ce k’anina kayi Hak’uri bacin raine idan banyi hakan ba bazan huce ba murmushi yayi Yace To Ai sai a sakeni ko?, k’ara k’an_k’ame shi tayi.
Bayan ‘yan mintoci ta sake shi ta Ce wannam fa ina kasa mota?, murmushi yayi ta ce kodai itama batada kowanne kam? Ya ce A’a Ina hassan ne kam?.
Cikin farin ciki ta ce yananam gaskiya yakamata kayi masa godiya Da badan shiba da sai dai kazo kasamu ‘yar uwar ka ta zama gawa.
Isma’il ya ce subahanallah Mushiga ciki, Kutsa kai sukayi, Isar su kenam, Saudat Ta fito ta ce mezan gani har ‘yan iska kike kawo mana Gida laillai yau zaki bar gidannam, k’iran hajiya tayi suka fito tareda hassan, Hangosu hassan yayi yana isowa ya mik’awa isma’il hanu suka gai sa, Hajiya tace kai yaya zaka shigo mana gida kafita kona maka ihun barawo na tara maka jam’a hasan zaiyi magana ta dakatar dashi.
Ta ce dole seya fita, ya juya ya fita ‘‘Zainaba” ta juya zata bishi ya ce Kekam zaki iya zama tare da Aisha, Juyawa tayi ta k’arewa hajiya kallo tace haba da girmanki kina maganganun batanci Kan mutumin kirki Wana bolar gidan naku, A wannam lokacin Ran hajiya ya baci tace To na yanke hukunci Aisha ma ta tattare kayan ta ta bar gidannam Ta ke hassan yace haba Mama bekamata Kiyi Haka ba, Juyowa kan shi tayi Ta ce yau Zan baka zabi daya kazaba ko wannam Karuwar Ko ni shiru yayi yace A’a mama hak’ikanin gaskiya Ina son kowannen ku.
Ta ke Aisha ta tattaro ko matsen ta ta kama hanya zasutafi Ta juyo tayi murmushi, ta ce Hajiya Nabar ku lafiya Hassan ya kalleta tana kallon shi yagagara cewa komai fita sukayi Bakin Gate din Gidan.
Suka yi tafiya mai nisa Gabadayan su sungaji, Aisha ta ciro wayar ta tace K’anina kasaida wayar nam Musamu musamu Dan abunda zamu sa A cikin mu, Daganin wayar Zainaba ta ce Akwai Kati ne A wayar Ta ce Akwai ragowar Nera Hamsin, ta ce mik’omin mik’amata tayi ta karba tasaka lambar wayar mahaifin ta tayi ringin Jitayi An dagawayar akace Yana sallah, Ta ce Idan ya idar da Sallah Kace Ya k’ira zainaba ce.
Haka suka zauna sunata hamma, Yamma lis taji Kira tana dagawa tace Alhamdulillah, Mahaifina ne yake k’ira Sallamah yayi Jiyayi Ance Baba, ya ce muryar wa nakeji kamar zainaba na, Tana shekar kuka ta ce Baba ita ce, Yace kina ina ne tace Gaskiya Baba, yace a’a dakata yanzunnam zan turo A daukeki duk inda kike abunka da mai Hali, take ya sa cibiyar Sadar wa ta binciko masa inda ta ke, Yace Kashewayar Yanzu za’a zo A daukike karki damu ki kula, Minti shabiyar Jimkadam wa ta mota ce ta faka A ka dauke su Dukanin su su Uku, motar duk abinda kake bukata Akwai shi tindaga Abunci da gun kwanciya.
Bude k’ofa akayi Suka fito Jirgine na musamman A kadauke su, Ya tashi Dasu betsa ko Ina ba Sai Cikin babban birnin tarayya (ABUJA). Jigin ya sake su wata mota ce Ta alfarma Tazo ta fa ka, Nam ma sukashi ga, basu wani dau lokaci mai tsahowa ba se ganin su sukayi cikin wani gida Mai kyan gaski, Daga ka gidan kasan bana k’aramin mutum bane.
Tindaga mashigar gidan Mutanene Kawai inata hidinmar Buki, Aisha ta ce to wannam Shagalin fa kuma, Isma’il ya ce nake ga kamar na nakine ranki yadade, tayi murmushi Ta ce Mukarisa Tafiya suke Abi nam dasu Ashiga chan dasu, Daga ne sa ta hango mahaifiyar ta ta taho da gudu suka rungumi juna.
Tindaga mashigar gidan Mutanene Kawai su nata hidinmar Buki, Aisha ta ce to wannam Shagalin fa kuma, Isma’il ya ce nake ga kamar na nakine ranki yadade, tayi murmushi Ta ce Mukarisa Tafiya suke Abi nam dasu Ashiga chan dasu, Daga ne sa ta hango mahaifiyar ta ta taho da gudu suka rungumi juna.
‘‘Kuka kawai suke, Bayan wa ‘yan su mintoci, Mahaifiyar zainaba ta juyo ta kalli mutane guda biyu mace da namiji, Ta ce Farincikina wa ‘yan nam fa?.
‘‘ZAINABA” ta k’irawo su ta ce Yaya isma’il ku k’ariso mana, Tahowa sukayi suka gaida mahaifiyar Zainaba, Hajiya ta ce Sudin kuma suwaye ne?, Zainaba tayi murmushi, Ta ce Yan zudai so nake A basu masauk’i na musamman Zuwa gobe Zan fayyace miki komai sudin marayu ne basuda kowa, Hajiya ta ce Allah sarki!.
A ta ke Aka kaisu wani Fanin daban Aka ajesu I dan Kaga wajen cewa zakayi Anya kuwa wannam Gurin A nageriya Ya ke kuwa?, Kale_kale suke Aisha ta kalli isma’il ta ce k’anina ina ma A ce Wannam Gidan Mallakin mu ne, Gaskiya Ina matuk’ar son wajen nam Amma nasam Na ‘yan wasu kwanaki ne, Zamu fita.
Washe Gari Da safe, zainaba ce da kanta ta garzayo Har wajen Da su Isma’il, daganin ta suka tashi Ta ce A’a kuzauna kusaki jikin ku Nam Ai gidan kune Zaku samu kulawa sosai Yanxuma haka Alhaji ne Yakeson zai tattauna tare Da ku na gama bashi Labarin komai Tin jiya da dare, isma’il ya tashi suna biye da zainaba A baya Har suka zo farfajiyar Alhaji, Sukayi sallamah ya amsa, Yana karatun Alqur’ani mai girma, Ya ajiye yace Ko iso Isma’il suka zauana kasa yace A’a tashi ku hau kujera, Isma’il yace Ba komai Alhaji hakan ma yayi, murmushi yayi ya ce.
Isma’il ba abunda zance maka saidai nace Allah ya biyaka da gidan Aljanna bisa taimakon da kamini Tabbas Kayi Abunda ka chan_chan ci yabo da jinjinar ban girma, Saboda yanda Kanuna kulawar ka sosai kan ‘yar mu zainaba, Naji ta ce Kunyi da ita akwai Wa ‘yan su kudade dazata baka ladan Taimakon da ka mata ko?.
Gyada kai isma’il yayi ya ce tabbas munyi haka da ita Amma ni har azuciyata kawai na tai maketa ne saboda Allah, Bana buk’atar wani Kudin ladan Hakan Abud’aya kawai nake buk’ata farin cikin yaya ta na mata Alk’awarin Gida na musamman Alhaji Wannam Alk’awarin nakeson Cika mata Sai kuma gashi Hakan Ya gagara, Alhaji yayi murmushi Yace Isma’il kenam.
Idan har kunada Buk’atar zama tare da mu Na bar muku Wannam fanin da aka kai ku jiya A matsayin ma sauk’i sannam Acikin gidaje na Dana ke dasu na mallaka muku guda biyu kai d’aya yar uwar ta ka d’aya besan lokacin da isma’il ya fashe da kuka ba ya ringa wa alhaji godiya.
Sannam Yace sannam zan sama maka Aikin yi da zaka dogara da kanka, kaji karkada mu, zainaba kuma na gefe tana ta murmushi Tana kallon isma’il Daga bisani Ya salla mesu, har sun fita zainaba ta dawo daga baya ta durk’usa gaban mahaifin ta tace Baba Dan Allah banaso isma’il yayi nesa da mu.
Kallonta yayi yai, murmushi yace to shikenam kuje ku sasan ta kawunam ku Ai bazan hanaki Abunda kike soba, Kunya ta kama zainaba ta rufe idon ta Tatashi ta fita.
Tsahon watanni Uku kenam, Isma’il tare da zubaina soyayah tayi k’arfi sosai, Ita kuma Aisha Kullum cikin tinanin ‘‘HASSAN” ita da hasan suna son juna amma kowa yana boye wa dan uwan sa Akwana atashi Watarana Zainaba tare da isma’il ana zaune suna hira suna bada labarain wahalar dasuka sha A rayuwar su, zainaba sai Hawaye ta ke tace Yanzu daman Yaya isma’il da kai ka yanke hukuncin Zama Bata gari ko?, ya tintsi re da dariya yace A mana to kowa ya k’i taimakon mu gashi dalilin haduwa ta dake ya zame mini Alkhairi ai, suka tintsire da dariya, Sakon (message), ne ya shigo wayar Aisha kamar haka:
Assalam dafatan kina lafiya Aisha Sarkin hak’uri Na dad’e cikin dakon son ki da kaunar ki cikin zuciyata, amma nagagara samun Gurin dazan sau k’e shi Cikin zuciyar ki, sena taho zan sauk’e Se na gagara sau k’ewa kuma kinsan da hakan Amma kuma ina ji ina gani Haka kika tafi kikabar ni, Tsahon wata daya kenam da wasun ‘yan kwanaki, Aisha Giwar mata, Tabbas nikam Tinda jimawa na kamu Amma ina da tabbacin kema hakan take, ina mai baku hak’uri da ke da isma’il bisa ga abunda ya faru Abaya, Tabbas hajiya bata kyauta miki ba Idan bazaki damuba ina so muhadu dake zan idan har kin huce Ina jiran sakon Amsar ki daga ‘‘HASSAN” muhuta lafiya murmushi tayi ta ce, ‘‘Isma’il Aunt zainaba” ina neman shawarin ku, Gyara zama suka yi su ka ce to muna sauraron ki, Aisha.
Dariya Aisha tayi ta ce inada wani wanda na dade tare dashi Amma kuma ina matuk’ar ji dashi sosai Amma kuma mahaifiyar sa ta gasa ni sosai A baya sannam kullum shi cikin kare ni yake A gunta dukda yasan Nine mai gaskiya Amma duk da haka yana daraja ni nima ina mutun tashi sosai amma kwatsam rana daya mahaifiyar sa tamini korar kare Tun lokacin da na bar gidan Naga ranshi baiji dadin hakan ba kwatsam seyayito ro mini sakon Yana mai bani hak’uri kan Abunda ya faru baya.
Shin wace shawara zakubani?.
Shiru isma’il yayi ya ce Aisha kinsam bazan juri ganin wani abu ya sameki ba Amma idan har kin yadda da shi ba komai, kinji ‘yar uwata farin cikina murmishi tayi ta turawa isma’il sak’on sunam Anguwar da suke, Da lamabar gidan da suke, Washe gari da misalin k’ar fe Goma zuwa shad’aya na safiya, K’iran hassan ne ya shigo Tana amsa k’iran yace Ga ninam na iso ki taho ki mana jagora, Ta taho tare da Aisha suka tari Hassan tare da mahaifiyar sa.
Daganin Aisha mahaifiyar Hassan ta gagara had’a ido da ita rik’iya ta musu har wajen hajiya suna zuwa aka musu karba ta musamman, Hassan na kallon Aisha yaga ta k’ara kyau sosai fiye da yanda yasa ba ganin ta da chan baya.
Zainaba ta fahimci hakan setayiwa aisha rad’a a kunne Ta ja ta suka fita ta barsu daga ita sai, hajiya se shi hassan, Hajiya ta ce Hassan zamu baka Aisha Amma da sharadi idan har abunda ya faru a baya ya kuma faruwa bazakar be ‘yar mu, mahaifiyar hassan ta ce A’a insha allah hakan ma bazai sake faruwa ba insha Allah, Munmiki Alk’awarin Hakan Hajiya ta ce to shikenam suntashi zasu tafi ta ce tafiya da wuri haka Isma’il ya ce A hajiya Sunkama hanya Suna tafiya Aisha tare da Zianaba, suka musu rakiya, Suka shiga mota sukayi musu by_by.
‘‘Suntafi da Sati uku se gasu Da jerin motaci, Iya kallon ta, *HASSAN* na waje Yana ta lek’e_leke Kozaiga *Aisha*, Ya k’ira wayar ta ba ta tafiya, K’iran ‘yar uwar sa, yayi Wacce da take mutu k’ar son shi, tana zuwa tace mekuma zann maka *Dan uwana* yayi murmushi yace “AISHA* na ke buk’atar Gani tayi murmushi ta ce zan jarraba ko zata fito Amma gaskiya shikenam, Bakomai.
Ta juya, tayi tafiyar ta, mahaifiyar zainaba da ‘yan uwanta ne Sunata lissafa kayan *LEFE* ‘‘MAIJIDDA” ta yiwa mahaifiyar Hassan rada Akunne, Tayi murmushi, Ana ta lissafa kayan lefe tace Ina amaryar ta mu ne Kam?.
Hajiya, Uwani, Mahaifiyar ‘‘ZAINABA” ta yi murmushi tace tana d’aki tare da yar uwar ta, K’aramar yatinya ce Ta ce Bari na k’irawo ta, Jim kadam *Asha* ta fito Daga nesa wani k’am shi ne ke tashi wanda ya bude kaffatanin gidan da k’amshi..!
Tana zuwa a durk’usa hark’asa ta sunkuyar da kanta ta gaishe da mahaifiyar *HASSAN* hajiya maijidda tare da ‘yan uwanta.
Sannam ta wuce ta bude Wayar ta, Tama gama kunnuwa, kiran Hassan tagani, tayi murmushi, Ta ce, kallagaban ka Ganinam ina kallon kak’ariso mu gaisa.
Murmushi yayi ya garzayo gurin aisha, Sunfi minti biyar suna hira Daga bisani Ta ce to ni zan koma, ta juya zata tafi, Hassan ya bita da kallo ya ce dakata…!
Kafin kitafi Ai ko murmushi Kya mini Kozanji sanyi A raina tayadda harna koma gida ina cikin shauk’i, ta juyo tayi murmushi ta ce kaji Dashi…!
Tayi tafiyar Ta,
Rana d’aya Aka saka, Daurin Auren ‘‘ISMA’IL” ta re da ”ZAINABA” haka ‘‘HASSAN” shima tare da‘‘AISHA”.
RANAR 22/GAWATAN SATUNBA/2019.
‘‘ISMA’IL” na dawowa da dare, zai wuce bangaren sa, ganin Zainaba yayi a zaune Beyi k’asa a gwaiwa ba ya toho Inda take, ya tsuguna A gafen ta Ya ce, Zainaba lafiya kuwa na ganki A zaune Kuma gashi lokacin sallar isha’i yayi, murmushi tayi ta ce wallahi bana jin dad’i ne, Isma’il yayi murmushi ya ce sorry, Be tsaya ko ina ba ya wuce Wajen ‘‘HAJIYA UWANI” yayi sallamah ta Am sa ya zauna gefe d’aya bayan ta idar da sallah, Ta juyo kan sa tayi murmushi, Ta ce To gata bata jin dad’i Anbata magani ta k’isha, Juyawa isma’il yayi ya ce Haba Zainaba Se kace wata k’aramar Yarin ya, Ya tashi Ya je Ya dauko magani Yana tahowa ta ce Akwai d’aci bazan iya shaba, Isma’il ya taho yadinga rarrashin ta har seda ta sha maganin, sannam ya debo mata zuwa a but tayi Alwala tayi sallah, Data Idar ta kalli isma’il tayi murmushi..!.
Ya kalleta ya ce Meya faru, Zainaba ta gyada kai ta ce ba komai, Kaje Ka huta Kaima, Sukayi ban kwana ya wuce Bangaren Sa, Akwana atshi ranar da aka saka ta buk’i Saura kwana uku.
Tin ranar Laraba Aka fara Shirye_shiryen buki, Ranar Asabar aka daura Aure, Da misalin K’arfe Hudu na yamma, Aisha ta na cikin d’aki tare da zainaba se rusar kuka ta ke…!.
Akazo Daukar, Amarya Isma’il ya taho Ya kamo hanun ta, Ta k’an k’a meshi Tanata famar kuka Yayita rarrashin ta, Yana kuka, Zainaba na kuka Aisha na kuka, HAJIYA ce da kanta tare da ‘yan uwanta Suka raka ta har izuwa wajen mota, Hassan na gefe Yataho suka gaisa da isma’il, Isma’il ya ce Hassan Zainaba Tana sonka sosai Dan allah ka rik’e mini ita amana Hassan yayi murmushi ya ce, isma’il Insha allah zan rik’eta Karkaji komai, Haka suka tafi Tana kuka ana rarrashin ta har izuwa Gidan ta.
Isma’il kuma suka tare da amaryar sa shima, Alhaji Yayiwa isma’il tara ta arzik’i Haka suka cigaba da Rayuwar su ba tsangwama, ba nuna warayya.
Amina ce zaune a kan wani lotsatstsen katifanta Kamar an taka bredi,gefe wani kwano ne with a remained smelly stinky tuwo miyan kuka Wanda da alama tunna jiyane
kuka take rizga Kamar ranta zai fita
innace ta shigo dakin domin ganin Lpy yau yar lelenta shiru? turus tayi tana ganin ikon malik .
wani Abu na yar lele sai ita idan Ba haka Ba ya za’ayi mutum shi daya ya zauna yana kuka babu dalili
innarce ta rafka uban salati Kamar an kama malam da karuwa tace me zangani haka aminatu Lpy ?wa yatabo min tuwalle? me ya saki kuka?
Sai alokacin Amina ta dago ta soma magana Kamar haka inna Dan Allah ki yafe min,ki roki kanwata deejeh ma tayafemin,awararta Dana karba tayi hakuri,dukan da nake mata ma na daina,kuma…kuma bazan kara zubar mata da abinci Ba kuma Wlh bazan sake kwace mata rakenta Ba Nayi alkawari har naira 50 din tama zan biyata duk rashin mutincin danakeyi Allah na dena Wlh na dena ta kara fashewa da kuka.+
Galala inna tayi tana kallonta Wai yau aminatuwa ke Neman yafiya harda kiran deejeh kanwarta, lallai za’ayi ruwa da kankara
Inna tace toh yar lelen inna yi shiru kisanar dani ya akayi.
Minal tace inna aradu mafarki Nayi Wai cutar laser fever ta kamani Wai na mutuuu!
Inna tace kinga irinta ai mutum ace sai shegiyar kazanta yaushe Rabon da Kiyi wanka Yanzu?
Kina ganin kin kyautawa kanki kenan ?
kuka ta fashe dashi tace kwana biyar ne kacal fa.
Inna tace wannan Ba laser Ba har ebola ma zata kamaki ai.
Kuka ta kara fashewa dashi tana shure shure tace haba inna dama Ba sona kike Ba ?
Kuma ai dukda bana wanka ina canja pant fah.😭4
Inna tace ni rufe wannan bakin naki karki taramun makwabta gashi duk kin cikani da warin baki.
Tashi dallah kije ki wanke baki Kiyi wanka.
Kurma ihu tayi tahau shure-shure.
Nan inna ta lallabata tace mata ai mafarki Ba Gaskiya bane…. haka dai ta hakura nan inna tace taje tayi wanka taci abinci Dan yau zata rubutar jarabawar karshe a makaranta daga shi next term zasuyi WAEC haka dai ta hakura ta shirya.
Ta fito zata tafi tace inna kin Tina wannan 100 Dana taba aramiki?
inna tace yaushe? tace lokacin nan sanda muka fara jarabawa
inna tace na Tina tace ki Dan banishi,inna tace haba yar inna nawa na baki atsakanin wannan lokacin?
Tuwalle tace ehheeeen wato dama badan Allah kika bani Ba inna ?!cabdi wallahi Nide sai kin bani kudin nan.
Inna tace sarkin jaraba, kin fita naci Kamar me, ta since bakin zaninta ta miko mata wata kodaddiyar Dari biyu tace ingo kuma kikawo mini canji domin shi kadaine gareni. Inna ta fadi dukda ko tasan da wuya ta kawo chanjin.
Yamutsa fuska minal tayi kamin ta karba tare da Cewa dande ina bukatar kudin ne da yasin bazan karba tsohuwar kudinnan Ba.
Nan ta rungumi inna Kamar da gaske sannan ta fita tare da Cewa sai na dawo sannan ta biya ta gidan su kawarta zaliha domin tafiya makaranta.
Koda aka tashi Tara(break) tsallaka katangan makaranta tayi taje tasiyo gurasa a kasuwa na duka kudin tayi sadaka dashi wa almajirai akan Allah ya kara rufawa iyayenta asiri
(dukda Cewa Amina akwai tsiwa da rashin mutunci ga Wanda ya nema amma akwaita da tausayin iyayenta sosai domin kazantarta Nada nasaba da haka acewarta Idan sabulu da turarenta basu Kare Ba ai iyayenta bazasu kashe kudi wajen siyan wani Ba shiyasa sau biyu take wanka a sati su inna har sun gaji da mata magana)
Amina Yusuf yarinya ce er shekara 18-19 farace sosai ga hanci shima daidai misali 8 figure ce ga tsayi daida gwargwado idonta ko sexy eyes ne gashin kanta kuwa ba’a magana.
Babanta wato malam Yusuf Wanda akafi sani da baban kowa carpenter ne bashida karfi amma yanada rufin asiri sannan duk anguwar ana ganin girmansa sosai manya da yara.
Asalin sa fulanin taraba ne wadda yarasa kowa NASA sanadiyyar gobara tun yana shekara 18 haka yarike Kansa har yakai 25 ananne ya dawo kano da zama inda ya hadu da falmata wanda ake kira da inna wacce take kanuriyar barno ce gyaran miki da turaren wuta take a kanon har sukayi aure dagabaya suka Koma Kaduna da zama Inda suke can cikin malali ahaka har inna ta haifi danta na fari wato Abubakar Wanda yanzu yake project a ABU amma shi yake rike kansa domin ya ragewa iyayenshi nauyi sannan yakanyi musu aike idan ya samu hali tunda Ba zaman banza yake Ba.
Daganan inna bata kuma haihuwa Ba sai bayan shekara takwas Inda ta Haifi Amina wacce take yarr jagwal ce ga neman magana,ga tsiwa, saide matsoraciya ce na masifa amma ta rike addininta dukda ko Ba ganewa ake Ba.
Minal rike da sakamakonta a Hannu miftahu (kanin hannatu zamu ganta a gaba #chapter 8 ) yace manya manyan Yan boko har an karbo sakamakon kenan da fatan wannan karan ma ba’a dauko ajinba. Cukumosa minal tayi ta naushi bakinsa tace aiko Ba Komai ni nane makarantar wasu a yawon banza za’a kare. Daidai lokacin sani (yayan bilkisu itama zamu gantaa gaba #chapter 8) ya wankawa minal mari juyowa tayi tace buhun bala’i bai ankareba yaga an nunashi wa sama an nana da kasa suka minal tamai jina-jina sannan tasa yara sukabuleshi da kasa.
A guje yara suka rugo Suna oyoyo baban kowa oyoyo baban mu! dama ya saba Dan haka yasa kullum baya rabuwa da tsaraba, hanjin ligidi mai yawa acikin bakin laida ya ciro ya basu suka karba Suna godiya kamin suka raba, wata yarinyace tace baba yau wani tatsuniya zaka mana yace tatsuniyar gizo bakin barawo zan muku.
Lado ne ya shinfida masa buhu Kamar yadda suka saba sannan Suma yaran suka zazzauna nan dattijonnan ya soma musu ta tsuniya……
Wasu samarine zaune Suna busa sigari wayan dayansu ta soma kara daukowa yayi yaga karfe alarm dinsa na large hudu ne take ya kashe sigarinsa yace kai yau fa alarm NASA mana aradu lokacin dawowan tsohonnan yayi,dariya suka fashe dashi wani yace Ba mamaki ya tsaya yiwa yara tatsuniyane. Sukace Ba shakka amma fa tsohonnan yana yiwa mutane cikas ka duba abinda yar b*ra ub*an yarnan tasa tayi dazu.
Daidai lokacin baban kowa ya karyo kwana,a take suka karkade jikinsu tare da wulla alewa a baki Dan kar yaji warin sigarin tasu.+
Nufosa suka farayi Kamar abin arziki shima da murmushinsa yaje nufosu domin yaune karo nafarko dabai kamasu Suna busa sigari Ba.
Saide kash suna motsowa kusa dashi ya jiyota aiko take annurin fuskarsa ta dauke sukace babanmu sannu da zuwa Suna masu durkusawa
bata rai yayi yace Duba su Kamar da haske Kamar mutanen arziki, Wai Ku fi sabillilahi bazakuyi wa kanku fada ba, Kamar da gaske nadau kunyi hankali Ashe da sauran Rina a kaba,
Bakusan cewa wannan shaye shayen naku yana janyowa iyayenku Bacin sunaba?ko kunaso duniya tazagesu ne?girgiza kai sukayi sukace ayi hakuri baban mu Insha Allah zamu daina.
murmushi takaici yayi domin Indai wannan alkawarinne to an karyasa tun kafin adaukesa yace Allah ya bada ikon dainawan,kuna batawa kanku rayuwa ko bakusan Cewa duk abinda mutum yayi yana kuruciyar shi zai bishi har girma ba ko kunaso idan kun hayayyafa acewa yaranku kun taba busa wiwi ?girgiza kai sukayi yace Idan yaranku suka sha Ku ya zakuji hada baki sukayi wajen Cewa bazamuji dadi ba yace Idan Baku sani bama Ku sani wannan shaye shayen yana haifar da tabin hankalin,lalacewar koda da zuciya kuma tsaf zai kashe mutum. Ku a haka zaku hadu da Allah? Kuma kuna tunanin Idan an tafi a haka ba matsala?Ba Arabic Ba bokon?Allah ya Shirya….
Tafiyarsa ya cigaba dayi yana mai fada akan yadda matasa ke bata rayuwarsu.
Majalisar su malam yakubu zai wuce sukace salamu alaikum baban kowa barka da war haka murmushi ya soma musu sannan ya mika musu hannu sukayi musabaha.
Malam isa mai wankin hula ne yace ya naganka haka ne ? baban kowa yace kaide bari yaran yanzu basu rabuwa da kayan bakin ciki yanzu na…..
Malam saminu ne yazo yana girgiza kai alamun alajabi jikinsa a sanyaye ya zauna
Baban kowa yace haba malam saminu ya haka zakazo ka zauna bako sallama? inkai kayi haka ‘yan’yan mu kuma yaya zasuyi ?
Malam saminu ne ya cire hularsa ya ajiye kana yace wato wani abune yayi mugun jijjigani, Wai yar gidan malam ado salma akayiwa fyade saboda sakacin maihaifiyarta. fita tayi bayan magariba ba’a saniba uwar kuma da bata ganta Ba bata nemeta Ba sai da taga kusan goma ya wuce shine ta Sanar da malam adon. neman duniya an mata ba’a ganta Ba yau da asuba aka yadda ita koda aka kaita asubiti likitoci nata kokarinsu amma ina. yanxu yanzunnan rai yayi halinsa,Allah ya mata rasuwa!
Shiru wajen ya dauka kamin caaan malam sambo Wanda tun dazu baiyi magana ba yace Wai salma dai guda Dana sani yar shekara 6?itafa wannan salmar dai inji malam saminu
Salati suka rafka jikin kowa yayi mugun sanyi kamar an musu duka.
Allah sarki salma yarinya mai hankali da Shiga rai. Allah yaji kanta bari anjima sai mu hadu muje muyi masa ta’aziya nan dai suka Dan tad’a kamin malam Yusuf yayi gidansa.
Koda yake tafiya a hanya sai surfo masa gaisuwa ake ta ko’ina manya da yara. Atakaice de baban kowa mai jama’a ne.
Yana isowa kofar gidan sa, basheer mai shago yace baban kowa ina wuni,Lpy klau basheeru ya shagon?basheer yace Alhamdullah baban kowa yace masha dafatan dai yauma minal bata taba kowa Ba Dan yau da safe tace Mani Wai tun jiya akace suje su karbo sakamakonsu. Basheer yace Gaskiya baban kowa yau minal bata yi hayaniya da kowa Ba hasalima ko fitowanta bangani wadda nima abin ya bani mamaki da alamu dai kawattamu ta natsu(haka basheer din ke kiranta domin ya kasance abokin ya abubakar ne tun yarinta shiyasa ma yayiwa baban kowan karya Dan kar yasa wa ransa damuwa sosai)
Baban kowa yace to Masha Allah haka akeso ai ni bara in Shiga Daga ciki ko? Allah yayi albarka basheer yace amin.
Minal na zaune tana yanka kubewataji sallamar mahaifinta hantar cikinta ne ya kada da gudu ta mike har tana tuntube a 360 ta fada daki,garin sauri ta barar da yakuwar da take yankawa innace ta haba er lele lafiyarki kuwa zaki barar mani da……
Bata ida maganar ba baban kowa ya shigo yana cewa inata sallamma Baku amsa ba Kamar ba kowa a gidan inna tace yi hakuri malam sannu da dawowa Wlh wannan yarinyarnance ta fada daki da gudu har tayi Mani bari banjika ba yi hakuri bara na kawo ma ruwa
Takalmin sa ya cire ya zauna a tabarmar dake shinfide a tsakar gidan yana Cewa halan wayanta aka kira take wannan gudu , inna dake shirin bude randa domin sachet watern su ya kare tace anya kuwa?hira fa muke daga jin sallamarka ta rusa da gudu Kamar taga aljani,baban kowa najin haka jikin sa yayi sanyi bayason irin faduwsrnan da yarda keyi a makaranta domin Hanson tayi karatu ta inganta rayuwarta
Yace takarbo sakamakon jarabawar tasu kuwa inna tace eh ta karbo dazu gasucan yana kan yana kan taaga(window),tashi yayi jiki babu kwari ya dauko ya Duba aiko Kamar yadda yace ne ankuma na 48 tazo acikin su 52 a Dan fusace yaje kofar dakin yace aminatu me kikeyi acikin dakin nan,minal tace Riga make canjawa yace inba so kike na Shiga Ba maza ki fito tace baba aradu Babu Riga ajikina wanka make shirin yi yace Kamar da haske rabon da Kiyi wanka keda kanji Ba tare da dance Kiyi Ba yanzu shekaru 6 kenan amma shikenan ni bara in dubo sakona waje.
26th April 2019
Oya show some love
By voting,
liking,
sharing
and
commenting
Tnxs for reading
Mzz untichlobanty💕Sanda ta kara kusan 5min sannan ta leko da kanta duk ta hada gumi saboda rashin gaskiya
Saukan rankwashin da tajine yasa ta sankare a wurin na wani sakanni
durkushewa tayi a wurin tana tutturo baki kamar zai taba kofa
baba ne yace rufi min baki kamin in kara miki,
Maza tashi
Mikewa yayi tana zuzzunburewa tace haba baba ko Dan wannan rankwashin da kake samani kamar abinci Ba dole na KASA kokari Ba kana taba min CPU na bakasan Cewa itace masarrafin Dan Adam ba?
yace yimin shiru kamin in da’da maki wani yar kaniya kawai,me kwakwalwar kifi Allah dai ya bude maki wannan toshesshiyar kwakwalwar taki.
kuka ta fara yi tana buga kafa ni Gaskiya baba kwakwalwata ba a toshetake baaa😭 inna tace ni yimin shiru karki taramin makwabta ehe
murya ta kara baba yace bari kiga ikon Allah mikewa yayi ya dauko sanda.
yanda Kasan Anyi ruwan sama an dauke tsit ta shanye kukan da takeyi tana tsitstsilla idanu tare da sheshsheka baba yace banson jin sheshekar nan. Ki natsu bari inga tsiyar da kika shukowa mutane wannan karan.
Mutum bashida aiki sai fada ni Nayi mamaki ma yau kusan sati 2 ba’a kawo kararki Ba.
Turo baki tayi duk yasha mai sai yalki take tace yo ai dannayi mafarkin na mutu ne kuma ko yanxu ma Ba fasawa nayi Ba.+
Kallonta baba yake har ta ida maganan ta already ya Ciro takalmi Dan haka ya lafta mata.
papers din ya fara dubawa yaga subjects 2 ne takeda A amma saura Wai sai a slow saide rubutun nan war inka gani zaka dauka wata Dr ce tayishi sai ka karanta ne kaji Kamar kayi kuka.
takaicin rashin kokari na diyartasa abar kaunarsa ne ya taso mai.
Kansa kawai yake girgizawa saboda takaici bazai musaba Idan akace masa Dan primary five ma yafi yar tasa kokari.
Tsawa ya daka mata ke zonan !
Simi simi taje ya kalleta sannan yace yanxu ke ahakan zaki tafi makarantar gaba?ki Duba fa gododuwar banza da wofi. Murmushi tayi
inna tace Allah zanci mutuncinki ana miki fada kina dariya saboda kin daina mutane ko? Tace Toh Toh Toh ni inna me Nayi ? Dakuwa inna ta mata tace kaniyarki kikayi
tace to yi hakuri bazan kara Ba shikenan aiko?yauwa inata Dan Allah ki siyan awara?harara inna ta banks mata tace ba’a siya dinba
Baba dake jinsu ya tattare takardun yana cewa ace mutum anmai repeat har sau biyu amma bai gyara ba nasan duk ajin keda zaliha kun fisu girma amma kanku Kamar kifi har gara ita akanke.
antara dakikai biyu a aji daya bakuda aiki sai ciye ciye kuma da kunada kokarinku tunda kuka fara Hulda da wannan fatiman shikenan lamuranku ya tabarbare.
tace toh Ba kai kake Bani kuddin Ba? Kuma ai fatimamma sun Koma kano.
Yace au haka zakice?
Inna tace kaga malam rabu da ita kar hawan jininka ya tashi
Mika ma innatakardun yayi yace jeki ajiye min adakin ki Dan in ina ganinsu takaici ne zai kasheni
ni inanan ina fafitikar biya miki WAEC kan arufe amma naga alama asara zanyi
Zama kusa dashi tayi ta Washe baki tace baba kawai ka barni in fara aiki a gidan abinci Dan Gaskiya ni karatun bokonnan sai a hakali bazan maka karya in batama lokaci da dukiya ba yasin dakyar in zan hada ko credit 4 me kyau a wannan WAYES din
Yasin Gaskiya kake fadi kwakwalwartawa a to she take nakifinne maganarka Ba karya.
Abin yaso bashi dariya amma sai ya Girgiza kai
yace ai ga irintanan ana WAEC kina WAYES dubaki ko ajikinki Yan ajinku zasu makarantar gaba amma ke oho ko ?kinacewa inbarki Kiyi aiki a gidan abinci
Bakiji abinda ya faru da salma Ba ko ‘yar gidan malam ado ?tana gidan ubanta ma ba’abarta Ba balleke budurwa kin tallata kanki a gidan abinci
Nan ya labarta musu abinda ya samu salma sannan yace Suma suje suyi ta’aziya.
Inna kam salati take harda kwalla tace kai duniyar nan Ba imani.
Minal ko mikewa tayi tana bubbuga kafa tace Toni baba idan ma bazaka iya barina inyo aikin Ba kawai kamin aure ka huta
Ai da gudu sukayo kanta ba shiri tayi waje tare da Jan mayafi akan igiya.
Baba yace da shegiyar kazanta ma wa zai soki?ja’ira yar kwal uba
Inna tace abita da addu’a da fata na gari kawai.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Wakarta takeyi tana tafiya ta hango murtala da wani abokinsa mai kawo masa ziyara babba yake kowa?waishi a dole Santa yaje. Zukar sigari suke Suna busa abarsu.
Tsayuwa tayi a wajensu tace anya murtala kanada hankali kuwa kullum kayita busawa ‘ya’yan hanjin ka hayaki Kana biyewa wannan sha katafin?
Dariya ya bushe dashi kamin yace minal kenan ai na Fiki hankali ma. Babba yace ke yar shila karki kawao mana raini Anan fa ko kinga sa’anki ananne?
Bata kulashiba taci gaba da yiwa murtala magana da tayi:
Dalla tafi can wallahi baka isa ba kayi kadan.
Kaikuma ta nuna babba da yarda kama daina nuna ka sanniwata kila ma sanadinka ne samari basa kulani to ka kiyaye ni.
Babba ne ya bushe da dariya Hahaha sannan yace kinfaiyi kwantai babu mai sonki sai yawo a unguwa
Dariyar takaici ta kyalkyale dashi kamin tace kaji banza botorami, yo da na Sauri miji irinka a gara na zauna Ba aure sha katafi kawai. Kuma in mijin agidan uban mutum ake rabawa sai ya hanani.
Murtala yace Ke yarinyannan zanyi maganinki fa, abokin bawa kuke fadawa maganar banza?
Minal tace da wacce itaciyar zakayi magani na? Kasan ni annobace da banida magani. Nan gani nan bari dumamen mayya in fada ma.
Murtala yace kinci darajar babanki mutumin kirki ne kuma banason rigima yau da kinga yadda ake balla kafar yarinya. Tace yo inba tsoro Ba kamaso mana wallahi kaga yadda na fito dinnan babu mutunci…. Mtsw ni banma da lokacin Dan shaye.
Tafiya tayi abunta,babba Wanda ya tsaya yana kallonta sai alokacin yace kai murtala babe dinnan tayi aradu. Kaga jiki me kyau kuwa……..
Tsaki murtala yaja kamin ya tashi yabar wajen yana gunaguni akan irin yadda babban ya nuna halin ko in kula gameda abinda minal din tamai.
27th April 2019
Show some by
voting,
Liking,
Sharing
And
Commenting
Mzz untichlobanty💕UNGUWAN SARKI,KADUNA STATE.
Unguwa ne hadadde da manya manyan mutanen Nigeria masu matsayi da kudi ke zama,unguwa ne wanda ba Wanda ya damu da me Dan uwan sa ke yi saide bangaren da jama’a ke kasuwanci toh nan ne ake gulma kamar baza’a mutu ba. Wani me machine har hantsilawa yayi saboda gulma ganin gidan mutane.
Gida ne Dan kare kamar sauran kuma ko wanne da tsarin ginin sa saide wani yafi wani amma ko wanne da kyan sa.
The mansion after passing the gate
1
Furanni ne jere gaban gidan masu ma banbantan kaka da kuma yanayi sunyi das das dasu sun kawata gidan ga bakin gate da ya kara wa gidan kyau ruwan gold ne gaba dayan sa.
Gidan a hade yake waje daya saide yana da bangare 3 ne kuma ko wanne an tsara shi ne bisa yanda mai bangaren ke son nashi da kaya me kayatarwa ba tare da anyi almubazzaranci ba.+
Wasu motoci ne guda 5 suka shigo gidan sunyi convoy dukan su bakake ne banda na tsakiya Wanda yake fari wani kurtun sojane yazo ya bude motar
Wani kyakkyawa,dogo,fari,mai saje,ga diri tabarakallah masha Allah Kamar balarabe ne naga ya fito sanya yake cikin kayan sojoji fuskannan a daure babu alamun wasa ko kadan dukka sojojinne suka Sara masa a tare baiko kulasu Ba ya shige ciki abinsa
Mahaifiyarsa ya Tarar zaune a parlour tana kallon news ga fruit a gefe tanasha hankali kwance cikin fara’a da walwalan ganin mahaifiyarsa abin kaunar sa yace mom! jin muryan Rabin ranta kuma danta wato CPT YAZEED ABDULMAJEED UMAR ta tashi yazo da sauri ya rungumeta tare da manna mata peck a kumatu yana fadin I missed u mom itama tace missed you too son
Dama tun dazu shi take jira domin tasan da dawowarsa
Tace son go and fresh up sai kazo kaci abinci ko ? smiling yayi yace okay mom tare da hayewa middle staircase saboda shine nashi , na hagu na matar shi zakiyya and the one on right for his mom.
Bathroom ya fada direct Ba tare da tinanin Komai Ba ya cika jacuzzi da ruwa yasa bathing soap and perfume ya shiga ciki ya rufe idonsa tinanin zakiyya ne ya fado mai,
shikam ya rasa yadda zaiyi da ita kai kace daura Mata shi akayi a kafa ba auren so sukayi Ba ace Sam batada time dinshi yauma da zai dawo daga tafiya she can’t stay at home just for a day thank goodness he hasn’t let her become a fulltime working wife as she wanted or else Hhhhhhh iska ya furzar domin abin ya fara isanshi Gaskiya saboda ko hakkinshi na aure yanzu da kyar yake karba agurinta.
Ganin tinananin bazai fisheshi Ba yasa ya gama wanka ya daura alwala, da Rigan wanka zai sa ya Fasa ya daura towel ya fito rike da karami yana goge silky,soft and dark hair dinshi he looking so sexy (Kamar yadda naji Yan mata na fadi danni haryau wannan shirmen baya birgeni amma danku sai na rubuta ko ya kukace? You are my first priority.)2
CPT YAZEED ABDULMAJEED UMAR kenan! Matashi me shekaru 35 da ga marigayi ALH. ABDULMAJEED UMAR
ALHAJI ABDULMAJEED UMAR is a multi millionaire international businessman with the organisations and companies namely jeedmar empire, jeedmar furnitures,jeedmar shoes and clothing,jeedmar oil company, jeedmar rice,jeedmar sugar,jeedmar cement,jeedmar orphanage and much more.
Asalinsa fulanin zamfara bayan ya gama karatu ya fara business ikon Allah cikin kankanin lokaci ya bunkasa har ya fara companies a different countries a yawon kasuwancinsa ne ya hadu da mom wacce take Nigerian-arabian wato babanta Dan Nigeria mamarta er riyad(saudi)amma a Dubai suke zaune.
Sun hadune ta sanadiyyar babanta saboda Suna kasuwanci tare sannan ya gaba da hankalinshi.
Haka dai sukayi aure kuma lokaci daya soyayya mai karfi ya Shiga tsakaninsu amma Abu daya suka rasa haihuwa haka sukayi shekara 12 Ba ko batan wata tukunna daga baya Allah ya dube su da idon rahama ya basu da namiji wadda suka samai YAZEED tun yana Yaro yakeson armies shi baya kallon cartoon irin na yara in ka Ganshi ya na kallo to sojoji ne har faint na dakin shi na sojoji ne. wata rana ALHAJI ABDULMAJEED ya tattari family dinshi gaba daya akan zasuje aikin hajji dukda Cewa wasu daga cikinsu sun sha zuwa amma wannan karon a tare yakeso suje saide mom bataje Ba itada YAZEED domin Ba tada Lpy sai akabarta tare da kakus Maman ALHAJI ABDULMAJEED.
Bayan sun sauke farali ahanyarsu ta dawowa sukayi hatsari a jirgi inda yawanci suka rarrasu wasu kuma suka sami matsalan haihuwa shi kuma ALHAJI ABDULMAJEED was paralysed. Alokacin YAZEED na shekara 13 saboda tsananin Sabon da yayi da mahaifinsa hakan yasa ya zama so moody rayuwarsa duk ta canja ya zama shiru shiru lokacin dayatafi makarantar sojoji at that tym he was 25 Anan aka aiko masa da rasuwar mahaifinsa yayi kuka har ya gaji tun daga lokacin aka dena gane kansa bayan ya kammala ya dawo anane ya saida some companies na dad dinshi to the some Arabian and British partners na dad din nasa wasu kuma ya rarrabawa family members marasa karfi sosai akan su kular mai da companies din,sai su dinga yin 50 50 atakaice de bai rike ko company daya Ba domin shi soja yakeson zama.
Alokacin da yaje wani mission a Washington Anan ne ya hadu da zaliha lokacin tana shekararta na karshe a university wasa wasa soyayya maikarfi ya Shiga tsakaninsu bayan ta kammala sukayi aure amma ita tace burinta aduniya shine ta zama businesswoman amma YAZEED yace shi bazai iya juran zama babu mace a kusa dashi Ba amma idan ta yarda zai bude mata boutique
Ganin da babu gara ba dadi yasa ta yarda plaza guda ya siya ya mayar mata boutique da office dinta aciki Dana wasu masu mukamai kadan daga cikin masu aikinta.
Amma duk da haka bai tsira Ba domin kullum batada aiki sai boutique da ka tabata boutique dinta kawai ko lokacin kanta batada shi.
Wannan kenan
Show some love by
Liking,
Sharing,
Voting
And
Commenting.
Love you Lodi Lodi sweethearts
29th April 2019
Mzz untichlobanty💕Bayan ganin tunani bazai fisheshi Ba yasa ya shafa mai ya saka 3quater irin na sojoji da bakin T-shirt ya fito mahaifiyarsa ya Tatar a parlourn tace son sai yanzu? Sosa kai yayi yace sorry mom dina na I kept you waiting ko?
Tace is okay,come and eat your food saboda na sanka idan aka biye maka zaka wuni bakaci abinci Ba gashi nan yanzu ulcer ta maka kamin kawo wuka.
Yace haba mom ya isa mana zanci muje dining din haka ta kama hannunshi takaishi taja masa kujera ya zauna ta zuba mai abincin yace kai mom this is too much tace see you, wannan abincin a 5 years old child can eat it but you hmm you will never change
smiling kawai yayi yafara ci.
Baifi 6 spoons yayi bah yace ya koshi babu yadda mom batayi Ba yace Sam ya koshi haka ta rabu dashi yaje daki domin ya huta
11:59pm (night)
Suna zaune a parlour yana kan cinyarta tana shafa gashinsa Suna Dan hirar su na uwa da d’a zakiyya ce ta shigo taci wani suit na mata takalminnan dogo Kamar zai karye
kwas kwas kwas kakejin takun takalmin ta koda ta shigo ta gansu kawai hannun tadanyi using irin hii dinnan kamin tace wlcm baby tawuce abinta
Girgiza kai kawai mom tayi kamin ta juyo ta lura Cewa dan nata na matukar son yabi matarsa amma kunyan idonta yakeji hakan yasa tace kai dagani ka gani bacci nakeji Ba musu ya tashi tare da mata peck yace good night mom sannan yahau stair case din dazai Sada shi da side din da matarshi take.+
ZAKIYYA’S POV
Tana shiga dakinta

ta yarda jakanta ta fara cire takalminta kamin ta fara rage kayan jikinta tare da daukan ribbon tana kokarin daure Malaysian attached wig dake kanta Wanda yake red,blue and black in colour taji anyi hugging dinta ta baya
Tsaki tayi kamin tace look baby am soo tired,and am not in d mood so leave me alone pls shinshinan wuyanta ya farayi yana Cewa I missed you Bea tasan sarai me yae nufi hakan yasa tayi saurin tureshi tare da fadawa toilet.
Koda ta fito yana zaune a kan gado Kamar maye yana jiranta bata ko kalli Inda yake Ba taje ta daura hannunta akan wani Dan machine Wanda zaiyi detecting tomb print dinta Wardrobe dinta ne ya baiyyana yayi typing nighties sai daya daga cikin kofofin Wardrobe din suka bude ta dauka wani brown din nylon riga tasa iya guiwa tazo ta kwannta tare da Cewa switch off d light when you are done taja bargo tare da juyamai baya
Mamaki ne ya cikashi Wai dama batasonshi ne ta aureshi koko wani abinne ya sameta coz wata matace za’ace mijinta yayi tafiya ya dawo babu ko sannu da zuwan arziki balle ayi zancen su abinci. Duk da Cewa ya saba da irin halinnan NATA amma nayau is worse haka dai yayi ta sake sake daga karshe yaje ya kwanta a bayanta yana Dan tattabata bige hannunsa tayi yace baby pls Wallahi I need you kinji ?
yadda yayi maganar ya bata tausayi hakan yasa tarabu dashi amma sai mita take masa Wai tagaji hakan yasa bai sami wani biyan bukata sosaiba masu iya magana na cewa da babu gwara Ba dadi
Koda ya tashi da asuba ya tasheta he entered the toilet did all the necessary routine,came out and found her still sleeping ya sake tashinta sannan ya fita masallati ta koma ta kwanta abinta har sai 6 ta tashi Wai bazata iyayin sallahn Ba sai ta dawo(ehm araina nace inkin dawo kuma kice kin gaji Ba Allah sai ya kyauta).
Around 7 ya dawo direct dakinshi ya wuce ya kwanta itako lokacin harta shirya tasaka pink suit mai wandon pelazu ta sauko sai shan kamshi take, ta buga uban extension akai sai yarfeshi take
Mom ce zaune a falo tana kallon news ayayinda take shan coffee,hade rai tayi domin bataso ganin mom din a parlourn ba.
Tace good morning mom,mom tace morning
Zata wuce mom tace zonan zakiyya
Zuwa tayi ta tsaya tana Duba agogonta
Mom tace yanxu abinda kikeyi ya dace kenan ki Duba wani shigar yahudawa da kikeyi koni Balarabiya banyiba,kuma ki fita tun safe sai dare sannan baki ko girmama mijinki balle ni ai ko…………
Bata karashe Ba zakiyya tace sorry mom inaso boutique dina ya tsaya dakafarsa sosaine kamin in Dan dinga samun time yanxu fai Ba wa’azi nakeso Ba ince de matsalarki bana girkine to me kikeso kici?ta fadi hakan cikin Sauri tana Duba agogonta domin tayi latti acewarta.
Mom ta girgiza kai tace zakiyya kenan so nake naci yar tsala da kunun tsakiyar tace okay kitchen ta Shiga tabi wata kofa Wanda zai sada ta side din ma’aikata taje bangaren masu girki tace pop out
Cikin kankanin lokaci sukayi layi a gabanta sanda tagama zuba musu kallon raini sannan tace waya iya kunun tsamiya da yar tsala duk sukayi shiru domin Continental dish yawanci suka iya
tsawa ta daka musu Ba daku nakeba
Ehm kwanna biyu ban tsokalo muku minal ba karkudamu yanxu Muka soma tafiya
Show love by………
Kungane ai
Love you all
1st may 2019
Mzz untichlobanty💕Daya daga cikinsu ne tace na taba gani kaka ta nayi may be zan iya
Zakiyya tace oya do it right away and take it to that old hag watace tafito daga toilet tana bada hakuri kan Lattin da tayi wani wawan mari ta sauke mata tare da Cewa you are fired ! What a piece of shit! hakuri ta fara bata tana Cewa cikinta ne ya baci ta kewaya amma ko kallonta batayi Ba
Tanashigowa parlourn tace mom am off! mom tace zakiyya nikam wannan kayan naki Kamar Ba musulma Ba zaki fita dasu kije ki saka mayafi mana
Bata rai tayi tana zunbure zunbure da huhhura hanci taje tasako wani Dan karamin hijabi. Tana fita ta tubeshi tare da Cewa haka kawai duk abi a takurawa mutum mtsww
…
Zaune take a office tana wani business deal. Telephone ta dauka ta dannan wasu lambobi bugu daya ya shiga tace coffee sannan ta kashe wata ce ta shigo dauke da kofin shayi ta ajiye tajuya tana tafiya kenan taji ruwan coffee a bayanta wani tsalle ta daka tare da Cewa jesus! Heeee I don finish oooo chai my back,my back
Zaliha ce ta wanka mata mari tare da Cewa keep your mouth shut,
Tsit tayi amma idonta bai dena zubda hawaye Ba
Are you out of your sense ya zaki kawomin coffee with white sugar while you knew that Brown sugar nakesha
Sorry ma I was not d one dat prepared the tea it was Sade.
Are you crazy?was is it not your job to make my tea? why will Sade do it?Jennifer!you are fired
Cikin kuka tace ma am sorry
Sakina is absent so I am the one attending to the customers that’s why am sorry ma
Shiru tayi kamin ta juya taje ta zauna tace I will give you last chance but if you make any mistake in the future sorry for yourself
Common get out of my office
Tashi tayi tana thank you ma,Tnx u kamin ta fita
Abangaren mom kuwa Anyi mata wani busheshshen kosai da wani tsulan kunu me gudaje kawai kallon abincin ta tsaya tanayi aranta tana Cewa”ya zama dole in nemo wadda ta iya abincin gargajiya Dan ni shekaru na ya fara ja I can’t always cook for my self la astadi’u wallah”
YAZEED kuwa sanda ya tashi duk ya gaji addu’an tashi daya bacci yayi Kamar haka (alhamdulillahil lazi ahyaniy ba’ada ma amataniy wa ilaihin nushuur )sannan ya sauka daga king size bed dinshi ya Shiga toilet yayi all the necessary routine sannan yayi wanka ya fito ya Shirya cikin kanan kaya
Yazeed’s bedroom
2
sannan ya fita domin yin break fast koda ya fito mom ya tarar tasa wani jagwalgwalo a gabanta domin shi baisan me me yar tsala ba balle wannan gaskamin da aka kawo da sunan yar tsala.
Morning mom ya fada ganin bata kulashi Ba yasa ya fahimci Cewa tunani take. Dafata yayi kamin yace mom , are you okay ? Smiling tayi tace yaron kirki har ka tashi ?
Da kai ya amsa kamin yace tinanin me kikeyi mom tace bakomai kawai ina tunanin karo mai aiki ne Wanda she will only cook and take care of me saboda duk wannan masu aikin are modern ni kuma na fara tsufa am 54 fa danma inada jiki mai kyau wani sai ya dauka am 47 so dole na rage wasu abubuwan danake yi da kaina especially abinci na. Yace to mom how do u expect us to find one ?
Tace assign one of your soldiers to go to any restaurant that cooks traditional food and then look for the best cook inso samune mace saboda banason namiji yana yawo acikin gida ba tarbiyyar musulunci bane.
A dining table tasha tea abinta shiko egg and plantain yaci
Sai brown coffee dan bai fiya shan black one Ba.
Bayan sun gama cin abincin side dinshi ya nufa yaje master balcony yana tunani rayuwarsa da zakiyya Dan so yake yace Mata ta dawo company dinshi da aiki.
Abangaren minal kuwa direct gidan su zaliha ta nufa bayan ta gama da Yan unguwantasu. Shiganta kenan iya(Maman zaliha) tace wa nake gani anan Kamar aminatu ‘yar jagwal?yau Anyi abin kai sai yanxu aka shigo? Ai mutumiyartaki tana tanata tsumayinki.
Bata rai tayi tace haba iya ni Gaskiya ki dena ce Mani yar jagwal to me zance aminatu aike da kinzo guri sai kin kawo matsala da kinzo Guri ake sanin kinzo gashi kullum sai kinzo gidan yar tsohuwa tafadi hakan cikin tsokana.
Kara bata rai tayi kamin ta tace wannan kanki ni ina zally take
Iya tace yaran zamani da wani shekiyanci suke yanzu zalihan ne ya koma zalla Toh tana daki ai sai ki Shiga
Shiga tayi ta sameta tana bacci daka mata duka tayi a gadon baya tace shegiya baccin asara ko? ana la’asar kina bacci
Zaliha tashi tayi harda er tusarta tana zare ido Dan atunaninta iya ne domin ta hanata baccin la’asar
Tsaki ta buga lokacin da taga minal ce1
Ke Wai me hakan mutun na bacci kin wani daka masa duka
Amina tace tsabar rashin Gaskiya kuma harda tusa ba
Suka fashe da dariya
Haka suka cigaba da hira kamin suka tashi sukayi sallan la’asar suka Shirya domin tafiya makaranta
Ahanyansu na tafiya ne zaliha ke Cewa minal gobe zata rakata gurin aunty fauziyya(auntyn zaliha ne wato Kanwar mahaifinta yaranta uku Aisha ,Abubakar da Muhammad tana Sana’an snacks)
Abubakar ya karye jiya a makaranta
minal tace dama Yaro da shegen kiriniya Ba dole ya karye idan Baku hanashi Ba gaba gaba har wasu zaina karyawa
Zaliha tace garashi yarone
Minal tace to me kike nufi tace me ko nake nufi?
Tace babu fa ta bude baki zatayi magane ta hango wasu en mata en Iskan anguwansu an caba ado za’aje yawon bariki Suna ganinta suka fara bata rai domin haushinta sukeji Wai ta fisu kyau,domin ko Kamar inna ta dauko amma hasken baba dukda Cewa innan ma Ba baka bace amma batada haske sosai amma akwai gashi masha Allah Wanda amina har tafita hakama kyau
Suna zuwa zasu wuce daya daga cikinsu mai Suna bilkisu(bakace er lukuta mai katon timbi ga katon lebe da kirji yadda kasan kwarya saide batada hips Wanda hakan yasa ta zama Kamar an ajiye buhun hatsi gata gajeruwa anci red lipstick,brows dinnan ba’a magana) ta bangaji Amina da kafada
Dan cika amina ta cika amma sai ta basar saboda tunda tayi mafarkin laser fever ya kasheta ta rage jagwal
Ganin bata kulasu Ba yasa sameera (doguwace siriiiiriya gashi batada shape,Ba gaba Ba baya atakaice de yadda Kasan sandar snooker ko ince 1 irinsu akewa kirarin singul amama no front no back gashi taci uwar bleaching had tafara zama danyen nama),
Tace ke Amina wannan wani irin iskanci ne zaki mangari billy ko hakuri bazaki bata ba2
Amina batace Komai Ba ta ci gaba da tafiya hannatu ce(wannan ita ba’a magana)tazo ta bankade minal ,Ai ji kake tas tas tas
TO READERS WA AKA WANKA WA MARI HAKA INDAI AMINA AKA MARA TO BA ZAMAN LAFIYA
Nide bara in labe daga bayan bishiya in debo muku rahoto
Give me some bossa
By
Voting
Sharing
Commenting
And
Liking
Your yar uwa
Examination mode on
Miss untichlobanty💕
12th may 2019Wani wawan mari amina ta sakewa hannatu har sanda taga tauraro
Sameera ce ta hayaiyako zata daki amina,wani lafiyaiyan mari
Amina ta aika mata atake ta dauke wuta ta suma zaliha ce tace ni amina zo mutafi kamin kisa da naushi Kiyi kisa taja hannunta suka tafi ayayinda akabar bilkisu sakoko a tsaye batada tudun dafawa gashi yau zasu wanki wani alhaji yace su ukun za’a hada lokaci daya (Allah shi kyauta)
Atake taji wani bakin ciki ya rufeta taji ta kara tsanan amina…..
Amina kuwa dasuka je islamiyya sunyi latti gashi malam isa ke taran latti ya iya bulala Kamar Allah ne ya aiko shi
Shikadai ne yake iya dealing da amina kuma tana tsoransa sosai amma tsabar bakin ciki da haushin daya rufe mata ido bata lura dashi Ba
Sai saukar bulala da taji batasan sanda ta karbi bulalan ta karya Ba hade da banka masa harara ayayinda ta murkuda cute pinky lips dinta tace Allah ya isa ta wuce
Malam isa sai da yasha jinin jikinsa domin yasan yadda take tsoranshi(saboda ya iya bulala itakuma duk abinda zai taba lafiyar jikinta bataso)
amma yau harda karya bulala wadda take tsoro Kamar maciji gashi fiskanta yayi jaaa(red)alamun Bacin rai kuma dama shima dai yana shakkunta karfin hali ne kawai irin nasa amma ya girgiza yau Dan haka satinnan dole ya Dan tsagaitawa amina idan Ba hakaba shima zai karbi rabonsa ko ta kullo masa jagwal.
Haka suka Shiga aji Amina tasha mur,zaliha nata aikin ban hakuri hakadai har aka tashi suka dawo gida tana kumbure kumbure.+
Bayan sallan magriba inna ta gama abinci ta kwalawa Amina kira bata amsa Ba ta kara kwala mata kira still shiru abinda bata tabayi Ba kenan akirata taki amsawa shiga dakin inna tayi thinking that something is wrong with her daughter to her surprise Amina was sitting down on her mattress
Ke yar nan dama kina jina kikai shiru to abincin ki zaki dauka she didn’t reply inna rather all she did was sip water from her tiny blue cup
Inna tace yar nan Ba lafiya Dan a yadda nasanki ko bata maki rai akayi baki wasa da tuwo amma yau ko motsi bakiyi
Ta fadi hakanne ayayinda take taba goshin Amina Dan inna ji take Amina batada Lpy domin ita bata wasa da tuwo
Jin ko magana batayiba yasa inna ta fita ta samu baba ta labarta masa abinda ta gani baba ne yace rabu da ita zamu hadu atakaice de ranan Amina bataci abinci ba.
Washe gari koda Amina ta tashi tayi shara da wanke wanke ta gama koko,
Sai wajen karfe goma ta tuna da Cewa zata raka zahra anguwa tashi tayi tasa hijabi taje dakin inna tace inna ni zan tafi gidansu zahra tace zan rakata anguwa
wani kallo inna ta watsa mata kamin tace shine gaisuwan ki ?
Amina tace mantawa Nayi ina kwana
Inna tace rike abinki
Sannan a haka zaki rakata anguwan kai Innalillahi aminatu yaushe zaki canza yau kwana uku kenan bakiyi wanka kuma a haka kike tunanin zaki samu miji ki Duba kullum in zahra zatazo gidannan kwas da ita amma ke a birkice
Since bakin zaninta tayi ta miko mata Dari biyu ki siyo sabulu da tirare dan d’uri da sabulun gashi kinji
Bubbuga kafa Amina ta fara haba inna zan bata mata lokaci fa
inna tace to wallahi inbakiyi abinda na fada Ba babu Inda zaki mutum sai shegen kazanta Allah ma daya taimaka bakida karnin kashi ai da mun mutu
Turo baki tayi tana guna guni har ta siyo ta dawo
Inna tace maza Shiga wanka ki wanke kanki sai kizo in miki kitso saura kiyimin gardama ma babu inda zaki
Subul subul tayi Kamar yadda inna ta umarceta ta shiga ban dakin shiru shiru babu ita babu labarinta inna tace wai me kike yine har yanzu kinsan dai jiranki nakeyi ko?
Fitowa tayi gefen kanta duk kunfa inna tace ke haka ake wankar duk dadewannan nanki baki daurayu Ba? Bata ko kula innar Ba ta shigewarta daki ta goge kan sosai ya zama saura damshi sannan ta zauna aka mata kitson ta dauko kayanta mai Dan haske ta saka sannan ta Dan shafa man baki sai tayi dass da ita.
Tana fitowa inna tace ko kefa amma ace mutum bayason wanka minal tace inna kwana biyu ne fa inna tace kaji banziya ko kunya bakiji har kina daga murya gararin makota suji
Tace to Nide na tafi tana fitowa Zaure ta hadu da baba tace baba ina kwana yace Lpy a’a aminatu ce haka ko bake bafa amma ace mutum kullum……………
Tace to baba ya isa mana tunda Nayi wankan ba he ka since min zani a kasuwa ba. Yace yauwa yar gari kinga in kina Dan kwalliyan nanne zaki samu miji ko Ba haka ba? murmushi tayi ya miko mata naira Dari biyu yace na sanki da awara ok gurasa watakilla shi zakije siyowa ko innan ki ce ta aike ki?
tace a’a gidan su zaliha zani zan rakata anguwa Dan auntyn ta ya karye kuma zamu tayata gyaran gida dashi ke basu Dade da kaura wannan gidan Ba
Baba yace Toh sai kin dawo amma karkiyi dare tace Toh kamin ta fita tanayi masa godiyan kudin daya bata
Tana fita tace Kamar baba yasan banda kudi wlh
Abangaren YAZEED kuwa yau ana shiri da mitimiyar domin bataje office Ba,
Ya Shirya musu evening outing zaliha anci ado makeup kamar ya zubo daga fiskanta attachment dinnan ba’a magana sai harhada rai take wai ita adole batason raini(nace uhm shi baice zaki rainashiba sai ke?)
Taku daidai take har ta iso gaban wani Mercedes Benz

sai yauki take alokacin YAZEED ya Dade yana jiranta domin yace shi da kanshi zai tuka su kuma bayason escort na soldiers ko daya.
How is the novel?is it good?any suggestions?
Ramadan Mubarak and happy sallah in advance
2nd June 2019
Show some love
Mzz untichlobanty💕Tana shigowa ya kunna mota domin yaji haushin bata masa time da tayi domin he values time so much. Tafiya suke a hankali babu Wanda ya kula kowa2
……
Abangaren minal kuwa ta isa gidan su zally ta sameta tana kwalliya an rike mirror da bakin eye pencil sai zana girannan ake baki wuluk abin abin dariya
‘Daka mata duka tayi a cinya
Kinga abinda kika jawomin ko? kullum in zakije anguwa saboda iyayi sai kinyi kwalliya kinsa inna ta Mani kitson dole ta sani kwalliya.
Sai alokacin zally ta kalle ta tace kawai kice kinyi kwalliya kinaso ki nuna mini shine zaki fake da guzuma ki harbi karsana!
To wallahi bashi dukannan.
Minal tace wannan ke ta shafa sannan ta zauna tace kinsan yau Dana hadu da baba a Zaure na dauka duka na zaiyi saboda tabarar danayi musu a gidan
Ga mamaki na bemin maganar Ba kuma harda bani kudi
zally tace iye lallai kwalliya ta biya kudin sabulu,wato haduwar taki har akan baba tayi tasiri, yo ina batun su babba?hararanta minal tayi taci gaba da cewa amma matsalata dake ko kwalliyan baki iya Ba kinsan mu yan boko kuma wayayyu anaso adinga yin make up mai kyau amma kin wani shafa powder da man baki+
Minal tace iye sannu wayaiya yar boko.
Zaliha tace ke nifa zan cigaba da karatu domin suleiman yanason inyi karatu har kudin WAEC ya biya min a wata makarantar private kuma yace zai Nayi mini lesson in munyi aure.
Minal tace lallai ma yarinyar nan wato haka zamuyi dake? tafiya makarantar gaba zakiyi ki barni? Zaliha tace a ah zama zanyi in jiraki harsai kin zama farfesiya. kallon zaliha minal takeyi yayinda zalihar taci gaba da kwalliyarta.
Can zaliha tace ni yanzu banida burin daya wuce in Tara kudin Indan siya man kara haske Dan ba’ki na yayi yawa wallahi. Minal tace man me?! Sauri zaliha tayi ta rufe mata baki tace toh sannu sarkin karadi so kike iya taji ko?
Tureta minal tayi tace to in tajin ma ai haka akeso ni ban taba Sanin bakida hankali bama sai yau,ke bakisan Cewa butulci wa Allah bane ace yayi ki baka kice Wai bakinki yayi yawa ? Kin FISA sanin daidai ne? Kuma ai koba Komai mayukan blitin dinnan yana ‘bata fata bara kiji kuma iya da lahani sosai saima kinji ciwo in yaki warkewa zakiyi bayani.
Karkiga ke baka ce wallahi wani zai iya mutuwa akan bakar mace kuma wallahi sai kiga fara ko a kafa aka daura masa sai ya kunceta.
Kima godewa Allah kinada kyau farare nawa ne munana?mtswww!
Ajiyan zuciya zaliha ta sauke kamin tace kuma fa maganar ki Gaskiya ne waje daya kika kwafsa Ba man blitin akace Ba bleaching ake Cewa. minal tace Koma menene Nide tashi mu tafi.
Zaliha tace Gaskiya kizo na Dan miki kwalliya minal tace Wanda Nayi ma ya isa. Zaliha tace shiyasa bazaki taba samun saurayi Ba ki Duba ki gani kafin a tsaida lokacin aurena samari na dayawa amma ke wa ya taba miki kallon birgewa ma?
Shiru minal tayi kamin tace kuma fa hakane wato shine sirrin baki taba fadamin Bako,Allah ya isa Zaliha tace ai shiyasa kullum inna ke miki fada akan wanka baki gane Ba. Ba sai kin nuna tsiraici ba amma de aga fuskarki da kyan gani.
Minal tace to me mike jira zana mini ado Yan mata zama tayi zaliha ta shafa mata Jan powder aka zana giran nan akayi mata Layin baki da green Yadda Kasan yar tashe
Fitowa sukayi zasu tafi sukayiwa iya sallama tanata kodasu Wai yan matanta zasu haska titi
Koda suka fita zaliha ta ballawa Amina harara tace yar uwa matsalata dake baza’a taba iya gyaraki Ba kaf duniya Ba Wanda zai iya in aka gyara nan sai asamo wani matsalan wannan wani irin tafiyane?Minal tace me matsalar tafiyannawa ?
Zally tace kinga yanda ake tafiya yanga ta soma Kamar talo talo (lol karfa kuce ina kushe characters dina zasu Waye, just for entertainment ne 😂😂)
Minal ma ta fara kwaikwayanta abin har gwara na Zally domin minal ita nata Kamar agwagwa😂.9
Ana cikin haka aka fara ruwa Kamar da bakin kwarya. Yan matan ka suka nemi wurin buya domin kada ruwa ya musu duka, amma sanda aka sami matsala domin ya ca’be musu ado
Abangaren yazeed kuwa parking yayi domin ruwan ya tsagaita ganin zakky baby ta ‘bata masa lokaci gashi ko kulashi batayi Ba balle yasa ran zata bashi hakuri abin sai ya bata masa rai
Yace
Zakky what’s all of this ?
Tace
Meaning?
Yace
first you wasted my time,also came out walking like a snail and you can’t even apologize?
Tace
What wrong have I done that I will apologise? Is it wrong to walk majestically?
Look that’s fashion
She said that Prolonging the fashion
Yace
Fashion my foot,the hell with it
Alokacin ruwan ya tsaya kunna motan yayi
Ayayinda zakky ke Cewa
Look idan ka fito dani just to disgrace me ne am not in the mood please hurry up ma ni am starving gushhh
Wani wawan acceleration ya kwasa ya kure speed din motan shi dama ba mutane akan titin
Alokacin dadai su zaliha sun fito daga Inda suka labe domin su tsallaka titi takalmin minal ya Tsinke tsallakawa zaliha tayi koda ta juya ta hango minal bata tsallako Ba tace Ki tsallako kamin abawa motocin Hannu .
Minal tace ke aradu sai na gyara takalmi na.
Zaliha tace wallahi ko ki tsallako ko in tafi in tafiyata minal tace da nace ki jiranine?
Tsugunawa tayi ta cire takalmin ta fara kokarin gyarawa yayinda zaliha tayi tafiyatta tana mai jin haushin minal din.
Neman kara minal ta farayi bata zamu Ba aiko tana Daga kanta taga wani a tsakiyar titi Dan haka Ba tare da nazari Ba ta hay kan titin domin burinta kawai ta gara takalmin ta.
Alokacin kuwa aka bada Hannu kuma daidai lokacin fada ya kaure tsakanin zakiyya da yazeed CeCe kuce suke tayi yana hankalinsa kenan daga titi yana Cewa zakky don’t try me this evening
Minal kuwa ta dauko karanta tana kokarin gyara takalmin tare da tafiya a hankali akan titin domin itama ta tsallaka taga mota a guje yana iyowa kanta
Duk kayan cikinta sanda suka kada.
Daidai lokacin yazeed ya lura da ita kokarin kaucewa yayi ya fada cikin wani Dan rami Wanda ruwa ya taru kuma ya daki motan wani
Tun daga sama har kasa yawatsawa minal ruwa ta sule ta fadi kasa yayinda mai dayan motan ya fito………………….
Hhhhh finally!
This is my sallah gift to u guys hope you like this chapter
NOTE:
All pictures of characters shown here are not related to the story.
Kindly share,like,vote and comment thank you
Much love and eid Mubarak once again
4th June 2019
Miss untichlobanty💕
Juyowa yazeed yayi ya kalli zakiyya
yace oh gush! look at the mess you caused!
Minal ko lokacin da ta d’aga idonta taga Wanda ya watsa mata ruwa ya juya yana magana da wata(saboda motar Ba ita yake using ba babu tinted)abin ya mugu bata haushi
Minal ta fara magana a hankali lallai ma mutuminnan ya watsa mini ruwa sannan ya tsaya magana da budurwarsa?
Mikewa tayi zata zazzaga masa rashin mutunci daidai lokacin me motan nan ya fito yazeed dake shirin fitowa shima yace bawan Allah kayi hakuri….
Mutumin ne yayi saurin katseshi ta hanyar Cewa wa make gaji Kamar captain yazeed murmushi yazeed yayi yace nine Dan Allah a Duba ma asarar da Nayi sai inbiya ga card dina ya fadi hakan yana kokarin bawa katinsa mutumin yace ka barshi kawai yallabai ai paint nema ya Dan kurje Gaskiya Muna alfari dakai a ka sannan Allah ya kara yi maka jagora yazeed yace ameen amma dan Allah ko wannan ne ka karba mutumin yace waneni ranka shi Dade kuda kuka bamu rayuwarku Dan kukaremu shine har sai na karbi kudinka Dan ka gurjemin mota?ai kake wallahi Ba Komai sai alolacin ya lura da zakiyya cikin fara’a yace ina wuni madam ? Ya tsine tayi kamin kasa kasa tace lafiya tana mai kauda kai.
Dariya mutuminne ya dauke yace ranka shi Dade zamu iya yin selfie? Murmushi yazeed yayi yace Ba matsala. Quick selfie mutumin ya musu sannan ya Shiga motarsa yana mamakin abinda zakiyya tamai dukda ko bai Santa Ba amma da alamu tanada alaja da yazeed din.+
Yazeed ko da ya mance da ya watsawa minal ruwa dukda ko laifinta ne tana tafiya ahankali akan titi amma shima harda laifinsa daya biyewa zakiyya ya kunna motarsa zai wuce minal tayi saurin riko hannun kofar
sauke glass yace baiwar Allah dan Allah Kiyi hakuri ban lura bane wallahi hankalina ne ya sauke Daga titin amma kema hada laifinki kina tsallaka titi bakya kallo ki kula Dan Allah
ya fadi haka yayinda ya zabgawa zakiyya harara yana kokarin Ciro kudin a aljihunsa.
ganin zakiyya ta fashe da dariya, abin ya kara bawa minal haushi
Su watsa mata ruwa amma ko su kallo Inda take yarda wani tsayawa Suna surutu da photo da wani mutumi sai kace Yan film bayan sun gama Iskancin nasu zasu ta fita rikosu shine ya wani kwame a mota yana bata hakuri
Sannan budurwarsa tana mata dariya
kwafa minal tayi kamin ta kama kwankwaso ta fara jijjiga tayi kicin kicin da ido
Tace wallahi Allah ya isa na ya za’ayi Ku watsan ruwa kuma kunai mini dariya
Babu abinda yazeed ya tsana Kamar ayi masa Allah ya isa
Hakan yasa shi mugun mamaki amma ganin fiskanta kwalliyar ta cabe bakinnan sai yalki yake Kamar tasha man gyada
Abin ya basa dariya amma ya shanye,50k ya miko mata yace gashi ki siya sabulu kije a Duba ki kiji kanwata ?
Minal tace me kuddin zai min kuma babu wani batun Kanwarka ni karkayi min zakin baki Dan bazaiyi aiki Anan Ba. Ta fadi hakan sannan ta murkutsa baki
The girl is now getting on his nerves
He just pressed his car accelerator trying to leave
Not yet Mr.yazeed abdulmajeed
Wani tsalle minal ta daka ta sake rike hannun kofarsa
Zakiyya babu abinda take sai dariya Dan ita ganin clown takeyiwa minal,fadan nasu yana kayatar da ita hakan yasa ta dauko wayarta ta fara video.
Malam ya zaka watsamin ruwa ka kusa bigeni har na fadi kasa amma ka hakimce a mota kana miko mini kudi me zanyi da kudinka?ai fitowa zakayi ka Duba Lpy ta.
Fitowa yayi a harzuke
Kusa da ita yazo ta daga kanta
Wai Wai Wai wannan dakyar in takai kafadansa ma tabdi
STORY CONTINUES BELOW

Ai bata lura gardi bane wannan sai sai basamude ma ai da batayi masa rashin kunya ba
ta wuce abinta salin alin babu wata hayaniya yanzu wannan Idan ya mata naushi daya ai har lahira.
Gaskiya dukda tana jibgar maza bazatayi koda kuskuren tunanin dukan shi Ba balle ta aikata
Yazeed yace ke wa kikeyiwa fitsara?
idonta ya ciko da hawaye a take tsoro take kar ya daketa Dan taga ya dunkule Hannu jikinta na rawa ta girgiza kai
Yace Nayi kama da sa’anki?
Tace a’a
Yace shine kike min rashin kunya
Tace ai kai ka jawowa kanka kana Abu Kamar baksan darajar dan Adam ba
Ya dalle mata baki da yatsansa
Tace Allah ya isa na wallahi bazan yafe makaba kuma bullukutut bakar mutuwa.
Yace ke zan canja miki halitta fatace Bismillahi
Daga hannu yayi Kamar zai mareta dashi bata dukan mata tace wallahi kana marina zan kira Yan sanda kaga wayata?
Yazeed yace to sai me dankin kirasu?
Tace sai en sandan su kama ka
Yace idan ni kakansu nefa?
Tace sai sojoji su kamaka
Yace idan ni ubansu ne fa?
Tace da gaske nake fah zan kirasu inka tabani
Ya matso kusa da ita yace Bismillah
Tace a ah fa
Ya kara matsowa yace ki kira mana! Ya fadi hakan da kakkausar murya
cire dayan takalminta tayi ta rike a hannun dan ta lura zaliha da haske ta tafi tun dazun ta tafi tun dazu
Tace mai zubin samudawa da ido kulya kawa sannan ta Diba aguj
Bata tsaya a ko Ina ba sai gidan aunty fauziyya zata fada a guje taji gate a kulle ga wani mota shigen na yazeed ya shigo Latin take fitsari ya cika mata Mara take gumi ya fara karyo mata.
Bubbuga gara din ta farayi aiko zaliha na bude mata ta nufi ban daki tana mai cillo da takalmanta.
Bayan ta fito aunty fauziyya tace ina kika tsaya tun dazu muMun dauka kin Koma gidane ma kuma ya akayi kika bari fitsari ya matseki?
Labarta musu abinda ya faru tayi aiko sukayita dariya zaliha tace ai in kinsan wata bakisan wata Ba 😂
Nandai zaliha ke fadamata irin haushin data bata har ta tafi ta barta
Nan aka dago da zancen auren zaliha har minal take basu labarin baba nason ya mata aure amma yace sai mai Dan ilimi
Minal tace nidai indai gidan da abinci Toh shikenan banida damuwa kai amma fa banda mai warin hammata.
Aunty fauziyya tace har kura zatace da kare maye ?
Keda bakyayin minti uku kingama wanka? Harvwani bakison mai wari?
Zaliha tace ai ta gyara yau bakiga har kwalliya na mata Ba
aunty Fa’iza tace dallah dubi wani gira Kamar Anyi bakin fenti dukkanku Ba abinda kuka iya
Haka dai suka dinga hira suna kwasar dariya Kamar Ba gobe
Minal shaf ta manta dacewa Ba kwana zatayi Ba
Aunty fauziyya kuwa ganin a holiday suke kuma taga minal da katan jaka sai ta dauka kayanta ne aciki
Zaliha kuwa dama sati zatayi mata
Aunty fauziyya Ba laifi mijinta yanada rufin asiri mijinta Dan kasuwa yanada shago akasuwa
Itakuwa tana gyaran jiki,dasu makeup,da turaren wuta Wanda inna ce ta koya mata makeup kuwa
Training class tayi
Kuma Ba laifi tana samun alheri.
Da daddare suka dafa Dan malele

suna cikin sha
Minal tace Innalillahi wa inna ilaihi raji’un
Aunty da zaliha sukace menene?
minal ta side manjan dake bin mata hannunta kamintace na manta baba yace karnayi dare
Atare sukace dama Ba kwana zakiyi Ba ?
tace eh
Aunty fauzy ta kalli agogo pass 9 tace dare kuma yayi Tara ya wuce
Wayar baba tanananko?
Minal tace eh
Aunty fauxy tace yauwa bara na kirasa na fada masa
Nan ta kira baba tace minal zata kwana a wajenta
Yace to Ba Komai daganan ma ta kara mata fada akan tsafta Dan yau yaji dadin yanda ya ganta tace Ba Komai Insha Allah zata musu fada dukkansu biyu ma
Nan sukayi sallama
Anan suka tattara suka kwanta dama mijin aunty fauziyyan bayanan.
Yazeed’s POV
Yazeed kuwa koda minal ta falfala a guje tsaki yayi yace idan na kama yarinyannan sai Nayi mugun saba mata sai ta gwammaci ba’a haifeta ba
Komawa mota yayi zakiyya nata dariya tace swthrt kaga bakinta kuwa itafa gani take ta kure kwalliya
Yazeed yace gaba zakky ke wato duk rashin kunyar da tamun Ba dameki bako? Tace wannan tsakaninku ne ai
Dear pls let’s go !
Yace my zakky you will never change
Sannan ya kunna mota suka tafi yanata gungunin abinda minal tamai zakiyya sai dariya take Kamar tababbiya
Abin mamaki take basa zakky wace iriyar mutum ce?kawai yayi smiling.
At night
After sun dawo daga dinner dinsu
Suna hira a parlour mom tana fada masa Cewa she is planning on visiting her family
Wayan YAZEED yayi ringing it was his aboki,a brother as well Jamal
Jamal yace Hello captain.
Yazeed yace Dude how far?
Jamal:guy I have a surprise for you?
Yazeed: and what’s that?
Jamal:gobe zan shigo garinku
Yazeed: are you serious?
Jamal: of course yes!
Yazeed:okay I will send habu(personal)driver to pick you up
Jamal: guy pls kazo da kanka
Yazeed: no need to plead with me I will come,by what time would u land?
Jamal:that’s why I like you,emm we will land by 12:30pm Insha Allah
Yazeed: okay see yah
Jamal: bye
Yazeed: bye…………
Hope you love this chapter?
Juma’at Mubarak
7 June,2019
Mzz untichlobanty💕DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
Morning
Koda su minal suka tashi akayiwa yara wanka sukayi karyawa suka ci Suma sukayi wanka suka danyi hira anan aunty fauziyya tayiwa minal fada sosai akan tsafta sannan ta bata wasu yan turare tace tanayin aiki dasu
ta bata wasu sako ma ta kaiwa inna(nima bansani me acikiba)
Waje ta fice domin nemo almajiri ya kai mata gyaran takalmi aiko taci karo da kandala mai gyada wanka mata mari tayi tace ke kandala da ub*nki me kikazo yi nan unguwar iye? Kuka kandalar ta fara tana kokarin kwashe gyadatta daya bare tace wallahi saina hadaki da aunty salma minal tace inkin fada kinki Allah ita kanta salmar tayi kadan. Dama Daga haka itama ta fara Daga talla ta fara bin masa unguwa unguwa yanzu ta zama magajiya. Bankadeta minal tayi tace sh*giya jaka.+
Gyaro mata takalmin akayi sannan ta kama hanyan gida domin Azahar ya kusa pass 11:00am………..
Yazeed’s POV
Yana tashi da safe after yayi all necessary things needed ya gaida mom sannan yadan fita. motanshi fara

Tare da guards 2 kamin 12:00pm yayi ya dauko Jamal
After yaje wani cafe yanashan favorite cappuccino

dinshi phone dinshi yayi ringing
Zakiyya:swthrt awhile naga fita ko?pls if you don’t mind kabiya restaurant da mukaje jiya ka siyo mana pizzan naga akwai a menu dinsu kaga sai ka daina siyowa a dayan wajen kasan yaufa Thursday
She said all of that in not more than 2 breath
Yazeed: haba dear!can’t you atleast say good morning, u didn’t ask about my well being or anything all you care about is the pizza which we will eat later at night ?
Zakiyya: sorry good morning
Hope zaka siyo pizzan ?
Yazeed: naji
Zakiyya: and also kafin ku dawo kudan biya ta boutique dina Ku karbo min wani sako( legendaries), bye love you tiiit
Yazeed:love yo…..
Oh god,bukatanta ya biya she can’t even wait for me to say bye
He called the waiter,paid for cappuccino dinshi
STORY CONTINUES BELOW

And went out security men dinshi guda biyu na biye dashi
Kofa suka bude mai ya Shiga motan sannan suka rufe daya ya Shiga drivers seat dayan kuma front passenger seat
Na driver’s seat ne ya kunna motan ya kama hanyan airport
yazeed yace we are going to zakby unique boutique before going to the airport
Drivern ya karya kwana sukayi hanyan boutique
Minal POV
Tana cikin tafiyarta tana er wakenta akan babban titi wasu en shaye shaye suka hangota
Thug 1:boss kaga wata er shila kuwa
Thug 2:kunama yarinyannan tayi
Thug 3:boss kawai mu sankacota mana
Thug 4:boss nifa inason sidin kwano
Thug 2:goje(thug1) Ku kai min ita
Mansion amma kuyi ahankali Dan yarinyar ta Shiga raina
Thug 1:lallai yarinyannan ta Shiga ranka boss tunda har sai an kaita mansion baza’ayi Anan Ba
Boss:banason maganan banza ni har kishinta ma fa ya kama ni
(Kaji min rashin kunya irin na Dan tasha Wai kishinta ya kamashi ni yama bani haushi)
All thugs:hahahahaha boss kenan mude in an gama a aiko mana
Boss:zundum me kuke jirane Ku dauko min amaryata2
Minal tana tafiya taga en shaye shaye sunyo kanta fuska tayi taci gaba da tafiya
Goje ne yace amaryar mu ji mana
Bata kulasu Ba amma tana fake dasu
Scorpion ne yayiwa Goje alama da ido akan su kamata basu ankare Ashe Amaryar su ta Dade da arar kafar kare acan nesa suka hangota ta auna a guje suma da gudu suka bita
Gudu take batasan inda take wulla kafarta ba wulan keluwa (kwana)tasha inda ta hango booth din wani mota a bude da gudu ta daga kayan ciki ta Shiga kasan kayan yazeed yaji jijjigar motan kuma baiga fitowan su ezikel Ba a karo na biyu hakan yasa ya leko
Alokacin su scorpion Suna arean motan minal ta bace musu ganin yazeed ya fito daga motan gashi wandon sojojinshi yasa da farin T-shirt Ba shiri suka bar wajen shikuma da baiga kowa Ba kawai sai ya koma
Su ezikel ne suka fito da guntun kayan suka saka a booth din kamin suka rufe
minal tana hangosu suka daura mata kaya gashi ta gansu da kaki atake wani mugun fitsari ya matseta
Yazeed ya Duba agogo yaga 11:45 sai yace kawai su kaiwa zakiyya kayan sai su wuce airport
Dan ko su Jamal din sun iso kamin su sauko, kayansu ya taho, ya fito zai bata lokaci shi kuma bayason jira
Sai yace muje gida mu sauke kayan
Driver ya kunna mota suka nufi gida
Minal tanajin an kunna motan tace shikenan za’a kaini barikin sojoji na Shiga uku na lalace.
AT JEEDMAR
Suna shigowa yazeed ko fita daga motan baiyiba yace su sauke kayan daga motan su shigar gida
Sukace yes sir!
Booth suka bude fara Ciro kayan lukman na daga Leda taga Kamar kafan mutum
Ahankali ya radawa ezikel “be ready something no dey right here
Ezikel ya Ciro AK47 dinshi ya saita daidai minal
Lukman ya ajiye ledan hannunshi ya daga daidai na kanta
Wata yar kyakkyawa ya gani mai cute pinky lips tana bacci babu Komai a fiskanta sai uban man baki Kamar zai digo
Suka furta wow a tare
Kallon juna sukayi Suna magana da ido akan yanda zasu fadawa boss
Lukman ya gyada kai alamun zaije ya fada
Kewayowa yayi murya kasa-kasa
yace boss an sami matsala
Yazeed: meaning?
Lukman: dama…em da Muka..mukaje Ciro kayan….shin……..
Yazeed: hope Ba Barin kaya kukayiba ?
ya fadi haka adan tsawace
Lukman: a a dama acikin booth…..
Ezikel ne ya tsindumo baki
Ezikel: boss lukman dey shy for u ooo,wani Yaro ne beauuuuutiful
Muka ganshi asikin booth yana bassi
Yazeed: ezikel what nonsense are you talking about ?
Ezikel: boss if adey lie,thunder fire me
Yazeed: let me go and see
Futowa yayi yazo wurin booth din minal ya gani tana bacci hankali kwance
Tabbas bazai manta wannan fiskarba
Wannan yarinyarce Wanda tamai fitsara jiya dole ya shaidata kodan man bakinnan lebensa na kasa ya gatsa
Sannan ya dakarkare ya daka mata duka a gadon baya yaga ko motsawa batayi Ba
Aranshi yace lallai wannan yarinyar ni zata nunawa jarumta
Kwata kwata bekawowa kansa Cewa zai iya yuwuwa suma tayi saboda babu ninfashi, Wanda haka abin yake suma tayi Saboda rashin ninfashi inba hakaba minal ko cinnaka ya cije ta an Shiga uku balle soja ya watsa mata yatsu biyar.
Sama ya haura domin dauko bulalar sa na sojoji sannan ya sauko ya fita sai huci yake yana Jan ido kamar wani kumurci.
Zuwa yayi ya kalli minal tana kwance yanda ya barta su lukuman a tsaye kowa da abinda ke zagayawa a cikin kwakwalwar sa.
Daga bulala sa yayi zai sauke Mata lukman yayi saurin rike hannun sa yace boss mace ce fa ina ganin kamar suma tayi a gwada yai yafa Mata ruwa. Cikin tsawa yazeed yace toh me kake jira janyo tiyo ka fesa ma yar iska.
Ezikel yace boss ruwan akwai sanyi sosai fa. Wani kallo yazeed ya aika masa yace na fika sanin haka Kamin ezikel(Ezekiel) ya kara magana
Yazeed ya warci tiyo ya fesa wa minal ruwan sanyi a kofar hanci…………..
Share
Vote
Like
Comment
And follow me!
9 June,2019
Mzz untichlobanty💕
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.A zabure ta wantsalo daga cikin booth din tana salati ta fado a gaban lukman tare da kurje hannunta
Bude idon da zatayi taga takalmin soja
sai alokacin ta tuna mai ya faru kawai sai idonta ya ciko da hawaye
Fitsarin da takeji dazu ya dawo ya cika mata Mara taf
Yau tasan ta Shiga uku kashinta ya bushe ta Shiga hannun soja
Tsawa yazeed ya daga mata ke mike tsaye !
Maza, allurar ta motsa.
Ba ita kadai Ba har su lukman Saida suka tsorata
fitsarin da takeji atake yabi jikin skirt dinta tana zazzare ido
tace kuyi hakuri walla…..
Bata karashe Ba yazeed yace shut up my friend, kalleni!
Sai alokacin ta kalleshi babu shakka wannan basamuden datayiwa rashin kunya ne jiya itakam ta shi uku Ashe soja ta tsokalo+
Duka kam yau zata shashi harda na sadaka
Tace Dan Allah kayi hakuri ka yafe mini wallahi bazan kar….
Yace shhhhh yimin shiru
Yazeed yace Samuel cage dinnan a saka kayan aiki.
Samuel yace yes sir an gama sannan ya juya da sauri har kadan sa na hardewa saboda yadda yaga tan ogan NASA ya baci.
Minal kuwa da ta San nata ya kare tafara Cewa oga sir kayi hakuri karka hadani da arna a caji office dinka wallahi ban sake wa.
Gashi idonta ya ciko da hawaye amma sunki su zubo tayi tayi sunki su zubo
Shi kuma yazeed abinda ke kara bashi haushi kenan takiyin kuka ita a dole jaruma
Karti biyu ne suka fito daga wani lungu tare da Samuel yazeed yace zaki da kadan ki ko raka ki?
Tsalle tafara tana ihu innalillahi wayyo inna na Shiga uku na lalace amma still babu hawaye waiyo Allah na Dan Allah kuyi hakuri kar ku daken.
Ganin fa da gaske in bata Mike ta fara tafiya inda suke so ta tafi ba toh akwai yuwuwar su sheke ta Dan bata Dan alamar imani a fuskan su ba.
Alokacin duka masu aikin gidan sun taru tsabagen muryarta. Shiyasa inna batason minal tana kuka ta kwammaci dije tayi sau goma akan minal tayi sau daya.
Kowa na tsoran bada hakuri kar a hada dashi,wasu kuma na mamakin mai ya hada oga da wannan yar kyakkyawar innocent yarinya Dan basu taba ganinsa a wannan yanayi Ba
dukda sunsan Cewa bayada sakin fiska ayanzu
Gashi mom batanan taje gidan friend dinta zasuyi sulhu ma yar kawar nata da mijin ta sun Sami sabani balle tasa baki
Madam zakiyya ma batanan ta tafi wani get together da sukeyi ita da business partners dinta Wanda yazeed bai Masan dashi Ba. Haka ta kwashi kafa har garin Lagos.
Da minal tayi hawaye yazeed zaisa a rabu da ita saide besan tsananin tashin hankali yasa ta kasa hawaye ba yo taga Garada kamar yan wrestling ba imani a idon su gasu ko Riga babu.
Kallonta yayi yace ke al’amarinnaki bayan tsiwa harda taurin kai ko ?
Tace wallahi oga sir Ba taurin kai bane Yazeed yace take her away. Damko ta sukayi tana burburwa tana fadin ku sake ni wallahi ku sake ni, can dai batasan yanda akayi tace wai ku wasu irin arna ne zaku rike musulma ko bakusan darajar mace bane a rayuwar ku?
Faduwa gaban yazeed yayi saboda flash da ya gani a idon sa idan zakiyya matar sa ne fa? Yazeed yace ku sake ta ta tafi da kafan ta, in tayi muku taurin kai ku harbe ta.
Sum sum ta isa har gaban wani tsamurmurin daki daya daga cikin su ya hankadi keyarta tare da rufe kofa. Tana juyawa wasu bakaken beru sukayo kanta babu shiri ta antaya a guje saide ba hanya.
Da iya karfin ta take buga kofar har Amma shiru kake ji. Kawai tayi shaddar kuda ta dauki wani guduma da ta gani cikin kayaiyakin da ke dakin. Batasan shima kayan horo bane.
Gini ta samu ta fasa ta dayan barin tana fita caraf aka danko ta. Batasan yazeed yana sane da motsin ta ba saboda yana kallon komai. Hakan yasa ya je ya jira ta gama fasawan.
Cizo ta gatsa masa a hannu Abu na farko da ta fara gani shine bushiya kawai ta dale fitsari nabin skirt dinta domin ahalin yanxu ta tsula yakai sau biyar haka ta makale bishiya kyam Lamar ranta yana jiki gwaliyo tayi ma garadan dake kokarin jijjigo ta.
Yazeed da ke kallon inda ta cije shi yace ku barta sannan ya janyo kujera ya zauna. Hakan yasa take tunanin ko kofan rago akayi Mata, AI kuwa ta samu amsar tambayar ta ne lokacin da taji mahauniyi/hawainiya ta hau jikin ta.
Da gudu ta sauko yazeed yayi musu alamu da hannu akan su kamo ta,Gudu take Suna binta har suka iso wurin swimming pools Wanda ke bayan gidan

Toh anzo wurin minal nason wasan ruwa amma bata taba Shiga mai yawa Ba gashi Ba tashin kauye tayi ba balle ta iya nitso da linkaya a rafi. Amma kuma ga kartin nan Suna tunkarota kuma wa dannan bazasuyi mata da kyau ba.
Kawai sai ta yanke shawara gwara ta fada ruwan koba Komai gawanta zatayi mutunci da ace duka ne ya sheke ta.
Finndumm!! ta fada swimming pool din, Yazeed Wanda ke tafiyan kasaita har ya iso wajen Alokacin lukman na shirin fadawa ruwan Dan ya cetota Yazeed ya dakatar dashi
Rigarsa ya cire sannan ya fada ruwan alokacin har tasha ruwa nimfashinta ya kusa daukewa ya daukota
Akunnenta ya rada mata bashi sannan ya fito da ita yacewa masu aiki su hada mata shayi mai zafi tasha sai su nuna mata side dinshi Tasameshi acan. Sannan su lukman suje su dauko jamal kuma karkowa ya sake ya fadawa mamy ko Jamal abinda ya faru
Yana kai wa nan ya wuce side dinshi
Wet trouser dinshi ya cire sannan
Ya saka wani tare da farin T-shirt kamar Wanda ya cire sannan ya fada gadonsa yana tunanin abinda zaiyiwa minal Idan ta farfado batayi kuka ba
Domin yaga sanda ta suma a hannunshi……..
Am feeling so sleepy yet typed this happy because of the love I have for u guys
Show me some love as well
11 June 2019
Mzz untichlobanty💕minal kuwa shayin dazai taimaka mata da condition din da take aka hada mata
Kamin suka samo bowl da ruwan dumi da tsumma
Sannan suka dauko first aid box domin ciwon dake hannunta har yanxu yana zubda jini duk ya bata mata hijab dinta Wanda sharkab yake da ruwa.
Tabbas ta bawa dukkan maids da securities din gidan tausayi hatta sojojin domin duk rashin imanin wasu daga cikinsu sunsan Cewa minal ta horu
What so ever her fault is.
They all look at her pitifully, how young she is,yet going through all these sort of troubles
First was her hiding inside the Booth,
Then passing out due to lack of oxygen,
Then waken up by a chilled bottle water
Then fear of being in an army’s house as an offender
Then the blood cascading from her hand making her clothes look like………
Then the looks and presence of those horrible and terrifying,wicked and huge hooligans.
Them chasing her is the biggest fear of her life
Her falling into the pool.
That one is called hopelessness………………..
Wata maid me suna tala (mai shara)ce ta sa’a tsumman a ruwan zafin ta matse sannan ta fara goge ma fiskanta
Wani nifashi taja kan ta sauke hawayen wahala suka fara zarya a idonta yadda kasan ruwan sama
Cikin 2 min harta jika sabon hijabin da ta canja ta fara jika pillow da hawaye
Maid uku ne Dama a dakin da take daya da first aid,daya bowl din warm water,daya kuma tea and toasted bread
Dukkansu idonsu ya ciko da kwalla musamman da suka ga yadda minal take kuka
Wani mahaukacin atishawan data watsa ne ya dawo dasu saga duniyar da suka fada na halin da take ciki
Katrina wacce take baturiya itace first aider na gidan2
First aid box din ta bude sannan ta ciro su cotton,dettol,spirit,iodine,and Bandage.
Treating ciwon ta fara aiko ana fara goge jinin minal tafara yarfa hannu
(nace tabdi tun ba’a saka alhaji dettol da oga iodine ba)
Yamutsa fiska take yadda kasan mai nakuda,Dettol aka yi diluting aka saka domin ayi disinfecting aiko wani kara ta sake ta mike a take tana Cewa
Dan Allah Kiyi hakuri,wallahi ni Ba mai lafi nace karki min mugunta. Itadai Katrina ganin bats gane Ba sai ta kalli sauran with a questioning look
Fassara mata sukayi kamin tace oh sai tacewa minal din
No no my dear am gonna harm you,impact am being gentle with you
Minal dai anzo gurin domin bata gane ko Abu daya data ce Ba
Hasali ma banda harm babu abinda taji sai ta dauka Cewa tayi me yasa ta Tara gashin hammata yana damunta da wari
nuna kanta tayi da yatsa cike da takaici tace yanxu bayan cinzarafin da oganku yamin,da iriyar muguntan da kike mini shine harda cin fiska?
Ina ruwanki da gashin hammatana?
Tala ne tace Kamar ya?
Minal tace inba wulakanci Ba shine zatace hammata na yana wari Wai na tara gashi
Tala ta dan dara kamim tace kai da abin dariya kike wallahi ai Ba haka take nufi Cewa tayi………………
Kara kai minal tayi alamun gamsuwa tace kiyi hakuri
STORY CONTINUES BELOW

Katrina ta gane me tace domin zama a cikin su tala
dukda Cewa dakinsu daban amma ta Dan Koyi wani Abu a Hausa
suma dai su tala dasu maimuna dasu Rabi a primary suka tsaya zama da irinsu Katrina dasu Susan yasa suka koyi English
Sai tace is okay
Cigaba tayi da treating ciwon Inda minal keta tsala ihu tana raki
Lokacin da ta gama minal ta Dade da wanka da ruwan majina da hawaye
Zata fita ne ta tana fiskanta domin tace mata take care amma me zataji zafi radau Kamar garwashi
Atake tace oh my god your temperature is so high I must give you an injection
Dan Dan Dan……..
Minal tasan sunan allura ta English gashi matsoraciyar allura ne
Aiko zazzare ido ta fara kama mushriki yaga mala’ikan mutuwa
(Karkuga laifinta Dan nima mugun tsoron allura nake da ayimin allura gwara ace Insha 50 pieces of tablets daily.4
Karkuga laifi na wa zai so a sokara masa karfe a jika?
Sha wasu they prefer injection but to me that’s a total and absolute NO. )
Ciro allura Katrina tayi ta soma jan ruwa. Wani wawan tsalle minal ta daka daga kan gadon Wanda yasa ta fado kasa tare da kwale kafanta ihu ta kurma.
Ta diba a guje binta sukayi aiko ta fada bandaki ta masa key sannan ta zare
Bubbuga kofar suka fara itako Cewa take wallahi ko su baba basu iya sawa ayi mini allura .
Ko agida har saman bishiya nake hawa har Katanga nake haurawa Dan na tsira sai nan da yakeda wurin buya masu yawa? juyawa tayi domin taga Inda ta Shiga
Sink ta fara daura idonta akai wanda ya mata Kamar tasan abin amma ba’a haka tasan shi Ba
Jacuzzi ta kalla sai tace laa irin bahon gidan aunty fauziyya amma na masu kudi
Toilet din ta kalla tace la wannan ma irin salgan bayinta Saide shima na masu kudi ne
Yasin gwanin kyau bayin Kamar kayi bacci a ciki.
Bude kofar bayin da akayi yasa ta juya Katrina ta gani da allurarta ta a hannu tare da tala,da Rabi.
Wani mahaukacin ihun data kwalla yasa su murja, atine, meramu, safiya, Hauwa, Jenifer,Susan,Emma,rabecca,sanjana,suyunjin and others shigowa dakin domin in kaji ihun zaka rantse yankata akayi
Yazeed’s pov
Yana kwance a gadonshi yana nazari har bacci ya kwasheshi.
Sama sama cikin baccinsa Kamar a mafarki yakejin ihu hakan yasa nauyin baccin ya fara saukowa daga kanshi amma bai tashi Ba
Ihun da ta kwalla yasa yayi wani mugun zabura yana zazzare ido yana muzurai domin shi ya dauka wani abin ne ya faru har ya zama ready to fight.
sai ya sake jin an kwalla wani kara,iska yaja yace ya Allah wannan wata iriyar yarinya ce haka
ta mayar min da gida Kamar mental asylum
Fita yayi ranshi a bace jijiyan kanshi duk sun tashi
Minal kuwa lokacin ta nuna Kamar tayi surrender ta fito saboda ta fahimci basuda imani zasu iya matseta karfi da yaji a danna mata karfe a jika
Rabi ne tace ko ba ke Ba fah kinga lafiya zaki samu Indian Anyi allurar
Kuma sir yace kije ki sameshi gashin bayason jira danma yasan asume kike
Katrina ce ta matso da allurar zata mata domin har ta fara gajiya da wannan hali irin na minal
supan data watsa izuwa kan gado tare da kwala ihu yayi daidai da shigowar yazeed
Fuskar nan murtuke babu annuri ko kadan yanda kasan bai tana dariya tunda aka haifeshi
Ihu daya bazo mata shi yayi sanadiyar makalewar tata sauran ihun
Shiga dakin yayi sannan ya fincikota daga kan gadon yayi wajen da ita janta yake…………..
Finally,huh
Pls all I need from you guys is to vote,like,share and comment
And thank you so much for bearing with me
CHECK OUT MY OTHER BOOKS YA JI TA MATA da YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
Good night
17 June 2019
Your sweetheart
Mzz untichlobanty💕Janta yake tana turjewa “Dan Allah oga sir kayi hakuri ka rabu dani wallahi bazan kara ba, na tuba,na tuba”
Abinda taketa fada kenan tana kokarin zare hannunta daga nasa domin tasan idan ya kaita Inda sai kaita bazataga da kyau Ba.
Store room yayi niyyan kaita.
Atish!aaaaatiiiish!!aatish!
Atishawan da take sirnanowa yasa ya fasa kaita domin yasan ta fada ruwa sanyi ya kamata ga kuran store kuma?
Maybe ma she is asthmatic. Hakan yasa juya ya canja hanya zuwa side dinshi.
Ihu take tana bashi hakuri amma Allah cikin ikonsa wannan Karen ma hawaye sun dauke kafa
(Nace kekam minal kinga ta kanki sanda ake bukatar hawaye sai su kafe sanda ba’a bukatarsu kuwa yanda kasan ruwan sama me saka ambaliya)
Bakin wata kofa wacce take barin dama da dakinshi kuma next to it ya bude. Wulla ta ciki yayi ta fada kasa sannan shima ya Shiga.
Bakin gado ya nema ya daba mazaunansa sannan ya kalleta yace knee down!babu bata lokaci tayi Kamar yadda ya umarta jiki na rawa
Sai alokacin yakalleta da kyau yarinyace sosai.
Sama da kasa yamata aranshi yace kwailace ma amma she has the guts to……….iska ya fesar a bayyane yanaci gaba da kallonta.
Itako ganin ya tsare da ido yana mata kallon tsana yasa jikinta yayi sanyi Ashe bazata kara ganin innarta da baba Ba? gashi ya Abubakar ma ya kusa dawowa nanda wata shida shima bazata gansa Ba?
Gashi dije ma takusa dawowa saga boarding Ashe bazasuga juna Ba?
Ashe ajalinta ne ya fito da ita?dama mafarkin mutuwa da taga tayi Ashe zai zamto Gaskiya?
Maganar da yazeed yayi yasa ta dawo daya tunanin da take.
Ke?kin iya up and down?
Harara ta banka mai yasin bazanyi Ba
Kallonta yayi da mamaki da kuma takaici Wai ita bakinta baya mutuwa ne?shi tunda yake banda zakiyya babu mai iya kallon idonta ma tamasa magana balle tsiwa ko zakiyya ma tasan lokacin da take haukanta. hmm zaiyi maganin yarinyarnan da alamu kanta yana rawa.
Hannu yasa ya dalle Bakin Wanda yayi sanadiyar fitar jini kamin yace
Mike ki fara up and down!
Jikinta na rawa ta fara kwanciya yayi ya rufe idonsa fuskarsa na kallon sama.
Sanda tayi kusan na Minti Biyar alokacin ta gama had a gumi sannan ta dubeshi tace oga sir kayi min rai
Wallahi bani kara maka rashin kunya jin shiru ba’a amsa mata Ba yasa ta tsaya da punishment din ta sansado ta leka fiskarsa ganin idonsa a rufe yasa tace
Kutma lallai ma mutuminnan Dan rainin hankali ne.
wato ga inji ko?inyita aiki shi yana bacci,wallahi Allah ya isa na.
Sanda takeyi harta iso Bakin kofa zata fita taji yace
Da izinin zaki aikata hakan?kuma Waye Dan rainin hankalin?
Juyowa tayi a zabure tana zare ido dama Ba bacci yake Ba?
Wayyo Allah bakinta yaja mata.
Zama yayi yace dawo ki zauna.
A hankali take takowa Kamar kazar da kawai ya fashewa a ciki harta tsuguna
Gabansa ya Muna mata ta matso tana zare idanu harta rame Kamar Ba ita ba.
Yazeed yace dago kanki dagowa tayi amma idonta a kasa.
Yace Nayi kama da sa’anki? Ta girgiza kai.
Yace kinada matsalar kwakwalwa ne?ta sake girgiza kai. Tsawo ya saka mata yace use your fucking mouth !
Itadai bata gane ba saboda accent dinsa ya mata tsauri amma sai tayi shahada wajen Cewa kayi hakuri.
Yace kintaba ziyartar gidan mahaukata ne?domin kinyi kama dasu
A ranta tace kutma wallahi ni banyi kama da mahaukata ba Saide kai ne mahaukacin.
Kaine mahaukacin shi ya bayyana azahiri wadda bata masan ya fito ba
A fusace ya mike ya yarfe ta da mari yace nine mahaukacin ?tana girgiza kai tace tace a ah dan Allah na rokeka kayi hakuri subutan baki ne bazan kara Ba. Ball yayi da ita ya fita tare da sawa kofar dakin lock yana ma fadin zan nuna miki hauka yar budurwa!
Koda ya fita waje idonshi yayi ja lukman ya gani yace ya kawo masa igiya
Cike da mamanki lukman din ya dauko igiyar yana nazarin me ogan nashi zaiyi da igiya? Dan shi baiga alamun saniya a gidan Ba lol.
Saniya minal za’a daure
Jin shiru bai dawo Ba yasa ya kwada masa kira domin ya tsani waste of time.
Da gudu yazo a kasa da da’ki’ka 2 domin Dan tazarar dake tsakanin side dinsu da kuma main one
Miko masa igiyar yayi yana Cewa oga yaushe za’a mayarda yarinyar?
Yazeed yace my friend, get out of my side!
Har lukman ya fara tafiya yazeed yace zonan.
Dawowa yayi yace masa ya batun Jamal din Ba nace a dauko shi Ba? Lukman yace su bala ne suka tafi Daukoshi.
Juyawa yazeed din yayi ya tafi Ba tare da ya tanka masa Ba.
Shiga dakinsa yayi ya samu minal Inda ya barta tayi jugum
Ba Komai ke damunta Ba illa wani bahagon yunwa domin tana fashin sallah,Kamar dai yadda kuka sani minal muguwar acici ce.
Mu hadu a next chapter domin jin yadda zata kaya tsakanin minal da yazeed.
Gaskiya you need to support me by voting, commenting, and most important sharing
Thank you!
18 June 2019
Mzz untichlobanty💕Tsugunawa yayi a gabanta yace kawo hannuki !
Kallonsa take a ranta tana Cewa dama oga sir Dan iska ne?
Dama yawanci sojojin nan mazinata ne ga shan giya da sigari
Dan iska me zibin samudawa
Tafadi hakan a zuciyarta domin it a atunaninta wani abin zaiyi da hannunta domin tun batakai haka Ba inna ke ce mata duk namijin da ya tabata bada sannin innar Ba to Dan iska ne amma banda baba da ya abubakar
Tsawa ya daka mata aiko ta miko hannun nata. Igiyan ya fara shirin kulla mata ai atake ta fara kuka da hawaye
Kallon ta yayi kamin yayi murmushin gefen baki yace:
Ashe de baki cika jarumar Ba
ai nadauka taurin kanki bazai bari kiyi kuka Ba.
Ajiye igiyan yayi a wajan ya fita daga dakin ya jirkita pin din ya rufe.
Kuka ta fashe dashi tana burburwa a kasa har ciwon dake hannunta ya fara jini bata saniba
Wani sautin da cikinta ya bayar shi ya tuna mata da cewar bataci abinci domin sau biyar takecin abinci banda kananun kwamulashe da take yi
Tunawa tayi da wani lokaci
Flash back
Inna Wai haryanzu baki gama miyar bane nifa kinsan bama er mutunci da yunwa
Inna dake kitchen tace Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un
kinga ni ki rabu dani kinfiso Nayi irin wannan miyan naku na ‘ya’yan yanxu
Amina ce tafara waka tana buga gwannon hannunta da
Iyya yunwa batada kara,iya yunwa ba’a mata lahaula,iya yunwa batada Sabo wayyo iya yunwa na iya karwa Iya yun……….
Muryan inna ta jiyo wadda ta leko tana kallon ikon Allah
ta Ce to ai bazansan kinajin yunwa Ba sai kin fara bin makwabta
Turo baki tayi tana guna guni ta mimmike kafa a kofar daki tace
inna shiyasa nace kiban na dafa kika ki ki Duba fa yadda dare tayi
Inna tace wai karfe biyar kike so na dinga gama abincin dare ne ?
STORY CONTINUES BELOW

Kara turo baki Amina tayi tace inna to ai………
Sallaman da baba ya Watso shi ya sa ta antayo da guru tana Cewa baba sannu da zuwa
Yayinda take turo baki ta huhhura hanci
baba yace :
Uwata ya akayine?
Minal tace inna ce had yanxu bata gama abinci Ba gashi yunwa nakeji gashi had dare yayi
Murmusawa baba yayi yace uwata yanzun ne dare yayi?karfe 6:30 ai beyi Ba
kinga dauko mana taburma
Taburman taje daukowa yayinda inna ke Cewa
mallan an shigo kenan,ya aikin?ai wannan sususun bata ma bari min gaisa Ba
Baba yace Alhmdllh ,uwartawa ce Ba tada dama muryarta suka jiyo ta leko ta taga(window) tana Cewa
Allah ya kawo Mani har kunnena gulmata akeyi ko?
Dariya suka fashe dashi yayinda baba yace ja’irar yarinya kasa kasa
Inna tace malam bara in kawo maka ruwa
Sai a lokacin Amina ta fito ta shimfida tabarmar yayinda baba ke Cewa
ina Kanwar taki deeje ko duk gajiyar makarantan ne?
Tace Ba wata gajiya baba tana can de tana abinda aka saba baccin asara
Baba ya Dan dara yace gaba de baccin asara ai tana kokari kayi kusan wata hudu a makarantar kwana (boarding) baka ganin iyayenka ga wahalar labour ai dole tayi bacci
Labulen da aka banko ne yasa suka dago dukkansu suka kalli kofar
STORY CONTINUES BELOW

Deejeh ce ta fito tana watsa hamma Amina ta dauje bakin tace ke dallah rufe mana shegen bakin naki me zubin sokawe
Dije tace a ah salga ne Ba sok…………..
Ai bata karashe Ba taji bugu.
Babane yace uhm yarannan bara kuga, ya mike ya tafi waje domin yayi alwala yaje masalti ya samu falalar jiran liman domin yasan idan suka fara Toh sai Allah.
Kayi magana Kamar kana zugasu kayi duka su dau gaban duniya su daurawa juna
Inna da ta dawo da ruwanta a hannu ta taradda tabargazan dake faruwa nan ta saita ma kowanne notin kansa
Nan suka ballawa kuna harara wadda yake nuni da mun daura gaba.
Innako takaici ya mata yawa
Amina akwai gajan hakuri,saurin hannu da tsiwa
itako khadijah fitsara ta mata kaka tuku a tsuliya
Bayan baba ya dawo daga masallati nan ya dauko ledan daya shigo dashi dazu yace
Uwata d’azu dazan dawo isubu mai gashi yaban tsirannen yace na kawo miki. Minal tace kace Allah ? Tana mai jin dadi.
Inna ce ta shigo da farantin tuwo malmala biyarne a ciki ta ajiye.
Washe hakwara Amina tayi tace kai inna kin kyauta wallahi Dan Nasan bazan iya kara minti 30 me kyau Ba yunwa zata kar ni
STORY CONTINUES BELOW

Bude naman baba yayi yanke 5 ne Dan haka ya mikawa minal yanka uku ta karba tana Washe baki sannan tace na gode. Yanka biyun ya mikowa deejeh wacce keta cika tana batsewa,Inna na zabga mata harara.
Juya kai tayi tace bataci tunda na Amina ne girgiza kai baba yayi kamin ya mikawa Amina yanka daya.
Karba tayi ta ajiye akan ukunta alokacin har ta cinye Mara daya ta yanko wani loma kenan baba yace
Haba mana uwata ci ahankali ai Mara biyun duka naki ne wannan lomar aiko katan gardi meji da karfi a jika albarka.
Itadai Amina ko ta Kansu bata bi Ba wani loman ta yanko Wanda yafi na farko zatakai baki idonta ya fada akan iyaye nata
Gani tayi sunata fafatawa da yanka daya Ashe ma me kitse ne.
Hawaye ne suka cika mata idanu kawai sai ta dauki daya dake gabanta takai baki.
Wani kara ta saka duk hankalin su ya dawo kanta
Ajiye musu musu ukun tayi kuma manya ne tace baba gashi kuci banaci hakorina
Inna tace kici dai sai kici ta dayan gefen tace a ah na koshi
Mikewa tayi ta fita ayayinda take leko su
Allah ya gani tanason ci amma bazata iya cinyewa iyayenta suci kitse Ba.
Wanke hannunta tayi taje ta kwanta Dan already tayi sallan issha’i
Can wajajen karfe 10 lokacin gidan yayi shiru alamun sun kwanta.
Sanda tayi ta bude kofa ta shigo falon iyayen nata Inda aka rife guntun abincin aka ajiye a saman fridge tunda Ba nefa danma garin da sanyi
Ahankali ta bude farantin aiko taga sunci sun bar yanka 2.
Dauka tayi ta gutsira wani lumshe ido tayi harda girgiza kai tana murmushi sannan ta dauki cabbage ta harba tare da kuli kuli.
Inna da baba dake labe Suna kallonta domin sunji sanda ta bude kofan suka kalli juna komawa ciki su kayi suka zauna bakin tsohuwar gadonsu hawayene fal idon inna.
Tace ashe babu abinda ya sami hakorin nata kawai dama so take iyayenta suci?
wani kaunar minal ne ya Kara dabaibaye mata zuciya. Baba yace aini Nasan Ba abinda ya sami hakorin domin naga sands ta dago taga abinda mikeci idanunta suka ciko da kwalla Nasan zatayi wani abun
Shi yasa nace miki mubar yanka 2.
Rungumesa innar tayi kamin ya rarrasheta suka kwanta zuciyarsu fal cike da son yar tasu.
Hawayen da ya gangaro kan kumatunta shi yasa ta sauke ajiyan zuciya
Tayi missing iyayenta,itakam Allah ya isanta da wannan oga sir me kama da aljanu
Toooooh Anan zan dasa aya
kwana biyu kunjini shiru wallahi makaranta ne kunsan mu Yan 100 level dole mu zage dantse balle yanxu da muke second semester atayani dai da addu’a Allah yayi mini tsari da carry over1
Seriously need your prayers!
Thanks for understanding me
Show some love by:
Sharing
Voting
Commenting
10 July 2019
Mzz untichlobanty💕
Karamarsu babbarsu😘Fitowa falo yazeed yayi ya zauna tare da fara karanta wasikar jaki
Sallamar da mamy ta watso shi yadawo dashi daga Inda ya tafi
Ganin yanayinsa yasa tace son lafiya ya na ganka haka duk ka hada gumi ko bakada Lpy ne ?
Lumshe idonshi yayi yace lapiya klau mom kawai gajiya ne
Zama tayi kamin ta kira atine ta dawo mata ruwa da drinks
Ruwan ta kawo mata tare dasu coke da fanta da Sprite da maltina da 7up da ……….
Kallon duka drinks din tayi kamin tace son yaushe za’a kawo me aikin ne danni na gaji da wa dannan gases din
Yace wallahi mom an dudduba yawancin restaurant din ba’a samu Ba amma de had yanxu ana bincikawa
Cup mom ta dauka ta zuba ruwan kamin ta kurba zata kara kenan suka jiyo Jamal na suburbudo sallama+
Mikewa yazeed yayi tare da ware hannunsa yayinda shi da Jamal din suka antayo a guje suka rungume juna Kamar wasu kananan yara
Sai alokacin suka fahimci yadda sukayi missing kuna
Ai kam gogan naka ya manta ma da akwai wani hallitar minal a gidan
Jamal yake Cewa ai Nayi fishi shine mukayi zaka daukeni amma naga sabanin haka
yazeed yace afuwan nawan wallahi wani abune ya taso
Jamal yace sunfini kenan
Yazeed yace bazaka gane bane
Jamal:
mom masa’ul khair
(good afternoon)
ina wuni?
Mom:
masa’ul noor khaifa anta ya ibny Jamal
(good afternoon how are you my Darling son jamal)
Lpy klau Ykk Dana Jamal?
Jamal:
ana bi khair wallah
(am absolutely fine)
Lpy na klau
Ain zakiyya ?
(where is zakiyya?)
Ina zakiyya?
Mom:
zahabat ilaaa boutikiha
(she went to her boutique)
Ta tafi boutique dinta
Jamal:
mata sa tarji’i?
(when is she coming back?)
Yaushe zata dawo?
Yazeed:
anta uskut tatakallam kaseer wallah walakin arafta annany annany karihtul dajij
(hey pls keep quiet,you talk too much while you know I hate noice)
Kai Dan Allah kayi shiru ka fiya magana bayan kasan na tsani hakan2
Jamal:isbir ya sadiky la atakarir Insha Allah
(sorry dude I will never repeat it okay?)
Yi hakuri mutumina bazan sake ba
Yazeed :
khairullak
(better)
yafi maka
Point out shine abinda yazeed ya fada sai ga atine da salma sunzo suka tsuguna a gabanshi
yace do the right thing sumul sumul suka tashi suka koma kitchen gasu sundawo su biyar tare da kayan abinci iri iri Suna bin hanyar dinning room
sanda suka gama jerawa tukunna yazeed yace
Dan uwa muje kaci abinci ko?
Mom tace Toni bara in Shiga ciki Dan na gaji
Sukace to mom a huta gajiya
tace shukran
(thanks)
na gode
Dinning room din suka Shiga

Jamal ya kalli abincin
yace dude ya haka ina kasar waje inci wannan yanxu nazo Nigeria ina expecting tuwo sai naga abinda na baro.
Ya fadi hakan ne a accent dinshi na balabe sai hausar tayi wani zakwai da ita amma fah bai kai na yazeed ba.
Yazeed shima cikin accent nashi na larabawa-larabawa turawa-turawa kuma cikin sanyin murya
yace yanzu muka gama maganan da mom soon har sai wannan kazantar taku ta isheka.
Kallonshi Jamal yayi irin kaji dashi kamin yace
Ka kiyaye watarana abinda kake Cewa kazanta zakazo kanaci harda santi
Yazeed ya tabe fiska Kamar yaga danmalelen da yara suka jagwalgwal yace Allah ya kiyaye
Jamal yace munanan dakai zama sukayi suka ci abincin Suna hiran yaushe rabo
Bayan sun gama ci suka tafi side din yazeed domin yin alwala su tafi masallati
Amina da taci kuka har tayi baccin wahala ta tashi sanadiyyar fitsarin daya matseta
da gudu tayi hanyar wata kofa data gani wadda take sa ran toilet ce
aiko tana afkawa taja waya super sanadin kamin ta bude kofar ya Dan bata wahala Duba da batasan irin kofar Ba
hakan ya taimaka wajen fara saukar fitsari wadda ya hadu da tiles yayi sanadin zamewar tata
Ihun data rafka kamin ta suma shi yasa yazeed da Jamal yin hanyar dakin aguje domin shi yazeed shaf ya manta da ita a side dinshi Suna Shiga dakin sukaga jini jini akasa
Sai a lokacin yazeed ya tuna da Amina na dakin
Tsayawa yayi abakin kofa yayinda Jamal ya jiga bandakin Dan ganin meke wakana
Ganin Jamal ya fito jikinshi a sanyaye yana kallon yazeed hakan yasa yazeed ya dauka ko minal ta kashe kanta
a hankali minal ta fito jikinta duk jini tana dingishi sanadiyyar zamewan da tayi wani ajiyar zuciya yazeed ya sauke ganin tanada rai
Ko kallon Inda yake Jamal baiyi ba ya fita fiskannan a daure Kamar hadari
Sai kuma ya jiyo yace me nake gani?
Cukumosa yayi tare da masa tsawa yace yazeed kayimin bayani Idan Ba haka Ba mum ta sami labari
Yazeed ya kalleshi yace mai karka fasa fada yana Dan murmushin gefen baki don’t atunaninsa wasa Jamal yakeyi
Juyawa Jamal yayi ya fita
Direct side din mom ya wuce a lokacin har ta fara bacci Kamar a mafarki takejin yadda ake buga mata kofa hakan yasa ta bude ido
Adan tsorace ta bude kofar ganin jamal fiskannan tayi jaa tace son lapiya?
Kamo hannunta yayi sai part din yazeed hankalinta a tashe Dan tadau wani abunne ya samu danta daya daya
A Abangaren su yazeed kuwa harara ya banka mata kamin yaje ya kwanta akan gadon yace tayi knee down
Tayi tsamo tsamo da ita a cikin fitsari duk ta zama abin tausayi kwalliyan duk ta cabe
Kinyin tayi illa ma turo baki da tayi alamun gardama saukowa yayi daga gadon ya daga hannunsa zai dalle bakin
Puuuuuumm aka bugo kofar dakin duk suka kalli wajen
Abangaren su inna kuwa hankalin kowa ya tashi aunty fauziyya sai kuka take acewarta laifin tane tunda a hanyarta na dawowa daga gidan tane ta bata
Baba kam ya ma kasa yin Komai Dan jinya ce ta kamasa rif daya Ba abinda yake furtawa sai Innalillahi wa inna ilaihi raji’un
Kowa hankalinsa ya tashi abin dai Ba dadi gashi ya Abubakar saura 3days ya dawo
Anan ne ink din bairo na ya kare bara insiyo wani domin rahoto muku labarin kuruciyar minal
Ku Muna Mani soyayya ta hanyar
Sharing and commenting
Sannan Ku daga darajar kuruciyar minal da kuma darajata ta hanyar dangwala wannan tauraron dake kasa
Love u wujiga wujiga
10th July 2019
Karamarsu babbarsu ce fa
Mzz untichlobanty💕Kallon wajen dukkansu biyu sukayi
Minal hawaye da majina duk sun chabe mata fiska
Jan majinan tayi kamin ta mitsitsika hanci sannan ta goge a hijabin daya hada launi daban daban kama daya kalarsa da kalar jini,da jurwayen fitsari tare da kanzon majina😂
Takowa tayi cikin dingisawa ta tsuguna tace ina kwana au ina yini hajiya
Dan Allah kicewa oga sir ya mayar dani gida wallahi yunwa nakeji gashi Nasan hankalin iyayena ya tashi.
Dagota mom tayi ta Shiga dakin tana takawa idon ta cikin na yazeed Wanda ya kasa fassara yanayin mahaifiyar tas
Bai ankare Ba yaji saukan mari
Wani tashin hankali ne ya saukar masa tunda ya mallaki hankalin kansa bai taba ganin bacin ran mahaifiyarsa akansa Ba balle ta dakesa.
Hakan yasa lokaci daya zazzabi ya rufe oga sir Dan baima lura da Cewa yana ha’bo ba+
Zama yayi kan gadon jagab Ba tare da yace Komai Ba kuma bai motsa Ba kwakwalwarsa ce ta daina aiki
Baki mom ta bude ta fara magana dukda ko zuciyarta ta girgiza ganin ta fidda jini Daga jikin Dan nata amma abinda yayi ya wuce wannan.
Haba yazeed ban taba tunanin irin haka daga gareka Ba dukda Nasan irin zaman da kakeyi da matarka ban taba tunanin ko da wasa zaka Ra’bi zina Ba
Bama a zina ka tsaya Ba zinar ma fyade kayi?
Amina jin bata gano Inda mom ta dosa Ba kuma da alama mom ta saba layi Dan da alamu bata fahimceta Ba sai tayi saurin Cewa Hajiya dama oga sir da ya fita fyade yayiwa wata?
Juyowa mom tayi fiskanta da alamar tambaya domin kanta itama ya daure shima dai Jamal hakan ta kasance masa.
Domin duk Wanda yaga minal a yanayin da take kuma acikin side din yazeed to lalle Abu na farko da zaiyi tunani shine fyade yazeed yayi mata
Duba da yadda shi Jamal din ya samota a bandaki a sume sannan tana tashi abinda ta fara yi shine kuka to lallai abinda zaizo kanka kenan.
Mom tace yata dama Ba fyade yayi miki bah ?
Minal ta gyada kai kamar kadangaruwa atake nadama ya saukarwa mom kawai sai ta kama hannun minal tayi side din ta da ita domin jin Karin bayani.
Abangaren Jamal kuwa dakin yazeed yaje ya dauko cotton sannan ya dawo zauna a gefen yazeed,cotton din yasa ya goge masa jinin sannan ya tura wani a hancin ya ruko hannun yazeed din.
Rumgumesa yazeed yayi ya fashe da kuka mai sauti Kamar maraya gaba da baya me karancin shekaru.
Jamal bai hanasa kukan Ba illa ma bubbuga bayansa da yake yi alamun lallashi
Saida yayi mai isarsa sannan ya tashi zai fita Jamal yayi saurin rikosa tare da mikewa tsaye Suna fiskantan juna yace lallai mudin abokai ne amma abokantakan ya ya karfafa Yan uwantakan mu lallai nidin na kasance mai kuskure d…………
Hannu yazeed yasa ya rufe masa baki tare da girgiza kai yace lallai nine me laifi da ban sanar dakai Ba kuma ai sanda kace zaka kawo mom saina mata bayani,na dauka wasa ne Kamar yanda ka saba Dan nima baizo kauna Cewa zakuyi min mummunar fahimta Ba saboda yanayin yarinyar. Lallai kaidin amini ne na Gaskiya saboda alkhairi kake sona dashi Dan haka karka bani hakuri.
Rungume juna suka kara yi kowannensu na hawayen farin ciki kamin kuma suka fashe da dariya suka tafi domin yin sallh Dan lokaci ya tafi.
Abangaren su mom kuwa wani daki ta kawo minal

sannan taje dakin zakiyya wardrobe din ta ta bude Dan tasan pin din taga duk babu laces da atamfofin
Wani kofa acikin dakin ta bude dakine girman sa Kamar store babu Komai aciki sai akwatina 5 wasu takalma masu kyau amma zakiyya tasa a store Wai sun tsufa alhalin Kamar saga kwalinsu aka cirosu ko kurar arziki basuyi ba
Akwatinan mom ta bude ta dauko wani lace mai kyau da takalmi da kuma hijabi sannan ta rurrufe wurin ta kawo dakin da tabar minal
Ajiye kayan tayi sannan ta kalli minal wacce ta zauna a kasa tace Yan mata tashi ki zauna akan kujera mana ayayin da take nuna mata sofan dake dakin
Girgiza kai tayi tace Ba Komai nan ma yayi
Mom ta kamo hannunta ta zaunar da ita sannan tace
ya sunanki?
Tace Amina
Mom tace ya akayi kikazo gidannan kuma me hadinki da Dana
Kallon mom minal tayi kamin ta fara kwararo mata bayani cikin nutsuwa,kamunkai da tarbiyya Kamar da gaske tun daga fitowarta daga gidan aunty fauziyya har izuwa yanxu
Not telling her that this is not the first time she met yazeed
Shiru mom tayi tana nazarta maganan
Da ta tambayi yazeed kamin ta mareshi amma ai kowaye yaga yanayin aminan abinda zai ce kenan kuma ko Ba Komai soyayya ta jawo hakan ai Dan masoyinka ke hukuntaka akan laifinka
Makiyinka ne zai ganka kana Abu Ba daidai Ba ya barka ko ya kara ma kwarin gwuiwa
Kayan ta mika mata sannan tace tayi sallah za’a kawo mata abinci kamin ta fita tana tunanin lallai yazeed bai kyautaba na azabtar da minal da yayi Ba tare da yaji mai ya kawota motansa Ba sannan taya za’ayi ta miyar da minal gida a wannen yanayin?
smiling tayi wadda ke nuna ta samo mafita
Masu aiki ta aiko da kayan abinci
Lokacin minal ta chakare tayi das da ita har taji wani fresh a jikin ta murmushi tayi tace tsabta dadi
Dakwalin ta dauko zata daura saita fasa kawai tasa hijab
Zama tayi a bakin gado tana kalon tsarin dakin
Ya mugun tafiya da imaninta
Abincin aka kawo duk babu Wanda zata iya ci sai shinkafa haka ta daure ta tuttura taci rabi Dan ita shinkafa Ba gwanarta bace
Doctor mom ta kira aka da mata su bandage a inda taciwo aka Duba kafarta targade tayi aka daure mata shima likita yace tanajin wani ciwo tace a ah Dan tasan da tace eh to allura ne😂😂
(People like me and minal come and gather here lets know our selves)9
Karamarsu babbarsu ce fa kai yau Nayi rubutu chapter har uku fa kuma ina tunanin kara wani
oya ku kirawo kawayenku da Yan uwanku masoya karatu suzo su yar da zango Anan ehee
Sannan Ku naushi star din dake kasa domin daga darajar kuruciyar minal da marubuciyar wato
Mzz untichlobanty💕
Au Ashe bansa date Ba
10 July 2019Abangaren yazeed kuwa suna dawowa daga masallati dakinshi ya koma ya kwanta domin zazzabine ya kamasa sallan ma daurewa yayi
Gawani tsananin tsanar minal dake taso masa2
Wai yau shi mom ta Mara akan wannan kazamar bagidajiyar? Kuma har ta fidda masa jini?
Lallai sai ta gane kuranta a haka bacci yayi awon gaba dashi yana nazarin yadda zai yi maganinta minal.
Haka ta kasance Abangaren Jamal domin shima zaki ya nufa yayi d’are d’are a saman gado harda cire Riga sannan ya Lula duniyar bacci.
Abangaren su inna jikin baba Ba laifi ya Dan warware amma daka gansa kasan yana cikin damuwa.
Inna ce ta dinga yi masa nasiha tana kwatar masa da hankali har ya hakura ya fita domin zuwa gidan radio da jarida ayi sanarwa ko Allah zaisa a ganta
Aunty fauziyya ma ta daina kukan,mijinta yanajin labarin yayi gida haka zaliha ma ta tattara ya nata ya nata tayi gidansu.
Sanda mahaifiyar zalihan wato iyata sami labari kafafun ta kasa riketa sukayi.
Harga Allah minal yarinya ce mai Shiga rai dukda ko bata daukan raini ga tsiwa da tasha tayi tatul.+
Hankula Kam dan banace hankali Ba sun tashi, yan anguwan su minal ma sunji tashin hankali,Yan matan nan ko da minal tayi musu saitin hamma da gyaran kafureto kwanaki sai Cewa suke Allah ya kara.
Wasu daga cikin Yan anguwan sun yi farin ciki,wasu na yada jita jitan ai iskanci ta tafi,mafi yawanci kuma na tausayawa baba saboda shidin tsoho ne mai dattako kuma ansan yadda yakeson minal shiyasa Idan tayi wasu abin ma ake boye masa.
AT NIGHT(after magrib)
Minal tana zaune a daki tayi zugum gashi bata Masan Inda wayanta yayi Ba abin duniya ya taru ya mata yawa.
Ko wani hali iyayenta ke ciki?me zata ce musu?
Kofan dakin aka turo laraba ce tace Wai hajiya tace kizo.
Amsawa tayi da Toh sannan ta dauki hijabin da aka bata tasa ta fita.
Da dingishi sannan ahankali take saukowa daga upstairs saboda tsoro da kuma rashin Sabo amma inka ganta zaka dauka damuwa ce.
Mom ce tace sauko kizo wajena kinji my daughter.
Karasa saukowa tayi taje wajen mom ta zauna a kasa. Mom tace zo zauna gefena kinji hira ta fara janta dashi itakuma sai nokewa take.
Mom tace ki saki jikinki babu abinda za’a miki kinji kai ta gyada Kamar Kadangaruwa sannan ta Dan saki jikin nata.
Suna fira kawai alarm din 8 ya buga da gudu minal ta tashi mom tace relax is time for dinner.
Batade gane me akace Ba amma ta zauna tana zazzare ido.
Maids dinne suka fara fitowa da abinci ana kaiwa dining table.
Mom ta kamo hannun minal tace muje ko Ba musu ta bita suka he wajen dinning table minal de mamaki take Wai Ashe a duniyannan akwai masu rayuwa Kamar a aljanna masha Allah dama nida su inna nane.
Sai kuma tayi chuckling to the sound of her calling inna innana.
Warmers din suka fara budewa one by one minal taga duk batasan abincin bama.
Mom tace wanne za’a sa miki minal tayi shiru domin bataso tacewa mom bazata ci Ba.
Mom ta fahimci batason abincin daga yanda tayi da fiska sai tace atine kuje kitchen tare Ku kama mata ta dafa duk abinda takeso.
Suka amsa da toh hajiya.
Mom tacewa minal tashi kije kinji kunya ne ma ya kamata taga ya akeyi Wai manya suke ramfo ka duk wayon ka ?
Tashi tayi suka Shiga kitchen din tace musu sunada dawa gyararre wanda zatayi tuwo su kace ah’ah semovita ne kawai pack daya shima ya Dade bari su Duba ko yayi expire dubawa sukayi sukaga beyi ba sai suka bata.
Tace akwai wani Abu da zata iyayin miya Kamar kuka,kubewa,ogbono,taushe sukace a’ah amma akwai ganye tace to subata nan dai ta dinga fada musu abubuwan da take so Suna dauko mata saide bata bari Susna mata hannun ba.
Haka ta fara aikinta cikin kwarewa Inda ta dafa tuwo miyan ganye ya sha kayan hadi yaji kaza tun kafin ta gama yawunta ke tsinkewa Dan mugun yunwa takeji ga kamshi daya mamaye ko ina.1
Mom tana kallo a parlour ta jiyo kamshi smiling aranta tace yarinyannan ta iya data shinkafa Dan tasan yamatan yanxu akwai maitar shinkafa(Nide ahalin tuwone😉)2
Koda ta gama warmers
(foodflask) suka kawo mata madaidai ta.
Tuwonta Mara(malmala) 3 ta saka a ciki sannan tace su bata wani flask din Malmala 5 tasa a ciki sannan ta basu tace suci nasu ne ladan tayata aiki.
Godiya suka rinka mata yayin da suke satar kallon junansu me ma’ana ‘tanada mutunci ko me yasa oga sir ya mata abinda ya mata oho?” Sai kuma sukayi murmushi. Tray suka dauko suka daura flask din nata akai sannan suka kai dinning
Fitowa tayi daga kitchen din ta nufi palour wajen mom cike da kunya tana nazarin me zata ce?
Sai kuma ta tsaya “in banda hauka irin nawa taya za’ayi Maman oga sir taci tuwo?ehm kawai bara inyi mata godiya “
Parlourn ta karasa sannan taje kusa da mom ta zauna kanta kasa tana wasa da yatsu mom cikin wasa da accent din ta na Larabawa shigen na Jamal tace daughter har kin gama mana abincin ne? Murmushi tayi kamin ta gyada kai sannan tace Nagode hajiya da irin kyautatawan ki gare…..
Bata karashe maganan ba sakamakon riko hannuta da mom tayi tace”ni ba godiya nace kiyimin ba Dan Allah nayi sannan karki kirani da hajiya kinji?zaki iya kirana da mom”
murmushi minal tayi kamin tayi subutan baki wajen Cewa inkawomiki abincinne?
Smiling mom tayi Allah ya gani bata da niyyar cin abincin amma kar minal taga Kamar kyamanta mom take sai tace ki zuba mana tare.
Zare ido tayi tace tare kuma mom tace ehm.
Girgiza kai minal tayi tana wiki wiki da ido aiko karen haukane ya cijeta bazata taba cin abinci plate daya da mom ba taje wannan oga sir din ya ganta yaci ubanta tabe baki tayi tace ko ina yayi oho.
Muryan mom ne ya datse mata tunani ta hanyar cewa wasa nake miki kinji ki dibi naki kawai zanci anjima
Gyada kai kawai minal tayi sannan ta wuce ta dibi tuwonta Mara biyu tayi sama domin kunsanta ba wasa.
Aiko ta gyara wa tuwonnan zama sosai Dan ya mata dadi.
Abangaren mom ma haka ta kasance Dan tana diban Rabin marannan tayi dakinta ta gyara masa zama tare da yaba iya girkin minal sannan ta kara samin kwarin gwuiwa kan aniyarta.2
Nikam side din masu aiki Nayi domin kar ayi bani Dan nima fa tuwonnan ya biya raina
Bazakusha mamaki ba sai sanda naci tuwo Nayi nak ai bansani yadda akayi medical yet fashion looking glasses dina ya fita ba niqabi na kam ba’a maganarsa Anan bacci yayi awon gaba dani 😴ko wanke hannu banyi ba😂
Gaskiya na gode sosai da addu’an Ku domin Alhamdulillah result ya fito kuma Nayi passing harma andawo second semester Muna shirin tafiya hutun mid semester daga nan sai test Dan haka ina bukatar wani addu’an Allah ya saka muku da alkhairi da fatan ina nisha dantar daku masoya na
Eid mubarak in advance
Nice de the one and only karamarsu babbarsu wato
Miss untichlobanty💕
5th August, 2019
Wait oooo don’t forget to vote ehee……….Da asuba bayan mom tayi sallah taje dakin minal domin ta tasheta sallahn asuba
Sallama tayi ta sameta Zaune abakin gado
Saukowa minal tayi ta tsuguna tace ina kwana haji.. Au mom
Murmushi mom tayi tace lafiya kalau ya kwanan bakunta
Murmushi minal tayi domin yadda mom din tace bakunta da kaji kasan ba bahaushiya Bace kamin tace Alhmdllh
Mom tace Ashe har kin tashi? minal tace ai tun dazu ma na tashi
Smiling kawai mom tayi tace to bara in barki ko
Domin ta fahimci minal is no comfortable
Koda mom ta fita ajiyar zuciya minal tayi domin wani azababben ciwon mara takeji ko jiya ma tayi mamaki da ciwon bai dameta ba(abinda bata saniba shine pain reliever din da aka bata jiya domin ciwon dake jikinta shi yayi aiki harda maranta)
Bayan yazeed ya dawo daga masallati alokacin dai jikinshi ba laifi ya lafa masa amma still he is not active
jallabiya ce sanye ajikinshi ya zauna abakin gadonsa yana Yan nazarce nazarcensa,can sai yaji yunwa na Dan damunsa kawai sai ya fita ko zuwa kitchen ne domin ya hadowa kansa coffee domin shi Allah ya gani bayason masu aiki Suna dafa masa abinci kawai de babu yadda ya iya ne,idan yayiwa zakiyya maganan kuma to shikenan fa sai ta birkice masa+
Dan bazai manta ba akwai wani lokaci
Zakiyya ta dawo daga party a weekend ne ma gown ne ajikinta sai attachment data kwama Kamar matan pastor takalmin nan kuwa tsini yadda kikasan Biro taku take had ta isa dakinta babu Bismillah balle salati ta fada kan gado
Alokacin karfe ukun darene yazeed kam ya gaji da irin abinda takeyi ko bazataji maganarsa ba ai ta sauke masa hakkinsa ko?
Shigowa dakin ta yayi da Dan murmushi sa yazo kusa da ita ya kwanta tashi tayi awani zabure tana bata rai kamin tayi tsaki “ni Gaskiya baby kafiya jaraba haba ace mutum duk abin atakureshi yaushe yaushe kazo dakinnan na baka aka abinda kakeso is not more than 7 weeks fa shine har ka dawo,why are you acting like a sex addict pls let me be am not in the mood mtsww
juyawa tayi domin taje ta core kayanta wani wawan fincika yayi mata ya hada da jikinsa
” ke karkiga ana daga miki kafa ki nemi ki kawo min rashin kunya mana,is it not a shame to u wani yaji kina Cewa is not more than 7 weeks kika bawa mijinki hakkinsa?2 months Ba week daya kenan and u are even bragging about it.
Who the hell do u think u are da zaki kirani da sex addict,had it been am a sex addict ke do u think ko tafiya zaki iyayi ne ke kinsanni Ba wasa,but because bakisan ya kamata Ba shine amatsayina na mijinki kike fadamin all this nonsense,hakkoki na nawa na aure kike saukewa?baki min girki,baki darajani,baki ganin kimana amtsayina na mijinki, baki bani hakkina na gado,ko girki bakiyimin balle wanki yanzu haka Inda za’a tambayeki singlets dina nawa baki sani Ba balle boxers and short nickers .
Balle abinci kam da naci da banci Ba all the same talk less of ki dafamin mahaifiyata kuwa su ……..
“Ya isheka yazeed enough is enough ince duk blabbering dinnan dan nace no sex ne ko ?
Kawai sai ta rarumo lips dinsa, already tasan weak point dinsa yazeed kuwa Dama ahannu yake kawai sai ya fada ruwa
Fadawa gado sukayi ita Asama shi a kasa tana romancing dinsa,yadau abin arziki za’ayi. Ashe so take ta tsokalo masa masifa ta gudu Allah sarki babu yanda ya iya haka ya rabu da ita tayi iya son ranta dan shikeda bukata koda yaga abun ba karau Ba kawai sai ya juya da ita,aiko Ba wani on your mass,set,ready kawai go ne. Aiki ya fara Ba wasa babu kama hannun yaro. Mai nuna mata imani Ba Dan sanda ya biya bukata ya huce haushi.
……….
Tuntube yayi da wani babban leda hakan ya bada gudun muwa wajen dawo dashi daga tunanin da yaje
Kayan da ya siyowa zakiyya hakan yasa ya fara nazarin ko ina ta Shiga
Karasawa yayi izuwa kitchen sannan ya janyo coffee maker ya fara hada abunshi.2
Toh Anan zan dasa aya ina jiran comments dinku
Much love
Miss untichlobanty💕
18th August, 2019Coffee dinshi ya hada hankali kwance dinshi yama manta da zancen wata minal
Stairs ya haura sai ya hango Kamar giftawan zakiyya tana shiga section dinta
Hankali kwance ya karasa dakin nata koda ya Shiga baisameta Ba amma yaji karan ruwa hakan yasa ya zauna bakin gado ya fara shan coffee dinshi
sip 2 yayi kamin ya laluma aljihunsa yaji babu wayarsa dayan ya duba still babu sai ya tuna Ashe yana dakinshi kuma yanaso ya Duba wasu important abubuwa hakan yasa ya ajiye coffee din sannan ya fita izuwa dakinshi
Tafiyarsa yake hankali kwance had ya isa izuwa dakinshi
Neman wanyan nasa ya farayi amma bai gani Ba
arching giransa yayi yana nazarin to ina yasa wayannasa?dube ya fara can wani mind yacemai why not ya Duba changing room dinsa tashi yayi ya Duba aikuwa ya hango wayarsa ajiye gaban mirror dauka yayi sai taga message daga mom+
Budewa yayi Kamar haka:
“Good Morning habibi!
سأخرج،لا تقلق أرجع قريبا جدا إن شاء الله
(I will go out,don’t worry I will be back soon Insha Allah)
Take care
Reply yayi mata
“Good morning to u too mom,is okay take care of your self see u later
Love yah😘”
Sa wayan yayi a aljihunsa kamin ya koma part din zakiyya
ZAKIYYA’S POV
A gajiye na Shiga dakina hakan yasa direct jakana kawai na ajiye na fada toilet kayana na fara cirewa sainaji an turo kofan dakina
Shower na kunna abina
I can’t remember sanda masu aiki suka fara zuwa dakina Ba tare da na kirasu Ba jin wani sannannen turare da kuma alamun an zauna a gado na ya bani tabbacin Cewa Ba mai aiki bane jarabben baby nane ya lallabo ko me yaje nema ?oho
(Oni ‘yasu kajimin zakiyya da tambayar banza Wai ko me yake nema?shaa later on zan tattauna akan mata masu irin wannan hali)
Alamun Kamar ya fita naji hakan yasa nayi Wankana sannan na fito sanye da da bathrobe koda na iso gaban madubi
Hango cup Nayi a ajiye juyawa Nayi name na dauko coffee ne mai zafi
Allah sarki baby na Kamar yasan yau zan bashi good news kuwa
smiling kawai tayi ta dauki coffee din ta dawo bakin gado ta zauna tana sha domin ita ta dauka yazeed din kawomata coffeen yayi
Budo kofan dakinta yazeed yayi ya hangota zaune saman gado ta daura daya akan daya tana shan coffee while scrolling her tablet
Sakoko yayi yana kallonta,shi hallin matarnan nasa yana basa mamaki ita bata hada masa Ba Shiya hadawa kansakuma ta dauka tana sha
Gyaran murya yayi ta dago tana smiling Kamar da gaske sai yaji wani babarakwai namiji da Suna haajara
Shi Rabon da tayi masa smiling had ya manta in fact wani zubin ma sai yayi kwana uku bai sata a idonsa Ba grimacing(yake) kawai yayi ya kamin ya gama shigowa dakin
Ajiye cup din tayi tazo ta rungumeshi tare da yi masa peck
Shide kallon ikon Allah yake
Janyo hannunshi tayi suka zauna akan gadon yatinda take kan cinyanshi
“Thanks for the coffee baby”
Smiling kawai yazeed yakeyi yana Dan Sosa keya sai mamaki daya cika shi Dan Rabon da tayi masa irin haka tun 4 months after bikinsu
(Gaskiya fa koni ina mamanki balle kai Wai ! ehm muje zuwa)
“Baby surprise!!!”
Dan hade giransa yayi yace and what is the surprise?
STORY CONTINUES BELOW

Smiling tayi sannan ta kwantar da kanta a kirjinsa kamin tace for the next 3 month Bazan dinga zuwa office Ba I will be at home zandinga monitoring din
Work ta gida
Yazeed yace my zakky zakky bakida dama yau kuma Yan tsokananne suka motsa ?
Dagowa tayi tace am serious kasan I don’t have time for jokes
Kallon idonta yayi tabbas shide baiga alamun karya Ba
Yace like seriously my zakky zaki zauna dani a gida for 3 months? tace “yap”
Tace ko bakajin dadi ne yace no no no that’s not the issue Ba haka bane kawai de am shocked ne bama surprise Ba
Tace you shouldn’t be kaji ko?ka kwanta bari in saka kaya inzo
Toh kawai yace da ita kamin ya kwanta yanata binta da kallo tsohon sonta na Dada hauro masa
Dogon Riga ta zaka irin cotton dinnan na zaman gida
Sannan ta dawo gaban mirror ta saka roll on kawai Dan bataso ta dagawa yazeed tsohuwar liki gefensa tazo ta kwanta ta juya masa baya
Matsowa yayi ya rungumeta tare da Cewa zakky kinsan banason ana juyamin baya koh ?
Muryarsa Kasai ya isa ya fahimtar dakai yana cikin wani yanayi
Juyowa tayi tana facing dinsa kamin tace baby am sorry we can’t……
Bata karasa Ba ya fara kissing dinta sanda yayi kusan 3 min sannan ya tsaya shan iska2
Zai Koma tace baby am off1
Wani ras yaji Wai shikam me yasa rayuwa ke masa haka da yaga ci sai yaga rashi ?
Amma dai dukda haka bazai bar dama ta wuce masa Ba Dan haka romancing dinta yayi sosai sanda ya rage zafi tukunna ya tashi yayi wanka tazo ya kwanta a gefenta a lokacin harta bingire da bacci
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Around 7:30am su mom suka isa unguwan su minal.
Minal kam sai washe Baki take yawa gonar auduga zataga innanta da baba
Kallonta kawai mom takeyi tace daughter dadi ma kikeji zaki rabu dani ko?
Girgiza kai minal tayi tace kawai Nayi kewarsu ne shi yasa
Mom tace Allah sarki anguwanku akwai amajir dayawa gasu abin tausayi duk a ramko kayan sawa basuda shi kiga wancan Dan karamin ko takalmi baiyida shi danma saiya ya cancanta a taimaka musu they need some help
Minal tace mom Ba amajir bane fa almajiri ake Cewa sai kuma tayi Dan tunawa da turanci da mom tayi a karshe help kawai ta sani sai kawai ta basar
Tace baba bala kwanar dama zaka Shiga
Kamin ta juyo ta kallo mom tace ai almajiran unguwarmu ai sunada Khan gani akan wasu.
Wasufa ko wanka basuyi basuda wajen kwana amma wadannan Ba laifi wasu fa inkika gansu Kamar masu cutan ehmm……kwa..?!kwash….
Mom tace kwashoko
Minal ta gyada kai kamin tace kwarai shi cutan tamowa Ba
Sai tace ganan gidan mun iso
Tsayawa sukayi suka sauko daga motan almajirai da masu tuyar kosai da samarin anguwa Yan zaman kashe wando Suna bawa idonsu abinci
Acikin Land cruiser fara kal suka zo
ko minal ma tasha mamaki lokacin da akace Anan zasu tafi dan San da akayi cakwakiya da ita tukun tahau domin tala Cewa akayi in bata hau Ba za’akira oga sir
Saukowa minal tayi zata antaya da gudu mom tace daughter tafiya zakiyi ki barni ?
minal tace Ahe tare tare zamu higa
(tofa minal wannan phonetics din Yan kauye ko daga ina?)
Shiga sukayi yayi da akabar malam bala awaje domin jira
ASSALAMU ALAIKUM INNATA !INNA!!INNAROS!
Hazbiyallahu la’ilaha illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem wa nakeji Kamar aminatu na
Inna ke fadin haka cikin murya mai alamun zatayi kukan dadi
Fitowa tayi yayinda baba yake biye da ita rike da hotan minal a hannunsa domin kaiwa gidajen talabijin
Let me take a nap,hmm da fatan kunyi enjoying long chapter nan mude je zuwa
Ina team zakiyya ne ?are you happy da suka dinke da yazeed?2
Team minal kada kusami damuwa everything happens for the best a gaba zaku gane dalilin dinkewar
Team yazeed how far mutumin naku fa zai danyi chilling inji Yan birni😀
Masoya Ina jiran comments dinku
Your comment determine the longness and sweetness of next chapter
Love you all takuce
Miss untichlobanty💕
23th August, 2019Am so sorry, dear reader wattpad Suna bani headache,my chapter 20 is missing and I don’t plan on rewriting it saina gama novel din duka so here is a summary of what it contain:
Emotional moment akayi sharing tsakanin minal da iyayenta yayinda mom tace musu ai bige minal sukayi Allah dai ya kare bataji ciwo sosai ba saboda gudun kar hankalinsu ya tashi yasa bata dawo da minal dinba.
Minal tayi ‘kiw da ido mom ta mata alamun karta damu nan su inna suka yiwa mom godiya tana kara nasu hakuri.
Suna zaune cikin parlour minal tace zata gidansu zaliha akace yaje amma ta kula.
Mom tace tanson yin magana mai mahimmanci dasu daidai nan ya abubakar ya dawo daga zariya yana tambayan ko an sami minal akace aiko ba gaisuwa yayi sallama ko? Hakuri ya hada sannan yace shima ayi maganan dashi.+
Nan aka gaggaisa sannan akayi masa bayanin Wacece mom. Nandai mom tayiwa su baban kalamai masu kashe jiki sannan ta nemi auren minal kuma tana fata insun yarda ta turo uncles din yazeed next week.
Miss untichlobanty💕DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
Shiru parlourn yayi yayinda kowa ke nazari aransa,mom tana fata Allah yasa su yarda
Yayinda baba ke nazarin me Yan anguwa zasuce ai Dan abin duniya ya aurarta, Yayinda inna ke Mazarin anya minal zata iya zaman gidan miji kuwa?
Yayinda ya abubakar ke farinciki finally dirty sister dinshi ta samu miji nagarcacce Duba da mutuncin mahaifiyarsa kuma dai ruwa da kankara Abu daya ne samfuri ne kawai ya banbanta
Baba ne ya dago ya kalli mom kamin yace agaskiya hajiya………
Minal koda ta fito hanyan gidansu zaliha tayi malam bala ne yayi saurin kunna mota tare dayi mata horn sannan ya zuge glass yace hajiya kihau nakaiki Inda zaki mana
Allah ya gani malam bala naaon yarinyan saboda babu ruwanta gashi batada girman kai irin na madam zakiyya
washe baki tayi kamin tace malam bala da ka barhi kawai
yace a ah dai kizo muje
shiru tayi tana Neman hujjan da zata bayar da taji medulla oblongata dinta bai harbo mata Ba kawai sai tahau baya+
Owners kwana ta Shiga sai tayi wani das da ita kamar hajiyar gaske
Kwatanta mai ta fara yi………
Zaliha’s POV
Hm
Swthrt Wai me ya samekine duk kin canja min gashi na kosa na ganki amatsayin matata
Dagaske?
Eh dagaske nake, kina gida ne?
Eh ina gida Kasan tunda aminiyata ta bata jiya….hhhh….na dawo..daga….gid……
Sai kawai ta fashe da kuka
swthrt me kike Cewa kina nufin Amina jagwal ta bata?
Tace eh,yace
Kiyi hakuri ganinan zuwa kinji ki yi shiru kinsan kukanki yana tada min hankali.
Toh kawai tace kamin suka datse kiran taci gaba da kukanta
After 10 minutes
Karan mota zaliha taji a kofar gidansu ana horn
Mamaki take Dan Ba haka karan motan Suleiman yake Ba
To kodai yasai wani mota ne?
Hakadai ta dinga sake sake yayinda take saka hijabi da takalmi Dan yau Ba kwalliya aminiya ta bata
Kofar dakin iya taleka tace mata Suleiman yazo
Iya tace to tamai iso mana tace Toh sannan ta fita
MINAL kuwa tun ahanya take sake sake yanda zatayi surprising zally Suna isowa tace baba kayi mata horn Dan Allah
Yace toh yata sannan yayi horn Kamar bayan minti biyu saiga zaliha ta fito
Tsayawa tayi sakoko tana kallon motar kawai sai ta basar tahau waige waige tana Neman motan future hubby dinta da taga dai babu alamarsa kawai sai ta juya zata koma ciki tana mai yana kyau irin na motar
Daidai lokacin minal tace wa bala ya sauke mata window ta control din wajensa akwai Abu a hannunta
agaskiya dai babu Komai a hannuta tana tsoran kar yaje ta taba abinda Ba daidai bane ta lalatawa mutane mota wannen azzalumin oga sir din ya kasheta Dan bayida imani
STORY CONTINUES BELOW

(Kaji fa minal Wai bayida imani hmm Allah dai ya kyauta)
Yana saukewa kuwa tace “Yan mata ki mana” tana dariyan shekiyanci
Zaliha dai inba kuskure take Ba to lallai muryan minal taji may be depression na batan minal din yasan ta fara imagining things
Juyowa tayi aiki karaf suka hada ido murza idonta tayi yayinda bakinta ya budu mamaki da tambayoyi fal ranta
Da sauri ta karaso tana mai saka hannu domin taba fiskan minal Dan ta tabbatar da kokontonta
Aiko minal dince Ba gizo gizo Ba
Cikin dashasshiyar murya tace minal
Smiling minal tayi tana gyada kai
Zaliha tace Kece ?minal tace nice
Bude kofan motan tayi ta sauko kamin suka daka tsalle atare suka rungume juna suna ihu tare da juyi
Smiling kawai baba bala keyi
Nanfa minal ta juya tacewa baba bala zai iya tafiya
Yace hajiya kin tabbata Ba matsala? murmushi ta masa alaman eh kamin sukayi jikin gida aguje sai dakin iya bakinnan nasu har kunne
Aiko iya taji dadin ganinta sosai bayan ta mata jaje ne suka fito suka koma dakin zaliha
Zaliha tace kawas wayar dani, Wai yankan kai kika fara ne?ko sata?ko kidnapping?
Minal ta kyalkyale da dariya tace Kamar kinsan yanxu haka kanki nazo cira kuwa
Ai bashiri zaliha ta rufe kanta
Wannan karan minal dariya take harda buga cinya tace ke dallah wasa nikeyi matsoraciya
Zaliha tace anji ai tsoran ma da dalili nakeyi nidai yi mini bayanin yadda akayi kika samu mota irin wannan kuma harda driver
Minal tace “jiya……..
Nan ta labarta mata abinda ya faru Kamar yadda mom ta tsara har izuwa yanzu zaliha ko sai gyada kai take Kamar kadangaruwa alamar gamsuwa
Minal ko taki fada mata Gaskiya ne saboda tasanta da karadi yanxu sai tayi subul da baka ta fada Ba tare da tasani Ba
Aiko hira suka kafa minal na bata labarin yadda gidan su yazeed din yake wani abin ma Zaliha sai tace “kai minal arage na tomorrow”
minal tayita rantsewa amma zaliha bata yadda ba
Wayan zalihanne yayi ringing ta Duba Suleiman ne dauka tayi yace mata ya iso tace to gatanan zuwa kamin suka fito ita da minal
Jingine yake ajikin motarsa kin 406 Yace lallai ma swthrt dama kawai so kike kiga fiskana shine kika wani cemin minal ta bata minal tace eh hakane na bata amma yanxu na dawo
nan zaliha ta labarta masa abinda ya faru yace Allah dai ya kiyaye na gaba tace Ameen
Hira suka ci gaba dayi abinsu sai wajen azahar tukunna minal tace zata tafi Suleiman yace bari ya rage mata hanya
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
………agaskiya hajiya Duba da irin mutunci da karamci da kika nuna mana dukda Cewa kin fimu arziki zamuso kuma zamuyi farin ciki ace Mun hada jini dake saide wani hanzari Ba gudu ita yarinyan bamusan ra’ayinta Ba
Dan! Dan!! Dan!!!
Gaban mom ne ya fara lugude lallai dakyar minal zata yarda da wannan batu Duba da irin abinda yazeed din ya mata saide ikon Allah
Tace to shikenan ga card dina duk shawaran da kukayi sai kusanar dani ko?sukace Insha Allah
Sannan ya Abubakar ya amsa card din
Yayi waje shida baba yayinda inna ta bisu da Karin kumallo sannan ta dawo ta sami mom bata fara Ciba
Tace hajiya kick mana mom tace aike make jira muci tare sannan ki dena ce min hajiya kicemin yar uwa
Toh kawai inna tace sannan ta zauna suka fara ci tana mai kara jin mom har cikin ranta
Wajajen azahar saiga minal ta Shigo alokacin mom ta Dade da tafiya
Baba da ya Abubakar ta gani zaune suna dan hiransu yayin da inna ke dafa abinci
Tsalle minal ta daka taje ta fada jikin sa
Baba yace yi ahankali kada ki karya Mani d’a
//inal tace ai Nayi kewansa ne nan ta jona aka ci gaba da labari da ita can inna ta leko tace a ah har kin dawo kenan? Tace eh
Inna tace ya kika tadda kawar taki minal tace lahiyatta lau kawai de tayi kuka ne baba yace Allah sarki
Inna ce tayi ma baba Alama da ido Cewa ya fada mata
Gyara zama yayi yace AMINATU
Tace na’am baba yace ki saurareni da kyau sannan Kiyi tunani
Tace Toh
Yace nasama maki miji sunansa YAZEED……..
Tofa fans kuna ganin minal zata amince da wannan batu?
Ya ake cikine tsakanin yazeed da
Zakiyya
Ina jiran comments dinku kada ku manta da offer na.
NAGODE
takuce @mzz_untichlobanty
24 August, 2019
Miss untichlobanty💕Sunansa YAZEED Dan gidan w…….
Bai karashe maganarsa Ba sakamakon ihun da minal tayi
Alhamdulillah! Baba da gaske ka saman miji ?ai Ba sai Nayi tunani Ba indai gidan akwai abinci shikenan anwuce gurin
Murmushi kawai baba Dan ya fahimci kuruciya na dawainiya da minal fatansa de Allah yasa mijin Ba Yaro bane inba haka Ba to Akwai matsala
Ya Abubakar ne yace iye iye ‘yar kazamar kanwata zatayi aure an girma. Turo baki tayi “ni Ba kazama bace” yace ai na sani nan dai suka ci gaba da sabgogin gabansu
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Salati yazeed yayi lokacin daya bude idonshi
Ganinsa a dakin da Ba nashi Ba yasa ya tuna da abubuwan da suka wakana awanni kadan da suka wuce Wai yau shine matarsa kwance jikinshi batare da tashin hankali Ba balle ace ta tafi office.
Smiling yayi sannan yayi pecking dinta ya tashi ya fada toilet ya sakeyin wanka sannan yayi alwala ya fita domin yin sallh
Koda zakiyya ta tashi wanka tayi taci abinci sannan ta dauko laptop dasu tablet dinta ta fara Duba business
Yazeed ne ya shigo yace babyyyyyy!har kintashi?
Smiling kawai tayi sannan tace afternoon yace afternoon daga nan ya zauna yana shan green tea dinshi while tana aikinta+
After ya gama sha yahau gefenta ya zauna suna Dan taba hiransu
___________________________________
//om tana zaune a dakin ta wayanta ya fara ringing unknown number ne hakan yasa bata dauka Ba sanda aka kara kira sannan ta daga
Salamu alaikum
Wa alaik assalam mom ta fada zaka rantse bata iya hausaba
Mama ina wuni?Abubakar ne yayan Amina
Allah sarki Abubakar ykuke
Lafiya kalau,em……..dama akan wannan magananne Toh ta amince
Alhamdulillah, to ai shikenan next week Insha Allah uncles dinshi zasuzo
To shikenan zan Fadawa baba,ina gaida brother Inlaw
Kacewa su baban Muna godiya kuma yazeed dinma zaiji
Bakomai mune da godiya
Da haka sukayi sallama mom na mamakin yadda akayi minal ta yadda Allah dai yasa Ba’a boye mata wani Abu Ba,emm Allah dai ya kyauta
Minal kam fita tayi zata koma gidansu zaliha bakinnan har kunne
Ahanya ta hadu da su haruna(Yan shaye shayen nan from chapter 2) dauke da wani ghana must go cikeda atamfofi
Ah ah hajiya minal dama kina duniyar nan ?
Eh inanan sai akayi yaya ?
Allah baki hakuri mu Ba masifa muke so Ba
Ghana must go din suka dauka sai nishi suke zasu cigaba da tafiya.
Minal tace amma kude Anyi ragwaye wallahi anji kunya yanzu duk girman kunnan bazaku iya daga Ghana must go 1 Ba ? Sai Anyi magana kuhau cika baki Wai June karfafan anguwa.
Suka ce wa? aimu bazamu hada kanmu dake Ba ina babu ma hadi, saboda cin fiskane agaremu ace an kwatantamu da mace.
Minal tace wannan kanku akeji sannan taci gaba da tafiyarta Dan taga alamun zasu bata mata rai
Murtala ne yace ma ta “inkincika ke yar malam yusufa baban kowa ne ki daga wannan jakar ance miki kayan wasa ne aciki
😏?
Basu ankare Ba kawai sukaga Ghana must go a sama ta daura aka.
Haruna yace na Shiga uku ni dan mutum 2 jikan mutum 4,murtala munji kunya ta d’aga!
Ajiyewa tayi ta juya zata tafi murtala yace
“Nide ina baki shawara inkinyi aure a gaba karki nunawa mijinki kinada karfinnan Dan wallahi sakoki zaiyi Dan mu maza akwaimu da son mace me nuna rauni ko zata iya Abu ta nuna bazata iya Ba,macen da take nuna Cewa mu muka cika mata kuma muka gyara rayuwarta
kai haruna kama muje”
Jakarsu suka dauka simi simi suka tari Napep dama mamar murtalan ce ta aikesu
Minal ko tahiyatta tayi tana Cewa har Dan shaye shaye zai iya bada shawarar arzikine?yo jakar mafa Ba wani Nauyi gareta ba kawai de tsabar shaye shayensu har garkuwar jikinsu ta zamo batada karfi. Aikin banza!
Gidansu zaliha ta fada ta labarta mata abinda ta riska bayan ta koma gida nanko ta dinga tsokanarta sunata raha abinsu.
BAYAN SATI DAYA
Mom tayi magana da uncles din yazeed Kamar yadda tayi alkawari kuma sun sanarda ita zasuzo
Shirye Shirye ake agidansu minal makota da abokan arziki hardasu aunty fauxy da iya maman zaliha sun shishshigo ana ta aikace aikace domin taran baki
Minal kam Cewa akayi su Shirya itada zally su tafi gidansu zally
Suna cikin daki zaliha ke Cewa ke kawalliya na kasa yarda wai zakiyi aure
Minal ta daga hannu ta zuba mata duka acinya tare da Cewa da fatan kin fahimci Ba mafarki kike…..
Maganarce ta Koma sanda zaliha ta yarfa mata tafi abaya tare da fadin saura daya.
Bankarewa minal tayi saboda dukan ya shigeta kuma bazata akamata
Nan fa suka fara duke duke zaliha ce tayi surrender tace
Ke shegiya ni matsa hanunki saikace wuka
Minal tace zama Kiyi bayani
Suna cikin haka sukaji hayaniya ya karu
Lekowa sukayi sai suka ga luba Maman bilkisu tsaye tana fadin:Kamar da gaske ai dama wannan yar taku kazama ,ballagaza babu Wanda zai kalli ko Inda take balle ya shinshinata,yanxu haka Nasan sadakanta za’a bayar,wallahi kowaye ya karba ancucesa
Aunty fauziyya ne tace ke dakata inhar kinsan……
Minal ne tayi carab yayinda suke fitowa adaki rike da hijab dinsu tana mai Cewa “ko Ba Komai ai nafi su o’o tunda dai ankarbi sadakan nawa kuma zani da mutunci na wasu da ko a sadakan bazasu sadaku Ba fah?sai yawo a gari an zama shaddar kasuwa kowa zai iya tsuguna duwaunsa akai “
Daganan ta fizgo hannun zaliha sukayi waje yayin da ta balla mata harara
Sauran matanne da basufi goma Ba sukayi mata chaaa aka kowa da irin nasa comments din daganan akayi waje da ita
Bayan minti talatin saiga Yaro yayi sallama Wai inji baban kowa
Akawo abincin baki parlourn zaurensu.
Nan inna tace ya nemo yara biyu sai sukai. Haka ko akayi bayan sun gama cin abinci tare da santi suka sha zobo da kunun aya sannan aka tsaida aure nan da wata 3
Uncles din yazeed sunji dadi sosai da irin karamcin da akayi musu hakan yasa sukasan yazeed yayi dace domin lokacin da sukaje gidan su zakiyya ruwa da lemo kawai aka basu ko snacks basu samuba balle abinci gaisuwan ma sama sama .
Mom suka kira suka fada mata abinda yadda akayi aiko taji dadi daganan aka dinga Sanya alkhairi ana watsewa.
Minal sai 5pm ta dawo aka fada mata yadda akayi bakinta har kunne ya abubakar nata tsokananta.
AT NIGHT
mom,Jamal,yazeed and zakiyya zaune a parlour zakiyya na latsa waya while YAZEED and Jamal are watching football, mom kuma na rubuce rubuce
Mom tace yazeed,kowa juyowa yayi ya kalleta tace akwai aabinda nakeson in fada maka……
Dan! Dan!! Dan!!
Cabdi anxo gurin. Me mom zata Fadawa YAZEED kuma yaya zaiyi ko ince zasuyi reacting?follow me to find out….
Don’t forget to like,share and comment
Ur one and only karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
8 SEPTEMBER, 2019…..inaso inje ziyaran family na ne maybe nanda wata 4 kuma zanyi wata 1
Yazeed yace Allah ya kaimu nima next week zan tafi wani mission kuma zanyi Kamar 2-above month kamin na dawo
Mom tace toh Allah ya kaimu. Yazeed yace tare zaki tafi da Jamal kenan? mom tace eh,yace that’s good daganan kowa ya kama harkansa
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Akwana atashi yaune yazeed zai tafi mission dinshi zakiyya tace baby inajin zan Komai aiki tunda kaga tafiya zakayi
Yazeed perfume ya fesa kamin ya tako Inda take ya zauna ya rike hannunta yace Ba Komai u can resume sannan ya danyi pecking lips dinta
Hararansa tayi tace kaga matsalarka kenan kai da an zauna ana magana sai ka fara canjawa jiya abu daya akayita yi amma baka gaji ba ni matsa Dan Allah ta fadi hakan tana dan turesa
Yace haba mine na bankwana fa zamuyi 2 months fa zanyi babu ke
Tace ni rabu dani bacci nakeji+
Haka yazeed ya gama nacinsa amma zakiyya ta rufe idonta tace Sam
Dole ya hakura ya tafi tace Allah ya tura keya
Sannan ta kara lafewa acikin bargo ko wankan tsarki batayi ba sai bacci after 5 min ta zaburo a guje ta bude wani drawer ta dauko tabulet ta watsa kamin ta koma ta kwanta
🍀yazeed kuwa direct dakin mom ya tafi ya sameta har lokacin tana kan sallayanta tana azkar Dan lokacin to 7 ne
Assalamu alaiki ya Ummi
Wa’alaika Assalam son,kaif asbahata ?
Asbahatu bikhairin,just came to to say bye to u
Take care of ur self u know that I will miss u ryt?
Yes mom I do
Matsowa kusa da ita yayi yayi hugging dinta tare da peck a goshi miyar masa tayi ya dago sai taga idonshi ya ciko da kwalla tace son when did u became a cry cry baby ne?
Murmushi yayi yace kawai zanyi missing dinki ne
Kumatunshi taja tace karka damu kaji ?just concentrate on ur mission
Okay kawai yace mata sannan ya fita
Jamal ne ya rakashi har airport akayi clearing dinsa jirginsu ya tashi by 8am on the dot.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Akwana atashi yau yazeed zai dawo kuma saura 3 days adaura aurenshi da minal
Mom ta hadowa minal lefe na gani na fada tayi order from different countries; atamfofi,laces,material,jewellery,takalma,perfumes kayan kwalliya,inner wears etc
Abangaren su minal Komai ya kankama domin mom tace musu karsuyi kayan daki dakyar suka yarda amma dukda haka sukace zasuyi mata gara da show glass mom tace Ba matsala.
Minal ko gyara takesha sosai ta kara kyau sosai mom ma ta loda musu kudi tace idan Suna bukatan karu suyi magana
Dakyar tukun suka karba tare da yarjeniyan mom bazata kara kashe musu kudi Ba daga wannan.
🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Motoci ne Jere suka danno kai cikin jidmar mansion kamin suka tsaya yazeed ne ya fito ya kara kyau sosai yayi fari jikinnan sumulsumul
Ciki ya Shiga yayinda aka Parker motocin mom ne tayi masa sannu da zuwa tare da yaushe rabo kamin tace yaje yayi wanka sannan yaci abinci
Around 9 O’Clock Suna zaune a parlour mom tace yazeed yace yes mom ?
STORY CONTINUES BELOW

Tace akwai abinda nakesan fadama da fatan bazàka watsamin kasa a ido Ba
Yace mom kawai ki fadi magarnarki
Tace jibi za’a kawo Amarya gidannan
Amarya kuma?Jamal ne zaiyi aure?
Ah ah
To amaryan Waye?
Naka ne
Nawa?!mom kin manta I already married?
Nope,kasan Cewa zakiyya zabinka ne,kuma duk abinda kakeso nima inaso to shiyasa na yarda ka aureta Toh yanxu sai ka auri Wanda nakeso ko?
Amma mom kinsan banida burin kara aure?
Bata rai mom tayi tamike zata tafi yazeed yayi saurin rikota yace indai haka kikeso to na yarda
Murmushi mom tayi Allah ya maka albarka son
Ameen,amma mom wacece ita?
sunanta Amina Idan tazo zaka ganta
Karki damu sweetheart koma wacece ni zan aureta ai farin cikinki shine nawa kuma Ind…….
ME NAKEJI KAMAR MAGANAN AURE ACIKIN GIDANNAN?!
Kwass….kwass zakiyya ta shigo tana wani yatsine tana daga kofar hanci idonnan Kamar zai fado tsabar jaraba.
Zuwa tayi gaban yazeed tace to Baka isa Ba,Wlh yazeed baka isa ba kayi kadan kawai saboda ka kaskantar dani shine zaka wani ce zaka yi aure?ta fadi hakan Kamar zata makuro yazeed din
Mom kam batace kala ba kallonsu kawai take tana ganin ikon Allah na yadda zakiyya ke Abu Kamar Mara lafiya sannan kuma me yazeed zaiyi.
Yazeed bai nuna alamun ransa ya baci ba illa gyara tsayuwa da yayi hankali kwance yace kika ce ban isaba Toh ke a suwa? Ko ince why bazanyi aure ba😕?
Babu abinda zakiyya ta tsana Kamar tayi banbami taga be batawa mutum raiba
Sai tace tabdi jam eehh lallai why ma zaka ce?….to because I said so kanaji na ko yazeed? au Wai dama dagaske auren zakayi ? Wallahi za’a yi tashin hankali.
Kallonta yayi with an expression of I thought u don’t care about me,all u care about is your boutique,boutique, boutique.
With a less concern yace eh aure zanyi jibi ma kuwa thank goodness kinzo a dai dai so no need to stress my self.
Tsalle ta daka tace wallahi ni zakkiya nafi karfin ayimin kishiya god forbid ai ba haka mukayi zaka kara aure ba….na haramta maka yin aure a gidannan yazeed da fatan kana jina?ta fadi haka tana zazzare ido tare da huhhura hanci Kamar maiya
Mom ne tayi carab tace
Hey…hey…hey kikace kin haramta masa?and who the hell do u think u are ?ke asuwa kunun bayan ludayi….just a zero behind a decimal point….ran mom yayi mugun baci
Iyee, its all my fault da bansani Anyi wajen dake Ba kamin a Shiga da ita, shiyasa kika sani bakin magana. Listen to me very attentively! Idan kika sake kikayi mana tashin hankali a gida ki tabbata zaman ki ya Kare. Banason in zama sanadin daba aure amma abin naki ya isa. Kin fara wuce gona da iri.
Yazeed ne ya riko mom yace calm down sweetheart bade aure bane Anyi angama karki damu kinsan I love u ko?muje dakikinki. Haka ya tisa mom a gaba har dakin ta. Tanaji Kamar ta yarfawa zakiyya tafi amma batason ta zubda girmanta.
Zaunar da ita yayi ya bata ruwa sannan yayi assuring dinta Cewa ba mai hanasa aure sai Allah daganan ya fita…
Zakiyya kuwa tasan ta tabo Dan yadda taga ran mom ya baci babu abinda zaihana tasa a saketa she must calm herself down. Taso tayi musu hauka amma bazata iyaba saboda tanason igiyan aurenta
Haka taje dakinta aguje tahau watsarda abubuwa tana fasawa hannunta na jini kamin ta fada kan gado ta fashe da wani matsanancin kuka…..
Yazeed ne ya turo kofan dakin ya shigo
Tasowa tayi attachment dinnan duk ya wargaje tana sending masa murderous glare ahankali yazo ya zauna akusa da ita being conscious with the glasses kar ya taka.
Hannunta ya riko ta warce ya kara rikowa zata warta ya rike gam yace haba my zakky uhm….yanxu shine kikaje kikayi fada da mum kinsan mahaifiyata ne tanada hakki akaina ya kikeson Nayi kinaso na haukace ne?
Rungumeta yayi kamin yaci gaba da fadin na dawo ko kiss ban damu sai kihau yima mahaifiyata fitsara kin kyauta kenan?a hankali ta girgiza kanta yace ai kinsan ko Nayi auren ke nakeso waccan zabin mom ne ko?ta gyada kai yace promise me zaki bawa mom hakuri tace on one condition idan kayi auren bazaka hada gado da matar ba yace ai wannan ko baki fadaba kinsan haka yake Insha Allah.
Tace to nima zan bada hakurin yace good daganan aka Shirya kuma akayi wani duniyar.
Jamal kam sune kirjin biki bai samu haduwa da yazeed ba sai Washe gari Inda za’akai lefe
Your one and only karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
8 SEPTEMBER, 2019.
Kamar yadda kuka sani yau za’a kawo lefen minal
gidansu ya cika taf da dangi,Yan uwa da abokan arziki kai har makiya ma sunzo domin asamu abin fadi acikin gari
Ana zazzaune akaji sallaman kawayen mom da aunties din yazeed sun iso firfitowa akayi ana musu maraba tare da shinfida musu dardumai
Gaggaisawa akayi da fara’a da mutunci Yan gulma da tsurku tundaga ganin masu kawo lefen sunsan minal ta cafka tayi sa’a zata Shiga gidan da akwai gida mai maiko
(Wannan yana daya daga cikin kuskuren da mutane keyi Suna ganin idan har ka auri me kudi ko me kyau Toh kayi sa’a saide abin Ba haka essential qualities da ake bukatan mutum ya lura dasu shine:
1.shin wannan mutumin ya kwantamin ?
2.shin yanada addini?
3.zai iya ciyaddani da halal?
4.shin ‘ya’yana zasuyi alfari dashi amatsayin ubansu?
5.shin zasu gode min na zabanshi amatsayin baban su?
6.shin yanada akida mai karfi
7.is he loving and caring?
8.will always support me?
9.am I ready to live my whole life with him?
10.Does he respect my family1
if those questions are satisfied then you are good to go,bawai idan ka auri mai kudi,handsome shine kayi sa’a Ba pls and pls Yan mata take note Ku core San duniya aranku Ku sank duk mijin da kika zaba Ba kanku kadai kika zabawa ba har da yaranku.Ku guji ranan da ‘ya’yanku zasu kalleku suce muku kun cucesu kun zaba masu mafi munin uba.
Suma mazan idan kun aurensu zasusan Dan me kuka auresu Dan kudi ko Dan allah.
Shiyasa yanxu rate of zaurawa ke karuwa soboda tun kafin adaura aure an rusa ta an kasheta auren a mace tazo. AKIYAYE)
Abokan ya abubakar ne suka fara shigowa da akwatuna har aka Shiga da 6 akwai nasu Kate ba,7,8,9,10………18 set uku kenan Wanda Duke da kalar fari,baki sai sky blue ga stones farare masu kyau ajikin ko wanne
Wasu set shida aka shigo dasu Wanda suke kalar brown guda 3 na inna,2 na baba sai 1 na kawayen Amarya
Kaya aka fara budewa hmm abin ba magana atamfofi 50,laces 30,material 25,an dinka goma goma atamfofi kuma ashirin ,English wears 25,Arabian gowns 30,sleeping dress 20,pants da bras dozen uku uku,takalma da jaka set 20,cosmetic traveling bag daya,gold jewellery 5 sets
Inna tace kayan sunyi yawa a rage Rabi sukace ah ah ai kaya sunzo in zasu koma to saide in ankawo amarya
Haka inna ma ta nasu tukuicin ban girma ;cin-cin,bakilawa,cake,doughnut, alkali,meat pie da samosa buckets buckets Wanda aunty fauzy ta bayar amatsayin gudun muwa sannan tahada musuda turaren wuta
Haka aka watse kowa yana farin ciki da annashuwa
THE WEDDING DAY
yazeed ne tsaye abakin mirrorn dakinshi zakiyya makale dashi tana wani shashshafa fuskanshi zuwa wuyanshi baby Wai da gaske auren zakayi,yace Toh zaky ba maganannan an gamata ba meye na dago da ita,zakiyya tace Toh naji amma kar ka manta kace bakasonta kuma bazaka hada gado da ita ba yace ina sane da wannan,happy now?tace yes
Fesa turare yayi kamin yayi mata peck a kumatu ya wuce
Zama tayi abakin gado tace koma wacece ke to kisani zaki kawo kanji cikin masifa ne Dan kishi dani sai an Shirya yanda ba’ayiwa uwata kishiyaba nima bazan zauna da ita ba😈
(Wannan banziyar akida ce mutum yace Wai Dan ba’ayiwa mahaifiyarsa kishiya ba shims ba’a masa ba karku manta Allah madaukakin sarki yace acikin suratun nisa’i6
“Wa in kiftum allâ tuksidû fil yatamâ fan kihu ma d’aba lakum minannisa’i masna wa sulâsa war ba’a,fa’inkiftum allâ ta’adilû fa wahidatan au ma malakat aimanukum zalika adnâ allâ ta’ulû” 3:3
Allah madaukakin sarki ya umurci maza da su auri mata biyu,ko uku,ko hudu,idan bazasuyi adalci ba to su auri daya
Kinga da auren biyu ma aka fara kamin uku kamin 4 shikuma daya karshe
Kisani idan mijinki yace zaiyi aure kikayi adawa to kisani badashi kikeyi ba da Allah ne tunda Allah shi ya umarci ayi hakan
Dan Allah mata mu tashi munemi ilimi kuma muyi aiki dashi kodan gudun ranan da yayan mu zasu tambayemu Abu akan addini mutsaya muna zare ido mu Shiga kunya.
Ba’a tsufa ko girma daneman ilimi,idan bakusamu kunyi da yarinta ba lokaci bai kure ba tunda har yanxu kuna shan numfashi.
Kusaka yaran Ku amakaranta na boko da addini kodan suyi alfahari daku
Can u believe that ni Amina Abdulkadir Shettima will turn 15 years on 18 September,2019 amma Ku Duba abinda nake iya rubutawa?kuma ina university sannan na haddace takaddun addini?what do u expect idan nakai 18?what of 20? ba cika baki nake ba amma kuma kunsani akarancin shekarun da nake dashi inada tunanin manya.
Abin kunyane ace yar cikinki ko lanwar bayanki ta Fiki zurfin tunani.2
Wani abin da ke bani haushi shine ‘Yan mata masu shekaruna yanxu Kansu rawa yake,yanzu ne suke ganin Suma sun girma baza’a barsu a bayaba,Suna ganin sunyi boobs Kansu daya da uban kowa,basuda burin daya wuce ayi shigan tsiraici ana yawo a gari ana karya ka’idar da iyakar Allah,ana kara yada zina acikin alumma,tun daga fitanta har dawowanta mala’iku na tsine mata,manzon Allah ya tsine mata,bayin Allah salihai na tsine mata, ai tundaga nan ya kamata ta fahimci ta Shiga ukku,wallahi Mu kiyayi haduwar mu da Allah abin kunya ne kaje gaban Allah kana mai saba masa ka wulakanta aduniya ka wulakanta alahira.
Su mazan da suke ganinku suce u look breathtaking,u look sexy,u look hot ke tun daganan ansami matsala hot fa akace ba cool ba kinga ko anfada miki Inda mala’iku zasuyi dake ne in baki canja hali ba. Ancemiki zasu aureki ne ?babu mai aurenki lalataki zasuyi suyi gaba,wallahi ku ji kunyan randa zaku tsaya gaban Allah ana miki shari’ah keda iyayenki. Mu rufawa kanmu asiri mu nemi ilimi muyi aurenmu cikin rufin asiri har Allah ya karbi rayukan mu.)
Lovelies kuyi hakuri yau duk Mun kare a lecture wallahi rainane ya baci da abinda ke faruwa,duk mutane sun kwashe kayansu daga gaban annabi,amma karku damu I will make it up to you😉 Ku tayani da addu’a inada test guda biyu tomorrow masu zafi ne kuma chemistry and Arabic thanks for your love
Your one and only favorite yobe girl,karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
8 September,2019.An daura auren minal da yazeed akan sadaki naira dubu 50,Yan uwa da abokan arziki NATA taya murna makiya ma na hassada
Allah ka barmana makiyanmu kodan su zama dalilin da zamuyi nasara. Imagine life without munafukai ‘Allah barmana Ku Yan wuta😂’4
Mom ta aiko da kayan abinci da abubuwan da za’ayi walimah Dan babu wani event da za’ayi. saboda abin yazo a kurarren lokaci ko mai wa’azi ba’a sami daman kira Ba.
Bayan la’asar akayi da mom Cewa za’a daukan minal around 5 pm inji ango(mom anya wannan magana kuwa zan yarda da ita?).
Hakan yasa aka fara shirya Amarya around 3:50 bayan Anyi sallar la’asar.
Liffaya mai kyau tasa wadda aka siyo mata awajen reemah’s collection. Wani sarkan gold akasa mata Wanda yake na inna ne family necklace dinsu. Babbar ya ake bawa in za’a kaita dakin miji. Kuma ba’ayarda ka siyar Ba amma zaka iya upgrading.
Kyansa yananan Dan haka ba’amayi upgrading din Ba.
Dayawa daga cikin Yan makarantansu sunyi attending, ciki kuwa harda heedaya Muhammad da ma’ani yerima Wanda suke mutunci sosai.
Yan matan ne adakin minal yayinda aketa tsokananta itako sai cika take tana batsewa wai ita batason adinga zancen batsa a gefenta.+
Hidaya ce tace Nide sake fuskannaki in gama kwalliyan yayinda ma’ani ke Cewa nikam yau sai na cika camera ta da hotuna, inajin ma inna sami dama zanje in karanta photography😉2
Heedaya ne tace oh mude zamuzo muji ya aka Kare a Daren farko.2
Harara minal ta ballo mata,aka fashe mata da dariya Ashe ta shaka, minal tace ko ma dai menene ni kar a tura ma kowa hoto na cikin kayan nan tunda kunga dai gashi na da wasu bangaren jiki na a bude.
zaliha tace kai Ku rabu da ita bari ayi Daren farkon wannan Cuno bakin da take duk zata dena saide muga mutumiyar ka an zama miji dadi
Alamun zatayi kuka muryanta yayi tana Cewa wallahi zaliha karki bari na kamaki shegiya yar…..
Innace ta shigo tace inkika karasa sainaci ubanki.
Tunda ake hirar bansa baki Ba ina zaune a gefe ina typing a wattpad dina saboda kar ace na fiya rashin kunya sai alokacin na sako baki nace “assha!inna kin bata goma boyar bata gyaru ba in ita batayiba aike kinyi”
Dakuwa tayimin tace ingo naki yar jakan uban yarinya da baki cau cau Kamar babba kodan kinganki cikin Yan mata shiyasa kika falle ko?kinsa niqabi kamar da gaske ashe dai…….shegiya Da I damu Kamar na Yan chaina
Kafin ta karashe nayi Sauri nace wallahi Nide Ba yar China bace ina turo baki,aiko inna tayi kaina na fita a 360 har inacin karo da mutum Ashe ma sakina ce da habiba (from the nemesis of sakina)yi hakuri kawai nace kamin na buya a zaure ina haki sannan na sauke niqabi na,na saka gilashi na.
Ciki su sakina suka Shiga aka gaggaisa kamin suka wuce domin mazajensu na jiransu.
Kanwar dad din yazeed aunty nafeesa da Umma habiba wadda take step paternal grandma ga yazeed sai kuma aunty nina Kanwarka mom Wanda suka iso yau da safe sune sukazo daukan Amarya tare da motoci 3 kacal saboda basuso bidi’an tayi yawa
Aiko nan aka fara tashin hankali minal fa da taga da gaske tafiya za’ayi da ita kirjinta ya fara lugude duk dadin da takeji taji babu shi ya tafi kawai sai ta fara hawaye wiwi Ba magana nanfa wattpad fans dinta sukayi CAA anata bata hakuri amma ina kukan karuwa yake tunba sanda sukayi sallama dasu inna Ba dasu baba da ya abubakar.
Inna da baba hawaye suke hankali kwance yayinda idanun yaya abubakar suka ciko da kwalla deeje Kam an jika gaban riga ma da hawaye da majina sai alokacin na lura da kwalliyar da tayi kominta yayi matching da kayanta hatta Jan baki da eye-shadow, da brows din duka blue ne. Abin dai sai kun gani. Nikam share kwallan da zai zubo min Nayi domin tausayi. Rabuwansu was heart touching haka aka kwashemu mu 10 aka kaimu gidan amarya.
STORY CONTINUES BELOW

Tundaga kofa akayi mana maraba,kai Mun sami tarba me kyau dakin zakiyya aka nuna mana muka kai minal Dan bada amana mu Yan mata 8 da tsofi 2.
Ba yabo ba fallasa ta karbemu. Amma ni dai hankalina bai kwanta ba kuma naga alamun hakan a fiskan wasu daga cikin mu amma dai sai Nayi shiru. Kar aji mutuwan sarki a bakina.
nuna mana dakin minal akayi Wanda yake part din baki ne na sama kuma acikin sashin zakiyya yake ada amma an daba kuma an gyarashi kai ya hadu. Allah dai ya kyauta ya Kare Daga sharrin makiya
Aikuwa hidaya ta cika alkawari Dan photo kam gida yashashi har minal dinma sanda akayi mata pic amma sanda ta sake ado tukunnan.




1
Haka dai har dare yayi munata shewa da tadi kamin aunty Nina ta shigo tace mana motocin tafiya najiran mu haka Muka tattari kafufun muka tafi minal Kam kukanta ta bude sabon shafi Dan ta manta da Cewa ita daya zamu bari(saima ankai mutum kabari zai San kadaici. Allah dai yasa muyi dariya a kaburburanmu.).3
Hmm ai batamasan gidan wa aka kawota Ba saboda kanta na cikin gyale har muka kaita daki kuma ai batasan yazeed Nada mata Ba kuma bata tbna Shiga side din zakiyya Ba Dan haka bata gano ba.
Lokacin ko da akayi musu maraba kuka take ga hayaniya Dan haka bata gane muryan mom ba.
Aunty nafeesa da mom ne suka shigo,mom tayi Sauri taje wajen minal yayinda ta dago chin dinta tana mai Cewa ” ‘yata me ya sameki?”
Kuka minal ta kara fashewa dashi ta rungume mom Dan ta dauka mom tayi attending bikin ne
Tace “mom Ashe an gayyaceki?mom Dan Allah karki tafi ki barni kamar yadda su zaliha da untichlobanty da ma’ani da nasreen da hidaya da…”
Ya isa bazan tafi in barki ba mom ta fada hakan tana me daurewan kai ?kode batasan wa ta aura ba?kai maybe de tsoro takeji saboda first encounter dinta da yazeed wasn’t good.
Shafa bayanta mom tayi tana bata soothing words har tayi shiru tana shessheka (sobs).
Kinyi sallahn Isha’i ? mom ta tambayeta tace a ah. Mom tace to tashi kije Kiyi kinji
Shiga toilet din tayi taga irin na wannan dakin da aka kaita ne sansadowa tayi kamar barauniya Wai Dan kar fanfo din yaji motsinta ya bachi da gangan har zatakai hannu ta bude saide ta fasa
Fanfon dake jikin toilet irin na tsarkinnan tace ta matsa tayi alwalanta Dan akwai irinsa a gidan aunty fauxy so ta iya aiki dashi har wani smiling take irin itama ta Waye dinnan.
After tayi alwalan bata mayar da dankwalinta ba ta fito Dan ta manta da cewa ma su mom sunanan
Smiling suka mata ta miyar musu kafin mom tayi introducing mata aunty nafeesa sannan ta tada sallah
Aunty nafeesa Kam yaba Kyan minal take tunba gashinba shi yafi dauke mata ido.
After ta idar mom ta zaunar da ita ta mata wa’azi ya tsumata sosai.
Abinda ta fada last ne yasa minal shock.
“Daughter Dan Allah ki rikemin Dana dakyau kuma iyayi miki wani Abu ki sanar dani”
“Kina nufin oga sir?”minal ta tambaya hankali tashe.
“Kwarai shi”mom ta bata amsa. Atake minal ta………
Finally,Nayi post kuma sai Kiyi supporting dina by voting and commenting.
love you all😘
Karamarsu babbarsu ce
Miss untichlobanty💕
21st September,2019.Introducing new character safwan and sahir
Sahir and safwan ‘ya’yan yayar zakiyya ce Wanda ta rasu two years ago ana kiransu sahboy and safboy tashin turaine su. An dawo dasu wajen zakiyya ne last two month acewar mamanta Wai idan yazeed bashida matsala to su zauna awajenta tunda babansu irin sugar daddy dinnanne dama dan kudi yayar ta auresa kuma sanda sukayi sharadi inta sake ta haihu tofa yaran nata ne shi babu ruwanshi Dan baya bukatan yara.
To ta haifi sahir (6 years old) and safwan (4 years old).
Yaran are very sweet kuma sun saba da zakiyya Kamar mamansu adan zamansu tare tunda dama Ba aiki take zuwa yanxu Ba kuma already sun saba kawai shakuwa suka karayi.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Atake minal ta sauke wani ajiyar zuciya aranta tace na Shiga ukku na lalace, Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un sunana death.
Da badan tana cikin matsala Ba da tayi smiling domin ta fadi kalmar death daidai
Bude baki tayi zatayi magana kawai sai taji ta kasa Cewa Komai sai hawaye mom kuwa bata kawo Komai a ranta Ba ta dauka minal tana kukan yadda dare daya Allah ya sauya rayuwanta ne(eh tabbas sauyin Shiga tashin hankali ba).+
Mom tace bari inje intaho da angon naki Dan Nasan yanxu haka yana hanya idanma be karaso Ba kenan.
🌹
Abangaren yazeed kuwa tun kayanshi na daurin aure ne ajikinshi dama shadda ne fari kal.
Yana shigowa gidan side din matarsa(I think yanxu matansa zance) ya nufa dama haka yakeyi tunda suka Shirya da zakiyya inya dawo sai yaje ya taho da ita dakinsa wataran idan a sama yazo ma to Anan za’a yada zango. Watarana kuma ya samota already a dakinsa.
Yana shigowa ya kalli right dinsa wani iri yaji aransa Wai yanxu matarsa ne a part dinnan left dinshi yayi ya tura kofan dakin zakiyya yaji a bude…….
🌹zakiyya tayi wa Kanta alkawari bazata biyewa yarinyar (Kamar yadda taji su mom sunce)da za’a kawo mata Ba tunda ma mijin nata bayaso ai yazo da sauki duk da maza maciya amana ne ta yarda da yazeed din ta.
Sanda taji guda an shigo da Amarya wani ras ras ras ras gabanta yakeyi amma sai ta matse koda aka shigo da Amarya wajenta wani daci taji ya tsaya mata,tanaso tayi musu wulakanci amma su untichlobanty su hidaya su zasmeen su walia sun mata kwarjini.
Haka suka gaisa sama kamin suka fita itade idonta akan minal tanaso taga ma Wai wacece wannan yarinyar.
Koda suka fita wani Abu taji ya tsaya mata a wuya batasan sanda ta fashe da kuka ba kukanta take hankali tashe Wai yau ita zakiyya akayi wa kishiya da wani ido zata kalli mutane danma ita bamai kawaye bace saboda jiji dakanta.
Sahir da safwan kuwa na dakinsu.
Turo kofar dakinta taji Anyi tace Waye?yazeed ne ya shigo ta rungumeshi tare da fashewa da kukan munafurci. Sanda tayi shiru yace ina boys Dina yau daddy bai gansu ba? Tace Suna dakin su peck ya mata a kumatu yace taje ta kwanta sannan ya juya zai fita zuwa tayi ta tsaya a gabansa ta rike hannunsa tace baby kar ka ci amana ta Dan Allah.
Yace kar ki sa ma ranki damuwa ba abinda zai faru kinji?
Tace ni gaskiya hankali na bai kwanta ba wai me yasa ma mom tayi mana haka ne? Ya za’ayi….
Ransa ne yabaci saboda yasan abinda zata fada ba mai dadin ji bane hakan yasa yace haba zakkya why are you acting like this kinsan fa aurennan….
Fuck you yazeed! You are so fucking annoying i hate you just leave. Ta fada tare fashewa da kuka Dan gani take yazeed a dakin minal zai kwana tunda ya fara noke noke.
Baice mata kala Ba Dan yanxu shi yama rasa meke damunsa Dan haka yabar mata dakin.
Sai alokacin taji wani iri. Saita daura aniyan zata bashi hakuri da safe.
Dakinsa ya Shiga zai fara rage kayan jikinsa saiga mom Tisa kyayarsa tayi har dakin minal dukda ko baiso hakan Ba amma shima he is curious yasan wa aka aura mass Dan yaga mom na rawan kafa akan amaryar.
Salamu alaikum suka fadi in unison yayinda mom da yazeed suka shigo dakin minal. Aunty nafeesa na zaune agefenta daga alamu nasiha take mata.
Tanajin sallamarsu ta sauke Kanta kasa kirjinta na lugude duk ta tsure cikinta ya kada.
Wa’azi sosai aunty nafeesa tayi musu harda kuka wajen bashi amana kamin ta kara yiwa minal nasiha sannan ta fita domin taje ta kwanta Dan jirgin bakwai zatabi ta koma gida yayinda su mom zasubi na karfe ukun dare ita da Yan uwanta domin zuwa gida Kamar yadda tace(amma intention dinta shine ta basu Fili su wala tunda yayi sabuwar Amarya )kuma bata bada ranan dawowa Ba.
Mom ne ta dafa minal tace yata ki dago da kanki kinga ni Kamar mahaifiya nake awajen ki Dan haka babu wani batun kunya kinji?tsoro ne yadada balbale minal zuciyanta na dukan Tara tara yayinda captain yazeed Dada sa hankali ya zuba idanu Dan yaga face din new bride dinsa.
Shahada minal tayi ta dago fiskanta aiko stake captain yazeed ya sankare
Out of all Yan mata mom ta rasa Wanda zata aura masa sai barauniya?maybe Ba barauniya bace har leken asiri ce ko kuma …………. WAIT!so now he get it wato ta biyoshi ne last time dan taga yaya yake Dan tasamu yanda zata shigo life dinsa Gaskiya tayi making a huge mistake hmm he will deal with her
Kallon mom yayi ya mata godiya sannan yace Allah ya basu zaman lafiya tayi hakuri da abinda yayi mata. Kamar da gaske
Minal har hankalinta ya fara kwanciya tadauka an wuce shafin batasan ko bude littafin ba’ayiba.
Mom taji dadi sosai sannan ta sanar da minal Cewa yau ne tafiyanta sannan ta fita ta basu wajen domin komawa side din ta Dan agajiye take sosai.
Tana fita yazeed ma ya fito bayan yayi wa minal wani dangerous kallo yace Allah gaji kanki. Yun daganan tasan ta Shiga ukku, ta kade daga buzun ta har wutsiya
Da sassarfa ta fice ya shiga dakin sa ya tsaya gaban madubi yana kallon kansa, plan yake nema yanda zaici ub*n minal kamin finally yace yes that’s it.
Minal kam sanda ya fita aranta tace kai wannan oga sir din Anyi masifaffe ni inyazo ma wulakanci zan kafta mai. Wai zuciyan yace Kamar zaki iya tuno kallo daya mata kamin ya fita tayi atake ta tsure ta kidime yanxu ya zatayi gashi mom zata tafi ta barta waiyo Allah.
Kwanciya tayi abinta sanye da kayan jikinta gyalenta kawai ta cire kamin tayi baje baje atsakiyar gado tana yaba laushin katifar. Allah sarki harta tayi missing din tsohuwar gadonta yar karama da katifarta.
Tashi yayi ya dawo dakin minal domin aiwatar da aniyarsa Alokacin minal ta Dade da Shiga duniyar mafarki Wai tana baccin nan yazeed yazo ya caka mata wuka sannan ya binne gawanta a bayan gidan.
Wani wawan juyi minal tayi acikin baccin dama ita A ne wajen style din bacci ta iyasu kala kala dankwalinta ne ya zame gashinta ya bude dama ta cire ribbon din sanda zatayi alwala
Tsaki yayi aransa yace mata halinsu daya ka Duba iyayenta basuda karfi sosai amma sanda tasa wig mai tsada. Ko ina ta sami kudin? Wata zuciyarsa ce tace masa ka manta barauniya ce ko yar 419? Tsaki ya ja ya bubbuga gadon yayi fiskansa babu alamun wasa domin ya daura aniya kuma sai yayi…….
Toh fa ko menene aniyan yazeed? Fans me kuke gani yazeed zaiyi?don’t forget to vote and comment your ra’ayoyi.
Miss untichlobanty💕
23rd September, 2019.
Juyi minal tayi tace inna bacci nikeji,Wai har asuban yayi ne?
Haushi abin yabawa yazeed hakan yasa ya wantsalar da pillow din da take kai,aiko babu shiri ta mike ganin shine yasa taji wani faduwar gaba yazo mata
Tunda take arayuwarta bata tana jin faduwar gaba irin wannan Ba kuma bata taba jin tsoran wani Kamar yadda tsoron yazeed ya shigeta a yanxu Ba.
Wani irin kwarjini yayi Wanda tayi nadamar kallon idanunsa domin kuwa ko lokacin da suka fara haduwa bata kallesa da kyau Ba
Wani kirma jikinta ya fara ta fara karkarwa Kamar mejin sanyi.
A hankali muryatta Kamar zatayi kuka tace sannu da zuwa.
Wani kallo yazeed ya mata Wanda yasa hanjin cinkinta kadawa kamin yace uban Waye yabaki izinin kwanciya balle har kiyi bacci? Tayi shiru…
Bakida kunnene ko yaya?muryanta na rawa idanunta ya cicciko da hawaye tace kayi hakuri yace my friend will you get down, zaki sauko ko saina taka ruwan cikinki?
Zama yayi akan kujera tare da dago kansai yanaso ya karewa minal kallo amma ya hakan ya gagara sabida kirjinsa dake bugamasa da Sauri da Sauri amma dai baikai na minal Ba sai ya dauki hakan amatsayin baccin rai da ke damun sa.+
Dan haka sai ya jingina Kansa da allon gadon yana mai lumshe idanu Kamar yadda yayi can baya sanda ya fara haduwa da ita a gidansa saboda takaici da ciwon kai da ta hada masa.
Minal ko gabadaya jikinta yayi sanyi,ta sadakar Dan ita a ganinta Allah ne yake ramawa mutane irin tsiyar data musu sanda take gida.
Tayi tsuru tsuru da ido Kamar Mara Gaskiya,gabadaya jikinta ya jike da gumi ga wani fitsari ga zazzabi ya sauko mata tsabar rudewa.
Dukkanin shikashikan tashin hankali ta cikashi a halin domin ko hawaye sun Dade da fara safa da marwa a kumatunta.
Sanda suka dauki kusan minti goma a haka kamin yazeed yace sannu.
Minal Kam ta kasa dabbaka Komai Dan ita ko a film bata taba ganin irin yanayin da tashiga Ba ganin take ko yaushe ma zuciyarta zai iya bugawa ta mutu zaboda yadda yake bugawa har cikin dodan kunnenta takeji
Abubuwa dayawa ke yawo azuciyar yazeed Wanda yana fahimtar wasu,Wasu kuma baya fahimtar su
Kinsan dai jarumi sai jaruma, toh amma ba wannan ba ki sani ko ma waye ya aiko ki gidan nan toh fa ki sani ya cuce ki.
Mahaifiya ta ta Riga da ta aura min ke to amma ki sani ni bazan ciyar da ke ba Dan haka zan ciyar da ke da sharadin zaki dinga biyan komai har kudin haya idan ba haka ba kisan inda dare ya miki.
Baki na shirin zubar da hakwaran ta saboda rawa tace Dan Allah Allah Allah ni banida wata sana’a da Nike da ita bazan iya biyan ka ba amma zan iya yi maka aikin wahala.
Shiru yayi har ta fara tunanin ko yayi bacci ne kamin ta ji yace abinda nace kiyi agidannan su kadai zakiyi idan kina neman izinin yin wani abu to ki rubuta a paper ki ajiyemin. Kuma kada ki sake ki shiga sabgata Mata na tsakanin ki da ita gaisuwa. Saura kiyi ginin fadawa wani wannan zancen.
Sannan kar ki kuskura ki hau min kan gado tunda ba da shi kika zo ba. Zan iya miki alfarmar ki kwanta carpet ko kujera before I know what to do with you.
Itade taji bazata kwanta a gadon Ba sauran kuwa toh sai ta Allah.
Na gode shine abinda kawai ta furta kamin ya Mike ya bude toilet ko me ya duba oho sai ya fice. Wani nauyayyan ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin numfashinta Wanda bata masan ta rikeshi Ba sannan ta goge hawayenta sannan tadau bargo ta Komai kan kujera ta kwanta tare da rufe kafafunta
Yazeed kuwa yana komawa dakinshi yayi wanka tare da brush sannan ya fito dressing room dinshi ya Shiga ya dauko pyjama dinshi blue tare da Rigan ya saka sannan ya haye gadonsa ya kwanta yana mai lissafi yanda rayuwa ta kasance masa
Hakadai bashi yayi bacci Ba sai wuraren asuba koda ya tashin sallahn asuba Kansa yayi masa mugun nauyi hakadai ya daddafa yayi sallah yayi azkar yau ko karatun Qur’ani bai samu yayi Ba ya koma bacci. Dama Ba kullum yakeyi saboda yanayin life.
Minal ko tunda tayi asuba taje kitchen ta nemi kayan aiki aiko batasha wahala Ba ta samu ta kama aikinta karfe 8 cif saiga su atine da su larai sun shigo sukaga babu kayan aikinsu parlour suka leko jin motsin mutum aciki aiko da gudu gudu Sauri Sauri suka karaso
Atine tace Allah sarki yar uwa yaushe Rabon da mu ganki ziyara kika kawo manane ko wajen hajiya kikazo kika bage da aiki saide kash hajiya ma jiya da daddare tabar kasan itada danginta kinsan fa mai gidan ya karo aure
Duka atinen ta fada a numfashi daya zuwa biyu Asabe ta kara da ya karo wulakanci Ba larai tace baza’aji mutuwar sarki abakina Ba
Minal ko murmushi take tana binsu da idanu Dan batada abin Cewa
Aikin sukayi kokarin karba minal tace ah ah sukace to shikenan suyi tare kamin ta yarda amma dukda haka tana tsoro kuma tana ganin kamar haram zata ci.
Su kuwa sai hira suke mata harda tambayarta ko zata kwana musu Dan sunaso suyi kawance da ita tace musu ai Ba kwana Ba kwanaki ma zanyi ta fadi haka tana bawa kwanakin karfi, aiko sunji dadi Dan su basu gane me take nufi ba
kafin karfe 10 sun gama Komai saura part din yazeed Wanda dama tunda basu ke gyarawa Ba lukman ne kuma yazeed yayi masa message Cewa Ba sai yazo Ba.
Su atine sai janta suke da hira tun tana nokewa har ta saki jikinta sumo abin ya musu dadi, binta tace ni wallahi na kosa naga amaryar Allah dai yasa Ba irin madam zakiyya bace
Atine tace yo imma batada mutunci ai ita ya shafa minal de tayi tsit tana jinsu
Minal tace to ita bari taje sama tayi wanka larai tace Wai ko kema bikin kikazo ne naji kina Cewa bari kije sama kiyi wanka ? Rasa amsar da zata basu tayi sai atine tace kinada kayan sawa?
Binta tace ji wani tambaya dole da kayanta zata zo mana
Minal tacewa atine Dan Allah kinga rabu dasu zo Kiyi mini wani taimako
Sukace to sai kun dawo kamin su minal suka wuce dakinta ta cire hijabinta sannan ta kalli atine
Atine ko zare idanu takeyi domin in batayi kuskure Ba nanne dakin da aka kawo Amarya
Minal tace kinga kwantar da hankalinki nice amaryar ni zoki nuna mini Inda zan sami kayan sawa
Atine ta zaro ido tace Kece ME?
Minal tace kinga shiyasa ma ban dadi muku Ba saboda ban Shirya yin bayaniba zoni ki nuna Mani
Nuna mata dakin dressing atine tayi da yadda zata canja combination din daga 00000 sannan ta nuna mata na toilet ma
Kamin ta fita tana mamaki da kuma al’ajabi minal kam wanka tayi sannan ta koma parlour jin shiru yazeed bai fita Ba yasa tace kika ma ya five run asuba idan Ba haka Ba ya za’ayi ace mutum yana bacci har 12.
Alokacin data koma kitchen domin dauko su tsintsiya su atine na kitchen din Suna cin abinci Suna ganinta sukayi caaa Wai meyasa bata fada musu akwai chemistry a tsakaninsu da oga sir Ba ?Wai kuma me yasa yallabai ya mata abinda ya mata kaman wata 3 zuwa 4 da suka wuce?
Murmushi tayi tare da tabe baki tace sirrin ne
Daukar tsintsiyarta da packer tayi ta wuce side din yazeed
Kirjinta ne ya fara tsinkewa karfa yaje yananan,hakan yasa ta fara sanda Kamar Mara Gaskiya sannan a hankali ta bude kofar da take ganin side dinshi ne tunda de tasan na mom
Leko kanta tayi taga……….
Me tagani?
Uhm kun ganni all of the sudden ko?ai bazan iya babu Ku bane kun zama wani bangare na life dina
😭 I have 2 exams on Monday please karku manta dani a addu’o’in ku2
Ina sonku sosai wattpad fans dina😘
Don’t forget to vote,share and comment
Miss untichlobanty💕
4th October, 2019Leko kanta tayi taga wani tsararren parlour wanda bata taba ganin irinsa Ba
Ko babban parlourn dake gidan taga baikai wannan kyauba dukda ko wannan din Ba wani girma bane dashi na hauka amma ya hadu
Kamshin daya bigi hancinta ne yasata dawowa saga tunanin data Shiga ga wani AC daya bugota har yanasa tsulan cikinta tashi
Shahada tayi ta Shiga da yar karamar sallamarta Wanda ko ita kanta bata jishi dakyau Ba
Sanyi ne sosai a parlourn Dan har tadan soma rawar dari a kasan ranta tace kaji daki sai kace cikin fridge Allah yaso da hijabi nazo….
Kalle kallenta tayi kamin ta soma abinda ya kawota
🌹
Yazeed kuwa tunda ya Koma bacci bashi ya tashi Ba sai around 12:00pm
A sukwane ya tashi daga kan gadon nasa ya sauka Kamar bayason jikinsa ya rabu da lallausar katifar.
Bandakinsa ya bude Wanda yake tsaf Kamar Ba namiji ke amfani dashi ba, wanka yayi kamin yafito ya shafa mai yana tunanin yadda rayuwa ta juye masa
Wai yanxu shine yake da mata biyu,Wai jiya shi aka kawowa amarya kuma ma shi Ba wannan ke damunsa Ba
Ace mom ta rasa Wanda za’a aura masa kaf fadin duniya sai wannan yarinya,wannan fitsararriyar.
Hmmm nannauyan ajiyan zuciya ya ajiye sannan ya fara shafa wani mai me kamshi ajikinsa a hankali Kamar bayason ya shafa duk da ko nazarin da yake yi ne ya haddasa hakan.
Daga mutum ya gansa yasan Cewa lallai wani Abu na damunsa dukda ko hakan bai yiwa kyawunsa wani lahani ko sauyi Ba
Ahankali ya tashi yana tafiya Kamar bayason yayi tafiyar,Ahankali ya Daga Zara zaran yatsunsa Wanda ke dake da fararen nails ya danna pin din dressing room dinshi ya Shiga sannan ya tsaya agaban wata kofa na glass a hankali ya bude sannan ya dauko wani gray hoodie tare da black three quarter.
Drawan under wears dinshi ya bude sannan ya dauko gajeran wando amma banda singlet jin Kamar motsi a part dinshi yasa ya leko
Amma baiga kowaba hakan yasa ya koma ya sanya kayansa cikin nutsuwa
A hankali yaji kamar an bude kofan dakinsa Dan haka ya kara lekowa domin ganin Waye Ba tare da dauko socks din dayayi niyya Ba.2
Atake Dan guntun annuri dake tattare dashi ta dauke. Minal ya gani tana leken dakin domin tabbatar da Cewa bayanan ajiyan zuciya ta sauke tare da shigowa da Da karfin guiwanta amma Ba a rashin nutsuwa Ba.
Baice mata kala Ba itama bata lura dashi ba domin kuwa idanunta ta ware bil hakki da gaskiya tana basu abinci
Jingina yayi a bakin kofar da yake sada dakinshi da dressing room din yana kallonta kawai yama rasa mai zaice ko yayi mata
Sanda ta karewa dakin kallon tas tanata murmushi Kamar wata shashasha
A hankali ta tube hijabin dake jikinta tayi wulli dashi kan stool din dake gaban mirror Wanda tayi nadamar yin hakan domin atake wani sanyi ne ya daketa Wanda har yafi na falon hakan yasa tadan shafa jikinta
Wannan hali nata tunba yauba inna ke fama da ita na cillar da hijabi ta ko’ina Ba tare data ninke Ba acewar inna wata rana Zara wulla kan Dan aljani
A hankali ta karaso izuwa bakin gadon sannan ahankali ta janyo bargon dake kan gadon kamshin yazeed ne ya daki kofar hancinta Wanda yasata lumshe idanu tare da kara bude kofofin hanci domin ta shaki kamshi
Wani Abu taji yana mata yawo ajiki amma ta share Dan a halin yanzu bata bukatan wani distraction a ranta ko tunani take masu kudi suna sha’anin su saide ita matsalar ta da dukiya in bakayi wasa ba sai ya raba ka da mahaliccin ka.
Abangaren yazeed kuwa kallonta ma kawai yake takaici ya cika masa zuciya Kamar ya mata duka ya rasa yadda zaiyi
Wani karago ne ya tsaya masa a makokoro flinching and unflinching fist dinsa yake kawai saiya Komai cikin dressing room din nasa.
Minal ko ninke bargon tayi sannan ta ajiye badan ranta yaso Ba sai Dan kada hawan jini yazo ya tarar da ita a dakinsa (aikin gama ya gama)
Gadon ta fara gyarawa sanda ta gyara tsaf sannan ta kalli gadon taji batada burin dayawuce ta kwanta akai
Kunji mutuniyar Ku fa na dakinta ma anhanata hawa balle na oga kwatakwata
Aiko kankace me,saiga minal ta tsuguna a gefen gadon sannan ta daura fuskanta akai tanashafa gadon da hannunta mai dauke da baby fingers masu tayi da laushi Wanda suka sha lallen amarci
A hankali ta mike sannan tayi abinda ya kawota dukda Cewa dakinnasa Ba wani datti bane dashi domin yazeed dinma Ba baya bane wajen tsafta.
Tas ta gyara Komai sannan ta dibi kayan aikinta tayi gaba tare da manta hijabin nata adakinsa.
Shiko yazeed koda ya fito ya kalli Inda ta ajiye hijabin kwafa yayi dabadan dukan mace baya birgeshi Ba da babu abinda zai hanashi gyara mata zama,aiyana irin zaman dazaiyi da ita na halin ko in kula acikin gidan yake. Daga karshe ya tashi ya bude wani kofa na daban Wanda shi kuma balcony dinshi ne.
Mika yayi tare da furzar da iska yana mai shafa lallausan sajen dake habarsa Wanda suka a kwance luf luf.
Wayansa ya zaro a aljihunsa sannan ya latso number mahaifiyarsa domin taci ace sun isa yanxu amma yaji shiru bata kirashi ba
MEET MOM

Ringing uku yayi zuwa hudu ta dauka aiko atake yazeed ya shagwabe fuska Kamar tana ganinshi
Haba sweetheart dina ace kin isa tun yaushe amma shine ko ki kira Babyn ki kiji yanake?
Dariya mom tayi sannan tace Allah sarki baby na ai Nasan yanxu akwai wacce zata kularmin Dakai shiyasa kaga hankalina kwance Ashe har ka tashi Daga bacci.
Kwabe fiska ya dad’a yi yace haba mommy ni tun dazu na tashi yafadi hakan yana mai tura baki Kamar mom din na kallonshi.
Mom tace ai na dauka yau sai an hada da duka tukun zaka tashi saboda angwanci
Muryan kuka yazeed yayi yace “moooooom!”
Dariya mom ta karayi yace mom yaushe zaki dawo ? Tace aini son bazan dawoba har sai mun kusa sauka. Yace what!? Tace dagaske nake fa shiyasa na Baku space ma idan Ba kawomin labarin danakeson ji Ba tofa bazan dawoba yace haba mana mummy na! Tace uhm kai yazeed ni kaga tafiyana kit yaji ta kashe wayan.
Yasan Cewa she is very serious da abinda ta fada tunda har ta kirasa da sunansa na asali amma shi the last thing he wants to do on earth shine ko hannun yarinyar nan ya tana Allah ma ya kiyaye bara kawai yaje wurin zakiyya su samawa Kansu mafita.
Allah sarki fans Nayi missing dinku. Karku manta dayin voting, sharing and commenting.
Love you all😘
Karamarsu babbarsu ce
Miss untichlobanty💕
7th October, 2019.Bai tsaya yin wata wata Ba ya koma cikin dakinshi direct laptop dinshi ya dauko ya haye gadonsa sannan ya kunna CCTV dinsa domin rabonsa da ya Duba meke wakana acikin gidansa run shekaranjiya domin baya bukatar cin karo da kayan bakin cikin da baki ke aikatawa
Koda ya kunna forwarding yayi har izuwa na jiya tukunna ya tsaya
tundaga jiya da yamma ya fara kalla har izuwa Inda aka kawo minal zaliha ya hango tana rawar kai,tsaki yaja cikin ransa yace dubi wata me bakin fiska sai shegen rawan kai.
Kalla ya cigaba dayi har izuwa sanda mom ta kawoshi wani tsakin yaja tare da yatsine fiska sannan yadan kamo gefen lip dinsa na kasa yana tsotsa saboda takaici forwarding yayi har izuwa yau da safe
Bangaren masu aiki ya kalla yaga suna ta zirga zirgan su once In a while tunda asuba ne yawanci ma alwala Duke kamin sukayi wanka na minal ya Duba yaga ta tashi tana tafiya ahankali Kamar kazan da kwai ya fashewa take tafiya domin baccin bai isheta Ba .
Cikin nutsuwa yaga ta Shiga sanda ta Dade bata fito Ba ran yazeed ne ya kara back a hanklai yace shegiya kome takeyi aciki haka oho…
Can saiga minal tafito tayi sallh ta fita
Duba parlour yayi yaga banan yaje Ba Dan haka ya Duba na kitchen aiko anan yaganta tana neme neme
Tsaki ya kara ja yana mai cizan lebensa na kasa,can yaga tayi murmushi ta dauki tsintsiya ta fita abinta. kwafa yayi wato ma aikin dadi yaje mata tasaba kenan Ba irin zakiyya bace.+
Zuciyarsa ce tace masa yo kai what do you expect from a low class human being like her.
Girgiza kai kawai yayi irin zai San abinyi.
Ganin shiru bata dawoba yasa yasan Cewa ta fara aikin Dan haka bai bata lokaci Ba ya canja izuwa na dakin uwar gida sarautar mata.
Yawwnci Ba Komai bane sai yadda take kuka lokaci zuwa lokaci da yanda su sahir ke sha’aninsu hankali kwance illa in sunga tana kuka su tambayeta matsalarta in tace babu sai su goge mata hawaye suna masu jin tausayinta hardai izuwa jiya da akakai minal wajenta da kuma sanda yazo dakin da yadda su kayi fada har yau da safe.
Da wuri yaga ta tashi Wanda hakan yabashi mamaki matuka Dan shidai yasan Ba sallah take akan lokaci Ba yayi magana,yayi fada,yayi fishi har ya hakura amma yau ta tashi da asuba Alhamdulillah shiryuwa ya samu matarsa ta fara gyarawa.
To his disappointment wanka tayi ta Shirya tsaf shirinta na zuwa office Kamar yadda ta saba wani ras yaji a kirjinsa,bakin ciki yayi masa kaluluwa a zuciya,wato ba’a yaban Dan kuturu saiya shekara da yatsu. Ganin ta dauki jakanta DIOR yasan Cewa ta tafi hakan yasa ya koma kitchen yayi playing Daga Inda ya tsaya sannan ya fara forwarding a hankali can yaga su atine sun Shiga Suna hayaniya ba’ajin me suke Cewa saboda yadda muryansu ya kacame Kamar gidan Suna
Parlour yaga sun nufa Dan haka yayi pausing yaje yayi playing na parlour ya fara forwarding aiko atake yayi playing yana mai kara hade fiskaganin abinda ya tsana ta fito tana tafiyar nan nata Wanda ke kara bata masa rai saboda yadda zuciyarsa ke bugawa aduk lokacin daya gani
Shara yaga ta fara tana aikinta cikin nutsuwa da kwarewa,shi kansa idan yace batada kyau yasan San zuciyane kawai amma ai she is not his type worse of all she is a gold digger. Mtswww wani wawan tsaki ya kara ja sannan taci gaba da kalla su binta yagani sun shigo nan yaga sun fara yiwa minal murmushi Suna magana tare kokarin karban aikin duk yadda yayi kokarin jin me suke Cewa ya kasa saboda yadda suke maganar kaman marasa Gaskiya can yaga sun kara hanyar kitchen hakan yasa yayi pausing tare da komawa na kitchen yayi playing aiko gaji yayi sun Shiga kafin suka fara aikin tare sunata hira minal nata musu murmushi
Aransa yace lallai yarinyannan wato ta rainani ko?wato har wani nasu aikin da nasata take kuma har tana murmushi lallai rayuwa batayi mata kunci Ba tukunna kwafa ya kuma yi yana kara gyara kwanciyarsa tare da janyo laptop dinnasa sosai sannan ya kashe Dan takaici ya masa yawa. Ruf da cikin yayi yana mai lumshe rikitattun idanunsa tare da sauke ajiyar zuciya.
Bayan yayi sallar la’asar ya dawo gida tundaga mai kofan parlour yajiyo kamshin abinci wani kurrr cikinsa ya bada sauti aiko yana dago Kansa karaf ya hango minal tana saukowa Daga stair case sanye take da black short bun da white t shirt sai dogon hijabi mai hannun Dan haka baya iya hango abinda ke jikinta.
He was expecting her takoma da gudu Dan ta buya amma to his surprise yaga tana pretending Kamar bata ganshi Ba
Itako minal kokari take ta Koma kitchen domin Duba abincinta,Dan haka da Dan sassarfa take saukowa,wani Abu yaji ya tokare masa numfashi saboda bakin ciki taga alamun yarinyarnan zata kawo masa rainin sense,Dan haka shima da sauri ya fara yawa aiko minal bata ankare Ba taji tayi karo da gini amma abinda ya bata mamanki shine irin kamshin da gadon yazeed keyi irinshi taji ya bigi hancinta
Taga taga tayi Kamar zata dadi yazeed yayi sauri rikota aiko tsayuwarta na daidai tuwa taji tassss! Ya dauketa da mari wutanta ne ya dauke na Dan wani lokaci.
Yazeed ko baice komaiba kawai sama yayi abinsa ya nufi side dinsa hankali kwance Kamar Ba shi ya kaftawa har mutane mari Ba.
Minal Kam sanda ta daskare awurin for almost five min kafin hawaye ya tsiranyo a idanunta
Ahankli take Daga kafafunta har ta isa zuwa kitchen ta samu har atine ta kashe mata Dan haka kawai tace wa atinen su dibi nasu domin dama yam porridge tayi
Aiko atine tace to aunty Amarya sannan ta diba musu Dana securities din da’ake bawa abinci guntun ta juye a flask takai dakin minal da sallama ta Shiga amma bataga kowa Ba Dan haka ta ajiye kawai ta fice abunta zuciyarta kal yawunta har tsinkewa yaje tana Allah Allah taci abincin minal Dan bazata manta sanda taci tuwo Ba.
Minal ko tana dawowa daki toilet ta fada tabaje akasa sai kuka
Jin alamun antaba kofar dakinta yasa ta sassauta murya
Tanajin anfita ta kara bude makokoro ta sha kukanta Kamar umarni Daga Allah.
Da daddare…….
Show some love by voting and commenting.
Sauri nake so bye, love you all😘
Miss untichlobanty💕
9th October,2019.Duk Wanda kuke karantawa bakwayin commenting ko voting ina kallonku.3
😭idan kuka karanta bakuyi voting Ba kuna nufin bai muku Ba kenan.
Please Kiyi supporting dina by voting sharing.
DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
Asha karatu lafiya
Da daddare minal na zaune a dakinta idanunta da suka kumbura sanadiyyan kukan da tayi dazu sun Dan sace sai ajiyan zuciya takeyi.
Wani azababben yunwa ke nukurkusatta Kamar me Dan haka ta dauko flask din da atine ta kawo mata aiko tana ganin abinci mutuminta ta manta da Komai Kamar Ba ita ta gama sharar kuka Ba
Yam porridge dinta ta cinye tana mai side hannu kamin ta dauki flask din tayi kitchen domin ta wanke
Kitchen din ta Shiga ta wanke flask din kamin ta fito jikinta a sanyaye
Shigar jikinta na dazu ne saide yanzu ta daura zani domin Ba hijabin dazu bane
Zanin atamfa ne mai kyau Wanda ta dauko acikin kayan nata. Wani taku takejiyowa na isa da takama da nuna isa da kuma nuna kowa Ba kowa bane.
Tafiyarta ta cigaba dayi Ba tare da ta waiwaiya Ba domin wani bacci dake dibanta saboda gajiyar da tayi
Staircase ta kama za’a hau gaji an fincikota….Taga taga tayi kamin ta dai daita tsayuwarta da taimakon ginin dake gefenta wani nauyayyan ajiyan zuciya ta sauke kana ta hade ranta ta dago domin ganin wani uban ne yayi mata irin fincikar nan aiko tana dago idonta tage zakiyya ta hade rai tayi kananu da idanu+
Ke Dan ubanki ankawoki aiki shine kikewa mutane yawo agida sannan bakisa uniform Ba kuma kinajin alamun mutane baki iya gaisuwaba? Tukunna ma urban Waye ya baki damar hawa sama?oh Ashe ankawo kaskancacciya yar uwarki Wanda batasan dokokin gidan mutane Ba tazo tana tsifo mana iyayi
Ganin minal ta kafeta da idanu Ba tare da tace komaiba yasa tace idan baki dena kallona da wannan shanyayyun idanun naki Ba sai naci ub*nki common get out of my sight useless human being. karbi kikai min wannan sama tunda abinda kikeso kenan.
Atine Wanda ta Shiga domin yiwa uwargijiyatta ta 2 Kumar amaryar oga yazeed tajiyo abinda zakiyya ke Cewa Shigowa tayi ta russuna tana mai Cewa sannu da zuwa aunty.
Zakiyya dake kallon minal ta kallo atine kamin ta kuma kallon minal tace haka ake gaidani agidannan.
Atine ne ta aro wani jarumta kana tace rankin shi Dade ai wannan itace amaryar.
What!?wannan abar me zubin aljanu?
Jikin atine na rawa ta gyada kai kana tace Allah bamu alkhairi ta fice tana mai zazzare idanu alamar kidimewa Dan bata bukatar rashin hankali ana zaune lafiya
Minal kam shiru tayi Kamar wata kulya ta dunkule a lungu daya takaici ya hanata yin komai
Zakiyya da mamaki da kuma kishi ya cikata yasa batayi wata wata Ba tace au Ashe Kece wannan dabbar wacce talauci ta dama akayi auren jari ai da kin sanar dani Cewa kuna bukatar kudi na baki Wanda za’a ciyarda danginki baki daya bawai Kiyi kokarin hada kanki dani Ba JAKAR BAIWA kawai,wuce ki hadomin tea kamin na saba miki.
Minal kam yau da badan sharadin da yazeed ya gindaya mata Ba da babu abinda zai hanata shukawa zakiyya rashin mutunci amma tana tsoro kada wancen azzalumin ya kasheta Dan tasan sojoji Ba mutunci bane dasu bare imani ko tausayi.
A hankali ta koma kitchen din sannan ta hadomata shayin domin atine ta nuna mata Komai da yadda zatayi amfani dasu.
A bakin kofar dakinta ta tsaya ta kasa Shiga zakiyya ko tana Shiga dakinta ta fada kan gado ranta na wani irin kuna
Can wajen 10min taji shiru Dan haka ta fito domin ta antayawa minal rashin mutunci aiko daidai lokacin minal ma ta aro jarumta minal na daura hannunta akan handle din zakiyya ta bude kofar a zafafe aiko take kofin shayi ya watsu musu dukkansu biyu Wanda yamafi zubowa minal din sannan ya fadi ya fashe
Wani wawan mari zakiyya ta kwasheta dashi kamin tace kan buhun bala’i ! ke wace iriyar dakikiya ce dabba kina Abu Kamar jaka!saboda tsabar bakida hankali bare lissafi shine zaki kama ki zuba mini tea ajiki?
To Dan matsiyacin ubanki ki gyara nan wurin sannan ki hado Mani wani kamin in fito Daga wanka.
Minal dago rinannun idanunta tayi ta nuna zakiyya da Dan yatsa kana tace ahir dinki duk haukarki ta kare a kaina tunda dani kike kishi amma kada ki kuskura ki kara sako da iyayena.
Kuma baza’a hado shayin Ba inga abinda zakiyi tana fadin haka tasa hannu ta fara kwashe glass din.
Zakiyya ko a harzuke ta nufi side din yazeed Kamar wata zakanya
Bude kofar tayi tagansa ya fito Daga wanka da alama kwanciya zaiyi.
Yazeed ko mayatar ce ke cinsa ya kasa jurewa,yayi azumin,yayi addu’an,yasha magani amma desire nanan Dan haka ya yanke shawarar gara yaje ya samu zakiyyan ko kadan ne ya samu da babu gara Ba dadi. Gwara yaje yayi yanda ya saba ya danyi maneji abinsa Dan shikam hakuri kawai yakeyi shekara da shekaru bawai dan yana gamsuwa Ba Dan tunda sukayi aure da zakiyya baifi sai 3 ya zama satisfied domin Daga tazama satisfied to shikenan fa zata fara raki Wai ta gaji.
Sai gashi Allah ya aiko masa ita tsuntsu gasashe Daga sama
Ganin yanayinta yasa yace Matas ya akayi ne yana mai kashe mata ido tare da fara takowa izuwa gareta tsaki taja domin ta gano me yake bukata kana fara huhhura hanci tana jijjiga tace “baby kaga irinta ko? kaga abinda mom tayi ko?gashinan ai yanxu ta aro maka wata kaskancacciya kuma ma abin haushin Wai Dan tsabar fitsara har ta dubi idona Wai nasata aiki Wai bazatayi ba kuma harda nuna mini Dan yatsa
Rungumota yazeed yayi danshi bayason irin yanda takeyiwa mahaifiyarsa shiyasa duk sanda ta fara zai yi kokarin kawqr da maganan inata dage to saide suyi fada
Turesa ta fara yi ni Dan Allah cikani kai ko wani lokaci sai ana serious Abu sai kazo kawani hau kakabe kakabe ni banson jaraba.
Kallonta kawai yake tare da murtuke fiska Kamar basho yagama mata kalar tausayi Ba sannan ya hankadeta kadan Daga jikinsa yace zakiyya yanxu akan hakkina zaki kirani jarababbe, Toh gashinan nabar maki ki jika kisha nima zan rike abina.
Rigan baccin daya ajiye kan gadonsa ya dauko ya zura sannan ya kwanta tare da Cewa inkin gama zaki iya rufemin kofar daki sannan ya juya
Baiji takunta Ba kawai ji yayi an rungumosa ta baya……………..
🎶wetin be that nothing I can’t do for my bebe ma bebe🎶
Today I just felt like singing, su shaidan manya😉😂
🎵i am waiting for your comments
Don’t forget to vote
Miss untichlobanty💕
11 October, 2019.
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.Baice mata kala Ba yanaji tana shafa kirjinsa ahankali wani mugun kuma jahilin feelings ke taso masa amma ko dar baiyi Ba a hankali yaji ta fara saukar da hannunta wajan cibiyarsa tana yawo da hannunta tsaki yaja kamin yadan matsa gaba kadan still hannunta na jikinshi
Matsowa itama tayi tanakai hannunta kan abinda ai babu shiri ya mike tare da cire hannunta yayi wulli dashi
Kana ya fara magana a harzuke Wai me kika daukenine eh?ko kin dauka jarabata har takai nazama banida zuciya ne?ince P kuma nace banaso
Hannunta takai zata riko nashi yace karki kuskura ki tabani kinji na fadamiki.
Tace haba baby kayi hakuri mana kasan raina abace yake lokacin shiyasa na fadi hakan harara ya watsa mata kana ya kwanta Wanda yasa ta fahimci Cewa ya Dan hakura Dan haka ta fara aika masa sakwanni masu birki kwakwalwa aiko dama gogan naku ma a hanu yake Dan haka baiyi wasa da damarsa Ba ya bada kai bori yahau. saide kash zakiyya na zama satisfied ta fara nifa baby na gaji yazeed najinta kuma ransa na kuna danshi ko Rabi baije Ba ta cigaba da cea Wai baka gaji din bane ni ka barni na gaji please
Dan Allah ni ka matsa mutum sai shegiyar mayata Wai……..
Jin cak ya tsaya kana ya bar jikinta hakan yasa bata karasa fadar abinda tayi niyan fada ba sannan ta dubesa aiko hatta jijiyoyin kansa sun tashi saboda Bacin rai .
Kofa kawai ya nuna mata Da hannu danshi kanshi tsoran motsi yake dan gani yake babu abinda zai hanashi yiwa zakiyya dukan kawo wuka a darennan.
Zakiyya na ganin haka tasan ta kwabsa domin ko ta bata masa rai Wanda hakan ke nufin bazai hukunta minal Ba tunda dama ta bada Kaine saboda taci uban minal gobe never the less she enjoyed it.
Aiko dole ta gyara kafin reshe ya juyewa mujiya, matsowa tayi kuwa dashi yace out,tace bab….
Kofa ya nuna mata tare da maimaita mata Cewa tabar masa daki rungumosa tayi yace ke banson iskanci meye hakan? tace ban koshi bane .
Wani harara ya watsa mata irin me kika mayar dani kamin ya yakiceta ya fada bathroom yana mai jin zafin hali irin na zakiyya Sam Daga bukatarta ta biya to shikenan shikam ko oho
Son kai yayi mata yawa…….. Haka ya dinga sake sakensa yayi wanka tare da wankan tsarki sannan ya fito
Koda ya fito Bai sameta Ba Dan haka ya Shirya abinsa yayi kwanciyarsa zuciyarsa cunkushe ga kuma wutar déjà vu dake addabarsa yanajin Kamar zaiyi hauka.
Bashi yayi bacci Ba sai wajen 2:30 domin juye juye yaketayi dayaga babu sarki sai Allah kawai sai ya fara kuka hawaye nabin kuncinsa ga wani mugu Abu mai zafi daya tsaya masa a zuciya gameda abinda zakiyya keyi masa.
Abangaren minal kuwa kwashe ceramic din take tana kukan takaici da bakin ciki ita yanxu a haka zata karashe rayuwarta cikin bauta?Allah ka kawomin dauki shine abinda take fadi tana gama kwashewa ta zubar ta gyara wajen sannan ta tafi dakinta wanka ta Shiga ta Dade Kamar yadda ta saba(ko me takeyi oho muje zuwa daganan zamu gano)
Fitowa tayi sannan ta tsaya a gaban madubinta taci gaba da abinda take yi a bandaki kullum tun tana gida har ya zame mata jiki in batayiba batajin dadi.
Bayan ta gama Shirye shiryenta tayi alwala sannan ta kwanta tana mai nazarin rayuwarta
Zakiyya ko koda taje dakin ta Fadawa gadonta tayi tana mai tsaki kana tace kaika sani Idan jarabarka ta matso ka zama kazo ne sannan ta bingire da bacci Ba tare da tayi ko tsarki Ba balle wankan tsarki ko makamancinsa(uhm Allah kyauta)
MORNING
Yau kam minal sai 7 tukunna ta fito yin aikinta Wanda takeyinsa bisa kwarewa bayan ta kammala ta Koma daki tayi wanka ta Shirya cikin atampa blue mai mai circle yellow sannan ta zauna a kan kujera tunda batada right din zama a gado tana karanta wasikar jaki.
Banko kofar dakinta taji Anyi take jikinta ya dauki rawa domin tasan cikin biyu daya ne ko mijin ko matar sa
Aiko yazeed ne yana wani yatsine fiska Kamar yaga kashi sannan yace wato ke gaki hamshakiya ko in bada umarni ki take
Sai yayi murmushin gefen baki to ai shikenan kinga ko Ba Komai zaki ragewa washing machine dina aiki Wanda ke nufin bill din nepa da kuma kudin gas zai ragu domin Daga yanxu ke zaki dinga wankemin singlets and boxers dina Mara mutunci gold digger kawai.(uhm yazeed kenan sai kace kuddin bill din wani Abu yaje rage masa)
Zaki tashi kije dakina ki dibo su yanzu ko sai na wanke miki wannan shegiyar fiskannaki da tafi
Jiki na rawa ta mike zata fita yace “hold on! dakata” ta jiyo wannan karan ranta adan bace
Yace ya zama dole kibi umarnin matata
Batasan lokacin da tayi kicin kicin da ido tace wallah nanne kuma kayi karya na rantse……
Aguje ta fice domin yunkurin da yazeed yayi zai kamota ya gwabe bakin da Kamar zai bita sai ya Fasa ya nufi dinning area yana mamaki Wai yarinyarnan ce ke masa irin wannan rainin wayon da fitsara?
Zuciyarsa ce tace masa what do you expect from a ghetto girl like her?inbatayi fitsara bama sai Allah ya tambayeta(fadi Gaskiya babana?
Dinning room ya Shiga abinshi ya hada tea yasha tare da cin plantain baifi 5 slice ba Sannan ya wuce gym room dinsa.
Minal ko data dauko kayan wankesu tayi tas sannan ta shanya sannan ta koma ta nemi abinci taci
Zata koma dakinta taji ance ke!..ke!..ke! asararriyar baiwa zonan juyowa minal tayi a hasale kawai sai kalaman yazeed ya fado mata
Wani irin kallo takeyiwa zakiyya at any moment zata iya mata illa zakiyya ko dukda tana shakkun captain yayiwa minal din magana ko baiyiba amma bazata barta taci banza Ba
Zaki rama ne? Shiru minal tayi, zakiyya ta tabe baki kana tace zokiyi min tausa
Wani harara ta rafkawa zakiyyan aranta tace wallahi baki isa Ba saide mijinki ya kasheni
tasowa zakiyya tayi tana nufo minal domin dauketa da tafi minal ko rayawa take aranta irin rashin mutuncin da zata antayawa zakiyya Idan ta tabata Dan ita Ba jaka bace
Yazeed ne ya shigo cikin isa fiskannan Kamar bakin hadirin daya taso Daga yamma kamshin Cologne din da yakeyi ne ya Sanar da minal isowarsa
Atake kirjin minal din ya buga kana tsoro ya shigeta amma kunsanta da taurin kai bata nuna Ba saide tanaji jikinta har makarkata yakeyi
Wajen su ya iso ya watsawa zakiyya kallon me kikeyi Anan?tsaki taja ta wuce koda ya juyo ganin Inda minal ke tsaye yaga empty,ta arce.
Zakiyya kam ficewa tayi Daga gidan tana Cewa malam sule idan ya dauko yaranta kar ya kaisu gida ya Kaisu su siyo cup cakes kamin ya kawosu boutique dinta Kamar yadda ya saba
Yace to hajiya Insha Allah ta wuce abinta ta shige cikin 4matic dinta ta wuce .
Don’t forget to vote,share and comment pleeease because that is the only way zan gane yadda kukeson novel din.
Taku for life;karamarsu babbarsu wato
Miss untichlobanty💕
13th October, 2019.Sama ya haura direct dakin minal ya Shiga ya sameta tana ajiyar zuciya yace follow me
Ta dago idanunta ta kallesa domin neman karin bayani wani electric shock sukaji dukkansu biyu kamin ya waske ta hanyar Cewa ko bazaki iya zuwa bane kin kafeni da inu munafuka?
Shiru still tayi ya fice itama ta bisa subul subul tana mai gyara zaman yellow hijabinta
Koda ta shigo dakin akan coach ta samesa zaune ya daura daya akan daya yace bazaki iya karasowa bane?
Ahankali ta tako a tsure dukda bata bayyana hakan Ba ta tsaya a Dan gefensa
Yace closer tare da mata alamu da hannu ta Dan kara matsowa harara ya buga mata tare da Cewa cinyeki zanyi ta girgiza kai tana mai karasowa da Dan Sauri tsayuwa tayi a kansa
Ya kamo bakin hijabinta ya janyota kasa
Dan kara ta saki domin hijabin ya Dan kurji gefen wuyanta kana visa kuskure ta Dan taka kafarsa kamin ta zube,yace Dan kaniyarki haka zaki tsaya akan yayanki ta girgiza kai yace bakida baki ne tace a’a
Harara ya kwada mata yana mai hadawa da rakwashi kwas a tsakiyar kanta yace bakisan in antaka mutum hakuri ake basa Ba?girgiza kai tayi alamu tasani tana rarraba idanu Dan rankwashin ya shigeta
Janyota yayi ya matse cute pinky lips dinta yana kalla yace wato gani sarkin mahaukata ko ina magana kin bawa banza ajiyata+
A hankali hannunta na rawa ta daura akan nashi alamun ya sake bakin zatayi magana idanunta ko ya cicciko da hawaye saboda radadin da bakinta ke mata shikuwa wani yaaaam yaji Ba shiri ya saki bakin kana ya kauda kansa gefe domin jin bananarsa na kokarin kawo masa raini
Ahankali cike da in’ina tace kayi hakuri na taka ka,tsika jikinsa suka mike gabadaya yayinda hawayen da taketa boyewa ya samu nasarar saukowa
Ba tareda ya kalleta Ba yace nace miki kimin wanki shine Dan kin rainani ki kamin jika jika ko?
Muryarta na rawa tace wallahi me kyau Nayi kaga hannuna ma ta nuno masa gefen hannunta yadda yayi jaa Kamar ka taba jini ya fita tsabar yadda ta dirji kayan
Tsaki yaja yace raguwar banza dan kin wanke singlets 3 da boxers 3 Wanda nasa jiya shine zakina wani nokewa Kamar marainiya
Batasan lokacin da tace aide nafi wasu juyowa yayi adan zabure Dan baiyi expecting ta mayar masa da magana Ba
Hannu yasa ya bige bakinta yace zaki tashi kibar gefena ko saina maujeki in canja miki halitta.
Da Sauri tabar dakin tana mai zubda kwalla,lallai tayi kuskuren amincewa da zancen auren Ba tareda ta saurari ko Waye su baba zasu aura mata ba sai a yanzu ne take kara ganin wautarta
Dakinta ta koma ta tsaya agaban madubi tana kallon yadda tayi kyau dukda kuwa ko petroleum jelly bata shafa Ba balle powder amma idanunta sundan fada ciki sannan ta zama kalar tausayi babu walwala a tattare da ita.
Haka rayuwa taci gaba wa minal yanxu har tayi wata 3 a gidan captain tanayin aikinta Kamar kullum once in a while sukan hadu da zakiyya inta gama banbaminta minal kawai ce mata take Allah ya baki hakuri sannan ta wuce itako zakiyya babu abinda ta tsana Kamar tayima rashin mutunci ka nuna bai dameka Ba Dan haka sai tayita kumfan baki tana cika tana batsewa
Minal ko gani takeyi Kamar zakiyya taci noti kuma tana bukatan Sabo hakan yasa bata tanka mata har tayi ta gama
Aunty fauzy ta kawo mata ziyara har sai biyu Inda take kara jaddada mata girman aure da kuma yadda zata zauna da abokiyar zamanta lafiya. Ita dai minal kunne kawai ta kasa Cewa komi aranta ko tana Cewa cab ai bakisan halin abokiyar zaman tawa da mijinta ba da ko zancenta bazakiso muyi ba.
Yau saura 3 days auren zaliha Inda gobe ne za’ayi kamu
Minal nason tambayar captain izini tun last 2 weeks amma tsoro take yau kam shahada tayi ta turo kofar dakin da yar sallama a bakinta aiko abinda ta gani shi ya Daga mata hankali captain ne ya fito Daga wanka Daga shi sai gajeren wando fari kal da bathrobe Wanda ya barshi haka ba tare da ya daure igiyan ba wanda yayi sanadiyyar Nuna dukkan ilahirin faffadar kirjinsa mai dauke da gashi kwance luf luf Wanda keda laushi hamar gashin kan jariri.
STORY CONTINUES BELOW

Rikicewa tayi a maimakon ta fita saita fada bandaki aiko ta sule sai a kasa Inda ta bige makunin shower sannan ta gurde kafanta salati ta sake tare da sakin wata gigitacciyar kara hawaye kuwa tuni sun Dade da fara ture junansu wajen saukowa yiyinda ruwa ya mata sharkab.
Captain da bai San ta shigo dakinba yaji ihunta atake ya nufi bandakin ganinta shame shame a kasa ta jike da ruwa jakab ya sashi Jan tsaki tare da Cewa ke Dan ubanki me ya kawoki cikin bandaki na bayan yau ba ranan wankewa ba?
Kuka kawai take kamin tace Dan Allah ka taimaka mini wayyo kafata tsaki yaja da Kamar zai fita amma yadda take kuka yasa yaga bazai iya barinta ba yasa ya miko mata hannu aiko hannunta ta mika ta rike nasa take sukaji Kamar sun taba wayar wuta ba shiri ya saki hannun ji yayi jijiyarsa ta fara harbawa Wanda yasashi Cewa kaide kayi asara yazeed acikin zuciyarsa
Sake miko mata hannun yayi ya Dagata
Dingishi ta soma har zasu fita yace dakata !me kike nufi?
Kallonsa take alamun Neman Karin bayani yace au dake a haka kike nufin zaki Shiga dakina ki jika mini da ruwa saboda Yan garinku basuda lissafi?
Bata fiska tayi cikin rants tace badai garinmu ba wallahi
Yatsansa yasa ya dalle mata baki yace dani kike tayi saurin girgiza kai alamun a ah hannun yasa zai cire mata hijabin dake jikinta ta rike kyam kiciniya suka fara aiko yazeed ya riko hannunta duka biyu da hannu daya sannan ya zame hijabin da hannun daya yayi Ciro dashi
Kallonta ya farayi Inda idonsa ya tsaya kyam akan cikakkun breast dinta Wanda doguwar Riga jikinta da ta like mata har nipple dinta ana kallo wani yawun jaraba ya hadiya ‘kutt kana ya kalli fiskanta aiko shi take kallo and she caught him staring at her boobs red handed
Waskewa yayi ta hanyar tabe baki sannan yace yanxu dama wadannan tsiyar ake boyewa?uhm aike yarinya bama kida abin boyewa danko tsirara zakiyi yawo bakikai akalleki ba uhm kwaila lamba daya kawai sannan ya fice ya barta a wurin minal ko tabe baki tayi tanacewa jeka dai Nasan borin kunyace kawai kumanima ai jikina tafi karfin mugu sannan ta murkuda baki
After Kamar 1min saiga yazeed ya shigo rike da wata T-shirt dinshi fari kal wulla mata tayi sannan ya fice yana yana mai Cewa yi Sauri kibar Mani daki
Domin alokacin har wani hajijiya yakeji tsabar sha’awa
Dan Rabon da yayi harka sati biyu kenan amma yanagudun abin kunya kuma ai yarinyar gold digger ce so he should be very careful kar mazakutassa takaishi ta baroshi.
Minal ko tsayawa kallon Rigan tayi wai me mutuminnan ke nufine Wai ko bazai bata wando bane?
Jin shiru bata fito ba yasa yace Wai Dan kaniyarki bazaki fita bane kullum kika Shiga bandaki Kamar mai haihuwa
Sauri tayi ta saka rigar tana mai Cewa ko yaushe ya taba ganin sanda nake Shiga bandakin oho mutum sai shegen fi’ili
Iya cinyarta rigar ta tsaya Dan haka ta fito tana jajjan rigar domin rufe jikinta
Aiko yazeed na ganinta sanda yaji numfashinsa yadanyi seizing
Kana ya dawo
Ganin yadda takeyi da fiska ya bashi dariya amma taci mur
Muryarsa Kamar yasha giya yace zonan
Zuwa tayi ta zauna a kasa domin bata manta da abinda ya mata ba sanda ta tsaya masa akai yace me yakawoki dakina ?
In ina ta fara tace dama Ami..niya..ta..ce zata..yi aure shine….nakeson naje
Tabe baki yayi yace naji zaki iya zuwa amma ko gidanku ban yarda kije ba
Kallonsa tayi alamun lafiya kake kuwa ?
Baibi takanta yace zaki iya bar mini daki kuma kitabbata kin kwashe tsummokaranki
Fita tayi tana nazari acewai mutum rabonshi da iyayensa kusan wata 5 amma Dan rashin imani ace bazashi ba ALLAH YA ISA
captain yazeed zaune a bakin gadonsa yana buga game din chase a laptop dinsa Kiran mom ya Shigo dauka yayi
yace salamu alaiki ya habibaty
Mom tace Ameen wa alaikas salam son yakake?
Yace lafiya kalau mom i missed you amma ke naga baki damu da Babyn ki Ba
Dariya mom tayi tace Dan Allah dubeka wani kato dakai Wai baby na kai Wai bazaka barwa ‘ya’yanka shagwabar bane?
Kwabe fuska yazeed yayi yadda yara keyi inka kwace musu alewa yace ai kowa da matsayinsa nidai Nasan ni Babyn ki ne ya kashe ido Kamar mom na kallonsa
Mom tace Allah ya kawo masu albarka sannan tasa serious tune tace yazeed naji shirufa bawani labari gashi har kunyi kusan wata 5 da yarinyannan kuma kasan dai daya Daga cikin abinda yasa naso maka aurenta kenan tunda naga kaida zakiyya bakuda tsarin haihuwa kusa ni sai mai shirin Haifa ta haifo mini
Hade rai yayi yana yatsine sannan ya tabe baki yace ai mom yarinyan ce tukunna ina Duba natsuwarta da hankalinta sannan inga ta dace ta zama uwar yayana koko?kuma kinga bata gama wani girma dazan daura mata nauyina Ba.
Sakin baki mom tayi jin abinda yazeed din yace
Yazeed kuwa jin tayi shiru yasa yace mom kina jina?
Kamar Wanda aka watsawa ruwan sanyi mom tace d’annan dama duk zaman da kukeyi da yar mutane Ba bata hakkinta kake ba? Kai a haka zaka rike mata biyun yazeed ?kana danne mata hakki?ja’iri shine harda wani Wai bazata iya daukan nauyinka ba sai kace wani abin arziki ka ajiye acikin wandon naka?to bara kaji yarinyar da kake renawan tsab zata daukeka harda guntu Dan jakar uba kawai……..
Sai alokacin yazeed ya gane ya kwabsa Sosa ‘keya ya fara kana yace mummyyy kiyi hakuri zan gyara Insha Allah
Mom tace karma ka gyara kai ka jiyota kuma zan dawo kasar inyi sati a gidan naku kamin na Koma gidana na Abuja saboda association Suna bukata na dama Hutu na dauka
Nan dai mom ta surfo masa kwadokwandon bala’i kamin tayi masa wa’azi ta kuma tunasar dashi hakkin matarsa dake kansa sannan ta kashe wayarta tana mai jinjina al’amari irin na tilon Dan nata shiko yazeed tabe baki yayi yace Allah ya kiyaye ni dayin abin kunya da jawakai raini
I will be waiting for your comments
Don’t forget to vote as well
Miss untichlobanty💕
13th October, 2019.Saukowa yakeyi Daga stair case domin zuwa masjid phone dinshi ya dau ringing
Dubawa yayi yaga mom yace yau nadebowa kaina
Picking yayi yana Cewa sweetheart har kinyi missing dinane ?
Ta dayan bangaren mom tace dan Allah ni matsa mini ka rufen baki ka sadani da dadiyata
Marairaice fuska yayi yace haba mummy abin fa baikai nan Ba mom tace yama wuce nan. Zaka hadani da ita inji muryarta koko? juyawa yayi ya fara komawa sama kana ya nufi hanyar dakin minal sallaya ya gani a hannunta alamun sallah zatayi harara ya banka mata sannan ya mika mata wayan yana mata kallon kashedi alamun inata kwafsa zaici ub**ta
Karba tayi jiki na rawa muryar Kamar zatayi kuka tace sallam alaiki, mom?
Ajiyan zuciya mom ta sauke tace wa alaikis salam diyata yar albarka yakike?
Dashi ke wayan a hands free yake captain na jinsu tabe baki yayi yana mai lumshe idanu
Minal tace lafiya kalau mom tace ya hakuri da mijin naki?minal ta dago idanunta ta kafeshi dasu kana ta sauke tace Alhamdulillah
Mom tace sai hakuri kinsanshi baudadden mutum ne ga taurin kan masifa sai kina hakuri kinji tace Toh
Nanfa mom ta fara mata magana akan rashin hada gadonsu ita da yazeed itakam batasan Inda mom ta dosa ba Dan haka koda mom ta karashe kawai Cewa tayi Insha Allah za’a gyara Kiyi hakuri
Shiru ne ya Dan ratsa gurin jin shirun yayi yawa yasa mom tace da fatan babu wata matsala ko?minal tace babu mom tace Kin tabbata ? Minal cikin in’ina tace dama inaso inyi waya da gida ne salati mom ta rafka kamin tayi kicin kicin da ido tace to bari zanfadawa yazeed din ko?minal tace to na gode Allah ya saka da alkhairi mom tace Ameen. Sallama su kayi sannan ta jiyo domin mikawa yazeed wayarsa+
Yazeed ko tun sanda mom ta fara yiwa minal wannan magana ya Lula duniyar tunani.
Tunani kala kala yakeyi kamin. A ransa Gaskiya ni sweetheart tana kwafsamin wannan ai sai tasa yarinyar ta rainani.
Haba fi sabilillah ni Gaskiya…..
Tunanin nasa ne ya datse saboda miko masa wayar da minal kallon hannunsa yayi ya zabga mata harara da tsaki sannan ya Karba ya fice yana mai banko kofar sannan ya kara wayar a kunne yace haba sweetheart ai saikisa yarinyar nan ta rainani ya zaki dinga…..
Ba karashe ba sanadiyyar mom data datseshi ta hanyar rafka uwar salati sannan ta kara da Cewa d’annan wallahi ka fita a idona na rufe kanajina ko?yazeed!yace na’am, yazeed!! Na’am,yazeed!!!sai nawa na kira sunanka yace uku tace to wallahi ka kiyaye ni ka fita daga idona in rife wato Dan wulakanci shine ka rife er mutane a gida baka bata hakinta kuma baka taba kaita taga iyayenta ba?kai ance ma haka ake auren?ko Dan kaga Nina aura ma ita shine zaka nuna min ban isa ba? Shikenan yazeed ni bazan yi fishi dakai ba amma ka sani hakkin yar mutane ma ya isheka kuma ka wuce yanxu basai anjima ba ka siyo mata waya tare da sim da kati da kuma data aciki sauran ya rage naka kuma batun raini saide kar a kuma tunda ka Riga da ka aurota……. Tiiiiitt mom ta kashe wayar
Kallo yazeed yabi wayar dashi kamin ya sauke wata nannauyar ajiyan zuciya. Shikam ya rasa yadda zaiyi da ransa wannan itace rana zafi inuwa kuna.
Koda ya fito da lukman taci Karo a hanya lukman yace boss!boss ya akayine na ganka haka na lura tun da safe Kamar wani Abu na damunka
Harara yazeed ya banka masa yace yau kuma wani fi’ili ka tsiro dashi babu kowan ma kake kirana da boss?
Dariya lukman yayi yace kai mutumi kaide baka canzawa Nide ba wannan ba meke damunka ?yazeed yace babu komai lukman yace haba yazeed na lura tun lokacin da akayi aurennan abotarmu taja baya yes nasani bamu nuna wa duniya Cewa mudin abokai ne especially ta fannin aiki amma hakan ba hujja bace dazaisa ka dinga boyemin damuwar ka kasan babu sirri a tsakaninmu, damuwar ka damuwata ce.
Kallonshi yazeed yayi irin ‘look who is talking’ dinnan sannan yace dama ba soja kayi ba da gidan radio ka nufa Kamar da gaske fisabillillahi luku tun Muna primary mukaci buri Cewa zama sojoji kuma masu mukami amma me sanda lokacin yayi ka kasa fadamin Cewa bazaka iya zuwa makarantar ba saboda cancer daya kama mahaifinka bakuda hali,ka boye mini sai a diploma ka kare saboda cika burinka kuma ka zama recruit shine yanxu zakana cemin Wai babu sirri tsakaninmu ai boye boye ka gama min ita mtsww.
Sauri yazeed ya fara domin ya wuce lukman amma lukman yayi Sauri rikosa yace haba aminina kar miyi haka dakai mana Nasan ko wannan mahaifinnawa ne ya Daga kar in fadi maka bada son raina bane kaima ka sani yazeed yace naji
In a bossy tone Lukman yace to shikenan idan min fito Daga masjid din sai ka fadamin matsalar ka
Kallon sa yazeed ya kuma yi kamin yace irin oga yayi magana kuma angama ko?
Lukman yace to ya ranka?table baki yazeed yayi kamin suka Shiga masallati yazeed na lissafi a zuciya lallai ba shakka lukman ya kasance amini a gareshi babu karya sudin masu kauna da rike amanar junansu ne kuma tare suke komansu kuma basu boyewa junansu matsalarsu to amma anya kuwa zai iya maganin matsalarsa? zai iya bashi wata shawara da zata anfaneshi kuwa? Toh zaide jaraba ya gani.
Koda suka fito yazeed yace muje ko?gyada kai lukman yayi alaman OK sannan suka Shiga gate din takowa suke a kaga saboda tazarar (Kamar dai yadda kuka sani kuma kuka gani a photo gidan akwai dadi da tsaki ga fili na hauka).
Hanyan garage yazeed ya nufa lukman yace zaka fita ne?gyada kai yazeed yayi kamin yace muje ka rakani
Lukman yace ina?yazeed yace zaka gani. Bugatti Byron yazeed ya nuna masa Dan haka yaje ya dauko key dinta ya dawo ya bude driver’s seat ya shige ganin yazeed yayi kikam a dayan Abangaren yasa yace Shiga mana ko ka fasa ne ?
Koda yazeed ya nuna masa alamun abuse masa lukman yace aiko zaka kwana a tsaye yazeed yace an serious fa lukman yace nima haka….. Nan fa suka fara Daga karshe lukman yayi surrender yace kaide ka fita naci bata in bude ma Kafin ka cinyeni har kashi
Fitowa yayi ya bude masa kofar daidai zai Shiga lukman yakai masa kutfo a mazaunai
Shanyewa yayi ya nuna ko ajikinsa dukda ko ta ratsashi aiko lukman yana kewayowa ya Shiga zai rife kofa yazeed ya kafa masa rankwashi
Ouch! Ya dafe wajen sannan ya juyo ya kalli yazeed yace haba my guy irin wannan rankwashi yazeed Kam kauda kai yayi Kamar bashi yayi aika aikan nan ba yace inka gama zamu iya tafiya.
Hello wattys !yakuke ?
Toh kunji wata sirrin boye kuma Ashe yazeed and lukman are friends.
Kunyi tsammanin hakan?
Shin kuna ganin yazeed zai sami mafita a wajen amininsa?2
Shin abinda mom tayi ya dace?2
Ina jiran COMMENTS dinku and don’t forget to VOTE.
Love you all😘
Miss untichlobanty💕
19th October, 2019.Tafe suke babu mai magana can lukman yace ina zamu ne Wai?sanda yazeed ya dau Yan sakanni kamin yace muje makarfi plaza inason insiyo waya ne.
Gyada kai kawai lukman yayi alamun ok,Sannan ya kara speed din motar.
Chan yace inajinka. Yazeed sarai ya gane me lukman ke nufi da hakan amma saboda hali irin nasa yace kana jina name fa?
Side glance lukman yayi masa kamin yace zaka fadamin koko?yazeed yace me kenan?tsaki lukman yace sai ka rike matsalarka tunda bazaka iya fadamin Ba.
Shiru ne ya karade wajen kamin can yazeed yace ka tuna wannan yarinyar ?
Smiling lukman yayi domin plan dinsa yayi wato babu Wanda ya kaishi fahimtar abokin nasa idan ka nuna masa baka damu da Abu Ba to Anan ne zai dauki abin serious.
Luku yace wace yarinya kenan?yazeed yace wannan yarinyar data Shiga booth?
Lukman yace wannan yarinyar daka gasawa aya a hannu kuma kaso ka gasa mata gyada a tsakiyar kai Allah ya taimaka brother Jamal ya kira mom?
Tsaki yazeed yaja yace matsalata dakai kenan ka fiya surutu yanxu waya tambaye ka duk wannan jawabin?
Lukman yace Nide Ba wannan Ba meye da yarinyar?
Yazeed yace ita…sai kuma yayi shiru lukman ya ehm ita me? Yazeed yace itace amaryar da mom ta aura min
Wani wawan birki lukman yana yana zare idanu ya kalli yazeed a tsora ce yace dude me kace ?
Harara yazeed ya aiko masa yace banson iskanci ai sarai ka jini.+
‘Kefta idanu yayi alamun mamaki sannan yace kana nufin yarinyar nan daka gama shekawa rashin mutunci mom ta aura maka kuma ka zauna da ita ?
Kawai sai ya fashe da dariya harda rike ciki kai mutumina Gaskiya life dinka na birgeni,Wai ina self respect din naka da …….. Ya tafi ?
Wani kallo yazeed ke aika masa if looks could kill da an Dade dakai lukman kabari.
Yazeed yace banson wulakanci ya ina maka serious magana kanamin dariya?karka batamin mood fa. Dan wulakan ci bakasan in ina magana ba’a datseni Ba?’kwafa yayi yace dallah mallam zaka ja mota mutafi ko zaka tsaya kana batamin time?
Kunna Moran lukman yayi yana mai danne dariyarsa sannan yace haba nawan, Allah ya huci zuciyarka.
Tabe baki yazeed yayi yace in bata huce bafa?lukman yace zama ta huce Insha Allah .
Tsaki yaja sannan ya ci gaba ni yanzu Ba wannan Ba matsalarka shine Allah ya gani bana sha’awar kusantar yarinyar nan , mom kuma ta dage ita kawai a haifo mata jikoki.
Ajiyan zuciya ya sauke sannan yace zakiyya ko Kazan yadda muke ciki da ita
Gyada kai luku guy yayi alamun ya sani sanna yazeed ya kara da kuma inks lura amaryar tayi karama dayawa bana tunanin zata iya dani.
Wannan magana ta mugun bawa lukman dariya amma to avoid issues with his amini yasa ya shanye abarsa
Yace uhm sannunku manya manya su alharijunal auwaluna
Yazeed yace wallahi luk guy ka fita matsala na rantse da Allah zanma rashin mutunci inma harijancin ne aiba laifi na bane Allah ne yaso ya ganni haka wasu da kudi suke biya dan su zama harijan ?Toh Nina zamu a’bagas sai ince banaso?
Lukman yace chill man Daga wasa yazeed yaja tsaki kasa kasa yace aikin banza mutum matanshi biyu amma ya kare da azumi. Lukman yace karka damu wata rana sai labari.
Daidai lokacin suka iso plaza din, saukowa sukayi Daga Motan lukman ya latsa mukullin ya rufe sannan suka Shiga nan dai suka zabi latest Samsung Inda suka hau musu akan kalar wayan.
Yazeed yace lallai saide a siyi fari domin yafison farin kala ko shudi (blue or ruwan bula) yayinda lukman yace ai golden zaifi tunda itadin zata hau da kowa ni kaya kamar dai sarkar gold kuma ai mata nason kyale kyale ……..
Haka suka cigaba da arguing Daga karshe mai Saida waya yace wannan abu mai sauke ne su siyi fari inyaso sai asa mata cover golden.
Nan suka yarda yayin da suke hada baki wajen Cewa that’s it!
Bayan sun dawo Motan ne yazeed ya kalli luku yace guy bakace Komai ba.
Shima lukman domin ya rama abinda YAZEED ya masa sai yayi acting Kamar bai gane ba yace akan me fa ?yazeed yace abinda na fada maka mana
Lukman yace kawo kunnanka,yazeed yace ni in zakayi magana kayi lukman yace dadinta ni lamin lafiya nake kuma dadinta ba matsalata bace. Kanaso kaji koko? Yazeed yayi ajiyan zuciyar in defeat sannan ya matso na ya sanar masa da yadda zaiyi aiko yazeed ya zabura yace luku amma kasan if the plan backfired zai iya jawomin raini ko?lukman yace ‘in order to succeed, you must take the risk’ ko ba haka kake Fadawa mutane ba?gyada kai yayi alamar haka ne amma wannan din is it worth it?
Haka dai suka dawo gida lukman na kara karfafawa yazeed din guiwa sai wajen 10 tukunna suka rabu.
Koda ya shigo dakinshi wanka ya fada.
Ji yayi Kamar an Shiga dakinnasa amma ya basar Dan yasan bazai wuce zakiyya ba. Koda ya fito samunta yayi tana kwance tana chatting da sabuwar kawarta sumayya ,ko kallon inda yake batayiba,shima bai kulata Ba yayi hayewarsa ya kwanta.
Wajajen 3 yazeed gaji Kamar ana tabashi
Bude idanunsa yayi yaga zakiyya zaune tana kallonsa tace baby inason magana dakai dan daura fiska yayi yace magana bai iya jiran safiya bane ? Haba zakiyya fisabilillahi ace ki tashi mijinki tsakar dare Daga bacci lokacin da Allah yasa Dan bayi su huta Wai zakiyi magana dashi?to ina jinki
Tace baby wani urgent business trip ne ya taso min ana you know that next week fa za’a fara bikin cousin sissy kaga we have to arrive early so I think de I will not be around for 2 weeks.
YAZEED kam da mamaki ya cika shi danshi yanzu lamarin zakiyya ya daina bashi haushi ya fara bashi tsoro.
Tabe baki yayi alamun takaici yace OK jeki sannan ya Koma ya kwanta.
Tace baby Ba zancen tafiyan nawa bane ai.
Yace ok tunda dama Ba izini kikazo nema Ba to miye na fadamin?
Tace to katashi ka zauna magana is serious fa yace a haka ma inaji sannan ya rude idanunsa. Tace dama so nake na dauki white Prado dinka Ba.
Yace kinsan dai ko sweetheart bata tana hawa wannan Ba kuma kinsman ko tukani ba’ayi Dan kar ashiga min cikin Abuna.
Tace to jawabin na menene kuma aini Ba mom bace,kawai kaban motan.
Yace abinda jawabin ke nufi shine bazan bayar ba. Kuma zancen keba sweetheart bace kina nufin kin fita ne ? Ince mota 6 ne dake ko duk babu Wanda zaki iya tafiyar dashi ne?tace baby 4matic dina kullum shi make using its out of the picture,Prado na kuma paint dinshi ya tsufa kuma………..
Yazeed ne ya datseta ta hanyar Cewa ince paint ne kawai ya tsufa tace eh yace fine then use it mana.
Tace baby mutanefa zan Shiga yace anso gara ke,mutane nawa ne zasuzo da irin motan naki?the only help dazan baki shine ki dauki bakin not the golden one! Tace baby amma…… Hannu ya Daga mata hannu yayi sannan yace zaki iya barmin motata.
Tashi tayi tana gunguni bajar bajar tabar dakin shiko yazeed tabe baki yayi ya Koma tsakiyar gadonsa yayi d’ane D’ane.
Sarai yasan dalilin da yasa takeson tafiya da farin, saboda shidin customised ne. Hmm wato mai hali baya fasa halinsa,itadai burinta ko ina taje asan matar manya ta iso.
Baccinsa ya cigaba da narka kamar Ba gobe.
Ahh !THIS PART KEEP ON GOING MISSING!.
Miss untichlobanty💕
26 October, 2019
Koda asuba tayi yazeed da kyar ya tashi yayi alwala sannan ya tafi masjeed. Da ya dawo Shirye shiryen fita aiki ya farayi yanada meeting by 7-10 zai dawo gida dan yau sai ya kwashi gara zaibar zakiyya ta tafi (or akwai matsala)tunda business appointment din sai gobe,dan haka sai 4 na yamma tabi jirgi.
Koda ya fito Daga gidan tunawa yayi da wayan minal Wanda bai bata ba dan haka ya Koma yana mai Jan dogon tsaki da bakin cikin zai Sanya wannan aljanar a idanunsa well maybe ba bakin ciki yaje ba haushi yakeji saboda banzan plan din lukman Anyway Koma wannene shidai yasan bayaso yasata a idanunsa.
Dakinsa ya Koma ya dauko wayar daga charji ya kunna yayi downloading su WhatsApp da su Instagram da snap chat sannan ya tura mata katin 10k yayi sub na monthly 10GB to amma taya zai bata ?
Tsaki yaja yace banida time I better hurry up. Dakin zaky ya fara Shiga yace karta tafi akwai wani serious magana da zasuyi inya dawo (😁yazeed fadi gaskiya) inyaso saiki ni jirgi tace mortar fa yace malam suke zai kama hanya anjima,Tace okay.
Yanda tayi magana Kamar bazatabi umarnin ba dan haka yazeed yace idan kika tafi batare da izinina ba karki dawo,aiko Kamar yasani dan batayi niyan tsayawa ba amma tanajin wannan magana ta sauke duk makaman yakinta dan bata Shirya zama bazawara ba.
Komawa tayi ta kwanta tana mai janyo wayanta sannan ta fara chatting da sabuwar kawar da tayi.
Direct dakin minal ya wuceya samota tana bacci ta d’are d’are akan gado pajama ne ajikinta da rigarsa me dogon Hannu+
Ahankali yazeed ya tako yazo har Inda take abakin gadon ya zauna murmushin mugunta yayi koba Komai zaiyi enjoying game dinnab sannan ya ajiye wayar ahankali ya tattaro kafar minal ya hadota sannan ya dauketa direct kan coach yaje ya zauna rugume da ita kan cinyarsa sannan yakai bakinsa daidai kunnanta ahankali yace aljana !ke aljana! motsi tayi kadan tasa hannunta ta rungumosa domin tunaninta pillow ne tace kai inna! kai inna !yaushe ma aka kwanta?
Dan gira yazeed ya Daga yana smirking irin yarinya you don’t know what is going on.
Hannu yasa ya shafa kumatunta yace aljana tashi. Tsaki taja duk acikin baccin tace wallahi deeje ko ki ficemin a daki ko in mugun saba miki.
Allah yayi minal da mugun gigin bacci saide idan tâyi Baccin ya isheta wato ya sauka akanta amma inba haka ba wani zubin har magana zakuyi amma batasan Anyi ba.
Kallon agogon hannunshi yayi yaga har 6:23am yayi kawai sai ya kamo yatsan hannunta ya gantsara mata chizo zaburowa tayi tana yin kicin kicin da alamun bala’i yayinda take Cewa wallahi yau zanga uban dazai hanani chin uw**ki a gidannan,saina Keta miki rashin mutunci,wallah…….
Maganarce ta makale saboda kankamota da yazeed yayi domin kokarin sauka takeyi.
Fiskanta ne ya chanja Daga fada zuwa dan tsoro da kuma mamaki,zazzare ido takeyi Kamar ankama malam da karuwa sannan tamike a tsorace tasowa yayi zai kamota ta turo baki sannan tace;wallahi nidai karka matso niba har iska bace! Zaro ido yazeed yayi sannan ya hade rai ya finciko hannunta ya matse sannan yace ubanwa yace ki kwanta akan gado sai alokacin ta tuna Ashe tana chanja bedsheet tayi bacci saboda yayi kura tunda ba hawa kai take ba.
Ba Kare kai straight forward tace kayi hakuri gyara gadon nake bacci ya daukeni, gyada kai yake da ma’ana biyu;
1.ya gane Cewa ba da gagan tayi bacci akan gadon ba.
2.yayi accepting apology din.
Yace kinsan wani Abu?ta gyada kai yace saboda kin bani hakuri ba tare da mishkila ba Daga yau na yarda kina kwana akan gadon.
Washe hakora tayi tana grinning like a fool tace lâ dama kanada kirki ?ai na dauka …….sai kuma tayi saurin safe bakinta tana zare ido na abinsa ta fada dan batasô yâ fito Fili ba.
Matsowa ya karayi kusa da ita ya bata kwas yace da dance banida kirki ne?ina dai yin kirki nane ga Wanda yakeso. Hope kin gane ? Gyada kai tayi tace amma inada magana
Gira ya Daga alamun yanajinta,tace dan Allah idan kanayimin magana kadan dinga anfani da kalmomin turancin masu sauki.
Dan daure fiska yayi alamun nazarin yaushe yayi using complicated word ? Dan ware idanu yayi alamun ya gano yace hope dinne complicated word?tace to ai ka kara sani duhu menene complicated kuma ?yace oh. my. God! Kinyi makaranta kuwa?murmushi tayi sannan ta gyara tsayuwa tace ras! Har SS 3 ma kuwa. Jijjiga kai yazeed yayi.
Aransa yace I wonder how your teachers will be like kara kallon agogonsa yayi yaga har 6:39 yayi wayan yayi saurin daukowa yace ke ni ungo dallah banson shashanci wayace akwai Komai a ciki abinda baki ganeba ki nunamin sanda nake free Washe baki tayi tace Toh nagode Allah ya saka ya kuma mayar maka fiye dashi murmushi yadanyi domin yaji dadin addu’ar nata
Yace kin tana rike babbar waya kuwa ta gyada kai wani karfin guiwa ta samu na Cewa a dawo Allah ya kiyaye.
Alokacin har yakai bakin kofa kasakasa yace Ameen ransa wasai Daga damuwar jiya amma bai nuna ba.
Hade fiska tayi tana mai mamaki kamin ta tabe baki tace kaika jiyo mutum Kamar me aljanu yanzu yanzu sai ya chanja Kamar yama sunan abar?…. Emm…yauwa chameleon.
Washe baki ta karayi sannan ta dale gadon ta a guje tana mai bude kwalin wayar wow!masha Allah !wayyo Allah na wannan tawace?Allah na gode ma wayar mai kyau ni yanxu ko a mafarki akacemin zan sami wannan wayar a rayuwata ai bazan yarda ba kai Alhamdulillah kawai sai ta fara kuka su inna ta tuna tace bari anjima in rokeshi wata kila ya bari inje.
Wayar ta fara dubawa babu Komai a contact sai number din mom.
Camera ta Shiga ta dauki selfie kwalli daya tana turo kanta gaban cameran dan haka Rabin fiskantane ya dauku ga ranan hantsi ya dan hasko kumatunta abin sai yayi mugun kyau.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Yazeed ko a cikin mota a hanyarsu na meeting yayi shiru yana tunani Wai shin anya kuwa minal zata yarda da abinsa zaizo mata dashi ? Anya kuwa bazai bari yabi shawarar lukman ba batare da ya chanja ba?luku yace kawai su fahimci juna inyaso su hada gado da yardar yarinyar amma shi matsalarsa kenan kwanciya da Itan. Anya bazata masa ganin mahaukaci ba idan yace ta ara musu mahaifarta? As a surrogate mother? No !no! yazeed kar kayi haka.
Tsaki yaja yace bari kawai in zubawa sarautar Allah ido, amma na fasa kudirina.
Lukman ne yace boss yane yace ba Komai okay kawai luku yace dan ya fahimci abokin NASA is not in the mood.
10:15AM
Yazeed a mota Suna dawowa gira wayarsa ya zaro yayiwa zakiyya message cewa gashinan a hanya.
Yana dawowa ya samota parlour tana shan kanshi tana daddaga kai tana huhhura hanchi ita adole ga matar manya. Hannunta ya riko yana bata side hug yace Ashe zaki taroni dan smiling tayi kamin suka zauna a rants tana Cewa Koma wace magana ce Indai ba zancen zai bata white pradon bane to is useless.
Minal ce ta sauko domin ta fada masa batasan yadda zata buds au account din Instagram ba
Zakiyya cikin kallon wulakanci da kaskanci da nunawa dan Adam shidin ba kowa bane tace ke zonan.
Sumul sumul minal tazo ta tsaya adan gefe dan she is not in the mood to create a scene ga kuma yazeed ya kafeta da idanu.
Tace gani tana mai kafeshi da dogon kallo. Zuciyarsa ce ta buga na zakiyya ko girgiza yayi dan har wani tsorone ya shigeta saboda yadda minal din tayi maganar.
zakiyya tayi witnessing kallon da minal kewa yazeed amna bataga na yazeed ba dan haka zakiyyan tayi kwafa tana aiyana yanda zataci ub*n minal inta dawo sannan tace ni zanzo in sameki ne ko me kuke nufi ? Banson iskancinnan naku fa irin na talakawa.
Ran yazeed yayi mugun baci da yanda zakiyya ke gayawa minal magana dan haka yace baby ya isa mana me mayasa kika kiratane ?
Harara ta bankawa minal sannan tace ki kawowa MY LOVE coffee kuma saura ki tsaya kina tafiya Kamar tsutsa.
Minal aranta tace Nasan dan kinga idon mijinki ne kinsan bazan’kiyi ba da Kinyi kadan ki sani aiki wallahi tunda ke bakisan me ake kira da mutunci ba kema bai dace a mutuntaki ba, dadinta ma dai aikin mijina zanyi.
Kitchen din ta Shiga ta hado sannan ta kawo,bata ‘kara kallansu ba ta hayewarta sama tana maijin haushin yazeed din. yana gani akaci fiskanta amma baiyi magana ba
kallon zakiyyan yazeed yayi yana dan smiling dukda ko izuwa yanxu tsoran answern dazai samu yake yace baby I….uhm…hhhhh I need a baby!
Kallonsa tadanyi fiskanta a yatsine a lamun confusion tace you already have one, ko baby ka kirani ba ?……. Just wait a minute !do you mean kanason wanchan aba…..
Datseta yayi ta hangar Cewa no!d’a nakeso
Ajiyar zuciya ta sauke tace matsalar da dan sauki.
Hello team yaznal and yazya hope kuna lahiya ?by the way did you like this chapter?
Don’t forget to VOTE AND COMMENT.
See yah😘
Miss untichlobanty💕
26th October, 2019.Look yazeed ni bawai haihuwa bane banaso,matsalarta ne banso. Yanxu daga na aihu shikenan zan tsofe inyi loosing shape kuma I will be less attractive balle kai na sanka ina nan dagwas ma ya aka Kare balle na fara loosing shape,gararin ka Koma wajen wanchan yarinyar.
Murmushi yazeed yayi aransa yace to me anfanin shape din daba Mora nake ba ? Ai inkinsan wata bakisan wata ba. Afili kuwa Cewa yayi idan Kiyi loosing shape din basai ayimiki plastic surgery ba?
(haramunne fa kawai wayo yazeed keson yi mata )tace idan kuma banmakai ga rayuwaba na mutu tun a garin haihuwan fa? yace bazama ki mutu ba tace to inna haifar ma ai akwai shayarwa,ga kukan masifa,ga kashi,fitsari eww!,ga su takuri mutum. Haka dai suka cigaba in yazeed ya bullo tanan sai zakiyya ta toshe inya Koma tachan ta toshe bai Ankare ba har lokacin sallar azahar yayi.
Ajiyan zuciya yazeed ya sauke sannan yace okay bari inje in dawo ko?ko kallon Inda yake batayiba balle ta ansa shi Dan wani mugun haushi yabata saboda kawai gani take so yake ya tsufar da ita da kuruciyarta ko 30years fa batakai Ba.
Koda ta dawo samunta yayi da wayarta a Hannu tana chatting da sabuwar kawarnan nata sumayta Wanda take kira da sumy. Yadda ya barta haka ya sameta illa ma kwanciya da tayi Wanda gaba daya alamu sun nuna batayi sallah ba. To ko tayi ma ai Anyi ba ayiba tunda duk ta cika kai da braided attached hair ga uban artificial nails da tasa yazeed yace zaky kinyi sallh gyada kai tayi alamar tayi sallan ba tareda ta dauke idanunta Daga kan wayanta ba.1
Takowa yayi yadan zauna a gefenta kadan sannan ya karbe wayan yana murmushi ya ajiye a gefe tashi tayi ta zauna tana ciccin magani dan ta gano Inda aka dosa shiko yazeed janyota jikinsa yayi ya riko hannunsa yana shafawa kamin a hankali cikin kunnenta yace sweetheart zakiyi tafiya na sati biyu bazakiyi missing dina bane, ta dan tureshi tace is just two weeks fa? Dan zaro ido kadan yayi yace 2 weeks din just? Gyada kai tayi yace to shikenan I think I will take the second option ya fadi hakan yana mai danyin abin tausayi tare da turo bakinshi. Kallosa tayi dakyau tace and what’s the second option? Kallon hanya stairs yayi aiko atake zakiyya tahau tureshi tana Cewa ai saikaje din dama nasan halin maza,bak…….
Maganar ta nema ta rasa sakamakon jin soft lips din yazeed akan nata babu wani jan aji ta fara maida masa martani dan itama a Hannu take kan kamin kace kwabo zakiyya ta fice Daga hayyacinta.
Yazeed,hannunshi yasa a cikin gashin dake kanta yana shafawa yayinda bakinsu ke hade Dana juna. Wasu irin salo zakiyya keyi masa Wanda yasa numfashinsa fara daukewa. Magana yakeson yi mata amma ina ya kasa.
Ana cikin haka yaji zakiyya tasa hannu ta fara zurfafa sha’ani, lokaci daya wani kasala ya sauko masa dan haka cikin kwarewa ya zura hannunshi cinkin riganta. Motsi ya fara ji dan haka ya tsaya cak da abin da yakeyi kokarin Daga zakiyya yake Daga jikinsa amma batamasan yanayi ba dan kara Shige masa takeyi.
Dan gatsa harcenta yayi Wanda hakan yasa ta saki bakinsa sannan ta lafe ajikinsa tana cigaba da kokarin cire masa Riga shiko numfashi kawai yake saki.
Riko hannunta yayi muryasa Kamar ta mashaya yace zaky….kinsan fa bamu kadai bane a gidan akwai possibility masu aiki su shigo anytime ki bari mu Shiga Daga ciki.
Tana jinsa amma taji gaba abinda takeyi ko ajikinta.
Babu abinda yake maimaita mata illa wani zai iya ganinsu tun muryasa yana fita har ya fara shaking harma ya daina fita tsabar desire.
Zakiyya kam da taga ya dameta da surutu kara kamo lips dinsa tayi Kamar wata mayun waciyar zakanya.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Minal kam bayan komawarta daki dudduba wayarta tacigaba dayi har taji ankira sallah dan haka ta mike ta nufi kitchen domin ta hada kununta Wanda ta saba sha da daddare tunda yau zata je gidansu zally tasan zata gaji lubus,dan haka gara ta hada abinta tun yanxu.
Koda ta fito parlour zakiyya kawai tagani kwance tana chatting harara zakkiyan ta aika mata itako tasa ke mata smile sannan ta wuce kitchen.
Aiko hakan ba karamin haushi yabata ba dan haka tasha alwashin saukewa akan Wanda ya ajiye mata mara kunyarnan agida(yazeed Kenan).
Sharp sharp ta dama kununta sannan ta Koma daki batare da ta kallo zakiyya ba.
Sallah tayi abinta ta Ciro kayan da zata saka.
Alamun rufe kofa taji Wanda for sure ta tabbatar yazeed ne wanka ta fada da niyar inata fito zataje ta sameshi ya nuna mata abubuwan Daga nan ta wuce gidan biki.
Koda tayi wanka shafa mai tayi mai sanyaiyar kamshi sannan tasa atamfarta ta shafa powder da pink lipstick sai kwalliyar nata yayi making sense.
To yanxu akeyinta daurin dan kwali,ta daura ta since ta daura ta kuma sincewa dakyar ta samu tadanyi wani yadanyi ma’ana sannan tabarshi.
Dafe kai tayi sannan tace kash Ashe ma fita zanyi kuma hijab zansa,dungure kanta tayi tace keda wallahi wani zubin sai ahankali,Idan ba fita zakiyiba mai zaisa Kiyi kwalliya.
Smiling tayi tace aiko kwalliyar bazai tashi a banza ba,wayarta ta janyo.
Click!click! Ta watsa selfie abinta sannan ta tuge dan kwalin ji. Hijaninta ta janyo ta sakala a wuyanta ta fice domin zuwa wajen yazeed not forgetting to take her phone of course.
🌹 🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Takun saukowa Daga beni yazeed yakeji dan haka yayi kokarin fincike zakiyya Daga jikinsa Wanda ta like masa ajiki kamar chewing gum kuma alokacin tayi nasarar balle masa button 2,Kare kaimi take shima ko daddagewa yake wajen bincineta Daga jikinsa,saide kash bai sami nasarar kwakuleta ba har mai wannan taku ta sauko,cikin mutuwar jiki ya dago da idanunsa dan ganin ko Waye aiko minal ce ta kame ta tsaya cak tana binsu da wani kallon tsana,jin haushi da kuma mamaki.
Take yaji zuciyarsa ta buga Wanda shi Kansa ko zaka yankashi bai San dalili ba.
Did you like this chapter, if YES! Then don’t forget to press the star below.
NO negative comments ✖
More votes and comments, more updates😉.
Karamarsu babbarsu ce
Miss untichlobanty💕
27 October, 2019Ido cikin ido minal da yazeed ke kallon juna, wani irin kallo ya banka mata aiko ga mamakinsa ta mayar masa da harara zakiyya ko bata masan Anayi ba dan kokarin zuge zip din wandon captain ma takeyi.
Tabe bakinta tayi,taja tsaki sannan kasa kasa cikin makoshinta tace Yan iska kawai duk dakunan gidannan bai isheku ba sai kunzo nan?
Karaf maganar ta fada kunnen yazeed minal ko juyawa tayi tafara Komawa sama cikin muryarsa dake fita dakyar yace ke…..
Juyowa tayi tana yatsine yazeed yace me like Cewa zaro ido tayi Adan firgice dan bata yi expecting dinshi yaji maganar ba domin kuwa can Nasan makoshinta tayisa Wanda ko ita da tayi kunnanta basu jiyo da kyau ba.
Tsurewa tayi muryarta na rawa tace nifa bance Komai ba. Yace kizo nan yafada yana nuna mata kusa dashi da hannunsa yayinda yake kokarin mikewa da zakiyyan manne ajikinsa.
Wani abu ne yatasowa minal ya tsaya mata a makokoro ganin sunki rabuwa da junansu itako zakiyya sai faman romancing din yazeed take dukda ko alokacin ta fara gane abinda ke wakana amma ganin Cewa halittar da tafi tsana ce yasa tacigaba da aikinta dan wani feelings takeji Wanda bata tabajin irinsa ba.+
Abinda bata sani ba shine acikin juice din da sabuwar kawarta sumayya ta bata jiya da yamma kamin ta dawo gida akwai maganin kara desire Wanda zai fara aiki after 15 hours domin ko sumayyar year lesbian ce kuma ta mutu a son zakiyya,toh plan dinta shine tunda tare zasuyi tafiyar sai tayi using din wannan to her advantage amma yazeed ya rusa mata plan.
Ko dazu ma sanda suke chatting zakiyyan fada mata takeyi Cewa ansami chanjin plan Wanda ranta yayi mugun back kuma bata so ba.
Bazaki zo ba? Ya fadi hakan Adan tsawace yana daure fuska.
Jikinta ne ya soma karkarwa bakinta na rawa idanunta ya ciki da kwalla tace zanzo amma wallahi ni tsoro nikeji.
Yace okay tunda ke bazakizo ba ni bari Nazo da kaina daidai lokacin zakiyya ta sami daman zuge masa zip din wando tare da yin kasa dashi Allah ya taimaka akwai boxers .
Aiko minal ta saki kara da gudu tayi sama shima ko ya tattaro duk karfinsa ya fincike zakiyya ya rufe zip dinsa sannan yabi bayan minal din koda ya iso bakin side dinta gani yayi ta kulle. Knocking yayi yace ki bude minal tayi mirsisi.
Murmushi yayi ya Koma side dinsa da Sauri ya Shiga parlourn sa. Inda gaba daya Anyi tiling yaje ya danna wani Abu Kamar makunnan wuta atake wajen ya bude wani Dan siririn corridor ne ko da ya kure corridor din kofofi 3 daya a hagu daya dama daya kuma a gabansa.
Na hagu shine back door na part din zakiyya, na tsakiya kuma na minal sannan na dama na mom kenan back door din mom yana kallon na zakiyya.
Bude na tsakiyan yayi ya Shiga kofar dakinta ya karasa yaji shima ta garkama masa key date kai yayi sannan ya zauna a kujera sai lokacin ya da part dinta Komai tas sai kamshi yakeyi.
Zafi yaji part din nata sai yaga AC a kashe tashi yayi ya kunna sannan ya dawo ya lume a kujera.
Minal ko jin ya dena knocking kusan 10 minutes yasa ta bude kofar dakinta a hankali tana leken kofan side din nata sannan a hankali tana sanda ta fito ta nufi kofar dan bata lura da yazeed Wanda ya lume cikin kujera ba.
Shiko yazeed tun fitowarta ya ganta binta yake da kallo wani Abu na tsarga masa a jikinsa Wanda ya ajiyeshi a matsayin sha’awa .
Bakinta kofan ta karasa ta takama key din ta murda a hankali handle din ta kama ta bude ta leko da kanta taga empty murmushi tayi tana shirin komawa taji an rungumota ta baya.
Ihu ta tsala Kamar yadda wasu mata keyi Idan ‘kadangare yayo Kansu da gudu sannan ta daka tsalle zata antaya a guje😁. Da Sauri yazeed ya janyota baya sannan ya mayar da kofar ya rude yana mai lafta mai key.
Ihu ta kara tsalawa yazeed yayi sauri yasa hannunsa ya rufe mata baki sannan ya janyota tsakiyar parlourn.
Kokarin kwacewa ta somayi amma taji kyam saboda rikon oga yazeed ba wasa ba ko namiji karyarsa balle ita dukda ko ita ma ba wasa ba. Shima yazeed din yayi mamaki dayaga tana iya fiffincika domin inya Rikeka ‘kwa’k’kwaran motsi ma gagarar ka yake.
Sakin jikinta tayi shiko yazeed ganin ta saki jikinta yasa ya sassauta rikon da yayi mata aiko ta gatsa masa cizo sakinta yayi yana yarfa hannu dan cizon ta ratsashi,guduwa minal ta soma kokarinyi aiko yazeed ya fincikota sai suka fada kan kujera. Zaro idanu minal ta somayi domin jinta da tayi a faffadar kirjinsa yayinda ta fara Shiga wani irin yanayi.
Shima dai haka takasance ta bangaren sa saide shi lumshe idanu yayi domin jin tsayaiyun breast dinta a kirjnsa.
Zakiyya ko dake general parlour koda taji minal na tsala ihu murmushi take tana jin dadi sannan tace thats my baby kaci ub*nta,yarinya zaki gane da yazeed kike tunda kika datse masa jin dadi tashi tayi dakyar taje ta fara shirinta ranta wasai.
Koda ta gama shiryawa babu ko sallama tayi airport dan already yazeed yayi booking mata,sumayya ta kira sannan suka nema mata itama. Ta zamu first class din amma akwai mutane 4 a tsakaninsu.
Haka suka nemi wani Dan snacks a airport din sukwci kamin 4 tayi suka Daga izuwa birnin tarayya even though it is not a long journey.
🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹
Abangaren su minal kuwa yazeed yasa Hannu yana shafa fiskanta tsilli tsilli tayi da ido tana kokarin mikewa kara rikota yayi ta turo baki tace ni kabarni in tashi.
Yatsa ya daura a bakinta yace shiiii…
Me yasa kika fito?hararansa tayi Adan tsorace sannan ta kara zunburo baki tace to Ba Kaine kace duk abinda ban ganeba a wayan in fada maka zaka nunamin, to sabida zan tafi gidansu zaliha sai nace bari inje alokacin.
Yace ehmm cigaba tace to shine…..ina fitowa shine…
Sai kuma tayi shiru yace shine me?
Tace shine na…ganku…a parlourn….kunayi.
Yace Muna me ? tayi shiru murmushi yayi wanda ya kara fito da kyawunsa yace me mukeyi murmushi tayi tadan kamo hannunta tana wasa dashi tace ai banyi kama da yar iska Ba balle in fada. Yatsansa yadan sa ya dalle mata baki yace to su Waye Yan iska?Idonta ne ya ciko da hawaye ta turo baki sannan ta fara gunjin kuka tace dama kawai kace zali na kakeson ci. Ni kawai ka nuna min yanda zanyi infara su insaram din.
Daga gira daya yayi yana murmushi bata rai tayi ta hade gira tace ni kadaina mini irin haka nifa Ba yar iska….
Daure fiska yayi yace banson jin wannan Kalmar iskancin kinji ko?ta gyada kai yace ina wayan naki? Tace yana daki yace oya dauko to.
Yaga bata tashi Ba yace ko bakison in nuna miki ne?tace to hannun ka sai Alokacin ya lura da yadda ya riketa. Sakinta yayi ta tashi atare suka sauke ajiyan zuciya.
Jikinta a sanyaye ta Shiga dakin yayinda yazeed ya hadiye wani yawun jaraba kutt
Hala wattpad did you like this chapter?
Show some by VOTING and COMMENTING
Your one and only
Miss untichlobanty💕
28 October, 2019.
WAIT OO INADA TAMBAYA WAI DAN ALLAH ME YASA KUKE TSORAN KADANGARE?4
KOWA TA FADI AMSANTA.
Dauko wayar tayi ta fito nuna mata gefensa yayi tazo ta zauna karban way an yayi sannan ya bude mata gmail as Mrs yazeedjeedmar@gmail.com yana nuna mata. Instagram account ya bude mata shima as Mrs_yazeed_jeedmar. Tunani yake why ma yaje using mata identity dinsa? Ganin bashida answer yasa ya share. Bayan sun gama ya miko mata wayan yace Toh da fatan dai kinsan illolin social media ko?gyada kai tayi sannan tace ana wayar mana dakai a islamiya ai akan illolinsa yace good you should be careful karkina rubuta Komai kinji ?ta gyada kai yace kinga na bude mini Komai da sunana ne Dan haka ko me kikayi ni zai shafa tace Insha Allah zankiyaye bazan bata maka Suna Ba yace good girl.
Turo baki tayi tace ni Ba girl bace Dan zaro ido yayi da alamun tsokana yace kin zama big girl kenan ta gyada kai da alamun sakarci.
Murmushi kawai yayi ya girgiza kai shikam bil hakki da Gaskiya inyace minal na bashi haushi a halin yanzu karya yayi.
Saide yasani har yanxu baya Santa kawai dai yana kokarin ya fahimceta ne Kamar yadda luku ya bashi shawara.
Mikewa yayi zai fita minal ta riko hannunsa wani electric shock yaji itako minal da bata ma lura Ba giranta Adan hade tace Toni insaram dinnan kace hotuna ake posting ko ? Yace eh tace to naji ance insaram kuma Nide a sanina ram ragone toh Wai hotan rago ake sawa?
Dariya yazeed ya fashe dashi harda kama ciki sannan yace wayace miki insaram ne? Instagram akace, murmushi tayi tace au Ashe ma da sauki instaram ne Ashe,yazeed yace Instagram Ba instaram Ba minal ta turo baki tace Koma wannene.+
Yazeed yace kawomin ruwa toh tashi tayi ta fita shi kuma ya shige dakinta bayan Kamar minti daya sai gashi ya fito. Wajen ya nema ya zauna koda ta kawo masa ruwan sip daya yayi ya ajiye.
Bubbuga ka minal tayi tace yanxu Dana akan murna daya shine kasani harna sauka kasa? Hararanta yayi yace ke banson raini fa karkiga ina sake miki fiska, bankai insaki bane ko me?
Tace Allah baka hakuri, ni yanxu dai bari inwuce. Yace okay batare da ya kalleta Ba. Dan turo baki tayi tace Dan Allah ka barni inje inga su innata yace bazaki bafa wallahi ko kofar gidan bikin kika fito bada kwakkwaran hujja Ba nida ke ne.
Hade fiska tayi tana huhhura hanci alamun ranta ya baci sannan ta saki hannunsa Wanda batasan ma tana rike dashi Ba.
Dakinta ta shige ta dauko su Jakarta da hijabinta ta Shirya sannan ta fice. Koda ta fito baya parlourn nata. Idonta ne ya cicciko da kwalla tace ni wallahi inason inga babana.
Gidansu zaliha ko ya cika makil da mutane,anata shiryen shiryen kamu.
Zaliha Kam duk tarin kawaye da Yan makarantansu da sukazo Ba agabanta suke Ba Dan tun safe take tsitstsilla ido ko zataga minal amma shiru har gashi yanxu 4 ya kusa har an fara tafiya venue din kamu.
Cika ta farayi tana batsewa domin ko lokacin bikin minal tun asuba take zuwa gidansu.amma ita yanxu har za’a fara biki batazo ba,saka da warwarar irin rashin mutuncin da zata kaftawa minal takeyi, aiko yar halak sai gata ta fado aguje tana Cewa Allah sarki aminiyas kema dai kin kusa Shiga Daga ciki.
Harara zaliha ta rafkawa minal tace me yakawoki gidan mu? Minal tace kai yar uwa Nasan Nayi laifi kimin uzuri mana amaryar Sulaiman.
Murmushi zaliha tayi dadi lokacin aka fara Cewa Amarya da tawagarta su fito.
Kamu yayi kyau saide masha Allah domin ko Sulaiman yayi kokari sosai.
Minal ko hotuna taketa dauka amma baifi guda uku tayiwa kanta Ba kuma yayi kyau sosai.
Yazeed Kam minal tana fita ya wuce dakin zakiyya wayam ya gani babu ita babu alamarta, dunkule hannunsa yayi ya naushi gini atake gumi ya fara tsatstsago masa, duk target din daya gama wato wannan yarinyar ta rusamai ita? Kwanciya yayi a gadon zakiyyan ido lumshe yana nazarin yadda zaiyi da matsalarsa.
Bude ido yayi domin wata idea da tazo masa ya dau key ya fice, wani pharmacy yaje ya siyo sedative sannan ya dawo gida ziciyarsa fess.
Kitchen ya shiga da sedative dinsa ya zuba mata a kununta sannan yace ai Kinyi kadan Yan mata,yau yadda na gama shiri na zan more kikayi ruining min,to akanki zan rage zafi. Tsaki yaja yana mai jin haushin irin kwabsin da minal din tamai kamin yace asha jagwalgwalo lafiya sannan ya fice.
Dakinsa yaje ya dauko CCTV dinsa ya fara kalla Kamar kullum zirga zirgan minal din yake kallo dukda ko badan wannan yake kunna TV dinba domin baya ma kallon nata part din ko ya kunna saboda acewarsa baiga abin kallo a rayuwarta Ba. saide ya kalli na sauran wurare especially gate area.
Yaukam tsintar kansa yayi dason kallon nata part din na kusan wata hudu kenan Wanda bai kalla Ba
Kallo yake yana forwarding domin kuwa yawanci shirmenta ne ko yadda take laftar abinci,murmushi kawai yake aransa yana Cewa wannan yarinyar Ba badai shiririta Ba wannan loma sai kace kato.
Dariya ya fashe dashi yace bata yau zan tsokaneta. Dariya ya kuma fashewa dashi yace kash saide gone zan tsokaneta Dan yaukam…….
Kallonsa ya cigaba dayi har lokacin da yayi gamo da abinda ya Daga masa hankali
Minal ce tsaye kaban madubin ta ta bude towel dinta tana kallon yadda kirjinta ya kuma ciccikowa,murmushi take saki domin itafa bilhakki da Gaskiya kyau takeyiwa kanta gyara towel din tayi ta gaba sannan ta juyi ta baya tana kallon yadda mazaunanta suka cika.
Babu shakka ko ba’afada mata itadin kyakkyawa ce.
Nunfashin yazeed ne ya fara daukewa Dan haka yayi saurin yin forwarding dinsa zuwa washegari shima data fito Daga wanka same thing tayi haka yazeed yayita forwarding harna sati wasu abin su bashi dariya wasu kuma su Daga masa hankali su sashi yin zafafan muhawara da zuciyarsa.
Jinjina kai yayi yace wato abinda yarinyarnan keyi kenan in Anyi magana tace wa mutane Yan iska, hmm to yaude za’a Kare iskanci.
Koda ta dawo gida ta gaji lubus a parlour kasa ta zube tana lumshe idanu, tunowa tayi da kununta aiko da wuce direct kitchen ta cika cup tana yiwa Allah godiya dayasa ta dama kunun kamin ta tafi.
Dakinta ta haura tayi sallan isha’i domin tayi magrib acan,kayan bacci tasa ta kunna tv ta dane gado tana jin dadi yau zatayi bacci mai dadi. Kishingida tayi sannan ta dauko kununta tanasha aiko babu bata lokaci bacci yayi awon gaba da ita
Yazeed mafa yana yiwa Allah godiya da kika dama kamin ki tafi.
Fans what’s your favorite part Anan chaptern ?
Comment your opinion and don’t forget to VOTE
I need 15 votes sai inyi updating gobe
Miss untichlobanty💕
2nd November, 2019Yazeed zaune dakinsa yana aiki a laptop dinsa.
Jin Kamar an rife babbar Koran parlour yasa ya kunno CCTV dinsa.
Na parlourn ya fara gani aiko minal ce zaune kan kujera da alamu ta dibo gajiya can yaga tayi hanyar kitchen Dan haka ya Koma na kitchen ganinta yayi tsaye tana diban kununta yace great! Insaram kina saukaka min aiki.
Gani yayi ta fice dan haka direct na side dinta ya wuce babu jimawa sai gata tashigo.
Kofar parlourn nata tasawa key sannan ta Shiga dakinta ta rufe Ba tareda tasa key ba.
Sallh tayi sannan ta kunna TV ta haye gado tana mika da murmushi alamun farin ciki.
Kishingida tayi sannan ta janyo kununta ta fara sha gani yazeed yayi ta fara zazzare ido tana dunkulewa can kuma sai tadan zabura haka takeyi once in a while har tasha Rabin kununta Inda ta bingire da bacci.
Muhawara me zafi yazeed keyi da kansa after Kamar 10 mins yasan lokacin maganin ya tsumata ko yankata zakayi bazata tashi Ba.
Tashi yayi yabi ta secret way dinsa har part din minal tare da spare key din room dinta just in case ta rufe.
Babu wata wata sai gashi a cikin side minal dakinta ya Shiga zuciyarsa na bugawa dukda ko Ba laifi yaje shirin yiba.+
Ahankali yake dago kafarsa har ya iso Inda take jingine yana kare mata kallo ahankali yaki hannunsa zai tabata amma ya kasa,kawai sai ya zuba mata idanu yana cigaba da kallonta yayinda zuciyarsa ke tsananta bugawa
Tunani ya farayi karfa yaje ya fara son yarinyarnan,yar siririyar tsaki yaja yace yazeed why are you thinking about the impossible?
Tv din ya kalla yaga horror film take gani,wato shine dalilinta na tsurewan kennan.
Kashe TV din yayi yaje kitchen ya dauko coil paper ya rufe mata kunun.
Dalewa gadon yayi yama rasa mai zaiyi can ya tattaro jarumta ya kamo bakin riganta ya fara ja a hankali har ya ida dagashi. Idanunshi ne suka sauka akan fresh kirjinta Wanda suke farare fess kuma a tsaye kyam sai sheki suke.
Zuciyarsa ta buga dumm yayinda ya ja wata numfashi wadda taki fita Nadan wani lokaci wani gumi ke karyo masa,jiyake Kamar AC da fan din dake dakin basuda anfani.
Sosai ya birkice hannunsa na rawa yake romancing dinta, itakam minal da batasan ya ake ciki Ba sai kankameshi takeyi.
Ahankali yafara yawo da harshensa a wuraren wuyanta yana dan gaggatsawa leaving Hickeys .
Kissing dinta ya farayi a lips aiko wasu abubuwa ke taso masa tun Daga tsakiyar kai har kafansa. Wani taushi ne da lips din na daban saide koda yayi kokarin zura harshensa cikin bakinta kin budewa tayi.
Sosai ya murza minal din sai wurin 2am ya hakura yayinda ya rage zafi.
Toilet dinta ya Shiga yayi wanka sannan ya fito koda yazo yana mayar mata da Riga rungumosa tayi tana Cewa waiyo codon zai cinyeni kokarin zareta yayi amma ta makale,saide batasan wata wutar take rura masa Ba dakyar ta sakeshi aiko ya wuce dakinsa saboda gudun kar a sani matsala.
Washe gari koda minal ta tashi taga ta bata jikinta bata kawo komaiba dan batama lura da sauyin discharge din Ba atunaninta normal discharge amma abinda yadan daure mata kai shine daya bushe yayi kanzo.
Basarwa kawai tayi abinta tayi wankan tsarki sannan tayi alwalarta tayi sallah saide wani mugun kasala takeji da dan ciwon jiki Wanda ta barshi a matsayin ta kwanta Ba daidai bane tunda dama tana kallo tayi bacci.
Sai alokacin ta tuna da da kununta sannan ta lura TV a kashe,Daga kafada tayi sannan tace watakila cikin gigin baccinnan nawa na kashe.
Kanta ne taji ya Sara mata kawai sai ta zauna a bakin gadon,janyo kofin kununta tayi zata sha sai taga an rude mata coil paper.
Dan gira ta hade Dan bata tuna sanda tayi hakan Ba amma to batada wani answer da zata bawa kanta.
Budewa tayi ta kurbi abunta sai taji bazata iya sha Ba saboda sanyin da yayi.
Jikinta taji ya fara yin weak sai ta barshi a matsayin gajiya ne. Mikewa tayi aiko luuu ta Koma ta fada gado sai bacci.
YAZEED ko yau yaje planning zasu sabon gidan daya ginawa iyayen minal Wanda dakyar da sudin goshi suka karba Suna godiya sannan ya bawa baban aiki a daya Daga cikin companies dinsa dake dealing da engines na mota.
Ya abubakar ma antanada masa aiki yana gama makaranta zai fara.
Gidan dai daya Gina mom ce tasashi amma aikin daya nasu yin kansa ne domin tun alokacin da mom ta tursasa masa yaje ya gaida surukansa ya fahimci Cewa sudin mutane masu dattako da wadatar zuci, kuma taji sun kwanta masa shiyasa ya fita Daga harkar minal din watannin da suka wuce Dan darajarsu ne.
Shiru shiru har 12 minal batazo Sharan dakinsa Ba. Mamaki ne ya kamashi to kodai maganin bai saketa bane?to amma ai 6 hours kadai zaiyi yana aiki. CCTV ya kunna yayi forwarding duk abinda ya faru Daren jiya playing yayi lokacin dayaga ta tashi sallah yaga tayi tazauna a bakin bed dinta da alamun confusion a fiskarta saboda yadda ta hade gira.
Kunun yaga ta kurba harde izuwa sanda ta dungura ko motsi bata yi yace no wonder.
Tashi yayi ya tafi dakin aiko ya samota tayi Dane Dane akan gadon.
Kafarta ya daura hannunsa zai tasheta yaji wani taushi,shikam mamaki yakeyi yadda minal Sam batayi kama da yar marasa karfi Ba.
Bubbuga kafarta yafarayi yana Cewa instaram,ke instaram tashi…….1
See you soon, hope you enjoy?
Miss untichlobanty💕
3 November, 2019.DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
Janye kafarta tayi Ba tare da ta bude idonta Ba tace banaso….
Hannusa yasa ya janyo kafar yace tashi mana.
Kallonta ya tsaya yi fuskarsa Adan daure yayinda itako ko ta motsa sai ta lumshe ido ta bude ahankali tana kallonsa cikin wani irin kasala da yauki tuni ya soma kuncewa gaba daya, sai ya jishi on.
Wani siririn murya tasa mai gigitarwa tace ina kwana ?
Hararar ta yayi yace me ya hanaki zuwa aiki? Dan yatsine tayi domin wani mugun sarawa da kanta yayi tace kayi hakuri banajin dadi ne shiyasa.
Dariya ta bashi sannan ta Dan bashi tausayi ganin yadda take Abu don atunaninta jinya ne amma sai ya maske Dan karta kawo masa raini inya sake mata dayawa. Yace I don’t care…kamin in rife idona in bude ki wuce daki ki sameni bai ko jira amsarta Ba ya ficewarsa.
Cike da mamakin irin halin mahauniya na YAZEED ta mike a daddafe ta nufi dakin NASA domin ta samesa. Kallon me kika tsaya yimin a bakin kofa ya wulla mata ta shigo tana Dan tangadi domin jirin dake dibarta.
Russunawa tayi a gabansa yace wato kina jira inje in tunasar miki aikinki ko?me ya hanaki share min side?
A hankali ta dago zaka rantse cutar ke damunta tace nace banajin dadi ne shiyasa inajin fever ke damuna.
Batayi aune Ba taji hannunsa akan goshinta kamin ya tana wuyanta.
Harara ya harba mata yace karyar banza lafiyarki kalau. Tace wallahi banajin dadi muryarta har rawa yake sanda take magana idanunta sun ciko da hawaye.+
Dariya yazeed ke sonyi amma ya dake yace I don’t care just get to work nemo tsintsiya.
Tashi tayi Adan fusace zata fice yace zonan ta dawo ta tsaya tare da kauda kai.
Yace for your punishment Daga yau ko wani Daren Allah sai kinmin tausa kinaji ta gyada kai yace good zaki iya fara sharan.
Hanyar kofa ta nufa yace ina kuma zaki tace tsintsiyar zan dauko yace dawo na manta ne jiya nasa lukman ya kawo min machine din da yake share dakina so you don’t have to use broom.
Kallonsa ta tsaya yi batareda ta motsa Ba sai aloiacin ya tuna Cewa yayi using English ne Dan dafe goshi yayi aransa yace Imust find a way out ma wannan yarinyar dama yana daya Daga cikin hakkinta in ilmantar da ita.
Da Hannu ya mata alamun tazo matsowa tayi ya nuna mata wani lungu da yatsarsa yace zakiga wani Abu mai dogon baki Kamar na giwa dauko.
Dauko wa tayi ya nuna mata yadda zata kunna, ya ce gwada in gani gwadawa tayi tana Dan murmushi saboda har yanxu weak take jinta. Nuna mata yadda zata yi control din karfin yayi shima ta gwada.
Saboda karambani irin nata Kurewa tayi takai yatsanta wurin aiko taji Yana shirin zu’ke mata yatsa,janyewa tayi da Sauri tana Cewa waiyo Allah zai cinyemin yatsata.
Yazeed just chuckled and said da wa yace kikai hanunki wurin? oya kawo kiga yadda akeyi nuna mata yayi sannan yace Kiyi Sauri ki gama ki Shirya zamu fita. tace yaunefa auren zaliha yace ina sane da hakan. Dan turo baki tayi Dan gani take yazeed kawai so yaje ya kuntata mata. Tace to ina zamu? ya shhhh and work .
Kara turo bakin tayi kamin ta fara aikinta.
Bayan ta gama aikin zata fita yace karki batamin lokaci ki Shirya yanxu tace Toh
Tana fita shima ya Shirya cikin shaddarsa sky blue sabuwa fil da ita,ya feshe jikinsa da turare sannan ya kafa hularsa dinkin buhariyya amma mai tsadace saide bana almubazzaranci ba.
Chas ya fito dashi Kamar shine angon sannan ya fito domin har 1 tayi kuma 2:30 za’a daura auren.
Koda ya fito bai ganta ba Dan haka ya nufi part dinta dai dai ta rufe kofar kenan juyowarta keda wuya sukayi karo kallon kallon su kayi for what seems like eternity kamin yazeed yace muje ko? Tace yo Toni ka sakeni kullum sai kana wani rirrikeni sai kace na maka kama da yar iska.
Dalle bakin yayi yace ba kace banson jin wannan Kalmar ba? Tace toni Toni…..sai tayi shiru yace toke me? Tace babu kayi hakuri sakinta yayi sannan ya kamo hannunta suka fito.
🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹
Lukman ne rike da takalminsa a Hannu yaji wani mummunar faduwar gaba.
Hazbiyallahu wa ni’imal wakil yace sannan ya goge black covered shoe dinshi ya fara sawa.
Sanye yaje cikin farar shadda kal harda babbar Riga wadda zubinsu kusan daya Dana yazeed ne. Kallon karshe ya karayiwa dakinsa daya banbanta Dana sauran kuratan sojojin yayi domin tabbatar da komai tsaf yake sannan ya fice domin shi da yazeed su halarci daurin auren Suleiman da zaliha. Sauri yayi ya rufe kofar dakinsa yana mai Cewa bari in hanzarta kafin uban complain dincan ya fara.
Koda ya Shiga motar da zasu tafi
Ya share kusan 30 mins amma shiru babu alamarsu Dan murmushi yayi yace sh*ge mutumi na yana can ya makalewa yar mutane in Anyi magana yace bayaso.
Nazarin irin kirkin abokin nashi ya fara tun Daga gidan daya canzawa parents din minal da gudun muwar kayan dakin daya yiwa zaliha da yadda ya hadawa sulaiman dinma lefe ya bashi dukda ko dakyar da sudin goshi Sulaiman din ya karba sannan ya Sanar da ahalinsa yazeed dinne yamai suko sai godiya suke Suna sa masa albarka.
Jin an bude motar yasa ya Dan firgita tare da Cewa sannu da fitowa amarya.
Yauwa sannu ina wuni ta fadi hakan Adan kunyace.
Yace lafiya ya gidan da maishi?
Bata amsa ba yazeed yayi knocking glass din window din lukman din. Lukman dinma ya fahimci matsala Dan haka ya fito ya bude masa kofar sannan ya Koma.
Koda suka Shiga yazeed yace shine Dan wulakanci zaka tsaya kana yiwa matata wannan surutun naka ko?lukman yace sorry sir! Yazeed yace kai ni karka wani cemin sir sai kace saniya.
Dariya minal keson yi amma ta cinyeshi.
Yazeed yace ke ta juyo yace kinsan wannan? ta gyada kai,yace wayeshi tace driver dinma ne yace Toh point of correction amini nane.
Zaro ido tayi zatayi magana yace rikewa kanki tambayoyinki Dan bazan iya a amsasu ba, kai luku muje dayan wajan.
Kunna motan yayi domin ya gane me yazeed ke nufi sannan ya figeta a guje minal bata shiryaba ta rungumo yazeed tana zazzare ido shiko wani sanyi gabobinsa sukayi Kamar ammasa wanka da ruwan sanyi.
Gaba daya abinda ya faru jiya ke tariyo masa tsab aiko yanayinsa kana daya ya sauya cikin kankanin lokaci. Lukman ko yana ganin duk abinda ke wakana Dan haka ya kara wuta yana mai kunshe dariyarsa.
Minal kam kunyace ta rufeta amma wallahi bilhakki da Gaskiya bata sakinsa dan gani take Suna raba jiki zata mutu saboda a 120 luku ke tafiya kuma dai kunsan motocin yanxu.
What do you think of this chapter?
Inane yafi muku dadi?Ku Samar dani a comment section.
AUTHOR’S NOTE(JAN HANKALI): Duk Inda ake rubuta 🔞 dinnan bayarwa nake ina fada a dabarance ana rubutamin saboda Gaskiya kunya nakeji. In case kunga wani wajen ana bukatar rubuta irinsu amma bayi ba it means banida Wanda zai rubutamin ne Dan haka zan bada shi a dunkule.
Thank you and don’t forget to vote.
Miss untichlobanty💕
8 November, 2019.
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.A haka har suka iso sabon gidan iyayen minal, itakam ta rufe idonta kyam sai laftawa lukman da yazeed din kwandon Allah ya isa take a zuciyarta Dan gani take hada baki sukayi domin suyi mata mugunta.
Yatsa yazeed yasa ya dungure mata kai yace ai saiki sakemin Riga ko? Duk kin yamutsa Min Riga sai kace na fito Daga filin kokuwa, ko jikin nawa ne bai isheki Ba?
Bude ido tayi da sauri tare da hade fiska ta zabga masa harara kasa kasa tace sai kace wani abin arzikin ne ajikinnasa.
Yazeed yace me kikace zaro ido tayi tace babu aranta ko Cewa tayi Wai wannan mutumin aljanine ?taya akayi yaji me nace?
Wani smiling yazeed yayi yace matar aljani muje ko?
Wani numfashi me karfi taja ta zaro ido tana kallonshi tama kasa motsi.
Tabe baki kawai yayi ya fice sannan ya miko mata hannu ganin kawai kallonsa take Kamar taga fatalwa yasa ya fincikota suka fara nufar cikin gidan hannu cikin hannu.
Kallonsan kawai ta cigaba dayi shikam gabansa yake kallo yana murmushi Wanda ya rasa dalili, Ashe luku ya Ciro wayarsa yana watsa musu photo dan Ba karamin kyau sukayi Ba Kamar sune Amarya da angon.
Juyowa yazeed din yayi Dan ganin kallon yaki ya kare aiko tayi saurin kauda kai tana kyafta idanu cikin jin kunya. Aiko lukman ya kara hasko su Wanda su duk abinda ke faruwa basusan anayi Ba.
Koda suka Shiga gidan dauke da sallamar su suka zauna. A lokacin minal ta lura gidan mai mugun kyau ne. Yaba kyawun gidan take taji wata murya wadda yayi mugun tsoratar da ita dan batayi tsammanin wannan muryar anan ba. Saurin kallon wajen data jiyo murya tayi aiko Ba karya kunnanta sukayi mata Ba tabbas innarta ce sanye da super mai kyau ta kashe daurin dankwali tayi haske sai murmushi take kamin tace wanake gani haka? babban bako dan albarka zuwa Ba sanarwa ? Allah ya taimaka akwai abin naka ba bari inkawo ma.
Ah ah kace min tare kake da malam lukumanu. Murmushi yayi yace wallahi inna tare Mike ina wuni?…… Nan suka gaggaisa inna tace malan lukumanu irin wannan babban Riga haka sai kace ango Sosa kai yayi yace wallahi daurin auren classmate dinmu zamu.
Inna tace ayya Allah ya Sanya alkhairi.
Ganin Kamar inna bata lura da minal dake sankare scan kuryan parlourn Ba yasa yazeed Cewa inna bakiga bakuwar ki bane sai lokacin inna ta juya aiko minal ta gani tayi kuri tana kallon ta.
Inna tace ja’irar ‘yarnan kina kallona bako gaisuwa?minal kam mikewa tayi ta fara takowa wajen innar ga mamakinsu sai ta rungumeta ta fashe da kuka haka aka lallasheta tace inna banganeba innan tace kwantar da hankalinki wato……………..
Nan tayi mata bayani duk yadda akayi sannan ta kallo yazeed din tace baka fada mata bane? Murmushi yazeed din yayi yana kallon kasa yadan gyara hularsa sannan yace wallahi dama surprising dinta nakeson yi.
Inna tace dakyau aiko ta sufarasu dayawa harda kuka.
Turo baki minal tace bafa safarsu bane suprise ne. Hararar ta inna tayi tace o ni ‘yasu mai hali bata chanja halinsa, kice min bata chanza zani. To mike ki shige nan kofar ta bangaren hannun daman ki akwai firji cikin akwai sobo ki dauko. Acikin drawer akwai tray saman canter kuma akwai cup ki dauko musu Toh tace sannan ta mike ta nufi kitchen din.
Koda ta kawo so’bon suna sha inna sai hira suke da yazeed da alama sun shaku, minal kam abubuwan da suka faru da ita ayau Nada wuyan shanyewa lokaci guda.
Mikewa su yazeed sukayi Suna Cewa zasu wuce lokaci na kurewa,minal din kuma sai su tafi gidan bikin tare da inna tunda itama innar zata Kamar yadda tace.
Wajen suka fita inna tace bazaki raka mijin naki bane? Tashi tayi akunyace tabi bayan su koda lukman yaga ta fito mota ya Shiga yana Cewa bari in bada guri kar adaga mini hankali da rana tsaka.
Yazeed ne ya kalleta yana mai Daga gira alamun yadai?tace uhm dama so nake nace nago….
Yazeed ya datseta ta hangar Cewa in godiya zakiyimun ki barshi dan Ba irinta nakeso Ba tace to irin wanne kakeso yace zan fada miki Ba yanxu Ba. Dan tabe baki tayi sannan tace to Allah ya kiyaye sai kun dawo. Murmushin gefen baki yayi sannan ya gyada kai ya shigewarsa mota sannan suka wuce lukman na fadin wallahi sobon nan yayi yana hajiya dashansa yazeed yace dam inajin haushinka dan wulakanci shine bayan ka shanye naka ka dauki nawa ko?lukman yace afuwan mutumina santi ke dawainiya da ni,tsaki yazeed yaja yana mai kauda Kansa izu.
🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹
Abangaren ango Sulaiman Kam Sai murmushi take har yashiga dakin mahaifiyarsa cikin shirinsa na daurin aure nasiha tayi masa sannan tasa masa albarka domin kuwa Ba karamin so takeyiwa dan nata Ba cikin yara uku da Allah ya azurtata dashi wato;
Na farko Sulaiman mai shekaru 29, sai abdussalam mai shekaru 25,sai kuma fadeelah wacce take yar auta mai shekaru 17-18 kuma anfi saninta da deela ta zana jarabawarta this year.
Fita yayi ya nufi mota Inda abokansa ke jiransa domin tafiya wajen daurin aure.
Suna cikin tafiya sukayi realising ai birki bayaci nan hankali ya tashi salati suka somayi yayinda motar ke wujiga wujiga dasu akan titi kamin ta karasu da wani gini.
Allah sarki!cikin su Biyar da suka fito 2 ne suka rayu wato Muhammad da Ismail wadda akayi hospital dasu rai ahannun Allah amma ango da mutane biyu take suka cika. INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN!
Allah taji kan musulmi.
Abangaren wurin daurin aure kam su ango shiru har 2:16pm.
Cikin gida kuwa mata sun cikashi dam Kamar lokacin bikin minal. Ana cikin shagali Amarya tasha kyau sai murmushi take black beauty akaji mai shela na magana Kamar haka: jama’a salamu alaikum, andaura auren malama zaliha usman da malam lukman shu’aibu akan sadaki naira dubu 80 bisa malam yazeed abdulmajeed umar amatsayin waliyin ango,kuma malam abubakar Yusuf amatsayin waliyin Amarya.
Cak kowa ya tsaya gidan yayi shiru bakajin Komai sai numfashi kamin kuma ya sake kacamewa da surutu masu tambayar Dama Ba Sulaiman zata aura bane ?nayi,Masu zagi da habaici Nayi,masu al’ajabi Nayi mai suma ma tayi nata wato Amarya.
Nan Yan daurin aure suka watse akayi gidansu Sulaiman domin jana’iza.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Abinda ya faru kuwa shine ana cikin jiran ango sai……….
https://googleads.g.doubleclick.net/pagead/ads?us_privacy=1—&client=ca-pub-1056799479111612&output=html&h=280&slotname=6559387577&adk=3591653178&adf=688608087&pi=t.ma~as.6559387577&w=627&fwrn=4&fwrnh=100&lmt=1687443843&rafmt=1&format=627×280&url=https%3A%2F%2Fwww.bankinhausanovels.com.ng%2F2021%2F07%2Fkuriciyar-minal-complete.html&host=ca-host-pub-2644536267352236&fwr=0&fwrattr=true&rpe=1&resp_fmts=3&wgl=1&dt=1687443832668&bpp=334&bdt=10751&idt=1933&shv=r20230620&mjsv=m202306160901&ptt=9&saldr=aa&abxe=1&prev_fmts=0x0%2C350x100%2C627x280%2C627x280%2C627x280&nras=1&correlator=2452744655269&frm=20&pv=1&ga_vid=1577807978.1687443838&ga_sid=1687443842&ga_hid=547518263&ga_fc=1&u_tz=0&u_his=3&u_h=600&u_w=1000&u_ah=600&u_aw=1000&u_cd=24&u_sd=1&adx=55&ady=159305&biw=983&bih=600&scr_x=0&scr_y=1736&eid=44759876%2C44759927%2C44759837%2C31071756%2C31075412%2C31075464%2C31075473%2C44788441&oid=2&pvsid=3785175921245960&tmod=759134619&nvt=1&ref=https%3A%2F%2Fduckduckgo.com%2F&fc=1920&brdim=0%2C0%2C0%2C0%2C1000%2C0%2C1000%2C600%2C1000%2C600&vis=1&rsz=%7C%7CpEebr%7C&abl=CS&pfx=0&fu=128&bc=31&ifi=6&uci=a!6&btvi=1&fsb=1&xpc=X1vgwlCA8H&p=https%3A//www.bankinhausanovels.com.ng&dtd=11067
Kubiyoni acikin babi na gaba domin jin abinda ya wakana
Shin kuna ganin lukman da zaliha sun dace ? Yaya zaman nasu zai kasance?4
Don’t forget to vote,comment and share with your friends.
Thank you.
Miss untichlobanty💕
12 November,2019.Ana cikin jiran ango sai hayani ake ana gaggaisawa da Yan uwa da abokan arziki. Da kaga fuskokin jama’an kasan Cewa cikin farin ciki suke.
Wani matashin saurayi ne ya kutsa mutanen daurin auren sannan ya iso daidai da’iran wakilai da manyan mutane.
Sallama ya musu aka amsa sannan ya tsuguna ya Sanar dasu hatsarin su Sulaiman din.
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un suka dinga maimaitawa yazeed ne ya kalli lukman idonsa Adan zare yayinda shima lukman din yazeed din yake kalla.
Lallai Sulaiman ya kasance Dan clique dinsu lokacin da suke secondary wato su uku abokaine saide shi Baya burin zama soja sabanin lukman da yazeed.
Idanun su ne yayi ja musamman yazeed daya tuno yadda minal din keson aminiyarta zaliha. Yaya zasuyi in sukaji wannan labari matsala bibbiyu ga mutuwar Sulaiman ga rashin daurin auren.
Ganin Kamar wajen ya kara hautsinewa yasa suka daina kallon-kallon da suke.
Baban zaliha ne hawan jininsa ya tashi domin yasan yadda diyartasa ke mutuwan son Sulaiman din tabbas yasan akwai kaddara kuma ya zama dole yin tawakkali amma yaya diyartasa zata dauki wannan lamari? Abu daya ne mafita shine in ta samu Wanda zai kula da ita ya kwantar mata da hankali, to amma taya hakan zai kasance ? Da Kamar wuya tunda Ba bawa wani dama zata yi Ba.+
Wannan tunanin yasa hawan jininsa tashi lokaci daya.
Bakinsa na rawa yace Dan Allah Idan akwai Wanda yasan in ya aureta zai iya mantar da ita Sulaiman dinta dukda ko bazata mantashiba amma dai hankalinta zai kwanta ya taimaka ya aureta.
Hawaye ne ya silalo a idanunsa yayinda samari suka dagashi suka sakashi acikin mota akayi asubiti dashi.
Yazeed ne ya kalli lukman kallon aboki ka taimaka ka aureta girgiza kansa ya alamun bazai iya Ba sannan yace yazeed kasan Cewa ayush nakeso kuma how sure are you Cewa yarinyar zata aminta dani?
YAZEED yace na sani lukman amma ka Duba halin da mahaifin yarinyarnan ya Shiga Ina ga ita yarinyar kuma?
Shin kana ganin kaf na wajen akwai Wanda ya cancanci ya aureta? Kana ganin akwai Wanda zai iya kwantar mata da hankali? sannan ya Daga mata kafa ta dawo cikin nutsuwarta kamin ya bukaci hakkinsa?
Girgiza kai lukman din yayi ya budi baki zaiyi magana yazeed yayi saurin Cewa Idan maryam( kanwar lukman din) ne acikin wannan yanayin fa?
Ajiyan zuciya ya sauke yace yazeed ni yanzu Idan ma na aureta ina zan ajiyeta ? Yazeed yace karka damu da wannan ka amince kawai lukman yace amma yazeed kana ganin nayiwa ayush adalci kuwa?
Yazeed yace India har tanasonka zata fahimta kuma ai ita dinma zaka aureta sannan Idan itace awannan yanayi ai bazataso aki auranta Ba.
Lukman yace amma….. Yazeed yace Dan Allah. Ajiyan zuciya lukman din ya kuma saukewa sannan yace shikenan na yarda.
Murmushi yazeed yadan masa sannan ya dafa kafadarsa alamun bada kwarin guiwa sannan.
Tashi lukman yayi ya tsaya sannan yace ni zan aureta.
Kallonsa jami’a sukayi, babu bata lokaci aka aminta dashi musamman da akaga Cewa shidin abokin yazeed, kuma shi yazeed din ya kasance suriki na gari.
Kuma ai masu iya magana na Cewa inkanason kasan halin mutum to ka tambayi su Waye abokansa.
Hakan yasa babu bata lokaci aka daura aure sannan akayi sanarwar jana’izan Sulaiman.
Nan hankali Yan cikin gidan ya kuma tashi aiko nan wasu sukasa kuka yayinda wasu sukayi shewa Suna fadin “ahaiye cass, yo dama anga mai Hannu da shuni an like masa anaso ashiga Dan aci bagas toh ta Allah Ba taku Ba zaliha dai anzama Amaryar lukmanu 😀😀😀😀 auren shige aka mata” wata mata tace yo danma mutanen suna da mutunci naji ance anbada sadaki naira tamanin kome? Kinsan gidan ya kacame banji dakyau Ba.
Wata tace naira tamanin ko sanda rake yafi haka shewa suka kuma sawa dai dai lokacin waliyin zalihan malam ado (Wanda akayiwa yarsa fyade #chapter 2)yayi sallama.
Iya dake sharar kwalla tama kasa magana saboda halin da diyarta ta Shiga domin tunda ta farfado ta kafe waje daya da ido Ba tayiwa kowa magana Ba sannan bata yi kuka ba, ta amsa sallamar sannan ta nufi hanyar kofa tana mai saka hijabinta.
Gaisawa sukayi sannan ya mata ta’aziyya,addu’a sukayi ma Sulaiman din sannan ya miko mata 80k cas Kamar yadda aka bashi sannan ya Samar mata yadda akayi lukman ya auri zalihan.
Godiya tayi masa sannan ta basa 10k nan fa ya rufe ido yace Sam bazai karbi kudin ba. Haka iya ta hakura ta tafi tana kara masa godiya.
Koda ta shigo ciki daki ta nufa ta boye kudin tunda kannenta guda 3 ne kawai a dakin sai innar minal. Matsowa kusa da zaliha data sandake da minal daketa aikin kuka iyan tayi sannan ta lallashi minal nan hankalin minal din yadan kwanta tunda lukman din da aka aurawa zaliha lukman abokin yazeed ne ba wani ba kuma yanada mutunci.
Nanfa suka fara kokarin saka zaliha tayi kuka amma shiru sanda innan minal ta matso kusa ta yi mata nasiha sannan tace ta rike mijin ta da amana ta danne zuciya tunda Sulaiman din ya tafi Anan tayi breaking ta hawaye suka fara zuba tahau shure shure Kamar mai tabin kwakwalwa. Ihu take tana Cewa wallahi ba mutu ba ni Sulaiman dina bai mutu ba,Nasan bazai barni ba ku sakeni,ni kusake ni.
Kanwar iya mai Suna iya murja ce ta fita sannan tace wa jama’a sun gode da halarta da sukayi.
Wannan matarnan ce tace yo ai bansan baban zaliha munafiki,Mara mutunci bane sai yanzu, Ashe batada hankali shine zai aurawa Dan mutane.
Tasss!taji an dauketa da tafi.
🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹
Agidansu Sulaiman kuwa ana sanardasu wannan labari mahaifiyarsu ta yanki jiki ta fadi hospital akayi da ita Ashe coma ta Shiga.
Laila Kanwar Sulaiman rasa Inda zatasa ranta tayi. Kanin babansu Alhaji Ibrahim shi yasanar dasu wannan labari.
Lallashin laila da sauran family yake domin sunyi rashin da saiga goje(from chapter 10) ya shigo yana fito kallonsa kowa ya tsayayi
Shoki ya kwaso ya sauke sannan ya watsa zanku. Babansa ne ya daukesa da mari sannan yace kaide bansan me zanyi dakai ba da’ace a Asibiti aka haifeka da nace an canja Mani Kai, Allah ya Shirya amma ace mutum Dan uwansa ya rasu ko ajikinsa ?
Soka earpiece dinsa da yayi a kunne sannan ya kalli baban NASA yace kai tsohonnan ka kiyayen Idan ba haka ba kauna zaka raka wacan shegen Sulaiman din. Aikin banza duk kunbi kun cikawa mutane gida da kukan Munafurci.
Ke laila ki mana ko kallon Inda yake bata yi ba yace ba dake nake ba? Ta sharesa falla mata mari yayi yace ke Dan ub*nki Dan kinga anasonki shine zakiyi wa mutane hauka?
Kuka ta fashe dashi tace Allah ya isa wallahi Allah bazai barka ba. Wani mari ya dauketa dashi sannan ya take mata kafa yayi ball da ita yace kucaka kawai.
Fitonsa ya cigaba dayi har ya fice yana fadin Daga gadon asubiti uwar taku ma ta wuce.
Hey lovelies masu Neman update gashinan na muku.
Waiting for your votes and comments. See yah

19 November, 2019.Bayan daurin auren lukman ya kira ayush ya fada nata yadda akayi sannan ya fada mata yadda sukayi da yazeed tace Ba Komai ta fahimceshi.
Dadi yaji sosai kamin sukayi sallama irin ta masoya.
Sannan suka wuce wurin jana’izan da za’ayita bayan la’asar shida sauran jama’a.
Bayan andawo ananne sukayiwa iya sallama koda ta fito gaisheta sukayi tare da ta’aziyya ta amsa musu sannan sukace batun amaryan ne shine mukace bara muji yadda kuka yanke shawara saboda Asan yadda za’ayi.
Iya tace ai babu wani damuwa rana ita kuzo ku dauki amaryar ku sukace to ba matsala amma my again MJ tadanyi koda mako biyu ne tadan watstsake Daga radadin mutuwar iya tace hakan ma yayi bayan mako biyun sai kuzo. Insha Allah Nasan zaliha batada matsala.
Godiya sukayi kamin suka Koma gidansu Sulaiman domin yiwa Yan uwansa ta’aziyya.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Ya abubakar ne sanye da shaddarsa brown ya shigo gidansu Sulaiman domin yakanje once in a while Dan haka sun saba da Yan gidan bai taradda kowa ba sai laila dake zaune tama kasa kuka saboda duniyar tayi mata zafi Dana can ga rashin uba,yanzu ga mutuwar Dan uwa,ga mahaifiyarta rai a hannun Allah, ga takurar da isma’il (goje) yake mata Dan kafin ya fita ma sanda yayi mata zagin uwa da uba sannan ya fice tareda Cewa ko tanaso ko bataso sai ta aureshi. Ga ciwon boyeyyen soyaiyar ya abubakar dake nukurkusatta tun tana karama domin tun kafin su zaliha da Sulaiman su fara soyaiya sunsan juna saboda kamin baban zalihan ya rasu yayi aiki akarkashin baban Sulaiman din,Dan haka ya abubakar kan takoshi Duba da Cewa shidin bashoda da namiji.+
Anan dai ya abubakar ya zama abokin Sulaiman kuma ya saba da laila sosai tun tana shekaru 9 shi kuma 18 Inda yake ce nata baby laila har kwalliya yake mata sannan duk sanda tayi ado to shi zai fara gani. Shiyasa duk yadda goje ke mata naci ko kallonshi baikai tayi ba balle tasoshi gashi mugun Dan daba ne kuma tsaf zai iya kisa.
Sallama ya abubakar din yayi jin ba’a amsa Ba yasa ya shigo da alamu tayi zurfi a duniyar tunani Dan haka yazo gabanta ta yazauna Hannu yasa ya tallafo fiskanta dukda ko yasan Cewa bai dace Ba saboda yanxu ta girma ba kamar da ba yanzu shekarunta 17 amma yanayin daya ganta zuciyarsa ta raurawa bazai iya ganinta cikin yanayinnan Ba.
Da ido kawai ta kuresa yace baby laila Kiyi hakuri Nasan Cewa munyi dashi Kiyi hakuri kinji Allah ya jikan Sulaiman rungumeshi tayi tsam kamin ta fashe da kuka shima dai daskarewa yayi na wani lokaci domin rabon da susami kusanci irin wannan tun tana 12 barsu dai sukan rike Hannu once in aw while saboda Sabo dasukayi dayin hakan.
Kasa hanata yayi illa ma Daga baya ya zuro hannunsa ya rugumeta tsam.
Daidai lokacin su yazeed suka shigo ciki suma tunda bawani zaman makoki za’ayi Ba Dan basason bidi’a Dan haka babu mata a gidan sai waje ne ma mutane basu gama watsewa Ba.
Parking motarsu sukayi awaje kamin suka shigo suka ja suka tsaye baki a bude sallamar tasu ta makale domin abinda idanunsu sukayi artabo dashi ya Abubakar ne rungume da laila tan kuka yana shafa kansa da Hannu daya.
Kallon juna sukayi kamin suka sakewa juna murmushi.
Gira daya yazeed ya dagawa lukman yayinda lukman din ya masa thumbs up
Sidam sadam suka Shiga suka zauna a akujera yayinda ya Abubakar yace shh Dan Allah ki dena kuka sai lokacin laila ta bude baki cikin sarkewar murya tace ya abibi (yadda take kiransa) nikam na Shiga uku rayuwa tai min zafi.
Shafa bayanta ya farayi yace karki damu Komai zai wuce Allah ne gatan bawansa kuma ina tare dake ki daina kuka kinji tace to Ummi. Yace yes Ummi tana inane muje kiraksni inyi mata ta’aziya.
Kuka ta kara fashewa dashi tace Ummi ta fadi ankaita asubiti.
Kallon juna su yazeed sukayi alamun what ? Gaskiya rayuwar yarinyar yana garari.
Ya Abubakar kuwa Cewa yayi Kiyi shiru kinji zata zamu lafiya Insha Allah Kiyi hakuri ki daina kuka. Ko kinaso nima in miki kukane ya fadi hakan a muryar wasa. Girgiza kai tayi tana turo baki yasa hannunsa yadan ja kumatunta yace good girl murmushi tayi kadan yayinda yake goge mata hawaye.
Yazeed ne yayi gyaran murya yana Dan shafe sajensa, Adan tsorace suka saki juna laila tayi saurin cewa bari in dauko hijabi na mu tafi asibiti sannan ta gudu yayinda Abubakar ke Sosa kai yana Dan dariya yace a’ah su angwayene dakansu? Ai banjo shigowanku ba.
Gyada kai yazeed yake yana smirking irin ai dole yayinda lukman kuma ya fadi abinda ke zuciyar yazeed din.
Yace mutumina ai dole bazakaji shigowarmu ba irin wannan dumi da kake sha.
Chanja zancen ya Abubakar yayi ta hangar Cewa kun Shirya my tafi asibitinne? Sukace mukam a Shirye muke shiri ai saikai. Mikewa yayi yace ai nima na Shirya sannan ya nufi kofa yazeed yayi saurin rikosa tareda Cewa in-law dawo Duba rigarka dakyau. Lukman yace wani ai sai ya dauka dambe kayi.
Akunyace yadan Jade rigarsa squeezing din ya ragu. Lukman my man maganar nanfa bata Kare ba gara ma kaji.
Daidai lokacin laila ta fito. Gidan biki suka fara biyawa domin su dauki minal aje dubiyan da ita.
Fitowa sukayi a motan akabar Abubakar da laila daidai lokacin minal ta fito yazeed na kallonta ya saki murmushi.
Dan dunguransa lukman yayi yace my man kaima na….
ya Abubakar na kallon duk abinda ke faruwa Dan haka shima murmushi yake amma ba bakin tsokana.
Cikin gida ko zaliha ido ta rufe tace wallahi sai ta bisu. Aka buga aka raya tace Sam haka aka hakura akayi yarjejeniya da ita Cewa in aka barta toh Idan ta dawo zataci abinci.
Laila ko tana hango minal Yan hanjin cikinta suka kada domin ko bazata manta sanda suka tana haduwa sau daya ba sanda ta biyo ya Abubakar itada Sulaiman, minal ta dawo Daga islamiya ta mata duka Wai Dan tasha ruwa da kofinta. Shekaru 6 dasuka wuce.
Gaishesu tayi kamin su masa Shiga zaliha Kamar an jefota da takalmi a hannu.
Minal ne ta zaro ido Adan tsorace tace zaliha me kikeyi awake?
Lukman ne yakalleta sannan ya kalli yazeed domin a tabbatar masa.
Kai yazeed ya gyada masa alamun itace matar tasa take yaji zuciyarsa yayi masa nauyi domin kuwa bayada interest a bakar Mace shiyasa ma yakeson ayush abinda bai sani ba shine ayush bleaching tayi.
Kara analysing dinta yake yazeed shima ya dunguresa Kamar yadda yamai dazu sannan kasa kasa yace inyi magana ko inyi shiru? Still idon lukman na kan zaliha yace yanzu fito kayi?
Ya Abubakar yace Inlaw barshi ba yanzu zamuyi magana ba sai nan gaba.
Zaliha ko binsu kawai take da ido,yazeed yace kai dallah kamo matarka kasata a mota mu wuce. Ya danyi hesitating kamin ya taka izuwa wajenta ya kamo hannunta. Wani yar yaji amma ya basar zaliha kam da hankalinta baya wajen batamasan an riketa ba ta janye hannunsa taje ta shige motar kamin tace Wai me kuke jirane? Yadda tayi magana Zaka rantse uwar su ce babu Wanda ya mata magana illa shigewar da sukayi.
Lukman ke tuka motar yayinda yazeed ke gefensa sai a abaya kuma minal tana owner’s corner sai zaliha a gefenta sai laila a tsakiya sai ya Abubakar a karshe.
What do u think of laila? Kuna sonta?1
Next chapter is a boom💥.
Idan na samu 20 comments toh I will update da daddare.
Takuce karamarsu babbarsu wato.1
Miss untichlobanty💕
23 November, 2019.Yazeed ne yasa Hannu ya gyara mirror yadda zai iya hango minal abinda bai sani Ba kuwa shine lukman ke Satan kallon zaliha ta mirror din Dan haka shima ya hararesa bayan Yan sakanni yasa Hannu shima ya
Juya dauke kai yazeed yayi kamin shima yasa Hannu ya kara juyawa.
Duk abinda ke faruwa ya Abubakar bai lura domin duk hankalinsa ya ta’allaka a yadda yaje zaune kusada laila Dan haka ya kafeta da ido yayinda take wasa da Yan yatsunta ganin yadda ya kafeta da ido bazata iya kallonsa ba.
Minal kuwa window kawai take kallo tana tunanin rayuwa yayinda zally tayi zugum da alamu ta tafi birnin China.
Yazeed da lukman a tare suka kai hannunsa zasu juya madubin kallon juna sukayi yazeed ya harareshi shikuma ya sakar masa murmushi.
Lukman ne ya kalli cikin mirror din Anan ya hango abinda ke wakana a duniyar su Abubakar.
Nuni yayiwa yazeed daidai lokacin suka iso leka mudubin yazeed yayi suka fashe da dariya.
Zabura yayi yace har Muna ido ne ? Lukman yace bamu ido Ba Muna hanya tukunnan suka kuma fashewa da dariya su minal Kam da basu gane meke faruwa ba suka tsaya kallonsu.
Fice wa sukayi suka Shiga asibitin. Wata nurse suka tambaya Inda aka ajiye Ummi din ta nuna musu tare da cewa su Shiga bibbiyu saboda ba’ason hayaniya nan dai suka fara Shiga.+
A take laila ta fashe da kuka dakyar dai aka lallabata kamin min sukayi hanyar gida.
Mayar da zaliha gida sukayi,laila kuma aka kaita gidan Kanwar mamanta.
Ya Abubakar Kamar zai mayar da ita ciki. Sai bayan isha’i suka Koma gida, yazeed yayi sallama da lukman tare da Cewa akwai abinda zasu tattauna goben lukman yace ai baki daya kakeson yin magana Ba nima akwai maganar da zanyi dakai.
Shigowa ciki sukayi kamin yacewa minal tayi wanka ta Shirya ta sauko taci abinci Toh tace sannan ta sauko.
Gyada kai tayi sai ta tuna bayason gestures sai tace Toh sannan ta haura sama.
Wanka shima ya Shiga yayi sannan ya saka kayan baccinsa ya sauko yana Cewa yunwa nakeji amma hanji na ya daure maybe I should take some cappuccino.
Sofa ya samu ya zauna kamin ya janyo wayansa ya fara scrolling messages.
Minal ce ta sauko cikin wani farin rigan bacci na satin amma Ba shara shara bane saide yana like mata a jiki once in a while.
Kallonta yake tayi har ta ido gabanshi bai ankare ba tace gaji still kallonta yake.
Hannunta tasa ta tafa a gaban fuskansa tace nace maka gani.
Hannunta ya kamo ya janyota ta fado jikinsa kokarin tashi ta fara yi ya kankameta sannan ya Daga mata gira daya yace sannu da zuwa.
Kiciniya ta farayi tana Cewa ni Dan Allah ka sakeni Wai na maka kama da yar iska ne? Murmushi yayi yace Kayan jikinki ya amsa mini wannan,sannan tunda gaki kwance ajikina ai kinzama yar iskan ko turo baki tayi ta fashe da kuka ni wallahi ba yar iska bace yace time will tell. Itadai bata kulasa ba banda ci gaba da magana da tayi tace to ai kaika janyoni kuma ka wani rikeni sai kace zaka mayar ni ciki yace to wa ya sani ko cikin zan mayar dake.
Ganin babu sarki sai Allah yasa yasa ta kwanta luf ajikinsa babu abinda ke tashi a parlourn sai sautin numfashinsu kasa kasa minal taji yace “sai Anyi magana mutum yace shi ba Dan iska bane.
Tace me kace yace tunani nake. Harararsa tayi sannan ta kuma kwanciya can sai yace Wai meyasa bakison kirana da suna nane ? Saide kawai ki fadi magana,Ko kuma kicemin oga sir. Ko bakisan sunana bane ?
Girgiza kanta tayi a kirjinsa tace na sani mana ba kaima baka kirana da sunana ba saide ka dinga cemin insaram yace to mene sunan nawa?Dago da kanta tayi tana washe ha’kwara ita a dole kunya tace kawo kunnanka kaji.
Matso da kunnansa yayi a hankali kuma a kunyace tace oga ya..zeed.
Sanda tsikar jikinsa suka tashi domi. Tunda yake bai tabaji sunansa yayi masa dadi Kamar yadda yayi a bakinta ba.
Dan haka yace me ki kace ?ma’ke kafada tayi alamun bazata fada ba.
Puppy face yayi Yace please my insaram! Turo baki tayi tace ba gashinan ba kana sake cemin insaram yace to na daina Idan kika fadamin sunana to zan chanja miki suna.
Hannu tasa ta rufe fuskanta sannan tace oga yazeed
Yace to ki cire ogan tace yallabai zansa ?yace a ah tace to yaya kakeso Insa maka yace ah ah kawai ki kirani da suna na.
Tace a ah ba tarbiyya bace in kiraka da sunanka ko ba Komai ka girmeni.
Murmushi yayi yace beauty is secretly trying to be romantic da muryar tsokana. Turo baki tayi cikin shagwaba da wasa tace wallahi ya yazeed da gangan kake min turanci Dan kasan ban iya ba yace sorry Toh na daina karki damu kema zan koya mini turanci. kinaso ki Koma makaranta gyada kai tayi yace good zannayi miki lesson a gida inyaso sai Kiyi jamb da WAEC ko ? Tace eh yace beauty tace Waye beauty kuma yace Kece mana Sabon sunanki kenan. Ya miki? Ta gyada kai tare da Cewa eh yace kinsman ma’anarsa tace yana nufin kyau ba? Smiling yazeed yayi sannan shima ya gyada mata kai yadda take mai sannan yana kumatunta yace Ashe de beautyn tawa ba laifi.
Shiru wajen ya sake dauka kamin yazeed ya sake Cewa beauty ta dago ta kalleshi yace inason ki saki jikinki in Muna tare kinji? Ta gara kai yace kinaso ki zama kawata ? Ta sake gyada kai turo baki yayi yadda take mai inya mata abinda bataso yace bazakimin magana ba? Tace inaso in zama kawar taka. Tasar da ita yayi ta daina shima ya gyada zamansa Daga kishingida sannan ya miko mata Hannu yace friends? Shaking hannunsa tayi yace bakice friends dinba tace friends sai suka kyalkyale da dariya.
Daidai lokacin cikinsa yayi masa karar yunwa abinda bai tana faruwa dashiba ko a mission kuwa.
Pouting yayi yace beauty yunwa nakeji tace muje kaci abincinka to yace nope cappuccino zansha tace cup…po mene? Yace cappuccino kin gaba sha ? Girgiza kai ya harareta tace a ah.
Yace okay muje kitchen in nuna miki yadda akeyi kai kawai ta gyada suka nufi kitchen dauko duka ingredients yayi sannan ya nuna mata yadda akeyi tace kai Ashe da sauke itama ta hada wani cup karba yayi ya murna yaji yayi dadi sosai zai iya rantsewa bai tabashan cappuccino me dadinshi ba.
Kurba itama tayi kamin ya riko Hannunta suka hau kan kitchen island suka zauna.
Yazeed nasha ahankali yayinda a kurba uku ta tada nata har tana kwarewa yazeed yace sannu bari in dauko miki ruwa tace barshi kawai bari in hada lamurje (lemonade) Insha saboda wannan cappuccino din maka na Daga min zuciya okay kawai yace
Lemon tsami ta dauko yace Kiyi ahankali kada ki yanke tace Toh. Lemonade ta hada tana kokarin saka sugar taji cikinta ya wani murda Dan dafe cikin tayi amma Ba tayi magana ba yazeed ya lura domin tunda ta fara hade hadenta yake binta da ido.
Ajiye cappuccino dinshi yayi yazo ya rikota yace lafiya tace babu kawai sai ta saki kara kadan yace ki fadamun menene?
Girgiza kai kawai tayi sannan ta dauko lemonade din tace sha kaji yayi dadi? Kurba yayi yace yayi sosai ma kuwa kin tabbata you are okay tace eh sha Rabi sai kaban in shanye inna na cemin duk sanda mutum taci abinci to Tasha ruwan lemon tsami saboda yana taimakawa wajen narkar da abincin.
Kara kurba yayi sai yaga minal tana hade fuskatana cije lebe.
Ajiye cup din yayi ya dafa kafadarta da hannu biyu amma kamin yayi magana minal ta saki kara Innalillahi ya yazeed cikina! kamin kace me kumfa ya fara fitowa Daga bakinta.
Na Shiga uku ni yar mutum 2 jikar mutum 4 me kuma ya sami minal.
Lemme kuku run for my life before you kill me!
Miss untichlobanty💕
24 November, 2019.Sulalewa tayi Take yazeed ya bita Ya tsuguna fuskanta cikin tafukan hannunsa yace ke rosy cheeks! Rosy cheeks ! Menene? Kunfan dake kara bulbulowa a bakinta ke kata Daga masa hankali.
Cikin shakewa da kafewar murya minal tace ma..d..dara. Ganin kamar bakinta yayi motsi yasa yazeed ya saurara da tamboyin da yake mata Dan ya rikice.
Ahankali ta sake Cewa mad…darrr..aaa kamin wani kunfa ya kuma fito wa Daga bakinta.
YAZEED yace madara? Ta rufe idonta ta bude a hankali alamun eh. Da Sauri ya kwatar da ita ya mike ya dauko madara ya bude ko kallon Inda kofi suke beyi Ba ya kafa mata.
Tana fara sha ya sauke ajiyan zuciya Wanda yayi dadai da murdawan da cikinsa shima yayi.
Basarwa yayi amma murdin da cikin ta kara yi yasa yayi sauri zau ajiye gorar madaran daya kawowa minal.
Minal kam ta lura da yanayin yadda yake yatsine fuska Dan haka a take tayi saurin sa hannunta ta hade gorar da hannunsa takai bakinsa daya fara zubda kumfa.
Sanda ta tabbata ya shanye kamin ta kwantar dashi a wajen jiki babu kwari ta nufi fridge ta dauko ruwa da wani madaran sai kitchen towel.
Bakinta ta goge sannan ta goge masa nasa bude ruwan tayi zata kafa abaki taji muryansa kasa kasa yace ki dau kofi. Ba musu ta dauka ta zuba tasha sannan ta zauna ta daura kanshi a cinyanta sannan ta bashi ruwa.
madaran ta kara bude musu ta zuba cup din zata sha yayi saurin mikewa Daga cinyarta Dan karfinsa ya fara dawo masa.+
Pouting yayi Kamar yadda take masa kullum yace rosy cheeks ni zan fara sha. Dariya ta kyalkyale dashi saboda yadda yayi maganan Kamar wani Yaro.
Bashi tayi yasha sannan itama ta kafa kai tana sha, ji tayi ya fashe da dariya dan haka ta dago da idonta tana masa kallon dariyar me kake yi ?
Yace rosy cheeks literary we just kissed tace uhm? Yace munyi Sumba nida ke saboda daidai Inda na kafa bakina nan kika sa naki. Zaro ido tayi Take madaran ya kwareta sannu yayi mata ya shafa bayanta sannan ya bata ruwa.
Hararansa tayi idonta ya ciko da kwalla muryarta na rawa tace Nide wallahi bamuyi Sumba Ba danni ba….. Sai kuma tayi shiru.
Yazeed sarai yasan me zata ce dan haka yace uhmm? Tace babu sannan ta dauke cups din ta wanke ta nufi dakinta yayinda yazeed ya kira doctor tunda dare beyiba sosai 9:10pm nema.
Koda doctor yazo yazeed yayi masa bayani Dr din yace poison ne.
Yazeed yace ya sani. Dr din yace menene last Abu da sukaci kamin attack din yace cappuccino ne amma kuma abinda ya bani mamaki kullum ina sha ban taba samun attack dinba.
Doctorn yace lets check the expiring date then. Dubawa sukayi amma akwai har shekara 1 da wata 3 before yayi expire. Doctorn zan kaishi lab in bayar domin test dan something is fishy.
OK kawai yazeed yace ya raka Doctorn har bakin main door sannan ya rufe.
Dakinshi ya nufa ya kunna CCTV sannan ya tafi kitchen direct.
Forwarding Inda su tala sukayi su girki yayi making sure indonshi akan Ronan cappuccino powdern.
Chan bayan sun fita yaga Jennifer ta shigo tana sanda da waige aiko bata tsaya ko ina Ba ta dauko cappuccino powdern tayi mixing da powdered poison sannan ta zaro wayanta tayi kira kafawa a kunnenta tayi kamin chan tace angama aikinindai yasha to zai mutu murus…… gyada kai tayi kamin tace yes ma amma ma problem din baza’a budemin gate Ba sai da izininsa.
Shiru ta kuma yi da alamu tana sauraron dayan bangaren kamin tace yes ma karki damu zan labe da motansu ya shigo ni sai infita………..thank you ma.
Take ya dauki wayansa ya ranbadawa lukman text Cewa a nemo masa Jennifer ko a ina take a muce ko a raye.
Aikinsa ya fara a apple laptop dinsa amma hankalinsa Sam baya kan aikin da yakeyi hankalinsa ya ta’allaka ne akan wakeson kasheshi tunda acikin cappuccino akasa guban kuma shi daya ke shan cappuccino a gidan.
Bayan Kamar 30 minute wayanshi ya fara ringing dauka yayi ta dayan bangaren lukman yace sir mun samota a kawo motor park da alamu so take tabi motar asuba. Yazeed yace great! aikinka yayi kyau, Ina alfahari dakai.
Lukman yace thank you yanzu haka ma tana hannuna we tricked her to come with us.
Yazeed yace tayaya kuka yi ne?
Lukman yace my man Ba Kai daya bane charming fah kawai nuna mata Nayi ina bukatarta a gado Ba musu ta biyoni tana shigowa mota taga bani daya bane ta fara zagina tana kuka Wai na cuceta na yaudareta zanjawo a kasheta.
Dariya yazeed ya sheke dashi jin yadda lukman din ke kwatanta yadda tayi maganan yace shegiya ai kadan ta gani.
Minal ko bayan ta Koma dakinta wanka ta sakeyi ta canja rigarta sannan tasa hular baccinta ta nufi dakin yazeed domin yi masa tausa Kamar yadda ya umarta.
Koda tazo kofar dakinshi bude kofar tayi a hankali domin so take ta bashi tsoro Kamar dai yadda yara keyi.
Abinda kunnenta ya jiyo mata shiyasa ta tsaya cak tabbas Ba karya bane yazeed ne ke waya yana magana Kamar haka:
“Great aikinka yayi kyau ina alfahari dakai” wani aiki ne yayi kyau?
Wai tayaya kukayi ne?sukayi me?karde abinda nake tunani ne?kai noo yazeed bazai tana kokarin kasheni ba. Wata zuciya ne tace mata kin manta ya tsaneki? To amma in so yake ya kasheni me yasa ya CeCe ni? Kuma ai shima yasha.
“Shekewa yayi da dariya yace kadan ma tagani” tabbas damirin sunan mace yake aiki dashi towai me yake magana akai?
Ganin bazata sami answer dinta Ba yasa tazo gabansa tace ya yazeed dama so kake ka kasheni?
A zabure yazeed ya dago yana kallonta ido cikin ido…………..
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Zakiyya zaune gefen wata farar budurwa fat sai sharar kwalla take,Ba laifi tafi zakiyya kyau amma da kaga farinta kasan Ba na Allah da annabi bane.
I am sorry sis! Shine abinda taketa maimaitawa tana shafa bayan yarinyar wacca bazata wuce shekara 21 Ba.
Budurwacce ta kuma share kwalla tace Wai yanzu haka lukman dina yana tareda wata ko?
Girgiza kai zakiyya tayi tace baya tareda ita tunda kince baya sonta nima yazeed dina yayi auren amma ko kallon arziki baya mata ranananda na taho har jibganta yayi. Kidena kuka kinji sister AYUSH?
Let me kuku run for my life before ayi min duka dan yau Nasan zanbar fans Suna tsimayi na
Expect me soon!
Anyway result dinmu ya fito kuma it was masha Allah no problem.
Thanks for your du’as love yah😘
@mzz_untichlobanty 💕
26 November, 2019.Wasu hawayenne suka kuma zubowa Daga idanun ayush sannan ta girgiza kai tace sister zakiyya karki bani fake hopes Dan Allah kinsan namiji abin tsoro ne ta iya yuwuwa yanzu haka yana tare da amaryarsa ya manta dani.
Shafa kanta zakiyya tayi cikin murya mai laushi da nuna Cewa ta damu da yanayin da cousin dinta ta Shiga tace little sis have faith kinji ? I know that you are brave, ko sanda parent dinki suka rash you were so brave right ? Gyada kai ayush tayi zakiyya tace Toh kin bani you can go through it and kinyi trusting lukman dinki ko? Ayush ta kuma gyada kai tare da Cewa eh kamin wani hawayen ya silalo zakiyya tace good since have trusted him and you are sure that he loves you then there is nothing to worry about dago da manta tayi ta kalli zakiyyan tace are you sure?zakiyya tace 100% sure now give me a smile kinji?
Murmushin dole tayi zakiyya tace ko Ba ke bafa now tashi muje kick abinci.
Girgiza kai tayi tace banajin yunwa, hararanta zakiyya tayi tace zaki tashi ko yaya? Mikewa tayi tana Cewa sis wannan kallon ai sai ki cinyeni dariya suka fashe dashi kamin suka wuce dinning area domin cin da’am.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
What!? Minal me kike nufi me zaisa in kasheki? Harara minal ta aika masa kamin tace abubuwa dayawa. Wato dama duk wannan abubuwan dakake min kanayine saboda in na mutu kar a zargeka?minal ta fadi hakan tana mai daga murya.
Tsawa yazeed ya daka mata ya daka mata yace banson hauka fah kodan kings ina Daga miki kafa shine zaki kawo mini rain in hankali ? In da inason na kasheki ne da tuni na kasheki.+
Hararar sa tayi da rinannun idonta muryarta na rawa alamun zata iya fashewa da kuka at any moment tace amma wallahi bantaba nadamar aurenka Ba irin yau Nayi kuskure Dana yarda dakai Ashe Dama kai me kisan kaine? Ashe kasan abinda ka tanada shine harda cemin Wai mu zama abokai,Dama zaka iya min haka? zuciyata ta raurawa har yanzu na kasa yadda Cewa kanason ka kasheni, ya yazeed ka tasheni kacemin mafarki nake Ba dagaske bane,Ba kasheni kakeson yi Ba.
Tsintsiyar hannunta yazeed ya kama ya jata har izuwa bakin kofar dakinsa sannan ya wancalar da ita yace Anyi kokarin kashekin Kiyi abinda zaki yi sannan ya rufe kofarsa.
Wani irin zafi zuciyarsa ke masa Wai yau shi YAZEED ABDULMAJEED UMAR aka Cewa yana kisan kai? Da alamu sakarwa yarinyarnan fuskar da yakeyi ya janyo masa matsala.
Zaiyi kokari ya nisanceta ko tayaya ne domin ta fahimci kuskurenta sannan ta fada hakuri kamin ya yafe mata.
Wata zuciyar tace uhm tunda kuke da zakiyya ta taba baka hakuri ne inba tanada wani agenda ba.
Sai alokacin ya tuna da zakiyya yace ko ina ta Shiga oho bako waya? I will call her tomorrow.
Da sake sakennan ya fara bacci tare da aiyana irin azabar dazai ganawa Jennifer harsai ta fada masa Wanda yasata wannan aika aika.
……………..
Minal ko yana rufe kofarsa ta fashe da kuka. Sanda tasha kukanta ya isheta sannan ta mike taja kafafunta jiki a sanyaye taje dakinta. Itakam ta Shiga uku da rayuwarnan da badan kartayiwa Allah butulci Ba da tace inama ta mutu Dan wallahi sanda wannan abun ya farune ta fahimci ta fada tekun son yazeed dukda ko bata tana yin soyaiya Ba amma dai ai tasha jin abubuwa akanshi gashi ita Ba takaddun Hausa take karantawa ba, wannan sai zaliha wani ajiyan zuciya ta sauke me nawi tunawa da zaliha da tayi ko yanzu a wani hali take oho, sai yanzu ta fahimci ciwon da zaliha keji.
Yanzu da ace ya yazeed ne ya zatayi? Dukda ko yayi kokarin kasheta wallahi itanasonshi a hakan ma. To kode tayi kuskurene? Kode bashi yakeson ya ya kasheta ba? Kode wani zancansa daban yakeyi ? Kai ya cancanta ta bashi hakuri sannan ta nemi Karin bayani tunda ko a musulunci babu kyau zato.
Kallon sama tayi tace astagfirullah Allah na tuba,nikam naga takaina karfa in mutu yau mijina na fishi dani.
Mijina? Kai Ahe ban taba kiransa da mijina ba ta fadi hakan tana Washe hakora Kamar ba ita ta gama drama yanzu ba.
Kai Gaskiya bani iya bacci in banbashi hakuri ba ta fada a magana zuci. Saukowa tayi Daga gadonta tare da Cewa gadona kar kayi kewata yanzu zan dawo kaji ? Kamar gadon yana jinta (typical me😂 yeah I have that kind of connection with my bed and phone.)
Sautin tafiyarta Kadai ke tashi saboda yadda gidan yayi shiru. Koda ta iso kofar dakinsa knocking tayi a hankali taji shiru ta sake knocking still shiru
Murda hannun kofar take shirin yi sai alokacin ta lura Cewa Ashe kofar batada Hannu sai wurin saka pin ta ciki ne akwai handle.
Nambobi ta fara daddannawa amma koda tayi sai uku duka wrong sai kofan yace bazata iya sa’a ba sai after 15 second itako da ba ganewa tayiba taci gaba da dadaddanawa.
…………………….
Yazeed kwance a dakinsa har bacci ya fara daukarsa yajiyo taku na kara matsowa kusa da dakinshi kuma Idan ba kuskure yayi ba takun minal ne tayaya ta Shiga side dinsa ? Gush Ashe ya manta be rufe koda ba thank goodness kofar dakinsa in a rufe ba’a iya budewa ta sake sai ansaka pin da ace ba minal bace fa ?
Dawowa yayi daga tunanin da ya shiga jin minal ta fara knocking kamin kuma ta fara daddanna pin.
Yanaji machine din nata dit dit dit dit dit zu! Har sai uku alamun pin din ta is wrong amma yaji minal ta cigaba da daddanawa.
Tasowa yayi yazo bakin kofar yadda zaiyi magana ta jishi ba sai ya daga murya ba saboda girman dakin.
Yace ke dallah kibar nan wurin karki batawa mutane kofa aiko minal tanajin yayi magana tace ya yazeed Dan Allah ka bude Dan Allah baice Komai ba ya Koma yayi kwanciyarsa.
Minal ko jin shiru bai kara magana ba yasa ta jingina da kofar kamin tace Dan Allah kayi hakuri Nasan Nayi kusukure Dana zargeka ta fadi hakan tana shirin zubda kwalla.
Mamaki ne ya cika yazeed Wai hakuri ta bashi kuma ma da wur wuri haka ? Chabdi ai inda zakiyya ne wallahi saide ya mutu.
Baice Komai bayayi kwanciyarsa,can yaji Kamar shesshekan kuka wani zafi yaji zuciyarsa tamaisa amma ya daure wajen Cewa in kin gama kukan kibarmin side dina sannan karki sake ki kara zuwa inda nake.
Kuka ta fashe dashi tace Dan Allah karkayimin haka ya yazeed kayi hakuri bazan karaba.
Jin shiru yaji kulata yasa ta Koma dakinta zuciyarta cike da damuwa yanzu ita ta yaya zata bashi hakuri bayan yace bayason ya kara ganinta? Wani kukan ta kuma bingirewa dashi har bacci barawo ya saceta.
Good morning na cika alkawari,please make sure you spread a smile on my face comment and vote fah
Have a good day bye
Miss untichlobanty💕
28 November, 2019Da safe jiki babu kwari minal ta fito ta fara aikinta koda ta kammala,tayi wanka sannan lokaci zuwa lokaci takan sauko ta Duba dinning table ko yazeed ya sauko domin ta share dakimshi tunda yace bayason ya kara ganinta.
Komawa tayi dakinta ta zauna Jim kamin ta janyo wayarta sai alolacin ta tuna batada numbern zaliha kawai sai kawai taje gaban madubi ta shafa powder da lipstick saboda rage lokaci Kuma tayi kyau Ba laifi.
Fitowa tayi daga dakin aranta tana Cewa Nasan ya fita ma tunda safe kuma ko na hadu da shi ma nuna masa zanyi ina fushi dashi muga yadda zaiyi. Murmushi tayi kamar wata shashasha ko yadda yara keyi Idan sun kulla wani abin.
Laundry room ta Shiga ta dauko kayansa set 2 data goge dazu ta nufi part dinsa koda ta Shiga Ba kowa kuma parlourn nasa ma da duhu alamun babu kowa tace Ahe duk jirannan danayi na banza ce bayanan ma.
Ta bangaren yazeed kuwa Kamar jira yake ta Koma daki sai gashi ya sauko, kitchen ya nufa ya dauko hollandia yoghurt plain flavour saboda na fridge din parlourn sa ya kare sannan ya dauki cup ya fita.
Dakinsa ya Koma yasha yoghurt dinsa Dan baya mood din cin abinci. Kwantawa yayi abinsa ruf da ciki yana mai kashe wutan dakin sannan ya rufe idanunsa once in a while yana murmushi.+
Da confidence dinta ta tura kofar dakin Dan ba’a rufe kirif take ba sai ta dauka ko ya bar mata ne Dan tayi shara Kamar yadda yasaba bari Dan haka bata kawo Komai cikin ranta Ba ta shigewarta.
Hijabin dake jikinta ta cire tayi cilli dashi akan gado sai kan fuskar yazeed Wanda dama tun dazu yaji takunta kuma yasan ta shigo dakin amma ita batasan da zamansa Ba. Baice uffan Ba balle ya motsa yayi luf cikin bargonsa sai kansa dake waje wanda yanzu yake lullube da hijabin minal. Tunani yake aransa yarinyarna badai sa hijabi Ba kam. Allah yasa da kyakkyawar niya ce.
Ajiye kayan tayi akan stool kamin ta dafe goshinta da hannunta tace ni yanzu ya zanyi ? Kullum yananan yana budemin wannan yar iskanci kofar dakin kayan nasa to yau kuma bayanan.
Kicin kicin tayi da ido tace Idan na kamo yaya yazeed dinnan sai na naushi bakinsa. Sai kuma ta kyalkyale da dariya tace Wai wayaganni na danne ya yazeed sai jibgarsa nake.
Wutan dakin ta kunna kamin ta dauko kayan aikinta. Ganin bargon NASA a wargaje yasa tace kai Ashe ya yazeed dinma kazami ne fadin jumlar tayi daidai da janye bargon aiko atake ta kwala ihu zata arta a guje yayi saurin wantsalota ta fado jikinsa kokarin tashi take tanata tuttureshi amma ya riketa gam hannunshi ta fara mintsini tana Cewa ya yazeed ni ka sakeni nifa Ba yar iska bace. Bai kulata Ba illa ma tashi da yayi zaune sannan ya ajiyeta akan gadon couch ya Koma ya zauna sannan yace rosy cheeks gyara gadon kizo in fada miki wani Abu. Dan hade fuska tayi tace me zaka fadamin? yace sirrine a kunne ma zan fada miki tace toh……….
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Zakiyya zaune a parlourn gidansu Amarya tana oiling ma ayush din gashi Wanda Ba yabo Ba fallasa.
Wayanta ne ya fara ringing ta dauka kamin tayi magana akace madam the boutique has been on fire mun kira fire service sun kashe but we couldn’t retrieve our goods.
Zakiyya da batasan sanda mike Ba tace what?how comes? Are crazy? incoming call taji hakan yasa ta Duba ganin sectary dinta ne yasa ta datse da gaggawa tana mai Cewa hello maryam wani irin nonsense nakeji Wai boutique ya kam……….
Bata karasaba Maryam tayi Sauri Cewa Ba nonsense bane ma munyi gobara, the came out of no where. Yanzu haka ina hospital saboda na none a gefen hannuna amma Ba wannan Ba new boutique dinma an Shiga an kwasge kayan tas sanna aka rusa ginin.
Take zakiyya ta yanki jiki ta fadi kasa sumammiya. Ace sukiyar da tayi shekara kusan 5 tana Tarawa cikin minti 5 babu su?ina impossible.
Inda Allah ya taimaka baki nasu wani hallara Ba tunda har yanzu saura 4 days a fara shagalin bikin ma Dan haka akayi asibiti da ita.
STORY CONTINUES BELOW

Sanda tasha drip 6 a rana daya dukda ko bata farfadoba saboda tsabar shock.
Yan gaisuwa kam sun kasa karewa an mayarda asivitin Kamar gidan Suna sai Shiga da fice ake.
Ayush zaune akan wani kujera a gefen gadon zakiyya taga Kamar hannunsa yana motsi. Rike hannun tayi ta fara jijjigawa tana kiran sis?sis sannu kinji ? A hankali zakiyya ta bude idanunta aiko babu bata lokaci hawaye sukayi sallama suka bemi mazauni a idanunta.
Mamanta ne tazo kusa da ita tana lalkashinta kamin tace Kiyi hakuri zakiyya akan namiji kike Neman kashe kanki? Sakinki yazeed din yayi ayush ne tayi saurin Cewa gaba mama saki kuma ? To mema zakiyyan tayi da za’a saketa?
Mama tace to inva saki Ba mezaisa ta sume har gadon asibiti caraf akaji zakiyya tace dukiya, dukiya itace abin da ta janyo.
😭mama dukkan dukiyan Dana Tara sun tafi,mama tace ban ganeba, zakiyya tace Nayi gobara babu abinda ya fita a boutique dina.
Dakin dake cike da mutane ne ya kaure da Inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un.
Nanfa Yan Jaje ma suka fara rububi anata kawo gudun muwa.
🌹…………………
Abangaren malama zaliha kam Ba kanta Dan yanzu tadan dawo daidai Inda tace Allan katafur sai an nemo lukman ya saketa, ita bazata iya cin amanan Sulaiman Ba. Mahaifinta da aka sallamo washegarin faruwar abin ya nuna farinciki sosai dajin Wanda ya aureta.
Ganin dai kowa yanason auren yasa ta saduda amma da sharadi bazatayi zaman aure dashiba. Side ido suka zuba mata Suna kallon ikon Allah so saikace hauka? Allah dai shi kyauta ya kuma bata lafiya Dan gani suke ta tabu.
🌹……………………..
Laila na zaune a dakin da mahaifiyarta ke kwance rai a hannun Allah. Aunty kuma ta Koma gida bata dawo ba goje ya bankado kofar dakin. Harararsa tayi tace me ya kawoka? Murmushi yayi cikin muryarsa ta Yan shaye shaye yace rayuwar Abubakar na cikin hatsari.
Laila tace what? Wani Abubakar din ? Yace Abubakar Yusuf dai da kika sani Kiyi sauri.
Batasan Inda take wulla kafunta Ba hankalinta tashe tana rokan gone da ya hanzarta kar wani Abu ya sameshi
Koda suka fito farfajiyar asibitin babu kowa Duba da Cewa magriba tayi wasu masallatan ma har sun kira sallh matse bakita yayi kamin ya cusa mata tsimma ya daure sannan ya sakata a Booth.
Figar mortar yayi yabar farfajiyan asibitin wani gida ya kaita ko ince irin dakunannan da samarin yanzu Yan Abu yarima ashana kida,Yan zaman kashe wando keyi. Banda warin sigarin ,hamamin amai da zarnin fitsari babu abun da dakin keyi Ba Komai bane a ciki illa katifa sai karamar TV da wata akwati daya sai kwalaben giya a gefe da dusan sigari.
Cirota yayi Daga booth din ta hada gumi tayi jagab ya fara janta zuwa cikin dakin, turjewa ta farayi ya gaura mata mari take ta fashe da kuka. Hankadata ya dingayi har ya wullata kan katifan sannan yace zan since miki baki domin ya zama dole in dan dana su amma Idan kika sake kikayi ihu kinga wukannan daina Burma mini ita da fatan kinajina ? Hararsa tayi yace wallahi wannan kallon wani irin shauki yakesamin.
Since bakin yayi kamin ya kara da Cewa gara kiban hadin kai muyi mu gama lafiya asirinmu a rufe.
Tace wa’iyazu billah aini ina Neman gafarar ubangijina na shigowa wannan dakin da kuma zama a wannan katifar da bansan sau bawa akayi zina akanta ba. Ka since min hannuna! Bara kaji Wallahi tallahi karshenka bazatayi kyauba.
Kuma haihuwarka asarar nakuda da ragon Suna ce.
Wani mari ya kuma dauketa dashi wannan karan harbakinta sanda ya fashe. Ihu ta kwala tana kiran sunan mahalliccinta. Bata ankare ba taji goje ya danneta yana kokarin kai mata kiss kakkauda kanta ta fara yi babu abinda take tunowa sai yadda ya Abubakar zaiji inya riski wannan labari.
Cikin rashin sa’a goje ya cafki bakinta yana kokarin tura harshensa ciki. Ganin ta rufe bakin kam yasa ya matse mata bakin da hannunsa badan task ba ta bude ta mai ja masa Allah ya isa.
Aiko harshensa yana Shiga bakinta ta fara kwaranyo amai.
Cire bakinshi yayi Daga nata ya fara zabga mata Marika sanda ya ajiye mata takwas lafiyaiyu daidai lokacin Allah ya taimaka mata hannunta ya since
Kokarin Daga mata Riga goje ya fara aiko nan suka kama kokuwa Kamar ba gobe.
Yaga rigar yayi ya fara kokarin rabata da pant dinta amma taji yarda tun tana iya tureshi har ta kasa hakan yasa yayi nasarar zare wandon nata yayi wulli dashi.
Wani irin zafi taji a mararta ta kwalla ihu YA UBAN GIJI NA daganan bata kara ganin komaiba.
😭😭😭 oya join me along let’s cry!kuzo muyi kuka tare this chapter is so heart touching.
Long chapter ne so I expect you to VOTE kuma Ku cika min comments section da COMMENTS.
me kuke tunani game da wannan chapter?
Sai anjima wallahi bacci nakeji.
Takuce karamarsu babbarsu wato ;
Miss untichlobanty💕
30th November, 2019Ruwan sanyin da taji shi yasa ta bude idanunta batare da ta shirya ba, dishi dishi take gani har Komai ya zamo mata tar.
A take ta zauna dukda ko irin azabar da maranta ke mata,babu bata lokaci duk abubuwan da suka faru da ita suka dawo mata.
Kallon jikinta tayi taga kusan gabadayan kirjinta a bude.
Bedshit din da yake dukun dukun taja ta rufe jikinta badan ranta yaso ba.
Kallon dakin ta farayi jiki a bari saboda sanyin da takeji taga goje da Rigarsa a kafadarsa zaune gefen kafarta da Goran ruwa yana cin shinkafa da wake sannan sai ya busa sigari ya kara wata lomar.
Janye kafarta tayi Daga kusa dashi tana mai jin daci a zuciyarta.
Sai alokacin yace Ashe kina Raye aina dauka kin mutu ne shiyasa na Zuba miki ruwan zanyi Dan tabbatarwa. Zo muci abin ci kinji. Sannan ya kara wata wata loma.
Kallon sa kawai take Dan batasan abin nasa yakai haka ba tace Allah ya kiyaye inci da Hannu na yace in baki cita ba ai kinyita,ina fata ma Nayi ajiya.
Kuka ta fashe dashi wannan karan mai sauti tace amma wallahi ni ban taba Sanin Cewa kai Dan iska tsinanne Mara mutunci bane sai yau,yanzu……
Tas ya wanketa da mari yace ke yarinya iya bakinki,baki isa ki fada mini maganar banza ba kuma Anan zaki zauna harsai sanda naga daman ki tafi zaki tafi.
Tace wallahi……. Wani Marin ya kuma dauketa dashi yace ba nace karki kuma yi min magana ba to bari kiji babu Inda zaki ko mutuwa zakiyi.+
Wata kakkausar muryace a bayansa tace kaima baka isa ba kuma kayi kadan. Bai ankare ba yaji an damkosa ta baya aka jibgarsa Kamar Allah ne ya aikosa.
Gwara kansa yayi da gini sannan yace lailar?lailar kayiwa haka?toh wallahi ba me rabaka dani yau sai Allah. Naushi ya dinga kirba masa yayi kaca kaca cikin jini. Kafa ya dinga masa a tsakiyar kafafunsa. Goje ganin Idan bai ceci kansa ba, to fa zai iya kasheshi Dan haka ya tattaro duk karfin dayayi masa saura ya hankadeshi ya gudu.
Da Sauri ya mike zai bishi laila tace barshi ai aikin gama ya gama.
Da gudu ya nufi Inda take ya rungumeta. Tsawo lokaci suka dauka a haka kamin yace Laila me yasa kika biyoshi bayan kinsan halinsa?Ashe bakida hankali?yanzu ga idonta nan ai ko me yace miki bai dace ace kin bishi Ba! Ya fadi hakan cikin Daga murya, fada, da kuma nuna Bacin rai.
Laila da zuciyarta ke mata kuna ganin ya Abu ya rufeta da fada, Ba tare da ya bata Samar maganaba, cikin gunjin kuka tace haka fa yacemin Wai rayuwarka tana cikin hatsari shiyasa banmasan sanda na biyosa Ba idona ya rufe har nabar mahaifiyata ita kadai😭.
Shiru ne ya ratsa wurin na Dan wani lokaci kamin ya Abubakar cikin murya me taushi da ban hakuri yace me yasa idonki ya rufe da akace rayuwata tana cikin hatsari?
Zuciyarta ne ta buga dum! Jin tambayar daya Watso mata Ba tare da ta Shirya amsashi Ba.
Shiko jin tayi shiru yasa zuciyarta tayi sabyi domin bai sani amsar da yakeson Ba. Ga mamakinsa yaga ta dago ta kalli cikin idonsa kamin tace SABODA INA SONKA! Yaya na Dade da Fadawa cikin tekun soyaiyarka tun kamin Nasan ciwon kaina.
Na Riga da na nutse kuma bana burin a ceto ni, nafiso ace na mutu acikinta.
Ya Abubakar Kam daya daskare yama kasa magana Dan ko ya bude bakinsa sai ya rufe ta. Bai masa mata Ba dukda ko tsabar dadi jiyake Kamar zuciyarsa zai fado Daga kirjinsa.
Rigarta da ajayi cillo da ita ya dauko amma me duk a yage take Ba anfanin sata take farin cikin dake zuciyarsa ta sauyu zuwa bakin ciki.
Wani kububuwan kishi ne ya taso masa yana sararsa. Idanunsa ne suka cicciko da kwalla sai alokacin ya lura da Laila wadda taci gaba da kukanta.
Tazarce ne ajikinsa Dan haka ya cire ya bawa lailan yace tasa ta samosa a waje yana jiranta acikin taxi.
Hannu na rawa ta karba shi kuma ya fice.
Tana mikewa taga jini duk ya bata katifar da Sauri ta danne bakinta domin kar ihun data kwalla ya fita.
Durkushewa tayi a wajen ta kara bude Sabin babin kuka tana fadin ka cuceni ka lalatamin rayuwata bazan tana yafema Ba.
Sanda tasha kukanta sannan sako rigar ta dauko yageggen hijabinta tayi gyale dashi yayi da tayi kunzugu da rigarta tunda har lokacin jinin bai tsaya Ba, sannan ta fito.
Direct gidansu ya kaita har cikin daki yace tayi wanka ta gyara jikinta bata ya siyo mata magani sannan kar ta Fadawa kowa abinda ya faru tunda yanzu dare ne kar hankali ya tashi. Gone sai ya kaita wurin minal tunda inna ta tafi Maiduguri da zaliha acewarta Idan tabar kadunan zata Dan manta da mutuwar inyasi Daga nan ma sai a kara mata gyaran jiki.
Juyawa yayi zai fice cikin shesshekan kuka tace dama Nasan Cewa bazaka aminta dani Ba!me zakayi da second hand Wanda Dan shaye shaye ya karbe mata budurcinta? Kayi hakuri Nayi kuskure danace ina sonka.
Dawowa yayi ya riko hannunta cikin nashi yace Niko nakeda abinda zanyi dake,kuma batun budurcinki banida damuwa tunda bada kanki kika hada ba,karkisa damuwar Komai aranki domin irin soyaiyar danake miki koke bakimin irinta.
Tace Nasan kana fadan hakan ne Dan kana tausaya min😩 wallahi Idan haka sona gara ka fadamin ya fiyemin alkhairi. Yatsansa ya daura akan lebensa yace shhhh ! Karkice haka, kinsan kuma bans miki wasa in ana serious magana wallahi ina sonki koda wannan Abu bai sameki ba ni zan aureki balle da ya kasance akwai faruwar wannan lamarin ki Nayi an kara narka min dalman sonki a zuciyata kuma in kikaga ban aureki ba to Allah ne baisoba now give me that beautiful smile of yours kamin in tafi.
Small smile tayi masa hawaye ya tsiranyo, goge mata yayi yace Idan kika kara kuka Nayi fada dake tace na dena wallahi.
Shafa kanta yayi yace saina dawo.
🌹…………………..
Abangaren su yazeed kuwa minal Adan tsorace da kuma jin haushin tabata da yazeed keyi ta gama gyara dakin zuwa taji gefensa ta tsaya fuskannan a hade tace gani.
Binta yayi da kallo tun Daga saka har kasa da tabbas kayan sun karbeta ba karya.
Hannunta ya riko zai zaunar da ita a cinyarsa aiko ta mike zinbir Kamar ta zauna akan kaya.
Tace wallahi bazan zaunaba karfi da yaji nifa na ganoka ya yazeed dinnan so kake ka miyar dani yar iska ko? Juyawa tayi zatabar dakin yazeed ya janyota luuuu sai gata akan faffadar kirjinsa…..
Anan zan dasa aya, ina godiya sosai da irin soyaiyar da kuke nunawa takaddannan.
Karku manta wajen latsa tauraron dake kasa sannan Ku fadi ra’ayoyinku.
Ku sanarda Yan uwa da abokan arziki Wanda kuke ganin ya dace su karanta littafinnan.
DAN ALLAH KU SANAR DANI KO KUNAJIN DADIN LITTAFINNAN? SANNAN KUMA ME KUKESO NA KARA KO NA RAGE ACIKI?
Miss untichlobanty💕
3th December, 2019.
Kokarin tashi ta fara yi amma yazeed ya riketa kyam kuka ta saka masa tace idan ma magana kakeson fadamin ba sai in zauna a gefenka ba.
Yanzu so kake in name layinmu Na da su talatu suce na gama cika baki yanzu nima na zama kalarsu. Wallahi Idan baba yaji ub*ana zaici da takalminsa.
Yazeed da yayi sakoko yana kallonta yace wayace miki za’a ce miki yar iska? aike kinyi aure kuma nine mijinki Dan haka babu Wanda zaice miki yar iskanci Dan na tabaki. Ki daina damun kanji kinji ? Turo baki tayi tace Gaskiya saina tambayi aunty fauziyya nasani ma ko wayo kakeson kamin? Idan na fada mata yadda mukayi sai inji me zata ce.
Cikin wayo da dabara yazeed ya kwatar da minal gaba daya a jikinshi ba tare da ta lura ba yace ke in banda abin ki kin tana ganin Inda ma’aurata suka fitarda sirrinsu? Ko bakisan Cewa manzon Allah SAW yace: Idan ma’aurata suka shiga daki sukayi wani Abu sannan suka fita waje Suna yadawa to Kamar akan titin sukayi”
Tace kwarai kuwa an fadi mana a islamiya Toh amma abinda ban ganeba shine Wai wani Abu ake nufi ?
Kallonta kawai yazeed yaje cike da mamaki yayinda itako duk hankalinta ya ta’allaka akan gemunsa da take wasa dashi. aransa yace Gaskiya ina da aiki babba a gabana wannan yarinyar fresh karatu take bukata.
Yace kinason in koya miki abin ne ta gyada kai tare da Cewa em.+
Hannunsa yasa ya dago da ita ta zauna still tanakan cinyar tasa yayin da take Cewa “kai Gaskiya sajenka lauhi sai kace…..” Ba ta karashe zancen ba sanadiyyar hade le’bensu da yazeed yayi guri daya kasa motsi minal tayi saboda gaba daya notinan jikinta sunyi sanyi, wani bakon al’amari aka bijiro mata dashi ba tare da ta Shirya ba.
Yazeed ko tsotsan lips dinta ya farayi kamin ya fara kokarin zura harshensa cikin bakinta amma ita dai tayi tsam tana jinsa yana abunsa janye bakinsa yayi Daga nata kamin yace lesson 1. Duk abinda na miki ki miyarmin kinji ta gyara kai a hankali yace good gwadamin yadda na miki yanzu.
Kwantar da kanta tayi a kirjinsa tace Gaskiya ni kunya nakeji!yace to aiko zanje na karo aure kuma irin zakiyya zan auto Wanda batajin kunya da Sauri ta dago da kanta tace Dan Allah kayi karka karo zanyi wallahi Idan ka karomin irinta na mutu da daya ma ya nakare? murmushi kawai yazzed yayi yace yi mugani to.
Gyara zamanta tayi sosai sannan ta rufe idonta a hankali ta daura lips dinta akan nashi Kamar yadda ya mata.
Wani irin yarrr sukaji dukansu biyu yayinda abin yazeed ya mike sosai. Tsotsa itama tayi sannan ta sake cikin mutuwan jiki yace kitabbatar kin rike Idan yaso zamu daura Daga step 2 in lesson 1,sannan ki dinga yin wanka ko wani lokaci kina saka kaya masu kyau shi zai kara bani kwarin guiwa wajen koyamiki karatun kinji tace um Dan ita jikinta yayi sanyi sosai.
Kwantawa ta kuma yi a jikinsa sannan ta dukunkune Kamar yar kulya babu abinda ke tashi sai numfashinsu.
Yazeed ne ya soma magana a hankali yace ji yadda kika lafe wa mutane a jiki ayi magana mice ke ba yar iska bace😜
Dukan kirjinsa tayi tace ai kaika miyar dani yar iska dama dance zama da madaukin kanwa shine kawo farin gashi. Yace to ya kikaji babin Yan iskan akwai dadi? Daga kai tayi akunyace tana murmushi Kamar gabuwa.
Dariya mai Dan Sauti kadan yazeed yayi yanajan kumatunta alamun tsokana yace rosy cheeks dina ta zama yar iska shagwabe fuska tayi tace banaso Dan Allah ya yazeed.
Yazeed yace Gaskiya ai nake fada gobe sai in kaiki amiki register ko ? Harararsa tayi ya mata gwaliyo. Yace amma ki daina cemin yaya ki samamin wani Suna fah.
Tace toh zanyi tunani ko ka cancanci hakan. Faking heart break yayi ya daura hannunsa a kirji,table baki minal tayi tace Wai me kakeson ka fadamin dazun? Yace kawo kunnanki kiji.
Matso da kunnan tayi sannan yace Abu uku ne kinaji ta gyada kai, yace so nake nace miki kinyi kyau sosai, sannan ki dena cilli da hijabinki ta ko ina ko kinason ki wulla akan Dan aljani ne?ta girgiza kai, kuma Idan kika kara cemin kazami to zan nuna miki kazantana Kingane ko? Tace eh yace good.
Tashi take kokarin yi zata fita yace ina zaki ? tace wutan abinci zan kashe in dibo nawa yunwa nakeji, yace me kika dafa?tace dambu ne.
Dan hade gira yayi yace dambu? me kuma wani dambu? Zaro ido waje tayi tace kana nufin bakasan dambu ba yace ban sanshi ba tace cabdi ! nikam bari inje inci abincina.
Yace ki zubo in gwada ci first time in history inji ya abincinnan naku na gargajiya yake ne?
Kallonasa take ido azazzare kamin abincin Dana Daga zakaci? Yq gyada mata kai kamin yace ko zakimin rowane? Girgiza kai tayi tace kaida abinka,Ai ban isa Ba. Shafa kanta yayi yace duk abina naki ne kinji? Kai kawai ta Daga.
Mikewa tayi har ta iso bakin kofa yace inkinsan kinyi kazanta ki barshi.
Bubbuga kafa tayi tace Allah Idan nahadu da inna ko, wato yadani take a duniya ko?
Ince na dena kazantar? Ta karashe magana fuskarta Kamar zatayi kuka.
Yazeed yace au dama kinayin kazantar yanzu ne kika dena? Gaskiya Daga yau zan chaja miki Suna kin tashi Daga rosy cheeks kin Koma YAR KAZAME.
Kuka ta saka tace wallahi Allah ya yazeed karmka sakamin yar KAZAME banasoooo😟
Kashe mata ido daya yazeed yayi tareda gwaliyo yace yar KAZAME yi Sauri ki dauko mana abincina😜
Fita tayi tana kara volume din kukan shagwaban da takeyi. Koda ta isa kitchen zuzzuba abincin tayi sannan ta danna kararrawar kitchen Kamar yadda tala ta nuna mata.
Aiko baifi 2 mins ba saiga tala tace aunty Amarya sannu da aiki minal tace sannunku ga abinciku nan sai wannan na baba sule ya dawo ba tala tace eh ya dawo ina zai iya zama da madam zakiyya? Ai ko dawasa bazaiyi kuskurennan ba.
Murmushin yaje kawai tayi Dan ta tsani akawo mata zancen wani. Tace taka nace ba; Dan Allah Ku daina muzanta mutum abayan idonta babu kyau,wannan gulmace kuma kinacin namansa ne Idan yayi Abu ba daidai ba in zaki iya magana Kiyi in bazaki iyaba ki bishi da addu’a domin kema kina kuskure ya za kiji Idan akayi miki hakan? Ki dena kinji.
Taka wacce jikinta yayi sanyi tace na gode aunty kuma Insha Allah bazan kara aikata hakan ba Allah ya yafemana zunubanmu minal tace Ameen.
Abincinsu ta dauko da plate biyu na ita da yazeed tareda kunun aya mai sanyi wadda tayi tun da safeta daura akan katon flate sannan ta nufi bangarensa.
Ajiye tray din tayi a parlon sa sannan ta Shiga ciki domin ta kirashi yanda ta barshi haka ta sameshi tace na kawo abincin yana parlour.
Da Hannu ya mata alamun tazo karasawa kusa dashi tayi ya miko mata Hannu alamun ta dagashi.
Gira daya ta Daga irin yadda take mata alamun Idan naki fa? Yace ‘yar kazame ai baki isaba sai kin dagni duk lomar dakikeyi karkicemin ta banza ce.
Yayi hakanne dan ya tsokaneta amma ga mamakinsa yaga tasa hannunta cikin nashi sai gashi ya mike.
Zaro ido yayi abinda bai taba yiba hakan yasa wani sihirtaccen kyawunsa ya fito cike da mamaki ya kamo dantsen hannunsa ya na lagutsawa itako ji take Kamar ana mata cakulkuli Dan haka ta soma dariya tana kokarin ta kwace.
Cikin sa’a ta kwace hannunta yazeed ya biyota yana fadin ai baki isa ba, ina kika samosa karfinnan yar kazame?kode namiji na aura ?
Haka suka dinga kewaye dakin Suna dariya kamin Daga karshe yazeed ya samu ya cafkota. Ga mamakinsa kawai sai ta rungumesa sanda ya dauki Yan sakanni ya dawo Daga shock din daya Shiga kamin shima ya kewaya hannunsa a kwankwasonta.
Babu abinda ke tashi a dakin sai sautin nufashinsu kamin minal ta datse shirun ta hangar Cewa nagode.
Yazeed yace namefa tace na Komai ma.
Shima yace nima na gode ta.turo baki tace kwaikwayona kakeyi?ya girgiza kai tace to kaima name yace nima na Komai dukanshi tayi a kirji sannan ta falfala a guje tana fadin aradu kwaikwaya na kayi.
Murmushi yayi kamin ya fito parlourn ya sameta har ta zuba plate daya zata zuba wani yayi saurin riko hannunta yace me kike shirin yi?tace abinci nake zubawa mana yace a wuri zakisa mana ta zaro ido a karo na 5 tace kana nufin tare zamuchi ? Ya Daga kai tace a ah ka……
Bata karasa Ba sakamakon pecking lips dinta da yazeed yayi yace banasin korafi zuba mana.
Zubawa tayi ta cika plate din harda tozo yazeed yace Wai mu bawa zamuci abincin ne ?tace mu biyu mana yace shine kika zuba dayawa haka sai kace mu 5 ne?
Murmushi kawai tayi ta rufe flask din .
Dauko plate din yazeed yayi yakai kan carpet yayinda yaje riko da dayan hannunta.
Masu Neman update gashinan an muku kuma sai Kiyi voting da commenting
Good morning!
Miss untichlobanty💕
4th December, 2019
Salam my brothers and sisters I am so honored and happy to tell you I now have a YouTube channel MISS UNTICHLOBANTY which I post educating and interesting videos sunfi novels Dina ma dadi.
Kindly click this link https://youtu.be/Viz4VTJWM3Q and please subscribe to my channel!
Thank you!
Janyota yayi har gaban abincin ya zaunar da ita sannan shima ya zauna itakam kallonsa kawai takeyi.
Idan tace ta taba tunanin yazeed zai zama haka to karya takeyi. Da bayan aurenta da sati daya wani ya fada mata Cewa yazeed zai zama haka da babu dalilin dazai hanata jibgarsa.
Shiko yazeed ganin ta tsareshi da ido yasa ya hura mata iska a fuska yace yar kazame ya akayi ne?ko duk Kyan nawa ne yasa ki yin muhawara da zuciyarki?
Bata rai tayi tace duk Wanda yacema kanada kyau to ya cuceka, yace zama ki fadi Gaskiya ‘Yan mata.
Plate din data rufo abincin ya bude aiko atake yaji wani irin kamshi ta doki salansar hancinsa hakan yayi sanadiyar cikinsa ta bada wani kqra kuuuuu.+
Minal ne ta kyalkyale da dariya yazeed kuma ya turo baki yadda take masa yace yar kazame banaso! Gwaliyo tamai tace nima banaso.
Spoon ya dauka ya dibi loma daya ya fara taunawa wth a straight face. Minal da ta nutsu tana jira taga reaction taga ya yatsine fuska. Take idonta ya cicciko da kwalla yazeed ko harararta yayi cikinbdaga murya yace me wannan kika Fadawa mutane.
Take hawayen dake makale a idonta ya gangaro tace kayi hakuri ni wal………
Hannu ya Daga mata yace karki wani bani hakuri ya zaki Fadawa mutane abinci Kamar abincin Yan aljanna?so kuke na suma?
Tsayawa kallonsa minal tayi baki a bude yayinda ya sheke da dariya sanda yayi mai isarsa sannan.
Yasa Hannu ya rude mata bakin yana Cewa kar kuda ya Shiga bakinki,maganin mai cemin banida kyau.
Kicin kicin tayi da ido kamin takai masa naushi ya fara tarewa yana Cewa haba yar kazame na yi hakuri,haba yar kyakkyawa.
Hararansa tayi tace kaci sa’a.
Hannu tasa ta dumbuzo loma,yazeed Wanda ke shirin fauna lomarsa ta biyu ya kware a take saboda firgicin katan loman dayaga minal takai baki sannu tace masa sannan ta bashi ruwa yasha ta dawo ta gefensa tana shafa bayansa tunda dazu fuskantar juna suke.
Bayan numfashinsa ya dawo daidai yace yar kazame kicemin bana gani daidai tace da akayi me fa yace da gaske duk wannan lomar bakinki kika sa ? Ta Daga kai yace kafci ai wannan yakai inyi loma Biyar dashi. Tya kiga miko mata cokali yayi sannan shima ya dauka.
Spoon din yasa ya Dino daidai cinsa wani Dan Nasan a baking cokali yakai bakinsa yace lesson number 2, haka kakeson ki dinga cin abinci tace kafci wannan kawai kace na mutu da yunwa Gaskiya saide in gwada maka wani Wanda yafi wannan daina gani ko yayi.
Yace gwada mu gani. Cokalin ta cika sannan yakai baki yace atleast gwara wannan.
Tace to kauna lesson 1 dazan koyama shine ka dinga cin abinci da yawa bude bakinka ta fadi hakan tana ciko cokali, yace ke wannan yamin yawa ai so like in mutu?tace Allah sai kaci Idan Ba haka Ba kuma in daina kulaka. Masa bude bakinka kamin in zaneka ta fadi hakan Kamar da Dan shekara Bihar take magana.
Yazeed badan yaso Ba haka ya bude bakinka ta dinga dura masa itama tanaci sanda suka cinye tas.
Yazeed ji take Kamar an kika sa a wurin saboda irin cikar da cikinsa tayi.
Yace Inda in kara cin wani abinci sai bayan kwana 3 ya fadi hakan yana Dan nishi.
Minal ko dariya tayi alamun kana ruwa sannan tace ai bata in kara maka labari tuwo miyan taushe zamuci anjima kallonta yayi Adan tsorace yace menene kuma wannan tace zaka ganshi.
Yace to kije ki ajiye mana wannan abun anjima sai musha tace Ba sunansa abun Ba sunanshi kunun aya yace to kunun aya.
Yace yauwa har na kusa in manta duk dare zamu dinga yin karatu dake zan koya mini karatu da rubutu kamin ki koma makaranta,ko bakyaso? Washe baki tayi tace inaso mana Nasan baba zaiji dadi sosai in yaji wannan labari kuma Nayi alkawarin in maida hankali into karatu babu wasa yace good girl give me five ta miko masa Hannu sannan suka tafa Suna masu fashewa da dariya.
Mikewa tayi yace don’t forget after each lesson sai kin min tausana fa karki dauka na manta ne and also Daga yau karki kara yin wani aiki kinji kawai ki dinga share part dina sai ki mana abinci. Murmushi tayi tace na gode sannan taje ta ajiye musu jug din kunun ayan fridge din falonsa,tunda tasha dazu da safe shiyasa bata wani damu dasha yanzuba.
Bayan ta dawo ta zauna yace toh ni zan Dan fita kinsan Jennifer ce tasa mana poison acikin cappuccino Dan haka dole in tuhumeta Inji Wanda ya sata.
Minal tace ikon Allah mutum mugun ice,Wanda ka yarda dashi shine zai sokeka a baya Allah ka rabamu ka kuma karemu Daga sharrin makiya. Yazeed yace Ameen sannan ya mike domin ya shirya koda ya shirya cikin khakinsa yayi mugun kyau ya fito a parlourn ya tadda ita tana kallon TV yace Toh yar kazame ni na wuce tace to sai ka dawo Allah ya bada sa’a.
Yace Ameen Ba rakiya ne?tace muje Toh in rakaka.
Har bakinka main kofa ta rakashi zata rude kofa yace baki jiba tace um? Yace Daga yau in zan fita zaki dinga min bye bye hug and peck kinji ?tace Nasan me hug din amma me kuma peck?
Pecking lips dinga yayi yace shine peck. Hannunsa ya ware ta rungumesa tanata Washe baki itakam yanzu babu abinda zatayi sai godiya ga Allah Dan rayuwa ta ma ta dadi Alhamdulillah.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Da fatan ka yi aikinka daidai Dan banason kuskure irin na wannan banziyar arniyar Jennifer, nasa boka cuku cuku ya kaita gidanne dab tayi min aiki amma saboda rashin kwakwalwarta gashi an kamata.
Ta dayan Abangaren wayan ne akace ma babu wata matsala Nayi Komai daidai yanzu haka nabar gidan
Tace good I will transfer your balance yace thank you ma.
Datse kiran tayi sannan ta kara dialling wani number ringing biyu aka dauka tare da fadin shedaniya uwar shedanu,muguwa uwar mugu,dakalin majina a hauki a zame kihau uban mutum ki zauna daidai. Tawa ni kadai har abada Umarninki shine farin cikina.
Murmushi tayi tace daina Sakai kenan duk yadda raina ya baci to Dana kiraka nake wartsakewa.
Ya ake ciki da batun boka cuku cukun? Yace masoyiya yanzu nabar wurinsa kuma yace an gama Jennifer ko za’a kashe kowa dake numfashi bazata iya tuna Cewa ke kika sata aikin Ba balle ta fada tace good to me yaje bukata.
Saurayin yace yana bukatar jinin bakinka Kare da raguna uku ma aljanunsa naman kuma a soye ta tayi yaji sosai sai ayi dambu da naman Karen wannan nashine tace okay zan turo maka 500k sai kayi duk abunda ake bukata. Yace an gama my love tace to sweetheart sai anjima.
Wani number ta kuma dialling sannan tace da fatan kaga balance dinka yace eh na gani tace yauwa Gaskiya aikin yayi kyau boutiques din sun none kurmus shiyasa ma na kara maka akai. Sai kayi kokari duk kayan da kuka kwashen Ku kukai min warehouse din.
Yace ai nakai tun jiya tace excellent shiyasa nakeson aiki dakai baka disappointing dina. Yace na gode ma. Datse kirar tayi tana murmushin rashin imani tace just wait and see daina rushed rayuwarku gaba daya especially yazeed da zakiyya Dan kune salsalan matsalata.2
🌹…………
Koda yazeed ya Shiga mota domin su wuce su hadu da tawagar convoy dinsu,lukman yace mutumina karka dauka ban gani ba. Yazeed yace ni kuma Allah ya sakamin tsanan Dan sa ido ba. Lukman yace to ai ba saka ido bane tunda ina wajen abin ya faru karara a vaiyane yazeed yace kaika jiyota ai shiyslasa tunda ban yarda a Shigo min compound ko securities Suna can nesa.
Amma Gaskiya mutumi na gode domin kuwa shawar da ka bani ita na dauka kuma yanzu haka in nace babu Wanda ya kaini jin dadi banyi karya ba lukman ya sheke da dariya yace anyi abin kenan?yazeed yace kaji matsalata Sakai to babu abinda ya faru. Lukman yace zama faru ai.
Gidan da aka ajiye Jennifer suka shiga. Gaba daya fuskanta ya kukkumbura ba’a ma iya gane kamarta.
5k reads no be joke ooo thank you for always supporting me!
Don’t forget to vote,share and comment
GOOD NIGHT
Miss untichlobanty💕
4th December, 2019.
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.Tana ganin YAZEED ta kara fashewa da kuka tana oga ka temakamin kayi min rai wani soja ne ya naushi bakinta. Atake hakori daya ya balle ya fado aiko jini ma yace baza’a barni a baya ba.
Yazeed ne yace let go of her if she is ready to talk. daya Daga cikin sojoji Biyar dinne ya falla mata wani lafiyaiyan mari yace zaki yi magana ? Ta Daga kai da Sauri tana Fiki Fiki da ido Kamar yar wuta Dan haka suka suncota.
Da gudu ta karaso gaban YAZEED ta rike kafarsa cikin hausanta Mara kyau tace sir Dan Allah kayimin rai karsu kasheni ka yafemin.
Hannunta yazeed ya yarbe Daga kafarsa sannan ya take ya murje ya muttsika har sanda jini ya fita yayinda Jenifer ke ihu tana fadin jusus!lord have Marcy !my hand!my hand!my hand ooo!
Alamu yazeed yayi da akawo masa kujera still kafarsa nakan hannunta amma baya murjewa.
Zama yayi sannan ya kamo bakinta ya matse hawaye ta somayi sai ka ganta abin tausayi yazeed yace wa ya sa ki zubamin poison a cikin cappuccino girgiza kai ta fara yazeed yadan kara danna kafarsa akan hannunsa hakan yasa tace waiyo zan fada!zan fada! Yazeed yace ina jinki tace madam………….
Wani abune taji yazo ya sari kanta a take ta rike kamin ta kwala ihu kaina!. Murmushi yazeed yayi ya table baki yace na hadu da criminals da suka Fiki so don’t fool around fada min!
Ya fadi haka da kakkausar murya.
Girgiza kai ta fara tace oga na manta na kasa tuna Waye I promise yanzu naji wani Abu ya sari kaina daganan kuma naji na manta wacece ita.
Yazeed yace macene kenan ?tace yes sir yace kai ayo kuyita dukanta harsai ta tuna.
Suko abinnema ya samu nan suka juya bayan bindiga suka dinga jibgar ta Kamar ba mutum bane.+
Itako sai ihu take tana fadin I promise you sir na manta I swear on my life na manta!tun tana iya magana har kaji shiru can shu’aibu yaga Kamar ta dena motsi yace Gaskiya sir wannan matar tanada taurin kai Dan koda namiji ne da yanzu yayi magana Idan ba haka ba kuma to ta manta Dan gani nake Kamar Suma tayi.
YAZEED yace lukman! Lukman yace yes sir! Dauko ruwa a mota yace angama sir!
Koda lukman ya kawo ruwa aka zuba mata shiru kakeji Dan haka yazeed yace su sata a bayan hilux dinsu a kaita asibiti Dan karta mutu bata fada ba.
Aiko haka akayi koda akaje asibiti take aka karbeta bayan 2 hours doctor Muhammad ya fito yace Mr yazeed muje office ko.
Bayan sun Shiga office din doctor yace what’s your relationship da patient din? Wai hatsari tayine ?Dan mun karbeta ne Duba da Cewa you are an authority as well amma this is a police case.
Daure fuska yazeed yayi yace ba hatsari tayiba kuma she is my house made and she is the one that poisoned me.
Dr Muhammad yace do you mean ita tayi poisoning cappuccinon ka? Yazeed yace yes. Doctorn yace this is serious because that poison is strong Gaskiya. Toh amma yanzu dai Gaskiya tanada karaya 2 a Hannu da kafa sannan dole sai an yanke mata idon hannunta na hagu Dan ya back Gaskiya before ya rube yayi affecting sauran and also she is in a coma.
Yazeed kam Dage kafada yayi yace she deserves it!any way do what you think is right and help me check her mental situation. Doctorn yace we can’t do that because her brain is not functioning anymore and that’s why she is in a coma remember? Yazeed yace oh yeah.
So yanzu zanbar 2 men dina zasuyi gadinta Doctorn yace no problem. Shaking hands su kayi sannan yazeed ya dawo gida lokacin har magrib tayi Dan haka shida lukman suka Shiga masallati direct har sanda akayi isha’i sannan suka fito.
Bayan sun fito yazeed ke cewa lukman saura week daya fa amaryarka tazo. Lukman yace matarda ka auramin dai. YAZEED yace naji aide kanasonta. Lukman yace lie lie zuciyata na ayush ne ita kadai,bakaga yadda ta dinga kuka ba sanda na fada mata yazeed yace don’t mind her zata saba sannan munanan Sakai duk ranan da kazo kacemin kanason yarinyarnan saina ma duka, suka fashe da dariya lukman yace never.
Daganan hiran ta kara saboda sun iso.
Koda yazeed ya shigo kitchen ya nufa ya zamu minal tana jute abinci ta bayanta ya rungumota tadan tsorata saura kadan miya ya zubo mata kukan shagwaba tasa tace da yanzu na kone fa? Yace sorry my yar kazame kawai Nayi missing Fiki ne amma ke da alamu bakiyi kewana ba.
STORY CONTINUES BELOW

Tace wa yace maka yace alamu na gani mana tunda ko welcome hug baki bani ba.
Juyowa tayi ta rungumeshi sannan tace to sakeni inkai wannan dinning table yace ina ai yau ni zankai tace ka barshi yace Idan baki kaeoba munyi fada bashi tayi shiko ya nufi side dinsa direct Wanda ke nuna acan zasuci abin cin.
Binsa tayi a baya tunda dama tayi wanka ta saka doguwar rigarta navy blue simple but elegant.
Koda suka Shiga side dinsa Inda sukaci dazu nan ya a jiye musu, mika masa wayarta tayi sannan taje fridge dinsa da ta ajiye kunun ayansu ta dauko ajiyewa shima tayi sannan ta bude food flask din ta zuba musu tuwo Mara uku biyu nata daya na yazeed tunda yace ta dena cin abinci dayawa.
Yazeed yace Dan Allah karkice sai Muna cinye duka tace tasa ma kuwa. Ajiyan zuciya ya sauke yau ya Shiga uku.
Ruwa ta dibo a wani roba suka wanke hannu yazeed nata complain Wai ta barshi yaci da cokali bai iya ci da Hannu ba. Tace zan koya ma karka damu. Kunun ayan ta zuba musu yayi sanyi harya fara kankara hakan yasa atake kofin su kayi gumi.
Nanfa tasa yazeed agaba hard a zare ido ta yanko katon loma tace ma za bude bakinka abin tausayi yazeed yayi tace gara ma ka gyara fuskarka Dan ban ganiba wallahi.
Nannanuyan ajiyan zuciya ya sauke yace fine na yi surrender.
Abinda bansani ba kuwa yazeed kawai aji yakeja Dan yawunsa har tsinkewa yakeyi dukda Cewa lomar da ta dauko ta masa yawa bude bakin yayi aiko ta dannan mai take ya hadiya ba bata lokaci ya kara bude wa.
Kyalkyalewa tayi da dariya tace ayi magana mutum yace kazanta ne ko ya masa yawa amma gashi muduk ya cinye lomar tuwo turo baki yayi cike da borin kunya yace ai Dan inajin yunwa ne. Tace zama ka fadi Gaskiya ne sannan suka ci gaba da cin abin cinsu Suna tsokanar juna tare da kora kunun ayansu mai sanyi.
Yazeed sanda yasha 3 cups minal ne tasha 1 acewarta sai ya Dan huce kamin tasha saboda aunty fauzy tace Abu mai sanyi yanada illa ga mace ko menene shi.
Saide abinda basu sani ba Anyi musu aika aika acikin kunun.
Bayan sun cinye yazeed yace kai inajin sai Nayi sati kamin in kara cin abinci minal tace shiyasa dazu da kaci dambu da rana ka kasa tashi baka kara cin abinci ba sai bayan sati,yace tsokanata kikeyi ko ? Kinsan halina fa. Ko ba Komai kaci kazantar kazama throw pillow ya janyo zai Willa mata ta ruga a guje tana fadin tsaya in gyara maka gado muyi tausar danni kewa baba tausa a gida dariya kawai yayi yace excuse not accepted.
Wani wayau yakeyi bashida natsalar komi sannan ya fara jin wani jiri jiri idonta ta fara nauyi kawai shi daya sai ya tsinci kansa da yin dariya mai sauti cikin alamun buguwa . Gefensa ya kalla yaga wayan minal Dan haka ya dauka yaje ya buya a bayan kujera budewa yayi yaga batasa lock bama.
Bibbiyu yake gani Dan haka cikin murya buguwa Kamar mutum yasha giya yace kai dole nema in kira Dr Muhammad yaban glasses ban gani.
Neman number din Dr Muhammad din ya fara a bayan minal yace kai Ashe ba wayata bace.
Wayarsa ya fara nema ganin bai sameta ba yace bari in kira wayar inji ta Inda zatayi ringing hannunsa yasa a aljihunsa ya zaro wayarsa yayi dialling number din da yaga tayi displaying my number aransa yace har wayar ma tasan number na. Thumbs up yayiwa iska.
Kira ya fara yi amma sai line busy akece masa, cikin zuciya yace ko Waye yake using wayana oho.
Wayan minal ya kalla yace yauwa bara inyi using wayan aunty kazame, numbarsa ya rubuta yaga babu Dan haka yayi saving yana murmushi irin ya mata aika aikannan.
Minal ko tana Shiga dakin taji Kamar jiri na dibarta amma Ba sosai Kamar na yazeed ba tunda ita bata sha dayawa ba amma sai ta basar gadon ta fara kadewa taji yazeed yana dariya parlour tace ko me ya samu yake irin wannan dariya oho.
Gadon ta gyara Wanda alokacin itama ta fara maye amma Ba worse irin na yazeed ba ctafiyatta bata canza sosai ba amma takanyi tangadi sabanin yazeed da ko tsayuwa baya iyayi.
Handle din kofan ta kama zata fito……..
Yazeed ko jin engine din kofar dakinsa tace ‘dit yasa ya kara buya yana murmushi irin ta yara yana lekowa kadan kadan shi adole kar minal ta ganshi.
Abinda be sani ba shine ba a bayan kujera ya buya ba gefene dan haka da mutum ya fito Daga dakinsa zai gansa.
Minal ko tana fitowa ta hangosa a gefen kujera yana lekenta. Ganin Kamar buya yake yasa ta Daga gira alamun confusion😕
Da shike itama kan da sauki sai ta biye masa tana Cewa maci tuwo kana ina ? Maci towo nifa ban ganka ba.
Dariya kasa kasa yazeed yayi yace wawuyace bata Hannu ba, nemansa na karya ta farayi kamin can tazo Inda yake tace na kamaka!
Dariya yayi yace kai…aunty kaza..me A…she ki…..nada wayo?
Kallonsa tayi tace kai yaronnan giya kasha?tsutsuru yayi da ido yace aun…ty ni ban…sha giya ba. Allah da gas..ke na..ke Kiji ba..kina ma haha.
Ya fadi haka yana buso mata iskar bakinsa. Kauda kai tayi tace Allah giya kasha gashi muryakka tayi ta Yan shaye shaye? Wato su murtala da babba da nake musu fada akan shaye shaye shine suka kawowa mijina Mayan maye?zanhadu dasu.
Yazeed ne yace da..ma ni mijki ne aunty ? Tace eh a bugs kake shiyasa ka manta. Mikewa ya fara kokarin yi zai fadi ta rikosa dukda ba wani karfin gareta ba tunda itama ta bugu,kofar bansani suka nufa suna tangal tangal yazeed na fadin shhshhh karki Fada..wa kowa sa..boda kema kin…sha.
Kuma kina Fadawa mamana zan Fadawa innanki zaro ido minal tayi tace bazan fada ba Dan Allah karma Fadawa inna wallahi ub*ana zata ci.
Sai alokacin ta lura da yazeed zai bige da gini Dan haka tace kai Ashe ma gini ne?ni na dauka kofar katokoce ai. Sannan ta janyoshi suka nufi daki
Dariya yazeed yayi yace amma Gaskiya kin bugu yanzu ke baki taba Sanin Cewa da Leda akayi kofar dakina ba?
Tace Kaine dai ka bugu ka manta giya kasha yace kema giya kikasha tace kaima giya kasha sai suka hada baki wajen Cewa giya muka sha! Sannan suka fashe da dariya.
Longest chapter ever🙌
Da fatan yayi cheering mood dinku saboda inaso ana tafiya ana dariya, wani wajen ayi tashin hankali,wani wajen abin dariya,wani wajen abin tausayi kunga zaifi bada colour.
DA YAZEED DA MINAL WA YAFI ABUN DARIYA A YANAYIN BUGUWA?
Ina jiran comment dinku and don’t forget to
Suna shiga daki yazeed ya fara kokarin cire riga amma ya kasa minal tace kai me hakan yace aunty sanyi nakeji ki ciremin rigana sai kimin tausan.
Minal ta fashe da dariya tace amma ka bugu dayawa kai bakasan Cewa damina akeyi yanzu Ba? Shima dariya yayi yace woooo kin fado war was yanzu lokacin zafine toh, tace Ba zafi bane yace zafine tace Ba zafi bane yace ZAFINE tace na hakura zafine amma dai ka bugu tunda Cewa kayi sanyi kakeji.
Yace kin yarda kema kin bugu tace na yarda. Rigan ta taimaka masa suka cire. Sannan ta daura hannunta a kirjinsa tace kai yaronnan aradu jikinka Nada kyau gwaliyo ya mata yace banga naki baaaa.
Tace ai nawa yafi naka kyau yace karyane tace kai auntyn ka ne take karya?kunne ya kama tare da turo baki yace sorry aunty amma dai kinsan na Fiki kyau ko? Turo baki tayi Kamar zatayi kuka tace Allah Baka fini baaaa.
Yace nafiki manaaa ki yarda kukan shagwaba ta fara sannan tace Allah Baa fini Ba tsaya fa ka gani kokarin cire Riga ta farayi amma ta kasa Neman zip din riganta tayi amma ta rasa. Tace kai so ka dubawa auntynka zip din ta.
Yace ina zanzo kuma bayan kina rike da dayan hannuna tace mantawa Nayi dubamin tana sakinshi ya tafi luu tayi Saurin rikoshi tare da zaunar dashi. Juya masa bayanta tayi ya Duba can yace naga zip din amma banga kan Ba tace ka Duba na gaji da tsuguno can yace Allah ki kama telan dayayi mini dinkinnan ki hadasa da Yan San;sama a kasa yasa miki zip dinfa.+
Tace aiko saina kasheshi yace good aunty na!yauwa ga kan nan bude zip din yayi ta cire sannan ta juyo tace ya kagani ? na fika kyau yace wannan wayone fa ni ai babu brazier a jikina.
Motsowa kusa da fuskanshi tayi cikin ra’da tace kai Dan iska ne kakeson ka kalleni babu Komai abin tausayi yazeed yayi ya girgiza kai tace good yanzu abinda za’ayi ka rakani in dauko Riga shara shara kaga sai in saka sai kaga jikina amma mutane haka zasuce ai inada Riga kaga Mun musu wayo ko?ta fada tana murmushi ita a dole ta kawo idea.
Tadawa su kayi sannan suka nufi dakinta suna ta shirme amma yazeed yanzu zai iya tafiya saide Ba control.
Koda suka shiga dakin minal din, Yazeed Idanunsa a rufe yace ina kika ajiye rigunan toh ? Kicin kicin tayi da ido tace bude idonka! Turo baki yayi yace aunty bacci tace baka isaba bude idonka. Cikin muryan kuka yace Kiyi hakuri to na bude.
Tace good amma fa a akwatina suke babu rigunan a wardrobe dina saboda bana sawa tunda Ba mai gani ko nasaka. Yazeed yace aunty to Daga yau ki fara sawa zannan gani pleaaase! Shafa kanshi tayi kaman Yaro tace angama.
Karamin store din dakinta ta bude ta janyo akwatin sannan ta bude suka kwaso duka transparent rigunan Baccin nata suka jera sannan ta dauki wani baby pink.
Bayan ta miyar da akwatin ta fito tace zan saka rigan.
Hannu yasa ya rife fuskansa kokarin cire bra dinta ta fara dakyar dai ta cire Dan sanda tayi minti 3.
Yazeed ne ya fara kokarin lekota ta tsakanin yatsansa tace wallahi kana lekoni zancewa mamanki kai Dan iska neh. Da Sauri yace na fasa karki fada please.
Saka wancan rigan tayi sannan ta dauke wanda ta cire takaishi laundry koda ta dowo yazeed ya fara gyangyadi da hannunsa a fuskarsa.
Tace tashi mu tafi in maka tausan. Komawa dakinshi su kayi ya cire wandonsa Daga shi sai short nicker ya dale tsakiyar gadon. Turo baki tayi tace to NASA rigan Baka kallah Ba. Kallon yayi sai alokacin yaga yadda tayi kyau bai San lokacin da tazo ta zauna kusa dashi Ba hannun da tasa zata rife masa baki shi ya ciroshi Daga Inda ya shiga.
Tace rife bakinka kar sauro ya shiga. Yace Gaskiya ne Aunty Ba karya kinyi kyau. Washe baki tayi tace dagaske tana Dan Daga murya yace har cikin zuciyata kuwa. Peck ta masa a kumatu sannan tace amma Gaskiya ka mtsa Dan wajennan yamin kadan yace wa yace miki Anan zaki kwana dariya ta kyalkyale dashi kamin tace ai Anyi an gamayace zamuga ni bazaki kwana Anan ba. Tace to mu kulla, suka kulla yatsa sannan ta fara masa tausan Kamar yadda takeyi wa baba amma harda mugunta aciki.
Tashi yazeed yayi ya zauna a take kamin yace haba yan mata irin wannan dannan ai ko makiyinki albarka ai saiki karyamin baya. Tausa kwata kwata babu armashi.1
Hararan shi tayi tace Toh sannu mai armashi sai ka koyamin tausa mai armashi ai ni Idan Nayi wa baba tausarnan har kyautan kudi ko goro yake bani wani sa’in shine zaka wanine Ba armashi? Yace to ai baba kikace ni kuma Ba tsoho ba ne.
Kicin kicin tayi da fuska tace kana nufin baba na tsoho ne?girgiza kai yayi yace wasa nake fa Kiyi hakuri,Tace yafi maka. Kwantar da ita yayi sannan ya fara mata tausan ajiyan zuciya ta sauke tace kai wallahi dadi yace to wannan itace tausan me armashi tashi kimin tace Dan imin na minti biyar sai in ma.
Tausan yayi mata har na minti biyar ko kasa da haka tunda ba Duba agogo yake ba,itako dadi takeyi zatayi winning Dan haka ta fara Baccin karya. Jin saukar numfashi yasa yace toh tashi saura ni yaji shiru. Yace aunty yana Dan jijjigata shiru.
Sake jijjigata yayi yace aunty ki tashi mana kimin. Bude bakinta tayi da kyar tace bacciii….
Turo baki yayi yace wannan fa ojorone fa. Tace zanmaka double gobe daganan ta bingire gaba daya kuma babu lokaci Baccin gasken ya tafi da ita.
Kwanciya yazeed yayi akan ruwan cikinta shima ya bingire haka dai suka dinga auna style din bacci kala kala musamman ma minal Dan babu lungun da batakaiwa ziyara ba akan gadon tsaban birgima.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Da safe around 8 zakiyya ta hau ta dire Cewa sai ta kira yazeed yayinda mamanta tace ta bari a sallameta mana tace lala.
Wayanta aka bata aiko ta laftowa yazeed kira……
🌹…….
Yazeed kwance minal akan kirjinsa ko sallahn asuba basuyi ba saboda kwayar dake kansu.
Wayarsa ce ta fara ringing aiko ya tashi atake saboda yadan tsorata amma sai yaji wani Abu mai nawi ya danneshi kallon kirjinsa yayi yaga minal tana bacci hankalinta kwance Dan batamasan wani Abu waishi waya ya buga ba.
Dama kunsanta da nauyin bacci a haka ma ya aka kare?
Ahankali ya dagata ya kwanta da ita akan pillow yana murmushi kamin ya tashi ya dauko wandonsa dake wulle akasa ya Ciro wayan sai alokacin ya lura da yanayin da yake sannan duk abinda ya faru na haukarsu ya dawo masa kamin ya Lula duniyar tunani wayansa ya kara ringing hakan yasa ya dauka.aiko kuka ne ya fara ma dodon kunnansa marhaban.
Yace subhanallahi zakiyya menene ya fadi haka yana zama akan gadonsa gefen minal.
Tace baby boutique dina? Yace me yafaru da boutique din tace ya kone gaba daya Wai babu abinda aka cire sabon ma an kwashe kayan ciki sannan aka rusa.
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un kawai yazeed ya iya fada kamin yace Kiyi hakuri Allah yasa haka shine mafi alkhairi bari idan kin dawo zamuyi magana sai a gyara ko? tace Toh baby saina dawo.
Yace I miss you tace me too sannan ta kashe wayarta ba ko godiya.
Wallahi banyi niyan typing ba amma danaga comment din wata Wai batayin bacci dakyau kwana biyu saboda jiran update shi yasa na fara rubutu karfe goman dare.
Oya Kiyi voting,commenting and sharing. Ahhh!wallahi na gaji ga bacci nakeji.
Saida safenku ga wadanda basuyi bacci ba.
Wanda su kayi bacci kuma good morning!😜
Karamarsu babbarau ce
Miss untichlobanty💕
9th December, 2019Juyowa yayi domin ya kalli minal dake gefensa wacce ringing din wayarsa ta biyu ta tasa aiko suka hada ido tayi Saurin rufewa Kamar mai Baccin gaske.
Yazeed yayi murmushi cikin rashin kuzari saboda har yanzu bata gama sauka Ba tunda Ba saba sha yayi ba yace na kamaki kazame kallo na kikeyi.
Blushing ta fara bada San ranta Ba kumatunta yayi jaa Kamar tumatiri kamin ta tashi ta zauna tana mai rife ido da Hannu.
Tace ina kwana ? yace lafiya amma Daga yau Ba ina kwana nakeson kice min Ba. Tace Toh me zance? Motsowa yayi ya janyota jikinshi sannan cikin kunnenta yace good morning zaki ce min sai kimin sumba.
Girgiza kai tayi tace ni kunya nakeji. Yana smirking Yace humm! Amma Idan zan iya tunawa dakyau jiya rigarki ma kika cire a gabana kuma da kiketa rife ido a haka muka kwana.
Sai alokacin minal ta tuno aiko ta zabura ta fara kokarin Jan bargo yace rabu da bargo babu laifinsa.
Turo baki tayi tace ai Dan bana hayyaci nane.
Serious face yazeed yasa ya hade gira alamun tunani sannan yace zamu tattauna akan wannan ma amma yanzu karfe nawa ne? Minal ta zaro ido tace bamuyi sallah ba!!
Aiko ta tashi da gudu ta nufi toilet.
Wankan tsarki tayi dukda babu abunda sukayi amma dai a Kore kokonto.
Fitowa tayi yace ko dauko kayanki muyi sallah Anan sannan ymshima ya Shiga.
Dauko doguwan Riga irin na shan iska tayi sannan tasaka ta zauna a bakin gado tana jiranshi yayinda ta Lula tunanin me yasa aka basu Kayan maye?kuma Waye ? Sannan taga yaya aka zuba musu?+
Tana cikin tunanin na batasan sanda yazeed ya fito Ba saiji tayi ya hura mata iska a fuska yace kazame me kike tunani? Tace zan fada ma muyi sallah tukunna.
Kabbara sukayi sannan yazeed ya fara rero karatu da zakin murya ga taushi ga tausasa zuciyan mai sauraro. Minal mamaki ya cikata sosai jin zakin murya yazeed,jikinta yayi sanyi sosai saboda yadda karatun ya tsuma ta.
Bayan sun idar sunyi addu’a sun shafa yazeed ya janyota yace my kazame ya akayi ne?turo baki tayi tace nifa banason kazamennan Dan dariya yayi yace zanyi tunani.
Tace ya yazeed wa kake ganin ya saka mana abin maye a abinci ko kunun mu?Sosa goshinsa yayi yana kara samawa minal mazauni a cinyarsa yace nuna abinda naketa nazari kenan. Minal tace ni gani nake so ake a hada tarzoma tsakanin mu kuma ko Waye meyin abunnan yasan abinda ke wakana a gidannan saboda kasan da bakacin abincina……
Pecking goshinta yayi yace kuskuren da na tabayi kuma kenan Ba. Murmushi tayi sannan taci gaba da Cewa Toh kaga kenan ni aka zubawa tunda ansan kai bakaci ko kasha Ba. Kenan Idan na bugu sai ka dauka ni yar shayshaye ce kuma Allah ne ya tons asiri na kaga kenan Daga lokacin kome akace ma akaina zaka yarda.
Zama ya gyara yana kara zurfafa tunanin akan abinda take fadan domin tana making sense. Taci gaba da Cewa kuma kenan zaka iya sakina at any moment saboda wannan.
Toshe mata baki yayi yace shhh bazan taba sakinki Ba! Inaso kiyimin alkawari ko me aka fada miki akaina bazaki rabu dani Ba kuma zaki tun tubeni kuma bazaki rabu dani Ba Komai zafi Komai wahala.
Tace Nayi yace nima na miki alkawari bazan tana zarginki Ba kuma bazan rabu dake Ba.
Rungumeta yayi ajikinsa sannan yace ya Allah ka karemu Daga Sharrin dukkan mai sharri.
Minal ne ta mike yace ina zaki?tace ina zuwa. Parlour taje aiko kalli wayar a Inda yazeed ya buya jiya. Murmushi tayi tunowa da irin haukar da suka dinga yi.
Wayan ta dauka ta dannan on button aiko yana kan contacts Inda yazeed yayi saving numbern shi Ba fita Ba.
Kokarin karanta sunane da yayi saving yayi tunda ta iya karatun Hausa na turancin ma Ba laifi zata rubuta zata karanta saide abinda ba’a rasa Ba matsala shine batasan ma’anan abinda take karantawa ko rubutawa Ba.
STORY CONTINUES BELOW

Karantawa tayi taga an rubuta yazzy baby tace Waye kuma yaz…..
Inazuwa!yazzy – yazeed , yazeed -yazzy.
Okayyy wato shiyasa jiya ya buya a gefen kujera saboda zaiyi saving number sa a wayana? Dariya tayi tace hmmm bari inje in hadu da yazzy baby a daki. Dariya ta kara fashewa dashi sannan ta nufi dakin koda taje kofa ya rufu gaba daya tunda batasan pin dinba sannan thumb print na yazeed ne zai bude sai tayi knocking yace ki shigo mana tace ai ya rufu bansan lambobin Ba. Tashi yayi ya bude meta sannan yayi wasu danne dannan shi yayce tasa thumb dinta. Sakawa tayi ya danna okay sannan yace ta kara sa’a for confirmation sawa tayi sannan ya danna green button din ma’ana OK.
A kunnan ta ya rada mata Daga yau in kinzo a kulle kawai ki daura wannan yatsan naki sai ki danna green dinnan ki kara daurawa kinji? Ta gyara kai sannan itama ta janyo kunnansa tace me yasa kake rada min kunnan ta ya kamo yace saboda kar muje akwai masu kallonmu ko jin mu. Tace ta yaya?
Yace ta na’urar camera zo muje muga abinda ya faru a kitchen a na’urar camera na.
Binsa tayi suka zauna tace yazzy baby dauko ka nunamin Toh. Kallonta yayi cikin abin tausayi yace Dan Allah ina kika sani wannan sunane ki rufamin asiri kar lukman yaji. Murmushi tayi ta hasko masa wayanta. Date kai yayi yace Allah ya tsinewa abin shaye shaye.
Dawowa tayi ta gefensa ta zauna tare da sakala hannunsa a NASA tace yazzy baby nunamin Toh.
Saman study table dinshi ya nuna mata yace dauko laptop dina a saman can. Da fatan kinsan laptop tace na sani mana. Yace ki daiyi a hankali karki fasamin Dan akwai important abubuwa akai. Daukowa tayi ta kawo masa sannan ya kuna direct na kitchen ya Shiga suka fara kalla tun daga safiyar jiya. Yaga sanda su tala sukayi su shara,can minal ta dafa abincin safe tayi su kunun ayanta har izuwa sanda ta daura abincin rana.
Bayan ta fita can sai ga wani ya Shiga yana leke don tabbatar da Cewa Ba kowa.
Direct fridge ya nufa ya bude sannan ya balli wasu capsules guda 5 ya zuba acikin wani Abu dake fridge din Wanda babu shakka kunun ayan ne tunda basu sha Komai Daga fridge dinba banda kunun ayan.
Sansadawa mutumin yayi ya fita ta back door Kamar yadda ya shigo.
Caption din gate yazeed ya Duba amma baiga fitan mutumin Ba ya Duba na suka balbabalin gidan amma babu mutumin tunda ya fita Daga kitchen yayi kwana shikenan.
YAZEED yace shit! Toh ta ina ya shigo ko ya fita. Minal tace to kodai acikin gidannan yake ? YAZEED yace ko a cikin sojojina yake da zanga ya nufi side dinsu domin canja kaya amma wannan kwanan baya yayi shikenan.
Dukda haka yazeed baiyi kasa a guiwa Ba ya kira lukman……
Ringing uku ya dauka yace ya akayine? Yazeed yace kasa sojojinnan su Duba ko ina a gidannan a tabbatar babu kowa sannan biyu su dawo ta arean back door dina Suna monitoring.
Yanda zasu iya ganin mai Shiga da fita amma bazasu iya ganin na ciki ba. Lukman yace okay sir! Amma me ya faru an sake yin wani attempt ne? Yazeed yace Idan na fito zamu tattauna. Sannan ya kashe wayarsa, minal tace kai amma nature shege ne yanzu fa Mun kalli suka balbalin gidannan Muna dakinnan. Murmushi yazeed yayi yace hakane wannan shi ake kira CCTV. Jinjina kai minal tayi sannan tace yazzy baby amma dai babu acikin gidannan ko? Kallonta cikin idonta yayi sannan ya girgiza kai yace akwai a ko’ina amma handa dakuna.
Aranshi ko yace aike har ban dakinki akwai shi.
Minal Kam ajiyan zuciya ta sauke jin yace babu a dakuna Dan tsoranta kar ace yaga duk hakan da takeyi.
Kwantar da kanta tayi tace kadan sosamin kaina Dan Allah. Core human dake kanta yayi aiko a take gashin ya zubo babu ko ribbon.
Yace nifa banason kina Karin gashi ba dole kanji yayi kaikayi ba. Dago da kanta tayi ta kalleshi sannan tace Allah ya kiyaye in saka izgan doki ko gashin roba a kaina, wannan gashi nane.
Tabawa yazeed yayi yaji laushi ga kamshin sun flower shampoo dake tashi, lumshe ido yayi sannan yace kina kudin gashinki ne wannan? Ta gyada kai hancinshi yakai yana shinshinan gashin sannan yayi pecking yace kamshi. Murmushi tayi tace kanaso ne?yace sosai ma ki daina saka hula kinji ki barmin ina gani. Gyada kai tayi sannan ta kara kwanciya ya fara Sosa mata kan a hankali sai lullumshe ido takeyi.
Can yazeed yace ina rigannan na jiya tace yanakasan wannan yace tashi ki cire wannan din.
Mikewa tayi ta core dukda tanajin kunya amma tadan fara sabawa da nuna jikinta wa yazeed.
In ka ganta sai kace yar India irin model dinnan sanda yazeed ya kare mata kallo iya son ransa itako sai kokarin gyara Rican rake Dan ko guiwa bai karasa mata ba tashi ana ganin Komai.
Kwanciya ta sake yi yaci gaba da Sosa mata kai yana mai shara bayanta a hankali a haka har bacci ya dauketa bata sani ba.
Daukanta yazeed yayi yakaita kan gado sannan shima ya hau ya kwanta a gefenta sannan ya janyota ya rufe musu kafarsu da bargo bayan ya cire jallabiyarsa.
Shidai a Gaskiya akwai wani special Abu da yakeji a zuciyarsa game da minal kuma Idan dai abinda yakeyi wa zakiyya shine so to ba son minal ya keyi ba wani Abu ne na daban shima….
Irin wannan murmushi haka ai sai bakinki yayi ciwo. Ko duk jin dadin chaptern nanne?
Anyway don’t forget to vote,comment and tell a friend to tell a friend
1 to tell 10 sukuma 10 to tell others.
Idan kika karanta ke daya kinyi son kai😜
Miss untichlobanty💕
10 December, 2019Koda ya Abubakar ya dawo daukan Laila yayi direct sai gidan aunty fauziyya sannan yace kar ta Fadawa kowa abinda ya faru Dan bayaso su fuskanci matsala Idan yace zai aureta sannan abin zai iya shafan yaransu sannan next week zai kaita asibiti domin a tabbatar babu shigan ciki.
Itakam kuka take tayi Dan abin ya fara daura mata kai Dan har yanzu bata dena bleeding ba ga irin azaba da takeji amma dai tayi deciding zata Fadawa aunty fauziyyan matsalanta tunda ita daya ne tasan abinda ya faru da ita.
Koda suka iso sallama ya Abubakar yayi. Aunty fauziyya ta fito da Sauri domin dams su take jira ta riko Laila tana mata sannu da kai kawai take amsawa. Fiki ta Shiga da ita yayinda akabar ya Abubakar a parlour.
Direct toilet ta nufa da ita sannan tace ta fara core kayanta tana zuwa bata ta sallami ya Abubakar.
Parlour ta sameshi sannan ta tambayeshi Karin bayani tunda bayani kadan ya mata a waya.
Nan ya fada mata duk abinda ya sani da abinda Laila ta fada masa. Lokacin da ya gama bayani mamaki ya cikata tana kasa magana can ta sauke ajiyan zuviya tace Allah ya rabamu da azzaluman Yan uwa da dangi ya Abubakar yace Ameen. Aunty ni zan wuce tace tsaya kasha ruwa mana yace a ah babu Komai ai ina godiya amma aunty ki tabbatar babu Wanda yaji Dan Allah tace karma damu Insha Allah babu Wanda zai sani yace na gode Allah ya saka Idan kuna bukatan wani Abu sai Ku kirani tace Toh ba matsala sannan ta rakashi koda ta dawo ta sani Laila yanda ta barta babu wani kayanta da tacire.+
Aunty fauziyya ta riko kafadan ta tace hakuri zakiyi acikin gama ya gama Koma gode Allah kin zamu mai sonki tsakani da Allah Idan ba haka ba ai Anan zaki fuskanci tashin hankali.
Acikin sheshekan kuka tace ni babu abinda ke damuna illa yadda jinin yaji ya tsaya kuma marata azaba takemin.
Shiru aunty fauziyya tayi tana nazari kamin can ta girgiza kai domin kawar da tunanin da take Dan ba Abu mai yuwuwa bane.
Ruwan zafi ta hada mata sannan tace ta Shiga ciki kuma ta tsaya akanta Dan tasan Yan Mayan yanzu ba sason ruwan zafi(Cesar tsofi)
Fire kayanta tayi amma tabar vest sannan ta Shiga ga mamakin aunty fauziyya batayi ihu ko nuna wani alamu na Cewa taji ciwo ba Kamar yadda take zubda mini. Don’t ita a tunanin ta idai har taji ciwo da yake zubda wannan jinin to ko tafiya bazata iyayi ba. Kai akwai alamar tambaya Anan wurin.
Matsowa tayi kusa da ita ta zauna sannan tace Laila tana mai riko hannunta dago da rinnanun idanunta tayi ta kalleta. Auntyn taci gaba da Cewa zan miki wani tambaya bawai Dan inaso in banbaro miki tsohon ciwo ba sai Dan in gano wani abu. Gyada kai tayi alamun tanaji.
Tace kin tabbata Cewa wani abu ya Shiga tsakaninku?gyada kai tayi har lokacin hawaye basu bar sintiri a fuskanta ba tace Kiyi min bayanin yadda Komai ya faru Dan kinsan Abubakar bazai iya min bayani a faiyace ba.
Nan Laila ta fada mata yadda goje ya mata karya har ya kaita dakinsa da irin kokuwar da sukayi har izuwa sanda ta suma sannan ko da ta farfado ga yananyin data tsinci kanta.
Jinjina kai aunty fauziyya tayi sannan tace wato kina nufin bakiji sanda ya Shiga jikinki ba har kika suma kawai dai kinji maranki ya murda? Ta gyada kai.
Sake kallonta aunty fauziyya tayi tace yaushe ki kayi al’adar ki ?shiru tayi kamin tace kwana 28 da suka wuce.
Aunty fauziyya tace bayan kwana bawa yake kewayowa? Tace hakan kewayo min bayan kwana 27 ko 29 tace kina nufin jiya ya kamata ki fara. Ta Daga kai tana mai nazari domin itama ta fara hada possibilities da aunty fauziyya ke hadawa.
Tace Idan kina al’ada kina ciwon Mara ne?ta girgiza kai alamun a ah
Aunty fauziyya tace tambaya na karshe shin kinajin wani zafi hakannan Kamar ciwo Daga ciki banda na maranki? Ta sake girgiza kai.
Murmushi aunty fauziyya tayi tace ina tunanin bayi raping dinki ba. Kallon neman Karin bayani Laila ta bita dashi tace ban tabbatar ba amma alamun sun nuna bai miki Komai ba ni a ganina kafin ya miki wani abu al’adarki tazo Dan haka dole ya rabu dake.
Atake Laila ta fito Daga ruwan daya Koma jaa Dan basu ma lura da launin ruwan yana canjawa ba.
Kusa da aunty fauziyya tazo tace toh amma me yasa Mara ta kemin ciwo? Ta fadi hakan tana mai daina zubda kwallah Dan hope ya samu.
Aunty fauziyya tace abu biyu nake tunani ko stress yakawo miki cramps din ko kuma sauyin jikinki Dan wasu Idan suka fara baya musu ciwo da sunyi shekara 18 sai ya fara cramps wasu kuma da ciwo zasu fara da sunkai 18 sai ya dena wasu kuma kwata kwata baya musu ciwo wasu kuma da ciwon zasu fara kuma ko sunkai 18 baya dainawa sai sunyi aure yake ragewa.
Jinjina kai Laila tayi tace aiko 18th birthday na is few months Away. Aunty fauziyya tace bari na kira wata kawata likita ce ta dubaki.
[Advertisements⬇️]https://googleads.g.doubleclick.net/pagead/ads?us_privacy=1—&client=ca-pub-1056799479111612&output=html&h=280&slotname=6559387577&adk=2725166265&adf=1829019582&pi=t.ma~as.6559387577&w=627&fwrn=4&fwrnh=100&lmt=1687443844&rafmt=1&format=627×280&url=https%3A%2F%2Fwww.bankinhausanovels.com.ng%2F2021%2F07%2Fkuriciyar-minal-complete.html&host=ca-host-pub-2644536267352236&fwr=0&fwrattr=true&rpe=1&resp_fmts=3&wgl=1&dt=1687443832668&bpp=100&bdt=10751&idt=1950&shv=r20230620&mjsv=m202306160901&ptt=9&saldr=aa&abxe=1&prev_fmts=0x0%2C350x100%2C627x280%2C627x280%2C627x280%2C627x280&nras=1&correlator=2452744655269&frm=20&pv=1&ga_vid=1577807978.1687443838&ga_sid=1687443842&ga_hid=547518263&ga_fc=1&u_tz=0&u_his=3&u_h=600&u_w=1000&u_ah=600&u_aw=1000&u_cd=24&u_sd=1&adx=55&ady=210419&biw=983&bih=600&scr_x=0&scr_y=1736&eid=44759876%2C44759927%2C44759837%2C31071756%2C31075412%2C31075464%2C31075473%2C44788441&oid=2&pvsid=3785175921245960&tmod=759134619&nvt=1&ref=https%3A%2F%2Fduckduckgo.com%2F&fc=1920&brdim=0%2C0%2C0%2C0%2C1000%2C0%2C1000%2C600%2C1000%2C600&vis=1&rsz=%7C%7CpEebr%7C&abl=CS&pfx=0&fu=128&bc=31&ifi=7&uci=a!7&btvi=2&fsb=1&xpc=ZRxWZyrLYv&p=https%3A//www.bankinhausanovels.com.ng&dtd=11700[Continue Reading⬇️]
Dakinta yaje ta dauko wayanta sannan ta kira kawarta ta mata bayani a takaice. Nan likitan tazo ta dubata tace babu wani abu daya sameta mensuration ne kawai. Dadi kashe laila. Painkillers ta bata sannan tace ta rage damuwa Dan shi yayi causing zuban jinin dayawa. Murmushi tayi tace Insha Allah Dan farin acikin daya lullubeta a wannan lokacin tama manta da Cewa an mata rasuwa kuma mahaifiyarta na asibiti.
Kiran ya Abubakar aunty fauziyya tayi tace yazo da gaggawa akwai abinda zata fada mishi shiko duk ya tsure karfa aje cikine da ita dukda ko da wuya a gane cikin kwana daya inba Anyi test ba.
🌹……..
Itakam auntyn Laila da ta dawo bata ganta ba bata wani damu ba ta dauka gida ta tafi. Itace ma me Dan kokarin da take zuwa tana Dan zama akan ummin nasu Dan wasu Daga cikin dangi Cewa sukema Wai bata lokacin ne su zauna akanta Dan babu abinda zai hanata mutuwa. Sai kace su suke kashewa.
Koda taga har safiya shiru babu Laila babu alamarta kawai sai ta kirawo nurse tace ta kula da ummin zataje gida tayi wanka.
Allah sarki umminsu lailai!duk abunnan da take fuskanta saboda ita daya mamanta ta Haifa kamin ta rasu wanda ake zargin tsafi akayi mata. Shiyasa kaf Yan uban babu mai sonta saboda irin kaunar da babansu ke nuna mata.
Auntyn nan ce ma suke dan Fadawa kaf gidan.
Gida ta wuce abina ta Shirya sannan ta dawo asibitin wayan lailan ta kira taji a rife kawai sai tace bari zata sake gwadawa anjima maybe network ne sannan ta zauna taci gaba da taryan kawayen Ummi Yan gaisuwa da dubiya.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Abangaren su minal kuwa ita ta fara tashi jinta kwance jikin yazeed yasata yin murmushi sannan tadan kamo sajen dake kwance a fuskansa luf luf tana wasa dashi……..
Gaskiya na gode sosai da supporting dina da kuke yi Allah ya biyaku.
Sainaji comments dinku yau bakuga yanda na dinga murmushi da ina karantawane ba Kamar wata shashasha.
Insha Allah zanyi kokari ina yi muku reply
Ya kukaga yadda na warware matsala Laila?yayi ko?4
Karamarsu babbarsu ce fa😉
Miss untichlobanty💕
11 December, 2019.Yazeed jin Kamar ana Jan gemunsa yasa yadan bude ido ya kafawa minal wacce Keta jajjan sajen nasa Dan batama lura da Cewa ya bude idonsa Ba.
Hannunsa yasa ya riko hannunta da take ja masa gemu yace kazame yau kuma da gemuna za’ayi wasa? murmushi tayi tana kifa fuskanta a faffadan kirjinsa mai dumi da sanyin kamshi.
Murmushi yayi mai Sauti yace humm ! Yar kazame taga handsome. Dago da fuskanta tayi tana mai kicin da ido tace Allah yazzy baby Idan ka Kara cemin kazame zanyi fada dakai.
Rife ido yayi yace oooo not this name again please ki daina cemin yazzy baby Wai bazaki manta bane?tace har abada kuwa. Yace haba kazame na please ki dena cemin Yazzy baby tace saide Idan zaka daina cemin kazame yace to me kikeso in dinga ce miki?kinaso in dinga ce miki beauty?kindy? Sweet? Cup cake?cutie pie? Bl……….
Datseshi tayi tace ni banaso kawai ka dinga kirana da abinda kake kiran….. Um….. Ka gane ai ta fada tana kara sa dayan hannunta dake free Wanda bai rike Ba.
Yace ah ah ni ban ganeba,tace yadda kake kiran aunty uwar gida. Dan zaro ido yayi yace kina nufin zakiyya?Daga kai tayi yaja hancin ta yace na ganoki wato kishi kikeyi.
Bata rai tayi tace ni Ba kishi nake Ba yace haba my baby Nasan fa kishina kikeyi turo baki tayi tace ni Ba kishi nakeyi Ba. Yace Toh me yasa bakya kishina ? Tace saboda me yasa zanyi kishin ka?
Yazeed’s POV
Shiru Nayi jin tambayan data aiko min don bansan yanda zan amsa mata Ba.
Bansan lokacin da bakina yace saboda kinaso.
Murmushi taci gaba dayi da alamu bata dauki abinda na fada da muhimmanci Ba. Girgiza kanta tayi sannan tace ni bana sonka kawai kai aboki nane.+
Sanda zuciyata tayi tsalle dukda Cewa nuna ban tabbatar da Cewa songs nake Ba amma da tace bata sona take zuciyana ta fara suya. Da alamu ta lura da yanayin Dana Shiga domin atake naga damuwa dauke a fuskanta saide abinda ya bani mamaki sakan gemuna da tayi saijin lallausan hannunta nayi akan kumatuna tana goge wani Abu mai ruwa. Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un kuka nakeyi.
Minal’s POV
Ni ban dauki abinda yake fada da muhimmanci Ba Dan gani nake wasa yakemin. Ya za’a yi mutum Kamar ya yazeed ga kudi, ga kyau, ga Suna,ga daukaka yace Wai sonshi nake?
A Gaskiya na kamu da dinshi Ba tare Dana Shirya Ba domin bansani ina sonsa Ba,sai ranan Dana sameshi da zakiyya a parlour Suna hadiye fuskan kuna ji Nayi Kamar na mutu boyewa kawai Nayi.
Ganin yana jiran na bashi amsa yasa na girgiza kaina cikin shiririta na nace bana Sonka kawai kai aboki nane. Mamaki tare da tashin hankaline suka kamani ganin hawaye na saukowa Daga idanunsa bansan sanda nasa hannuna na goge masa ba. Me yake shirin faruwa ? Me hakan ke nufi? Me yasa yake kuka Dan nace bana sonshi? Yana sonane?
MY POV
Yazeed ne ya rasa yanda zaiyi Wai kuka yakeyi?kardai dagaske Sonta yakeyi to amma yaushe ya fara sonta? Ganin shirun yayi yawa yasa ya hade bakinsu Ba tareda yayi Komai Ba abinda ya basa mamaki shine mayar masa da tayi Dan haka baisan lokacin daya kara zafafa lamarin Ba. Sanda yaji zasu mutu saboda rashin numfashi ya sake mata baki.
A Dan kunyace ta tashi ta fice Ba tareda suncewa juna komai Ba.
Dunkule Hannu yazeed yayi sannan ya naushi iska. He ruined everything! What if da haske take bata sonshi?yayi gaggawa wajen nuna mata abinda ke ransa even though it was not intentional. Shima bai Shirya ba, yanzu ya zaiyi ya gyara abinda ya bata.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Zaliha kam though time take bawa Yan Maiduguri Dan Cewa tayi dole a miyar da ita Kaduna. Duk masifar inna sanda ta hakura ta bada gari.
Nan aka lallaba zaliha akace tayi hakuri gobe gobe zasu dawo Kaduna amma sai ta yarda tasha tsuminta.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Ya Abubakar yana shigowa Laila ta danno da gudu ta rungumesa. Shidai baisan me ya faru ba amma ganin yadda take farin ciki kuma ta wartsake yasa yasan Cewa alkhairi ne ya faru.
Janyota yayi har suka zauna yana dariya yace aunty fadamin abinda yasa Laila na irin wannan farin ciki.
Dariyan manya aunty fauziyya tayi kamin tace kafin wannan yanzu dai ka saketa tunda ba’a daura auren ba sai a lokacin ya lura da yadda suka kankame juna cikin jin kunya Laila ta gudu ciki yayinda ya cire hula yana sosa keya.
Aunty fauziyya tace ja’irin yaro ina ganinka Kamar salihi murmushin borin kunya yafi yace ba haka bane aunty.
Tace to Nide albishirinka yace goro kuma fari kamin ma ki tambaya.
Dariya tayi tace todai in fada maka babu abinda ya Shiga tsakanin Laila da Dan iskan yaronnan.
Nan ta fada masa yadda ta gano da yadda suakyi da likita.
Godiya ya dinga yiwa Allah harda sujjada baisan sanda hawaye ya zubo masa ba. Zaunar dashi tayi akan kujera sannan ta Dafa kafadan sa tace ba kuka zakayi ba hamdalan da kayi shine dai-dai addu’a zaka cigaba dayi allah ya kareku Daga sharrin makiya yace ameen.
Kicewa lailan ta samoni a mota zamuje gidansu yazeed tace Toh sannan ta Shiga ciki.
Fita yayi ya kirawo almajirai. Nan ya dinga daba musu kudi sanda ya raba sama da 10k.
Laila da ta fito sai murmushi take har tayi wani Dan kyau hakannan. Kai kwanciyar hankali dadi gareshi.
Gaba ta Shiga ta kwame ya Abubakar ma ya Shiga driver’s sit. Belt yasa sannan ya kunna motan hannunta ya kamo ya sumbata ta warce tana turo baki yace ya akayine gimbiyata? Tace ba’afa daura auren ba kake rikeni yace astagfirullah wallahi duk cikin dadin ne ni na manta ma Allah ya yafemin tace Ameen.
Motar su suka fita Suna masu jin dadi sai gidan oga yazeed.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Abangaren su yazeed kuwa minal cikin yar iskar rigannan ta nufi kitchen kuma bilhakki da Gaskiya yunwa takeji Dan 10am ma ya wuce ko time din canja Riga batada shi.
Hamdala tayiwa Allah Dayasa akwai sauran Mara 3 a tuwonsu na jiya Dan da babu da idomie zata dafa.
Aiko nan ta daura dumame ziciyarta na wurin yazeed da yanayinda ta barshi yayinda takejinsa a jikinta.
Yazeed ko shiru yayi kawai Dan bai Masan me ya dace yayi a halin yanzu ba kawai sai ya mike ya fada wanka bai wani bata lokaci ba ya fito dai dai lokacin wayarsa ta dauki ruri dubawa yayi yaga mom ne hakan yasashi yin murmushi Dan yayi kewarta Rabon dayaji muryanta tun sanda tayi masa fada.
Dauka yayi tare da fadin my sweetheart kaif asbahati? Murmushi tayi Dan itama tayi kewan Dan nata tace lallai Abu yayi dadi tunda har ka fara manta lokaci nida nake India ne yanzu safiyata? Yace sorry sweetheart kinsan Nayi missing dinki fah.
Murmushi tayi tace abinda yasa na kiraka kenan Dan gobe ina tafe. Murmushi yayi amma saboda shekiyanci irin na yazeed yace noo!sweetheart karki dawo zaki batamin honeymoon dina.
Kama ha’ba tayi Kamar yana kallonta tace dannan kace Abun naka ya girmama ! Lokacin Dana aurama ba iskanci zaka min ba? Ta fadi hakan sounding like a drama old lady.
Dariya yazeed yayi yace Allah ya kawomin ke lafiya my sweetheart kinsan fa you are my first and last love. Mom tace first dindai amma last din kam….
Yace tunda kince haka to hakan ne. Kinji abinda ya faru da zakiyya kuwa?tace me ya faru? Yace ai………….
Nan yazeed ya kwararo mata bayani tace subhanallahi Allah ya Kare na gaba toh, yasa kuma haka shine mafi alkhairi yace Ameen. Muryan Jamal ya jiyo yana Cewa my man zan biyo mom fa Dan wallahi inaso inzo in kalli love show kyauta Ba tare da na yanki ticket ba. Mom ne ta make keyarsa yace ouch da zafi fa. Mom tace araftu(na sani).
Nan su kayi sallama yazeed nata dariya yayinda mom Keta surfawa Jamal masifa Wai a gabanta zaina mata zancen soyaiya tsabar bashida kunya.
Sorry beautiful ladies this chapter was not that long na gaji ne irin sosai dinnan ga NEPA are on strike so dole Nayi saving chaji.
Anyway, don’t forget to menene ma?yauwa comment and vote andddd share😉
Takuce karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty
12 december,2019.Bayan Kamar 2 mins wayan yazeed ta sake ringing dubawa yayi yaga mom ne yayi murmushi sannan ya dauka kamin yayi magana mom tace my son bari muyi video call koh? Kasan na Dade ban ganka Ba.
Ta cikin wayan yazeed yaji Jamal na Cewa mom anya shi kikeson ki gani ?mom tace Allah zanci gidanku Jamal, izhab ila sallajah wa hadirny alhaleeb wal kaub minal matbakh
“إذهب الى الثلاجة و حضرنى الحليب والكوب من المطبخ”
“Go to the fridge and bring me some milk and cup from the kitchen.”
Dauko laptop dinshi yazeed yayi sannan ya kunna nan yaga mom tana kiransa ya dauka murmushi ya fara sheko mata tare da sauke ajiyan zuciya domin wani dadi yaji sosai daya ganta dukda ko Ba a zahiri bane.
Yace wow! my sweetheart kinga farin da kikayi kuwa?kin kara kyau! Turo baki yayi yace Gaskiya nima zan biyoki.
Mom tace dubaka kai baka kalli kanka bane ji yadda kayi ‘kiba kayi fari har kumatu ka ajiye da Anyi magana kace “ni banasonta Gaskiya tayi yarinya” ta fadi haka tana kwaikwayon yadda yazeed din keyi.
Bata fuska yayi Kamar yadda yara keyi Idan aka bata musu rai yace ni Nayi fishi ma kuma banyi missing dinki Ba.
Tace naji dama nima zakin baki na maka baki nakeson gani Ba. Ina diyata take? Yace tana kitchen mana.+
Tace yi Sauri kakai inga yadda ka miyar min da ita kuma Idan naga ta rame ka Shiga iku. Yace haba momy nifa Bana zalinci kinsani so bazan zalinceta ba. Tace ai wasa nake maka kai mata mu gaisa nagani ko jikoki na Suna kan hanya.
Girgiza kai kawai yayi yana murmushi yace you will be disappointed kuwa tace wato mai hali bata fasa halinsa yazeed yace ehm gado Ba karanbani Ba. Dariya dukansu suka kyalkyale dashi dai dai lokacin yazeed ya iso kitchen.
Ajiye laptop din nasa yayi akan kitchen island din Yanda yake hasko minal sannan yayiwa mom alamun tayi shiru.
Sansadawa ya farayi dai dai lokacin kuwa minal tana rufe flask din data juye dumamenta tana wanka Hannu a sink.
Rungumeta ta baya yayi zata zabura ya matseta tareda rada mata shh nine and mom tana kallon mu.
Zaro ido tayi tana kokarin cire hannunshi tare da fadin yaushe ta dawo?rikota yayi kem yace a laptop dinane zo muje.
Daukanta yayi cidak Kamin ya juya ya nufi wajen laptop din da ita mom kam bakinta har ya fara ciwo saboda murmushin jin dadin ganin yadda taga ‘ya’yan nata. Addu’a da fata take Allah ya karesu daga Sharrin dukkan mai sharri.
Sauketa yazeed yayi tare da riko hannunta yana fadin mom ga yar taki karki kiramin Yan sanda dariya mom tayi tace Gaskiya yazeed ka iya kiwo. Irin wannan kiba da daughter tayi sai kace ana hurata da iska masha Allah tabarakallah.
Minal sai lokacin a kunyace ta gaishe da mom saboda irin yanayin data ganta da yazeed ga rigar dake jikinta sai a slow.
Hira mom ta fara janta dashi yayinda yazeed ya tafi dakin zakiyya ya fara bude drowers dinta har sanda ya samo na ribbons sannan ya dauko 5 colours sannan ya dauko comb ya taho dashi. Koda ya shigo kitchen din ya zamu minal tadan saki jiki Suna hira da mom.
Comb din daya dauko ya fara yaje mata kai shareshi tayi taci gaba da hiransu.
Baki ya fara tsoma musu yayinda yaketa fafutikan daure mata gashin dai dai lokacin Jamal yazo yana lekowa yace wow bro masha Allah matarka badai kyau Ba Allah nima yar naija zan aura.
Hararansa yazeed yayi tareda matsar da minal Daga gaban cameran yace ayi Hiran a haka. Dariya Jamal ya kyalkyale dashi yace fadi Lanka tsaye kishi kake. yazeed yace ai bisa hakkina nakeyi.
Mom tace kai Jamal banson iskanci me yakai idonta kan matarsa nan dai sukayi sallama.
Yazeed ya kalli minal yace baby me kika Daga mana ne ?yunwa nakeji tace dumamen tuwo ne. Yamutsa fuska yayi yace dumamen tuwo kuma ? Tace eh yace please ki mana wani Abu mana tace anjima zan maka sounding serious dole yazeed ya bada gari. Zama su kayi akan island tasa Hannu ta fara fita masa tuwo. Mayan loma take tura masa yace na koshi, hararan sa tayi irin yadda kiyaye keyiwa yaransu Idan sunki cin abinci shiru yayi taci gaba dashi. Mutumin ka kan ace me ya lunkume Mara daya. Wasa wasa kan minal taci nata loman ya cinye nashi. Daga karshe ya tsoma Hannu. Bayan sun gama ci yace mata zaije asibiti Daga nan zasu fara Shirye Shirye gyara guest side na gidan ind a su lukman zasu zauna.
Har kofa ta rakashi baiyi tsammanin zatayi pecking dinshi Ba to his surprise tayi pecking lips dinsa sannan ta buya zata tafi rungumeta yayi yace please karkiyi fushi dani! Tace banyi fushi dakai Ba ai. Yace kin tabbata ?ta gyada kai.
Neme neme ya farayi tare da waige waige tace me kake nema ne? Yace matsa kiga, matsawa tayi can ganin neme nemen bazai kareba tace Wai me kake nema ne yazzy baby? Duk ta kidime saboda yadda taga yana cube cube da alamu Abu mai mahimmanci ne.
Hannu yasa ya tallafo kumatunta tare da pecking goshinta murmushi tayi yace shi nake nema tace me? Yace murmushin ki! Shi nake nema tun dazu kika daina min murmushi sai mom kika yiwa kuma ya sokeni har cikin zuciya. Ya karasa magana yana Daga saitin zuciyar sa.
Dukansa tayi tace shine duk kabi ka rudar dani na dauka ma wani abinne me muhimmanci.
Hannu yasa a kunkuminta ya janyota tare da farin murmushin ki abune me muhimmanci da tsada a gareni. Duk Wanda ya rabaki dashi zan rabashi da farin ciki sannan duk Wanda ya saki murmushi to zan faranta mai.
Hannun sa guda daya ta kamo da hannayenta biyu tace na gode sosai kuma Insha Allah nima zanyi iya kokarina wajen ganin na faranta maka.
Rungumeta juna sukayi Suna masu jin dadi yazeed ya dauko wayansa yace selfie!
Nan suka dinga watsa pictures tare da yin fuskoki iri iri abin gwanin ban sha’awa kamin yazeed ya fita badan ranshi yaso Ba.
Sorry masoyana Nasan babu yawa amma Kuyi manage.
Karku manta Ku latsa wannan star din sannan Kiyi commenting.
Love you all😘
Takuce karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
15th December, 2019.
Yazeed yana fitowa yayiwa lukman alamun ya karaso kusa sannan suka nufi guest side nan ya bashi dakuna guda uku tareda parlour yace zasu iya tarewa kan lukman ya gama gininsa tunda yaki yarda yazeed ya masa kyautan wani gida acewarsa yanason zama kusa dasu Dan haka ya siya wani gida kusa da mansion dinsu a unguwar zai gyara.
Godiya sosai lukman yayiwa yazeed Inda yazeed Kece masa Idan yanaso zai fitar dashi wajen yayi karatunsa na sojoji yace a ah yafiso ya kara karatu akan business inyaso sai ya fada kasuwanci Dan yanzu Idan kanaso kayi securing future na family dinka to ka tafi kasuwanci kawai amma aikin gwamnati kam Ba tseratar dakai zaiyi Ba.
Yazeed yace hakane nima ina tunanin Idan nakai 40 years zanyi retire in Koma business dina kaga sai ka fara Kumar min dasu kamin na iso ko? Lukman yace hakan ma yayi.
Asibiti suka nufa Inda yazeed yace bayason convoy,musa da ezikel kawai suzo su rakasu Inda ezikel shi zai tuka motan yayinda lukman da yazeed zasu zauna a baya.
Direct hospital sukayi daya ke asibitin yazeed akakai Jennifer kuma nan akakai ummi. Dakin da Ummi take suka Shiga suka samu ya Abubakar da Laila aciki.
Gaggaisawa sukayi Inda suke tambayan ya jikin Ummi ya Abubakar yace saide ace Alhamdulillah amma babu improvement. Shiru yazeed yayi domin he is planning on calling Dr mashkur wani abokinshi Wanda suka hadu a university sanadiyyar shan cuppucino.+
FLASH BACK
Yazeed ne ya shigo wani café me Suna untichlobanty cafe tareda neman sit dake gefen window ya zauna .
Waiter ne yazo yana murmushi saboda ya ganesa tunda regular customer ne yace good day sir!(barks da zuwa yallabai! )Welcome back to untichlobanty cafe! What will you like to have?(sannu da dawowa untichlobanty cafe! Me kakeson a kawo maka?)
Yazeed yace my favorite cappuccino and some pancake.(cappuccino din Dana fi da pancake)
Waiter James yace with syrup or honey? (da syrup ko Zuma?) Yazeed yace with honey(da zuma)
Tafiya waitern yayi dai dai lokacin kararrawan kofan yayi kara alamun wani ya shigo. Table din da yazeed yake zauna yace salam yazeed wace alaika assalam miko masa Hannu yayi sukayi musabaha yace my name is mashkur ahmad and I am a MBBS student yazeed yace nice to meet you. (Sunana mashkur Ahmad kuma ni dalibin karatun likitanci ne. Yazeed yace naji dadin haduwa dakai)
I am yazeed abdulmajeed Umar Army student.(ni kuma yazeed ABDULMAJEED Umar sannan ni karatun soja nakeyi.)
Mashkur yace can I sit with you yace yeah sure (zan iya zama dakai yazeed yace eh ba matsala)dai dai lokacin waiter James ya dawo da murmushi dauke a fuskansa domin ya ganesa yace welcome sir. What will you like to have? Mashkur yace my favorite cappuccino just like his.
Gyara kai waiter James yayi sannan ya juya ya tafi. Mashkur ne ya kalli yazeed yace are you from Nigeria?(kauna Dan Nigeria ne?) Yazeed ya Daga kai yace masha Allah kace kanajin Hausa yazeed yace eh. Mashkur yace that’s good to know.
Kana yawa zuwa nanne? Yazeed yace sau uku nake zuwa or hudu. Mashkur Yace wow! Nima haka ai inason cappuccino dinsu is the best shi kadai ma nake sha. Yazeed yace nima haka.
Mashkur yace we are cappuccino buddies kenan suka Dan kashe.
Mashkur yace sorry fa Mr yazeed kar kace na fiya surutu amma Gaskiya you look worried. Yazeed yace babu Komai kawai de na gaji ne Mashkur yace amma Ba haka idonta ya nuna ba. Yazeed ya Dan dara tareda Cewa ba Komai kawaide dad dina na tuna. Mashkur yace kana missing dinshi kenan ka kirasa a waya mana. Yazeed yace ya rasu ai, Idonsa cike da kwalla.
Daga kafadansa Mashkur yayi yace ai sorry buddy Allah yaji kansa. Yace Ameen dai dai lokacin aka kawo nashi cappuccino din suka sha sannan suka tafi after sin bawa juna.su phone number da address.
END OF FLASHBACK
Number din Mashkur ya kira ringing 3 ya dauka tareda fadin buddy kwana dayawa! yakake?yazeed yace lafiya amma ba lau ba.
Mashkur yace subhanallahi wani Abu ne ya samu madam din naka? Yace eh Toh hard a itama amma Koran na daban ne. Wato akwai patients har gida biyu da nakeda su and both of them are in coma.
Mashkur yace subhanallah ya akayi haka yazeed yace sai ka iso dai kawai na turo maka kudin enough please kazo nan if possible gone ma kazo. Mashkur yace right away kuwa Kazan ma na Dade banzo kasar ba tunda Nazi bikinka da madam zakiyya. Dan Sosa kai yazeed yayi cikin jin kunyan rashin kyautawan da yayi yace sorry buddy na manta ban gaiyaceka second marriage dina ba.
Mashkur yace wow!kanason kacemin ka kara aure YAZEED yace yeah. Mashkur yace congrats man! Idan Nazo zanci girkin Amarya kenan hope ta iya traditional food?
Yazeed yace sosai ma kuwa,Mashkur yace kace Idan nazo zansha labari. Yazeed yace Gaskiya kam har sai ka gaji. Nan suka danyi hira kamin Daga baya sukayi sallama.
Wajen Dr Muhammad yazeed yaje sannan ya bashi update akan yadda yayi da Dr Mashkur Dr Muhammad yace hakan ma yayi domin shi din babban likita ne an sanshi sosai ai.
Sallama sukayi kamin yazeed ya nufi office dukda yana yin aikinsa a gida amma sai yad’an Duba saboda abinda ba’a rasa ba.
Bayan Anyi asr yazeed yacewa lukman ya nemo musu abinci a favorite restaurant dinshi saboda ya yadda dasu kuma ya Dade baici abincinsu ba saboda ba zuwa office yaje ba kuma dams ba wani son cin abinci yake ba. Koda aka kawo yazeed kasa ci yayi domin ji yayi ba dadi ba dandano kwata kwata. Haka ya hakura yabar lukman yana fafatawa.
Koda suka dawo gida magrib yayi Dan haka suka tsaya har akayi isha’i ya Shigo gida yanajin yunwa sosai saboda ya kasa cin abincin dazu.
Zama yayi akan three sister tare da kwalawa minal kira.
Baby!baby sweetheart!! Kina inane?
Finally! Toh fans na gode da support dinku 7k reads ba wasa ba.
Don’t forget to vote and comment.
Love you😘
Your karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
16th December, 2019.Saukowa minal tayi cikin navy blue Arabian gown. Murmushi take sakewa yazeed harta iso Inda yake zaune ta tsuguna tareda fadin sannu da zuwa sannan ta dauki office bag dinshi zata juya tana fadin zo muje kasha ruwa ka Shirya ko bak…..? bata karasa Ba yazeed ya finciko ta ta fado jikinsa turo baki tayi tareda fadin kaga ka batamin kwalliyata ko?dariya yadanyi tareda Cewa ina kwalliyar Anan ji yadda kika lafta man baki.
Tace kana nufin banyi kyau Ba?yace wa ni na isa?irin wannan kyau dakikayi ai ko Amarya kawai dai kin tunamin da ranan dana fara ganinki. Turo baki tayi tace shine kukayita min dariya ko? Shafa bayanta yazeed ya fara tareda fadin Kiyi hakuri baby na lokacin ai bansanki Ba.
Kuka ta fara bilhakki da Gaskiya harda shessheka tace shine kuma….kuma ranan da na Shiga motarka…ka..kaci zalina a gidannan har ciwo kaji min. Serious face yasa tare da gyara zama mai kyau sannan itama ya gyarata sosai akan cinyarsa murya kasa kasa abin tausayi Kamar wani maraya yace Kiyi hakuri MINAL dina kinsan kuskure ne da Bacin rai sannan kuma da rashin sani amma Nayi miki alkawari Indai ina cikin haiyaci bazan kara cin zarafinki Ba tace kuma har lebena ka dalle Mun😭 yace na tuba please tareda hada hannaye. Hannun Nasa ta riko tare da turo baki da alamu zata fara shagwaba ne tace to na yafe maka amma da sharadi.+
Zaro ido yayi yace yafiyan ma sai an kara min sharadi?yace toh ko bakaso a yafe ne? Yace a ah Ba haka nake nufi Ba inajin wannan sharadin.
Janyo kunnansa tayi tace tashimuje daki ka Shirya sai…….
Yace ehm sai me?gyaggyara tayi ta kwala masa ihun SAI MUJE KACI SINASIR! Sannan ta diba a guje Yazeed har wani zuuut yaji a kunnansa tashi yayi hannunsa daya kan kunnansa yana fadin yau kin Shiga uku a hannuna.
Dakin ya bita ya samu tana hada masa ruwan wanka.
Ban dakin ya Shiga bayan ya ajiye jakankasa aiko tana ganinsa ta bude baki zata kwalla ihu ya hade bakinsu.
Mukut! Ta hadiye ihunta tare dayin lamoo a jikinsa. Murmushi yayi aiko ya fara mata cakulkuli. Dariya take kyalkyalawa tana bashi hakuri shima sai dariya yake mata yana fadin zaki kara min ihu a kunne?tana dariya harda hawaye take fadin ban karawa waiyo Allah cikina,kayi hakuri bazan kara Ba.
Garin shure shure ta bige makunnin shower nan ruwa ya musu sharkaf.
Dakyar yazeed ya lalumo ya kashe saboda karfin ruwan guduwa zatayi ya janyota jikinsa tareda fadin ai baki isa ki shigar min daki a haka Ba. Tace to kaima a jike kake ai yace dama ni wanka zanyi kinga sai mutu tare ko😉?
Girgiza kai tayi tace a ah fa ni iskanci na baikai nan Ba. Yazeed yace hmmm to ai sai ki jira inyi wankan in dauko miki kaya ta Daga kai alamun Toh.
Hannu yasa a ruwan tunda bata tana hada masa Ba yasanyi.
Kallonta yayi yace irin wannan sanyin ruwa haka. Tace to ai ni banga famfon ruwan zafin bane kuma famfo kawai na iya budewa ban iya aiki da sauran abubuwannan ba. Yace zo kigani Toh. Matsowa tayi nan ya gwada mata suka controls din jacuzzi din tare da aiyukansu sannan yace ga Inda zaki dinga ganin temperature din ruwan kuma ni ina wanka a 40°C. Gyara kai tayi yace good yanzu kunna Inda zai dumama ruwanda kika zuba Daga famfo.
Kunnawa tayi tana monitoring temperature din ruwan yana zuwa 40°c ta kashe yace give me five suka tafa yace my baby minal Ashe kanki yanaja. Tace ka dauka ni din wasa ce? Yace ko kadan kayanshi ya fara cirewa minal ta juya fuskannan yayi ja saboda kunya. Murmushi kawai yayi ya Shiga Ba tareda ya rufe glass dinba.
Dan karkarwa kadan yaga tanayi yace baby minal?tace na’am yace bude drawer din can ki dauko min turaren wanka na. Toh tace taje Inda ya fada mata ta fara dauko abubuwa tana shinshina har ta sami mai kamshin turare ta dauko ta dawo Inda take dazu sannan ta miko masa.
Yace kinmin nisa ai yana smirking Dan shi yasan me ya Shirya mata. Matsowa ta sakeyi tare da mikowa aiko ya cafkota ya janyota findummm! sai acikin ruwan.
STORY CONTINUES BELOW

Bata fuska tayi tana hararan yazeed yaja hancinta aiko ta fara dukansa.
Hakuri ya fara bata yana dariya. Batasan me yabi ta manya Ba sai tsintar kanta tayi tana mai core kayanta itama yazama Daga ita sai bra pant.
Ruwa ta fara watsawa yazeed tana fadin tunda so kake Nayi wanka dakai bari in haka ruwa.
Funcikota yayi shi zai bata ruwan tace waiyo Allah kayi hakuri aradu ban iya linkaya Ba. Yace me kuma linkaya?
Tace iya ruwa mana yace kina nufin swimming? Tace nima bansan sunanshi ta turanci Ba yace swimming ne. Oya say swimming tace smimming Jan kumatunta yayi yace swimming Ba smimming ba. Tace swim..ming? Yace hmm swimming. Tace swimming yace clap for your self. Tafawa tayi YAZEED yace kinason ki koyi swimming ta Daga kai yace to zan koya miki kinji ta sake Daga kai.
Nan yazeed ya fara koya mata sunayen abubuwan da yake toilet din. Sanda aka zo kan jacuzzi, kasa fada tayi Daga karshe aka barta akan jazuki.
Koda sukayi wankan yazeed ya dauko musu bathrobe guda biyu ita ya mata burgujeje saboda Ba size dinta bane dariya yazeed ya dinga mata yace muje daki inyi mana ordern couples bathrobe ko?tace menene couple kuma yace mata da miji.
Fitowa sukayi minal ta nufi dakinta ta bude wardrobe dinta tana nazarin wani kaya ya dace tasa sai ga yazeed ya shigo zuwa yayi ya fara hura mata iska a gefen wuyanta ta Dan zabura tare da fadin har kaban tsoro yace maganin mai Baron kofa a bude.
Kamo hannunta yayi ya zaunar da ita sannan ya dibi wasu kaya Daga cikin nata. Wani Riga ya miki mata me hotan lulu Katy yace tasa yana zuwa sannan ya nufi dakinshi kayanta ya jera a gefen nashi na hanging yayi hanging dinsu sannan ya dawo ya Dino Nashan iska da bacci ya zamu harta Shirya tana shirin fesa turare.
Zuwa yayi ya karba shinshina sannan ya ajiye ta kalleshi alamun lafiya girgiza kai yayi tare da fadin karki shaka wannan kisa Wanda kike sawa kullum.
Dan zaro ido tayi tace ya akayi kasan kamshin turarena ? Matsowa yayi yaja hancinta tare da fadin shinshinar ki nakeyi duk sanda kikazo kusa dani😉 gwaliyo tamai tace ai nima Nasan kamshinka yace hmm you are not as innocent as you act tace meh? yace babu.
Shafa turarenda da take shafawa tayi dama innace ta bata. Dakin yazeed suka nufa yace da fatan kin Shirya?tace na me fa? Yace muje zaki gani.
Zaunar da ita yayi a bakin gadonsa sannan yaje gaban madubi ya janyota drawer dozen din 60leaves da kwalin bairo ya dauko ya mikawa minal yana murmushi yace dazu na siyo miki wannan dashi zamu dinga yin karatu.
Karba tayi tana Washe baki tare da jin dadi ta rungume yazeed tana fadin waiyo yazzy baby na na gode yanzu nima zan iya karatu. Sakeshi tayi tare da fara tsalle a tsakiyar gadon tana fadin yay! Nima zanyi ilimi zaliha sai kin iso!zaliha sai kin iso !
Yazeed ne ya rikota tareda da fadin ke madam zaki kara Mani gado bakisan kin girma bane yar lukuta dake. Hararansa ta farayi yayinda dariyar nan ta dauke. Kicin kicin tayi da ido tareda fadin nice yar lukutar? A tsorace yazeed ya girgiza kai Kamar da haske tareda fadin Ba haka nake nufi Ba.
Tunkaroshi ta farayi Kamar zakanya yayinda yake baya yana Daga hannu alamun yayi surrender.
Ganin ta hayaiyako ta iyo kansa yasa ya arce a guje. Nan fa suka fara nuna fasaha da kwarewa wajen iya gudu. Sanda suka wargaza dakin kaf kamin minal can ta tsaya tana haki tareda fadin na hakura ka tsaya.
Zuwa wajenta yazeed yayi shima yana haki. Ruwa ya dauko musu a fridge din dakinshi sannan yace ai sai mu gyara dakin ko?minal tace Toh tana kokarin saita numfashinta.
Bayan sun gyara minal ta dauko takarda daya da bairo daya sannan ta ajiye sauran. Zama yazeed yayi tareda Cewa mu fara ko?murmushi take sake masa yace hajiya lafiya dai ko?ko bakyason karatunne?
Pillown da take boyewa a bayan ta ta fara dukan yazeed dashi tana fadin ancema na hakura ne? zaka kama ka kirani yar lukuta?dauko pillow shima yayi nan suka cigaba da jifan Muna da pillow kamin ta fara yiwa yazeed cakulkuli tana Cewa ya kaji abun? Dariya yazeed yake yana Cewa Kiyi hakuri,na tuba,bazan kara Ba,waiyo cikina,cikina fitsari nakeji.
Dariya ta fashe dashi shima yazeed din dariya yaci gaba dayi. Sanda dariyan ya lafa yazeed yace maza ki matso muyi karatu. Tace fitsarin fa? Tana dariya kasa kasa yace ai na fada ne Dan Nayi escape.
Matsowa tayi tace amma fa yunwa nakeji yace muje muci Toh Dan nima yunwan nakeji.
Abincin sukaje sukaci yazeed sai Santi yakeyi Anan yake ce mata ai bai taba cin abincin dayake mai dadi Kamar nata Ba. Sannan Gobe tayi abinci dayawa Dan su mom da Dr Mashkur zasuzo. Dadi ta dinga ji har yazeed yana mamakin yaushe suka saba har haka.
(Dan wasu matan da ance surukarsu zatazo Kamar ance mutuwanta zaizo. Wasu ma ko auren mutum basayi Idan uwarshi tana Raye sai kaji Suna “da fatan dai bashida hawan jini” Wai sirikarce hawan jini! Allah dai ya kyauta ya ganar damu amma lamarinku akwai gyara.)
Jinshi kawai takeyi Dan tasan yana cikin sinasir ne kawai. Wai bai tabacin abinci mai dadin shi Ba.
Tace yazzy baby, yace umm? Dan bakinshi ya cika da abinci. Tace wani abinci kafiso ne yace eh Toh ada dai pancake ne amma a yanzu tuwo ne.
Dariya tayi tace aiko kaci sa’a na iya pancake Dan aunty fauziyya tana sonshi sosai.
Yazeed yace Toh kimin gobe. Ma’ke kafada tayi yace please tace nope yace pleeaase! Ta sake Cewa nooo turo baki yayi Kamar zaiyi kuka tace fine zanyi. Murmushi yayi yace iye my baby kin lura da Cewa kin fara sirka English word acikin Hausa kuwa?dadi ta fara ji ya miki mata hannun hagu suka gaisa yana fadin congratulations baby! Murmushi tayi tace thank you, yace you are welcome. Shiru tayi yace my pleasure zakice ta gyada kai.
Abincinsu suka cinye cikin jin dadi sannan suka Koma daki…..
Bayan sun Shiga daki zama su kayi akan gado nan yazeed ya fara koyawa minal darasi Inda kullum zasu dinga yin vocabularies guda 20 tareda ma’anoninsu. Sannan zai dinga koya mata figure of speech.
Yayi mamaki sosai na yadda brain dinta ke daukan abubuwa saboda ta maida hankali sosai itama sai a lokacin ta gane Cewa abin Ba maida hankali ne.
Bayan sun gama karatu tayi masa tausa. Yace ta kwanta itama ya mata tace a ah ya Sosa mata kai kawai.
………………..
🌹🍀DAWN🌹🍀
Da sanyin ASUBA bayan an sallamo su zakiya Dan dole ta dage sai ta kamo hanyan dawowa gida babu yadda mahaifiyarta batayi ba amma tace Sam dole sai ta tafi.
Ayush tace haba sister Kiyi hakuri mana hijinki ya gama wartsakewa. Hararanta tayi tace ni da ke Waye babba? Ayush tace Kece zakiyya tace to ki shiryamin yarana mu tafi.
Ayush tace Toh zakiyya tace ina kudin yarda ke zamu tafi. Tace me yasa yarda ni? Zakiyya tace saboda ban gama warkewa ba kuma kema your heart is broken.
Mummy tace Toh kibar min su sahir din mana. Zakiyya tace sanda nace kar a kawo min su ba dagewa kikayi saina rikesu ba?so yanzu nima ina son abina.
Hakadai Daga karshe suka Koma gida kargi da yaji suka Shirya kaya tareda kamo hanyar Kaduna.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Kai Jamal tashi Daga baccinnan Mun kusa sauka. Hade rai yayi yace mom bacci nakeji sosai tace Toh sai ka Fadawa pilot din ai ya jira ka gama Baccin kamin mu sauka Dan Allah ni tashi.
Daidai lokacin tayan jirginsu ya Dan gwali kwalta.
Suna saukowa mom ta cire wayanta a airplane mode zata kira yazeed.
Mummy ni yunwa nakeji
Hararan Jamal din tayi tace waikai meye matsalarka ne kwana biyu uhm? Ko kaima aure kakeson in maka.
Zaro ido yayi yace nii?na shafawa kaina ruwan sanyi ki rufamin asiri…..
Tace Toh shikenan dama maganar bata tsaya ba. Yace dakata kiji mana ai Idan kikamin din ma bata baci ba.
Rankwashinsa tayi tace ja’iri zama kayi magana ni rabani da sabgar aurenku yazeed din ma ya na jare dashi?
Daidai lokacin ta kara wayanta a kunne bayan ta fara Kiran yazeed.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Koda su yazeed suka tashi sukayi sallah minal tace bari tayi tattare tattare ta daura abinci tunda Shigan safiya su mom zasuyi yazeed yace besan wannan zance ba kawai ta dawo su kwanta.
Ta buga ta raya amma yazeed yayi kunnan uwar shegu Daga karshe tazo ta kwanta a can kuryan gado tare da juya masa baya.
Sunane ya kira ta shareshi ya sake Cewa baby? Ta kauda kai tareda Jan bargo. Riko bargon yayi tareda wantsalarwa sannan ya finciko minal din fuskannan a mutuke idon shi yayi jaa Kamar bai tana dariya. Minal ko ta tsorata amma saboda taurin kai ta tsare tareda fading ni ka cikani kara matse dantsen hannunta yayi yace karkiga Muna shiru da zaman lafiya ki nemi ki Rena min hankali. Dan iskanci ana miki magana shine zaki wani juyamin baya? Bakisan yadda na tsanin hakan ba ko?
Hararansa minal tayi da alamu rants ya fara back kuma tasan Idan tayi kokarin yin magana to Mara dadi zai fito hakan yasa ta hadiye yawu dakyar tareda fadin kayi hakuri sannan ta warce hannunta tayi gaba. Yazeed Kam mamaki da Bacin rai ya hanashi aikata Komai.
Komawa bacci yayi Dan yana rasa me zaiyi ya huce.
Minal Kamar kitchen ta nufa jikinta duk yayi sanyi son ta rasa Waye ma Mara Gaskiya a cikinsu. Kawai sai ta basar tunda ta bada hakuri ta fara tunanin me zata dafa. Can ta yanke shawaran Zata dafa alale da kunun gyada Dan haka ta fara aikinta babu bata lokaci bayan ta gama ta nufi dakin yazeed domin ta Shirya Dan lokacin 7 ma yayi.
A hankali ta shiga dakin ta hangosa ya rufu har ka. Zuwa tayi taja Bargon a hankali ta bude fuskarsa taga yana bacci ya hade rai tare da cuno baki dariya ta fara yi kasa kasa kamin ta dangwali hancinsa a hankali tace mutum sai shegen kafiya.
Tashi tayi ta Shiga bandaki abinta domin tayi wanka.
Yazeed ko tun sanda ta bude masa fuska ya tashi amma sai ya shareta dukda ko ya huce amma bazai nuna mata ba.
Yana cikin Yan nazarce nazarcen sa wayarsa ta fara ringing Kamar bazai sauka ba amma ya daure ya dauko. Dubawa yayi yaga mom ne a take ya dauka take cikin muryan bacci kasa-kasa yace
Assalamu alaiki ya ummi! Gyara muryan mom tayi tace wa’alaika Assalam son yace an tashi lafiya sweetheart? Tace Alhamdulillah ya naji muryanka haka ? Yace bacci nakeyi ne. Jinjina kai tayi tace da alamu ka manta Cewa yau zan dawo ko? Dan zaro ido yayi domin ya mantan dukda ko minal ta tuna masa yau da safe. Yace hakane fa sweetheart na shafa’a ne. Yanzu zamu tasone?Dariyan manya mom tayi tace ai Mun ido ma yace subhanallah ! Sweetheart naso ace dani za’a daukoki but kamin na Shirya it will take time and I don’t wanna keep you waiting zan turo a dauko min ke. Tace ba damuwa sai Mun shigo yace okay sai kun Shigo din.
Muryan Jamal ya jiyo ta dayan ban gareb yana Cewa guy wallahi ka tanadi labarin duk abinda ya faru Dan ina zuwa zaka Samar dani. Harara yazeed yayi kamin yace mom wayan hands free yake ne? Tace uhm yace yaiwa kana ji na ko? Da wani farangan farangan din kunnanka Kamar antenna babu labari da zaka samu. Dariya suka fashe dashi kamin sukayi sallama.
Waya yazeed ya rambatsawa lukman yace yayi assigning ake a dauko mom with tight security.
Lukman yace okay amma fa Kazan in amaryata tazo bazaka na min irin haka ba ko?kira da sanyin safiya Yazeed yace wannan kai ka jiyota sannan ya kashe wayarsa. Tashi yayi yaje bakin kofar toilet daidai zaiyi knocking minal ta bude. Daure fuska yayi ya banka mata harara itama hade rai tayi ta hararesa. Ratsawa tayi zata wuce ta gefensa ya dungure mata kai. Dungure nasa tayi itama suka harari juna a tare suka wuce.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Masifa inna Keta surfawa Wai a dole zaliha tasata tafiya ba tareda ta Shiga ba ita dai zaliha ba inna bace a gabanta Mazarin yadda zatayi taga ta zauna lafiya da mijinta takeyi dukda ko babu hada makwanci dashi a agendan ta.
Tuno yadda suka dinga daukin aurensu ita da Sulaiman tayi kawai sai ta fashe da kuka inna ko salati ta rafka tareda farin lallai yarnan yanzu Daga miki fada shine zaki fashe mini da kuka sannu langai yar safara’u.
In baki min shiru ba sai kin Rena kanki a motannan Yan Moran ne suka tsaya kallon inna da zaliha ganin kallon yayi yawa yasa inna Cewa ba kaza Muke ci ba. “Min husnil islami mar’i tarkuhu mâ lâ ya’anihi” tunda dai ba dokar Allah nake rabawa balle kuce ya shafeku ai sai Kuyi abinda ke gabanku ko?
Cikin hausansu na kanurai suka ce Allah ya baka hukuri yar uwa.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Minal ko Shiryawa tayi abinta cikin lace me kyau ta shafa powder da lip gloss ta fesa tirare ta fice tana cikin saukowa Daga stairs taji Karan mota amma bata wani bada hankalinta ba ta nufi kitchen ta fara dibo abubuwan da ta dafa tana jerawa akan dinning table. Bayan ta gama ta sake hawa stair case zata Koma part din yazeed taji an narko wata ashar Wanda tunda aka haifeta bata tabajin irinsa ba. Kamin ta juyo taji an fincikota ihu ta kwalla Allah ya taimaka steps uku ta taka hakan yasa ta fadi warwas a Kasa tare dayin targade a kafa kuma dai lokacin taji wani ya dauke wani da mari Daga nan Komai yayi mata duhu.
Shin kunsan inada YOUTUBE CHANNEL KUWA? KARATUN DA NAKE KOYARWA AI BA KANTA GA LINK NAN KUYI SUBSCRIBING
https://youtu.be/Viz4VTJWM3Q2
Nasan ba yawa chapter din kuma is boring amma amin afuwa.
Gobe zan Baku new year gift.
Takuce karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
31st December,2019DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
Wani wawan mari yazeed ya sake fallawa zakiyya wacce ke dafe da kumatu cike da mamaki.
Zuciyarsa wani harbawa take domin ki yake Kamar hi aka jiwa ciwo dukda ko zakiyya matarsa ce bazai yadda da zalinci ba kuma dukda ba’ason suka a musulunci ita ta wuce Gina da irin Idan ta kasheta fa?
Masifa ya fara sarfowa Kamar makokoronsa zai fita yace haba zakiyya meye haka ? Kamar ba babba ba? Ko ance miki kishi hauka ne ? Yanzu Idan kin kashe yar mutane fa?
Idonta yayi jajir tace lallai yazeed banga laifinka ba ka sami yarinya danya yadda kakeso dole ka mareni!tukunnan ma uban Waye ya bata izinin Shiga bangarenka alhalin ban…..
Yazeed ne ya datseta ta hanyar Cewa kaji matsalar kenan Ku Daga an muku kishiya sai kuce ai Dan ba’a sanku ne ko Dan kun tsufa ko an sami yarinya wa ya mutu wa ya tashi. Ku bakwayin la’akari da Cewa ku ma canjawa mai gida kuke kuma ai dama in kida ta canja dole rawa ma ya sauya. Ki sani tun da inasonki kuma Dan na sake aurennan ba fasa sonki nayi ba. Da kike zancen wa ya bata izinin Shiga side dina, ni ba mijinta bane? Kinga ko right ta sameshi 100%.
Zakiyya tace namiji butulu,namiji ba Dan goyo bane amma ba Komai ba laifinka bane.
Ayush kam baki ta saka tana kallon ikon Allah in ta kalli yazeed dake huci Kamar zaki Daga shi sai towel sai ta kalli zakiyya dake kwalla sai kuma ta kalli minal dake kwance a kasa.+
Juyawa zakiyyan ma tayi ta bar wajen ta nufi dakin ta. Wani kallon tsana sahir ya watsawa yazeed da minal sannan yace you are a bad daddy I hate you! kasa momy na kuka sannan ya janyo hannun safwan domin subi bayan zakiyya. Wafce hannunshi yayi ya ruga da gudu ya rungume yazeed yace no! I wanna chtay wit daddy (no! I wanna stay with daddy)
Hararan safwan din sahir yayi kamin yace fuck you
Hade rai yayi yace fuck you ich a nejetiv(negative) word onyi babboys uses it.
Sahir yace I don’t care sannan yayi flipping off zuwa dakin zakiyya ayush Kamar tana kasa magana illa yaushe da YAZEED da tayi ta wucewarta part din zakiyyan izuwa room din da ta saba sauka since this is not her first time.
Kayanta ta ajiye ta sauke ajiyan zuciya kamin ta Shiga wanka bayan ta fito ta Shirya ta dauko wayanta ta fara kiran lukman amma bai dauka ba saboda yana hanyan airport.
Cilli tayi da wayar kamin tayi ruf da ciki ta fashe da kuka yanzu zakiyya da ke ta bata hope itama abubuwa sun cabe mata kai maza ba tabbas.
(kaji irinta ai wannan babban matsalan mata ne basusan me ake kira uziri da Daga kafa ba)
Abangaren minal kuwa daukanta yazeed yayi ya kaita dakinta bayan ya shafa kan safwan tare da Pecking dinshi yace yaje wurin mommy dinsu. shi kuma ya kira doctor Muhammad ya sanar dashi abinda ya faru. Bayan wasu mintina sai gashi yazo gyara akayi wa minal sannan aka bata magunguna. Dr Muhammad yace Toh yanzu zan barku da nurse zatayi mata allura. Kalmar allura ce ta fada carat a kunnen minal hakan yasa ta bude idonta war ba tareda ta Shirya ba. Hawayene ya fara sauko mata bawai Dan zafin ciwo ba sai Dan batada kafan gudu. Yazeed ne ya zauna a gefenta yace haba yar minal dina so kiji. Rungumota yayi cikin muryan kuka tace wayo zakamin ko? Girgiza kai yayi yace ni na isa ai Saide kiyimin wayo amma ke ai babu Wanda ya kaiki sense ga nutsuwa,ga tarbiyya,ga kyau,ga sanin ya kamata ko yar inna? Tace eh amma ni yar inna da baba ne. Yace Toh yar inna da baba zaki iya sakeni an gama tace me? Yace allurar. Zaro ido tayi aiko nurse ta gani tana kokarin yar da sirinjin . tace har Anyi Wai yace eh har an gama shirin kuka tayi tace dams Nasan wayo zakamin yace to ai gashi an wuce gurin ko tace emm. Yazeed yace yadai naji kin sake jikinki? nurse tace allurar danayi mata can lead to bacci though ba na bacci bane. Aiko koda ya kalli fuskan minal har tayi bacci gyara mata kwanciya yayi sannan ya fito domin ya raka Dr Muhammad dadi lokacin su mom suka shigo.
Gaisawa sukayi da Dr Muhammad mom na farin Muhammad Dan albarka zaka wuce kenan yace Insha Allah tace to ba damuwa Allah ya taimaka.
Fiki yazeed ya janyota tare da rugumeta sosai tace kai Dan sakanni kadan karka tatsemin hanji. Dariya suka fashe dashi nan suka gaggaisa mom tace ina matan naka? Yace Suna daki yanzu ma karamar ta Dan sule taji ciwo a kafa shiyasa ma kikaga Dr yazo. Mom tace subhanallahi muje in ganta. Yazeed yace ai bacci takeyi.
Jamal yace my guy ka fadi Gaskiya Baja ragawa yar mutane ko ? Sauri mom tayi ta dale sama tana farin ni kunga tafiyata yayinda yazeed ya harari Jamal yace matsalata dakai bakasan lokacin wasa ba. Jamal yace sorry abokina.
Bayan 10 minutes mom ta sauko ta sami yazeed da Jamal Suna kallo a parlour tace kai Jamal tashi muje mu karya kumallo.
Juya kanta tayi wajan da YAZEED yake zaune taga wayam tace ha’a ina kuma yayi? Jamal ma kallon wajen yayi abin Kamar tafi basuga sanda ya tashi ba balle yahau sama. Tace baki jamal yayi yace kika bibiya yaje ya damu yar mutane ne amma mu Duba jikinta zamuyi ance batada lafiya. Mom tace kaide ka Shiga uku,Ni babu ruwana.
Abinda nasu saniba kuwa mom tana fara maganan abinci yazeed ya mike da Sauri Kamar zai tashi sama ya nufi dinning ya dau plate ya ajiye a gabansa tare da rike suka da fork su mom kawai yake kira.
Mom Suna shigowa ya sauke ajiyan ajiyan zuciya mom tace yazeed?maza ara huna(me nake gani anan) Yunwarce? Daga yanda take magana zakaji tsuran mamaki a muryarta.
Washe baki yazeed yayi ba tare da yayi magana ba. Yazeed yace bari in kira su tala suyi serving mom tace bari kawai zanyi kasan a can bana motsa jiki kwata kwata.
Bude flasks din tayi taga alala tace yanzu ne gida ya zama gida. Sauko gida daya tayi sawa Jamal sannan ta saka masa sauce yayinda jamal ke fadin Gaskiya amarya ta iya reno mom kin lura da yadda wannan abin yayi kina kuwa?yazeed yace nine Abu?mom tace zaku fara kenan ko? Su kace sorry a tare. Kwalli biyu tasa a plate dinta sannan ta rude flask din Sauri yazeed yayi ya riko hannunta yace mom ban gan ganeba. Tace kamarya ?yace nifa? Tace kai me yace abincin….
Jamal Wanda ya kurbi kunu sanda ya kware yana tari yace WHAT? Abincinnan zakaci alala ne fa. Yace babu ruwanka. Mom Kamar an zuba mata ruwa a jiki ta bude ta yanko rabi’u tasaka masa.
Murmushi yayi ya karbi serving spoon din ya zaunar da ita.
Gida 4 ya zuba tunda na gwangwami ne. Mom batasan sanda cokalin ta ya fadi ba.
Adan tsorace ta taba goshin sa amma lafiya lau yake shikam jamal dama ya bar Komai ya ninke yana binsu da idanu.
Murmushi yazeed yayi yace sweetheart zauna lafiya na kalau.
Zama tayi ta fara cin abincin Adan tsorace yazeed ya cika mug dinsa da kunu sannan ya fara harba loma kan kace me ya tada alale guda 2.
Sanda ya cinye Tass ya shanye kununsa ya kalli su mom yaga Jamal ko canja position dinshi baiyiba balle yaci abincin mom ko tayi tagumi ta saki baki.
Knocking table din yayi mom sai alokacin ta lura da tagumin da tayi gira ya Daga musu alamar yadai ?
Mom ta girgiza kai yayinda Jamal yafi gaba dacin abincinsa.
Shikam yazeed alale guda 2 ya dauka ya nufi dakin minal domin ya tasheta taci abinci dukda sama allurar da akayi mata ba’a bukatan aci abinci.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
Zakiyya ko kuka take rizga sosai sahir yace ki rabu dasu momy Daga yau bazan kara kula brother safwan ba. Girgiza kai zakiyya tayi tace don’t say that kaji he is your brother I will talk to him okay? Yace Okay. But…… Tace no buts.
🌹🍀🌹🍀…………
Zaune take kan kujera ta mimmike kafafu wayanta akan kunnanta tace GET READY FOR THE NEXT PLAN….
Takuce karamarsu babbarsu miss untho…
Fans my apology bana celebrating new year so karkuce ban muku wish ba.
mzz_untichlobanty💕
1 January, 2020.
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.Make sure kunyishi ba tareda wani kuskure ba!
Ta dayan Abangaren akace yes ma.
🌹🍀
Ayush ne ta Shiga dakin zakiyya tace sister zakiyya tace yes kina bukatan wani Abu ne?
Still idonta Adan kumbure. Kamo hannun zakiyya ayush din tayi ta zaunar da ita a bakin gado tace sis nikam tunani na zauna Nayi naga Cewa tunda dai kishiyarki ta rusa miki gida nima an kwacemin saurayi why not muje mu nemi taimako.
Zakiyya tace taimako kuma? Wani irin taimako ? Gyara zama ayush tayi tace akwai wata kawata tacemin akwai wani malami aikinsa Kamar yankan wuka. Indai kikaje wajensa Toh matsalarki tazo karshe ga aikinsa babu wani tsada kuma ance…..
Zakiyya tace dakata! dakata!! dakata!!! Ke yanzu da ilminki da wayewarki zaki dinga yarda da irin abubuwannan ?kuma wa yace miki malamine? Boka ne shi babu wani malanta fakewa kawai yake a inuwar malantaka.
Yanzu ke akan abin duniya kikeson Nayi shirka? Toh bankai nan ba bari kiji tun wuri gara ki cire wannan Abu a ranki ku ko a modern way ai that is madness ba class dinki bane please! Use your sense duk macuta ne malamannan.
Ajiyan zuciya ayush ta sauke tace kuma fa Gaskiya kike fadamin da na kusa In tafka babban kuskure amma na gode da kika fada min Gaskiya Allah ya saka da alkhairi.+
Shafa kanta zakiyya tayi tace what are sisters for?Idan ban fada ma little sis dina Gaskiya ba wa zan Fadawa ? Dariya ayush tayi tace am not that little fah. Shekaru nawa ma kika bani ko 9 bai kai bafa.
Dungure kanta zakiyya tayi tace munji dai na girmekin Ashe.
Dan abin tausayi ayush Tayi tace sis Dan Allah Kuban key din motanki inaso inje in siyo wani abu. Zakiyya tace ki bayar a siyo miki mana yaushe muka iso garin ai akwai gajiya. Ayush tace abin is a little bit private kinga ne ai? Zakiyya tace okay bari in canja kaya muje tare mana nima dama inason inje shopping ayush tace yanzu fa kikace akwai hajiya ki bari gone sai mu fita ko? Zakiyya tace to kije dasu sahir mana kinsan birthday din sahir ya kusa he will be six years next month. Ayush tace nima ba dadewa zanyiba, gobe ba sai muyi Komai da Komai ba?
Zakiyya tace okay ba matsala amma karki Dade fa.
Ayush tace okay na wuce Toh saina dawo.
Fita tayi tana tafiya tadan kunna waka tana gyada kai abinta tana rausaya wa. Birki ta taka taji shiru kara takawa tayi still taji shiru ihu ta fara yi yayinda Motan ya fara kobo da ita akan titi.
Bata ankare ba motanta ya Shiga kasan wani trailer.
Mutane ne suka cika wajen makil ga hasken rana ya dallo wal bari yayi zafi Motan da ayush ke ciki bazaka dauka mutum zai fita ba saboda yanda Motan yayi raga raga ga ayush kwance agefe cikin jini atake akayi asibiti da ita.
Wayanta wani ya dauka wayar ma tayi raga raga. Cire sim din yayi yasa a wayarsa sweet sis ya gani Dan haka ya kira
Zakiyya zaune akan gado tana sulhu tsakanin sahir da safwan Cewa Idan suka raba Kansu kowa zai iya Shiga tsakanin su Wayanta yayi ringing ganin ayush ne yasa ta dauka da yar fara’arta amma labari da ya risketa shi ya gigitata tana kasa yin Komai.
Tashi tayi a zabure ta fice ta zauna dabas a parlour Kamar yar bori ta Cire wig dinma Ashe tanada gashi ba laifi rashin godiya wa Allah yasa ta yin karu ihu ta fara yi
Waiyo Allah na,na Shiga uku!YAZEED ka taimakamin yar mutane shikenan ta mutu !ta mutu waiyo ni Allah na.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Yazeed zaune a gefen minal fuskannan babu alamun wasa hannunsa rikeda takalmi. Minal ma fuskannan babu fara’a sai zunburo baki take Wai saboda dance taci abinci kamin yaje wajen mom Idan ba haka ba tasha takalmi.
Ihu suka fara jiyo sama sama yazeed ya ajiye takalmin ya nufi kofa yana farin wannan Kamar muryan zakiyya minal ma dauko sandan ta tayi tana fadin aiko itace.
STORY CONTINUES BELOW

Harara yazeed ya aika mata yace Koma ki zauna. Tace Allah sai na bika ganin Idan ya tsaya fada da ita zai bata lokaci yasa ya ficewar sa.
Zakiyya suka riska sai ihu take duk ta birkice. Durkusawa yayi a gefenta a tsorace dan bai gaba ganinta a irin yanayinnan ba yace menene? Sweetheart me ya faru? Menene?
Kuka taci gaba dayi tana farin shikenan an kashemin ita an kashemin ayush. Ta mutu ! Ta mutu
Yazeed yace what? Me ya same ta? Tana…tana asibiti trailer ya taketa.
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un ne ya kacame parlourn domin mom da Jamal ma sun fito.
Atake suka dunguma suka nufi asibiti
Koda suka isa su sahir da safwan sun jigata saboda kuka nan suka nemi Inda take akace ai har anshiga theatre da ita domin har Yan sanda sun gama aikinsu.
Zakiyya muryanta har ya fara dashewa ta fara ganin bibbiyu.
Ta zama abin tausayi idonta sun kumburo. Minal matsowa kusa da ita tayi da Dan crutches dinta ta dafa kafadarta tace Kiyi hakuri aunty zakiyya Insha Allah zata warke. Zata tashi Kiyi hakuri.
Office din likitan suka dunguma sukayi. Bayan sun shigo likitan yace ma yazeed menene alakar ka da patient ? Yace shi yayanta ne doctor din yace okay amma nikam Kamar Kaine captain yazeed ko?
Yazeed yace yeah nine Dan Allah ka fada mana halin da take ciki ajiyan zuciya ya sauke yace a Gaskiya ikon Allah ne yasa ta rayu domin kuwa a irin ciwon da taji ba’a magana yanzu de she is out of danger amma she is in coma sannan jini ya Shiga kwakwalwarta dukda Mun Cire there is possibility zata manta wasu abubuwa or zata iya samun recognition disorder.
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un shine abinda suke furtawa.
Daga kafadan yazeed minal tayi tace tace Allah ya nasu lafiya karku damu zata warke. Amma Dan Allah inada tambaya.
Kallonta sukayi dukkansu alamun sunaji tace kowa daga wani Abu ya sameshi sai a ce ya Shiga coma yanzu mutum uku Suna coma Wai coma dinnan menene.
Likitanne yace coma wani yanayi da mutum yake Shiga Wanda yayinda wani shock ya samesa ko yayi hatsari psychological issue ne which is cause by a traumatic event.
Minal gyada kai tayi bawai Dan ta gane ba. Wayar yazeed ne ya fara ringing. Dr Mashkur ke kiransa hakan yasa ya dauka tareda sallama.
Amsawa Mashkur din yayi yazeed yace harka iso kenan?Mashkur yace da izinin Allah gani a kasata kuma a garin Kaduna.
Yazeed yace masha Allah Toh gamunan zuwa saide wani hanzari ba gudu ba ka samu extra patient. Mashkur yace oh shit ! Buddy kar abin yayi yawa mana har 3 patients.
Yazeed yace aikinka ne ai so….
Mashkur yace of course what am I here for?
Sallama sukayi yazeed yace zan kawo maka surprise. Mashkur yace and explain why na jika so sad not as cheerful as you use to be.
Dafa zakiyya yazeed yayi yace sweet zamuje dauko Mashkur kinji karkisa damuwa a ranki Insha Allah zata tashi.
Riko hannun minal yazeed yayi tareda yiwa lukman ido alamun muje ko?
……………
Mashkur ne ya fito Daga departures door a airport din Inda ya hango yazeed yana Daga masa hannu.
Runguman juna sukayi sannan suka kashe. Mashkur yace buddy irin wannan kyau Wai miye sirrine?
Yazeed yace tsaya nan gauranci ya kasheka. Lukman yace koni nan da ka ganni da aurena yanzu.
Yazeed yace wannan auran maka dashi da babu ai kusan daya. Lukman yace haka kace?yazeed yace kwarai ma kuwa Idan ba haka ba gobe muga amarya a dakinta tunda an gama Komai.
Lukman yace is that a challenge? Yazeed of course is a challenge.
Shaking Hannu sukayi yazeed lukman yace challenge accepted.
Mashkur ne yace kudai gaskiya bakuda kirki yanzu ace duk kun yi aure babu gayyata? Sukace sorry man abunne yazo a murde.
Tsuguna minal tayi tace ina wuni. Sai a lokacin Mashkur ya lura da ita domin ta labe a bayan yazeed sai tsilla ido take. Yo tazo airport bata tana ganin jirgin sama ba sai a TV ko photo.
Baki Mashkur ya saka yana Kate mata kallon kamin yace Masha Allah tabarakallah.
Buddy wannan surprise din yayi kace kai ka tanadomin. Shine baka taba fadamin Kanada kanwa zukekiya irin wannan ba? Yazeed yace kai bawan Allah Dan yanzu ba wani buddy wannan da kake gani matata ce.
Mashkur yace matarka? Yace yup itace amaryar tawa ai.
Date saitin zuciyarsa yayi yace amma kaide baka kyautawa wallahi ya zakayi ta aure kyawawan to ni in auri me?
Finciko shi lukman yayi tare da yin tsaki ya dannashi a mota yace ni wuce mu tafi Dan Allah mutum sai surutu halinku daya da Jamal.
Gida suka nufa suka bawa Mashkur masauki yaci su abinci sai Santi yake yana kurba kunu. Daura minal yazeed yayi a cinyarsa sannan ya rada mata a kunne baby anjima da daddare kiyimin pancake. Murmushi tayi tace me yasa sai da daddare. Yace saboda banason kowa yaci. Ahankali sosai tace marowaci yace naji fa. Ta ai na manta Ashe kunnen aljanu gareka. Hancinta ya Dan gwala yace ke dinnan ko.
Tsaki lukman yaja yayinda Jamal yace please Ku nemi daki ka wani kakabe yar mutane a cinya yazeed yace yar mutane kuma matata ko ba haka bane baby? Daga kai tayi tana rufe fuska.
Yazeed yayi pecking dinta Mashkur Yace ni ban kalli wannan scene din ba yayindalukman yace son Allah ka bari kana sa yar mutane jin kunya.
Daukanta yayi in bridal style yace naga alamu duk kishi ke damunku sannan yayi gaba abinsa.
Laila zaune a dakin da aka kwantar da ummi tana karanta wasikar jaki yadda Komai ke faruwa cikin gaggawa har zuciyanta ya saba da damuwa yanzu ya zama normal taga hannun ummi na motsi da Sauri ta matso kusa da ita tare da dafa hannunta tana hamdala kamin ta fara fading ummi?
A hankali ummi ta bude idonta tun bata gani har Komai ya wartsake mata murmushi ta sakarwa Laila a gajiye da gudu lailan ta fice sannan ta nufi room din da doctors din jeedmar family suke domin an ware ward musamman jeedmar patients kawai ake kwantarwa.
A gaggauce doctor Muhammad yazo yayi attending ummi Inda yayi hamdala. Tambayanta yayi ko akwai wata matsala ta girgiza kai alamun babu yace ko zata iya iya tashi tayi tafiya ? Mikewa tayi da taimakon Laila jiri yadan dibeta,sannan tadan taka da alamu dai babu batun paralyse bude baki tayi tanason tace a bata ruwa. Taci dib! Ta sake gwadawa same thing hankalinta a tashe ta tunawa Dr Muhammad bazata iya magana yace wannan ba wata matsala bace within 2 months or less than that zata fara magana Insha Allah.
Kiran yazeed yayi ya sanar dashi ummie ta farka amma tayi loosing voice dinta temporarily, bazata iya magana ba.
Hamdala yazeed dake kwance akan cinyar minal yana bata labarin Mashkur yayi yace Toh ai haka akeso gamunan zuwa asibitin dama ina planning ayi transfer din Aisha cousin din zakiya zuwa hospital dinmu saboda wancan is a public hospital ba kayan aiki sosai Nasan abin gwamnati though gwamnatin mu yanzu tana kokari sosai. Doctor Muhammad yace hakane Allah dai ya taimaka shugaban kasan mu ya kuma kare beloved country Nigeria. Allah ya rabata da corruption and corrupted people yazeed yace Ameen ai aikin da muketa kokarinyi kenan kasan wani zubin ba laifin manyan bane na kasa damu dinne though ba duka aka taru aka zama daya ba kuma akwai wasu manyan Wanda suka sunada laifinsu saide gyaran Allah. Harkan tsaro ma Muna daidai kokarinmu matsala rashin hadin kai ne.
Dr Muhammad yace hakane yazeed yace bari gamunan zuwa amma zamu biya ta dayan hospital dincan sai muga yana za’ayi transfer din aishan ko? Dr yace okay.+
Kallon minal yayi wacce take kallonsa da alamu tana jiran karun bayani though ta fahimci abinda ya wakana confirmation take jira. Gyada kai yayi kamina ya mike ya zauna yana gyara gray T-shirt dinsa .
Gani yayi minal ta tsaya tana kallonsa tana murmushi yace lafiya dai ko? Matsowa tayi ta dale cinyarsa shide kallonta yake ga mamakinsa yaga ta riko fuskarsa da hannuwanta guda biyu sannan a hankali ta hade goshinsu.
Wani irin yanayi suka fara Shiga dukkansu biyu kamin ahankali minal ta rude gap din dake tsakanin bakinsu.
Firgigit yayi ya dawo Daga tunanin daya Shiga sanadin zama da minal tayi a cinyarsa tana jijjigasa cikin yanayin da yara Yan naci ke magana tana fadin yazzy baby tashi mu tafi mana tsaki yaja saboda haushin datse masa tunani da tayi.
Matso da fuskar nata ta farayi kusa dashi Kamar yadda ya gani a daydream dinsa. Goshinsu ta hada tana masa murmushi yayinda ya rufe idonsa yana jira yaji lips dinta kan nashi saide kash booo! Tace yadda yara keyi Idan zasu tsoratar da mutum kamin ta kwasa a guje.
Jagwal fuska yazeed yayi Kamar zaiyi kuka yace you are such a fool to believe that she will kiss you.
Why?why? Wai ita Komai saina koya mata ne? I should have known since from the beginning that this will happen.
Kwalla mata kira yayi yace you better hurry up ! tace yes boss yazzy baby.
Gurnani yayi yace not this name again. At least kan ba kwando bane.
Fita yayi ya sanar dasu Jamal improvement da aka samu aiko sunji dadi daganan yace su Shirya yanzu zasu fice. Mashkur yace ba Inda zani Daga isowa. Yazeed yace ai haka isa ba ka wuce kawai mu tafi. Dan dole Badan yaso ba ya tashi yana fadin Allah kamin nabar kasarnan ka samomin mata Kamar amaryarka. Hararansa yazeed yayi yace Allah ka dauke idonka akan matata. Hade Hannu Mashkur yayi yace sorry ubale (sarcastically= cikin gatse).
Dai dai lokacin minal ta fito tana fadin yazzy baby yanzu inna suka dawo kuma sunce direct asibiti zasu su Duba jikin ummi dayake Suna Dan dasawa kuma tace zata taho da mutuniyar.
Yace aiya nalama khadijatu ba dama ai kinsan mutuniyata ce sosai. Muje ko jin shiru abokan NASA basu amsa mishi ba yasa ya juyo ya kallesu aiko suka sheke da dariyar shekiyanci kamin suka hada baki wajen Cewa YAZZY BABY?😂😂😂 dariya suka kuma fashewa dashi harda rike ciki. Kicin kicin yayi da ido yana kallon minal atake ta make kafada tare da fadin ba laifina bane sabo ne.
Tsaki yaja ya hade rai kamin ya fice Dan yasan Idan bai yi taka tsantsan ba Toh haka zasuyita tsokanar shi.
Koda suka fito yazeed suka gani cikin wata farar BMW Jamal yace wannan gayen da maitar farin mota. Lukman yace mutumin fa ya hade rai. Mashkur yace ki yadda ya kwame a drivers sit yanacin magani. Kallon minal Mashkur yayi yace amarya ki taimaka mana irin wannan hade rai da angon naki yake. Hararan su tayi tace ai duk laifinku ne kamin taje tayi shigewarta gaba.
Kunnuwanta ta kama ta rike tare da fadin kayi hakuri bazan kara kiranka dashi a gabansu ba I promise kallonta yayi ya dauke kai.
Hannunsa ta riko tace haba mana angon minal yanzu bazaka iya yafemin Dan laifinnan ba?murmushi yayi ya kamo hannunta yayi kissing yace Luv ! Ai bake nake hadewa ran ba inayi ne domin Susan Cewa banason su kirani dashi only have that right. Tace Allah yace yup rungumeshi tayi tace am happy tunda ba dani kake fishi ba pecking din kumatunsa tayi yayi pecking lips dinta daban yace kiss me please! Tayi shaking kanta alaman NO yace please ! Tace no puppy eyes ya mata tace fine kallon kallo suka farayi ido cikin ido Suna matsowa a hankali da alamu sun manta a Inda suke Mashkur yayi gyara murya tare da fadin karku manta bamu bar gidan ba so is not too late zaku iya komawa ciki Ku samu daki dama ni bacci nakeji.
Daure fuska yazeed ya sake yi Kamar bashi ya gama yin abin tausayi ba kamin ya fisgi motan tare da matse totar.
Hospital din da aka kwantar da ayush sukazo inda sukabar su mom da zakiyya wadda ba abinda takeyi sai bin mutane da ido su sahir har sunyi bacci shatin hawaye bushe a fiskansu.
Mutane Keta aikawa captain yazeed da Dr Mashkur gaisuwa domin ko banza a jarida ka taba ganin su.
Koda suka Sanar da Dr bukatansu Cewa yayi akwai risk Idan akace za’ayi transfer dinta amma bara a gani zuwa gobe. Godiya su yazeed sukayi wa likitan itadai minal tana ganin Kamar ta tana ganinsa Amma sai ta basar saide hankalinta bai kwanta da irin kallon da likitan yake mata ba.
Janyo hannun yazeed tayi domin ta fada masa wani lungu suka Shiga babu kowa a wajen tace yazzy baby ni gas…… Bata karashe ba yazeed yace shhh… Na sani tun dazu kikeso in miki ba sai kinji kunyata ba. Tace me nakeson? Yace don’t act innocent I know that you wanna kiss me.(karki wani nuna ke saliha ce Nasan Cewa kinaso ki sumbace).
Hade rai tayi tace nifa ba yar iska bace yace a da kenen tace Toh Toh Toh naji ni karamar yar iska ce ban girma ba, yace wato ni na girma ko? shrugging tayi yace okay bari mu gani.
Hannunsa biyu yasa ya zagaye waist dinta kamin ya janyota jikinsa. Juyata yayi tareda daura wuyarsa a kafadarta lullumshe ido ta farayi Kamar Muna fuka hura mata iska yazeed ya farayi a kunne kamin a hankali yace ji yadda kike rufe ido yawa an kazar kudinka a bola zata mutu in anyi magana kice ke ba yar iska bace. Hardness dinsa minal taji a jikinta saboda yadda suke manne hakan yasa tasa hannu ta rike hakan yasa yazeed zare ido 😮 domin ta shammace shi gashi zata bata mai control button domin dai hakuri yakeyi.
Turewa ta fara yi tare da fadin yazzy baby Dan cire wallet dinka yana damuna jin numfashin ya fara canzuwa yasa ta juyo tana facing dinsa. Ajiyar zuciya ya sauke still da kaga fuskarsa Kazan he is shocked.
Kallonsa take alaman miye?
Hannunta ya kalla itama kalla tayi taga abinda ta rike ihu ta kwalla tareda rungumeshi Kam tare da fadin waiyo Allah na! Yi hakuri wallahi ban sani bane. Shafa bayanta yayi yace calm down ba Komai ai baki sani ba kuma ai ba laifi kikayi ba😜
Loud Applause sukaji a bayansu harda husur ba shiri yazeed ya saketa don shi ya fara Shiga wani yanayi na daban.
No dogon talk talk just don’t forget to vote,comment and share shikenan.
Kai amma tsayafa Wai Waye ma a bayansu su yazeed din tukunna?4
Takuce karamarsu babbarsu
Miss untichlobanty💕
9th January, 2020Cikin jin kunya minal ta gudu ta Koma ciki yayinda yazeed ya tsare kamar ba abinda ya faru ya nufo inda su Jamal suke. Mashkur yace ai bansani akwai free cinema a Nigeria ba, suka yazeed yakai masa yace Allah ka fita Daga idona in rufe.
Dariya suka fashe dashi yazeed yace dallah malamai Ku wuce muje ! Wani dariyar suka kuma fashewa dashi yarda buga kafa.
Tsaki yaja ya Koma ciki domin kiram su mom.
Tattarawa suka farayi domin wucewa FIRST CLASS MULTI SPECIALIST HOSPITAL Inda zakiyya ta damka amanar yaranta a hannun minal sannan ita ta zauna domin ta kula da ayush.
Dakyar suka samu suka Shiga dakin da ummi take saboda tsabar yadda Yan dubiya suka cika corridor din Suna Shiga aka fara gaggaisawa. Inna na fading tayi kewa yazeed da yanda yake shanye mata zobo.
Ummi kam sai murmushi takeyi domin taji dadin ganin iyalinta da abokan arziki cikin farin ciki.
Yazeed ne ya fara Jan rigar Laila wacce Keta dariya saboda jokes din da minal keyi.
Da Hannu ta mai alamar miye? Ba tare da ta bari kowa ya gani ba Dan ta fahimci bayason aji
Alamu ya mata da ta dauki wayarta zai mata sms.
Message ya tura mata a take ta bude taga an rubuta sako Kamar haka
Yazeed: ke ina matan gayennan?
Laila: wanne fa?
Yazeed: lukman mana
Laila:oh zaliha kake nufi ai ta fita siyo abinci ne Dan acici ce Kamar matarka.
Harararta yayi afili tayi masa alamun ko karya Nayi?
Numban minal yayi joining ya zamto su uku zasu iya message
Yazeed:baby kinji me Laila ke fadi kuwa.
Wayar minal ce tayi haske Dan haka ta Duba reply tayi
Minal:me take Cewa?
Yazeed: Wai keda kawarki acici ne
Minal:😮kut shiyasa tun da bama shiri saboda rashin kunyarta.
Laila: ke kuma kin fiya son girma ba.
Minal:ban girmeki bane?
Laila amma ai ‘ya’yanki zan aura kinga kokirana yaya dole😜
Minal: typing…..
Yazeed:Inda mijinki Waye babba?
Laila : Kaine
Yazeed: Toh ta girmeku ke da mijin naki.
Minal: I love you..
Laila left
Yazeed:what?!
Minal : yes
Yazeed: ni bana sonki ai yanzu
Minal: typing……
Minal: typing……
Minal: typing……
Yazeed:what are you typing ne?
Minal: zansha ruwa
Yazeed: seriously?
Daga kai yayi ya kalleta yaga hawaye nabin fiskarta zaro ido yayi domin shi wasa yakeyi. Dan yasan irin son da yake mata.
Daidai lokacin wayan lukman ya fara ringing fita yayi tare da dauka….
Da gudu minal ta fice ganin yazeed na kokarin zuwa kusa da ita.
Kallo kowa ya bisu dashi kamin suka table baki tare da ci gaba da huldodin gabansu sha’anin mata da miji ka Shiga kaji kunya.
Lukman na Daga wayan yace salam
Yorubanci yaji an fara masa nan yayi bayanin Cewa wrong number ne sannan ya kashe wayarsa zai juya ya Koma kenan ya hango zaliha tana tunkaro ward din ita da wani saurayi kuma zalihan tana dariya baisan sanda kafunshi suka nufosu ba ya danki kwalar saurayinnan ya surface masa mari tau kake ji take yayi adungure sallar mage bakinsa ya fashe da Sauri zaliha ta hankadeshi tare da farin miye haka ? Ya Daga ganin mutum zaka hau dukansa?
Saurayin na mikewa yasan Inda dare yamai yayinda zaliha taci gaba da farin ai bansan tababbe aka aura min ba fincikota yayi zuwa wani daki a ICU din dakin babu kowa. Huci yake Kamar zaki yace nine mahaukaci ko ? To bari kiga belt ya fara cirowa tace wallahi kasa ka sake ka tana zalihatu inba rainin hankali ba Daga ganina dashi zaka wani rufesa da duka Toh mai Saida recharge card ne dariya yayi yace wow what an awesome story shiyasa naga har murmushi kuke mai.
Dariyan itama tayi tace fadi kanka tsaye kace kishi ke damunka ba ka tsaya kana nuku nuku ba
Tsaki yaja tare da fadin kishin wa ? Allah ya tsareni yo ni me zanyi dake wani Abu Kamar an goge bayan tukunya, yo ke anace miki bakar mace wani Kyan gareta da har zanyi kishinki ? Naga dai kina nema ki tsallake min igiyar aure Kiyi wani abin ne Idan bakisan darajarta ba ni na sani.
Ashar ta danno tace me kake nufi kana nufin ni yar iska ce. Tabee baki yayi yace wa ya sani Abu a duhu a bakin Leda?
Kwalarsa ta riko idonta ya cicciko da hawaye tace ni ? Ni kake kira da yar iska? Ni zaliha ?
Hankadeta yayi aiko suka tafi tare.
🌹🍀🌹🍀……………
Yazeed ko yana fitowa ya janyo minal jikinsa yace menene? Kokarin turesa ta fara yi tare da fadin kasake ni tunda baka so na.
Kuka ta fara masa Kamar yarinya yace shhhh Kiyi shiru Kiyi hakuri wasa nake miki Allah ina sonki wallahi Allah ina sonki ki dena kuka yana tana mina zuciya na gaba tawan gaba amaryar yazeed murmushi tayi kamin ta soma sana’ar shagwaba
Turo bakin tayi tace aini Nayi fishi ma tunda sanda ka sani kuka tukun kace kana sona.
Yazeed being a drama king ya taba zuciyarsa tare da fadin my chest wallahi karki kara Cewa baki sona. Gwaliyo tamai yaja hancinta suka fashe da dariya tare da rungume juna cikin farin ciki da kauna juna.
(Su o’o andauka ya Kare Toh da saura)
Daidai lokacin suka hango lukman yana janyo zaliha kamin ya wulla ta adaki.
Da Sauri suka karasa bakin dakin amma nasu Shiga ba tunda ba sha’aninsu bane sunjene ma ganin yanda gaba daya lukman din ya canja Kamar kace hi ya kasheka duk idonta yayi jaaa jijiyoyin kansa sun tashi.
Sunji duk abinda suka fada minal na tsaye a gaba yayinda yazeed ke rungume da ita ta baya hakan yasa ya fara mata magana a rada
Baby dole fa mu Shirya aminanmu kinga dai yadda suke fada. Gyada kai tayi suka cigaba da lekensu dai dai lokacin su zalihan suka fadi murmushi yazeed ya sakarwa minal tare da pecking gefen wuyanta.
Kallon kallo su lukman suka tsayayi kamin zaliha yaja tsaki ta hankadeshi tare da fadin dalla malan Daga ni.
Tashi yayi cikin borin kunya yace sekace wani abar zanji a kashinnan. Murkuda baki tayi tace a hakan dai aka danneni aikin banza dadai lokacin lukman ya lura dasu yazeed Dan shi yake facing kofa hakan yasa ya janyota ya rungume ta kam yana shinshinanta Kamar romance suke Dan a tunaninshi lokacin su yazeed suka zo ganin zata kwace yasa ya kara kankameta abinda be saniba kuwa zaliha wani Yan ayi ta fara Shiga saboda margin sha’awarta Dan har tafi minal dukda minal dinma ba’a barta a bata ba.
A kunnenta ya rada mata su yazeed Suna kallon mu so act.
Jikinta ya sake Dan haka ta kasa reacting ma balle ta masa taurin kai ko ta bijire.
Sakan jikinta tayi tare da kamo fuskarsa ta fara kokarin sunbatarsa Dan tama manta Waye a wajen.
Minal ne ta kwalka ihu a take suka zabura hard a yazeed Wanda ya shagala da kamshin jikin minal din.
Yace minene? Tace cinnaka ne ta cijeni janyeta yayi suka bar wajen Inda aka bar zaliha da borin kunya tsaki taja tare da fadin Dan iska kawai biyota yayi ta fice a guje yace zan kamaki yar renin hankali kuma tare zamu tafi gida.
Juyowa tayi tace me ? Yace kwarai tace kana nufin yau zan tare yace tarewan ma taci ub*nsa daganan sai gidana kimaji da Wai.
Tattarowa sukayi suka Koma gida bayan sunyiwa su ummi sallama mom sai dadin ganin yanda yazeed dinta ya canja take. Ya Koma ainihin yazeed dinsa me faran faran kamin rasuwar dad dinsa.
Inna ko sai tsiya takewa su luku wai daga ganin nina sun kasa nakuru a tare ma su zasu tare. Sai dariya ake kamin aka rabu.
Godiya dubu ga dunbin masoya na da kuma masu sharing littafinnan Allah ya saka muku
Wannan page na sadaukar dashi ga fans dina baki daya
Ina kaunarku sosai! Takuce karamarsu babbarsu.
Miss untichlobanty💕
12 January, 2020Koda suka shigo gidan zaliha na kokarin fita Daga motan luku ya riko hannunta kyam wani yar sukaji amma bai saka ba saima harara daya banka mata. Kiciniyar takeson masa ya mata rikon maza mom Suna fita ya zama saura su biyu ya lafta lock. Wancalar da hannunta yayi yace Menene ma wannan tsiyar hannun naki Kamar muruci? Tsaki taja tareda fadin dalla malam budemin mota na fita.
Banson wulakanci baza’a kwana a gidan naka ba ana dole ne?
Take motar yayi Wanda yayi sanadiyyar da yasa zaliha fasa baki tare da Kwandale kai a window kicin kicin tayi da ido kamin tace kane bala’i na rantse da Girman wallahi Bashi Idan ba saina rama ba me nake.
Daidai lokacin suka iso Dan haka ya fice yana fito kallon part dinsu zaliha ta tsaya yi ba karya ya hadu. Ko nasu minal saide ya Nuna musu girma da tsadan kayan furniture amma saboda hali irin nata tabe Baki tayi tare da fadin saboda wannan tsiyar gidan aka raboni Dana iyayena.
Shrugging yayi yace Aike rayuwarki tsiya tsiya ne iyayenki ne kawai na arziki.
Tsabar tsiya sadakarki aka bani kuma na kawoki matsiyacin gida zaki kare matsiyacin rayuwarki acikinsa tareda matsiyacin mijinki. Ya fadi hakan yana mai mata murmushi.
Iya shaka kam ta shaka kuka ta fara tare da fadin Allah ya isa na nikam an cuceni wallahi da aurenka gara Lauren kolo. Wannanta wuce bazar bazar ta mangajeshi ta fada wani Daki yace jeki dama nanne dakinki. Leka dakin yayi ya ganta kwance kan gado tana kuka yace my wife dagowa tayi tana aiko masa wani harara kiss yayi blowing Mata tare da cewa kayanki na wardrobe ayi kuka lafiya sannan ya fashe da dariya. Tasowa tayi kamar zakanya. Yayi saurin rufe Mata kofa dadai zai fita daga side dinsu yaga minal tana shirin shigowa hannunta rike da sahir da safwan….+
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Su minal suna Shiga gidan su suka labe suna kallon abinda su zaliha keyi dafe kai yazeed yayi yace gosh wai ace bazasu taba yin shiri ba ? Dole ne mu hada kansu. Miko Mata hannu yayi yace plan karba tayi sukayi musabaha tace yes plan.
Daughter! Daughter! Mom ke kwalawa minal Kira tana fadin zoo ki tayani kunce kayana in baki tsarabarki. Zata tafi yazeed yayi saurin rokita kamin tace mom zatazo anjima yanzu ina bukatar matata.
Lekowa tayi ta sama tace iyeeee mai mata manya. Umm Nide kada ka riketa dayawa yafi awa daya Dan yunwa mukeji kuma abincinta mukeso. Zaro ido yayi yace mom bafa haka nake nufi ba magana zamuyi fa sai in danji duminta. Dariya mom tayi tace zama kayi bayani Nide na fada maka.
Sannan ta Koma tana mai jinjina halin rashin kunyan yazeed don atunaninta wani abar za’ayi.
Yazeed ko minal yaja zuwa kitchen wadda duk kunya ya rufeta saboda ganin da mom ke mata.
Fuskar yara ya mata yace babe kiyimana pancake dinki muci please.
Gyada kai tayi ta fara hado abubuwa sai murmushin jin kunya take yazeed ko daya hau kan island ya zauna tareda dauko wayarsa yanata daukar hotonta tana aiki saide duka fuskarta bai fito ba.
Ajiyan zuciya yake sauke wa yawunshi har tsinkewa yake yace kai nikam ataimaka min na fara cin nawa. Zuba mai tayi ta bashi zata Koma taci gaba da suya ya riko hannunta cikin shagwaba yace ni kibani a baki.
Hannu tasa ta taba goshinsa da wuyarsa ba zafi. Yace yadai tace na dauka bakada lafiya ne naga kana Abu Kamar baby. Yace aini Babyn ki ne kashe gas cooker din tayi ta dawo ta zauna a gefensa bayan ta dauko juice da honey da lemon. Tace da wanne kakeson honey ko lemon yace lemon dinde saboda tsami tsami.
Haka tayi ta bashi sunaci Suna hada plan din yadda zasu hada kan su zaliha da lukman da kuma yadda zasu gudanar da bikin su Abubakar Dan sun dano taragonsu.
Saide kash bansamu Dakar mina abinda suke Cewa ba saboda ina can ina satar pancake dan Nasan ko na tamabaya yazeed bazai bani ba tsabar santi Dan naji lokacin dayake Cewa in so samune minal ta bashi duka pancake din sai ta dafawa su mom wani abincin.
STORY CONTINUES BELOW

Bayan sun gama ci cikin raha da kaunar juna. Yazeed yace kai kullum sai kiyimin irinsa har iya tsawon rayuwar mu. Kuma duk ranan da banci Shiva Toh ko me naci saide inci Dan yunwa. Girkinki na daban ne masoyiya. Hugging dinshi tayi tace Insha Allah kullum zannayi maka girki kuma duk ranan da ban Daga ma abinci da hanuna ba Toh ko wa na dafawa aikin banza ne.
Karashe aikinta tayi yazeed ya tayata jera dining table.
Kowa sai Santi yake sahir Dan taurinkai tasowa yayi ya rike hannun yazeed yace daddy I am sorry I called you a bad daddy you are the best daddy because you married the best aunty who can cook the best pancake.(baba kayi hakuri nacema kai ba ubanl na gari bane. Kai din uba na gari ne daya a cikin miliyan saboda auro aunty wacca tafi kowa kuma ta iya soya pancake dayafi ko wanne dadi.) Shafa kanshi yazeed yayi yace is okay my boy. Wajen minal yaje yace aunty will you be my friend?(aunty shin zaki zama kawata?) Daga kai tayi tana murmushi tace yes peck ya mata a kumatu sannan ya hau cinyanta ya zauna bayan ya janyo abincinsa gabanta yace ita zata bashi yazeed yace my boy ka girma fa karka balla min aunty.
Safwan ne ya taso yazo wajen yazeed yana turo baki yace am I not your boy? (Ni ba yaronka bane?) Yazeed yace yes your are my dearest son(eh kai danane da nakeda kusanci dashi). Gwaliyo sahir ya masa. Kallon minal safwan din yayi tace masa karka damu kai amini nane ba abokina bama. Din buro fuska sahir dake cinyanta yayi tace sorry sahir karkayi kuka kaima amininane.
Bayan sun gama cin abincin ne minal tacewa yazeed tanaso taje gidan zaliha yace taje no problem.
Fita tayi yazeed yace ta tsaya a kaita a kafa tace ba damuwa zataje da kafa saboda exercise.
Riko hannun su tayi tiryan tiryan Suna tace Suna hira kankace me sun saba Idan ka gansu zaka dauka ita ta Haifa abin gwanin ban sha’awa. Dukda ko Cewa sahir ya nuna rashin kauna a gareta da farko bata nuna Mara waraiya ba kuma ai ko ba Komai ya nemi yafiya sannan yaro ne shekarunsa 7 ne kawai.
Abakin kofa ta hadu da lukman suka gaisa yake tambayarta ko yazeed yananan tace yananan.
Yace Toh tayi masa alfarma ta lallashi kawarta. A tsorace tace me ya sameta yace sabani Muna samu kamin ya wuce su safwan suka bishi da kallon rashin fahimta. Sahir yace safwan kasan menene ma’anan sabani?girgiza kai yayi yace kai da ka jirmeni ma Baja cani ba balle ni.
Minal ne tace shh bakyau sa ido kunji ? Chocolates ta dauko a jakanta ta basu sannan ta kunna musu TV already an hada tace suyi kallo zata he wajen matar uncle lukman. Zaro ido sahir yayi yace dama aunty baka matar uncle lukman ne? Minal tace aunty baka kuma? Ka dena fadan haka kaji ai baki da fari duk Allah ne yayi mu babu Wanda yafi wani sai Wanda yafi jin tsoransa. Yace Insha bazan kara fadaba amma Gaskiya bakinta dayawa ne ysoro ma take bani. Dariya minal tayi tace karka damu zata Baku sweet. Kaima safwan kaji me nace ko? Yace dama ni bana fada kuma kawatace tun a hospital Dana ganta.
Shiga dakin minal tayi ta sameta tana kuka tace kai zally me haka? Kuka sai kace yarinya ? Idan ma aurenne bakyaso kin kaini ne. Nifa a shashanci na ko mijin ban saniba ma. Dukda banyi nadaman yadda da aurensa ba amma ai sanda na wahalu tukun naji dadi ba gashi yanzu ya wuce ba? Karki damu bari in baki sirrin da zaki sato zuciyarshi da wuri.
Ki tabbata kuna samun body contact koda kuwa kuna fadane hakan ne zaisa ya saba da jikinki yadda duk ranarda baiji dumin fatarki ba zaiji Kamar bayida lafiya Daga nan zaku saba da juna with time har Ku fara lobaiya.
Zaliha tace ni rabu dani waddannan shirmen se ta kaddar Hausa ko film din India. Minal tace yo ke da kike karanta takaddun hausar kenan.
Bari kiji ni shaidace akan wannan ina miki magana ne with experience. Hararar wasa zaliha ta mata tace shegiya kawata nifa banason karyar turanci minal tace dalla tafi can yanzu kin isa ki nunan iya turanci. Zaliha tace Allah baki zanyi tunani akan shawararki. Minal tace ke kikajiyo kinsman dai ba rabuwa zakuyi ba Dan haka gara ki fara action da wuri ko duminsa kidan dinga ji. Dariya suka fashe dashi zaliha kai shegiya kwata kefa yar bara ub*ce da dukum kike ba abinda kika sani ko Dan 10yrs yafi ki sanin harkannan yaushe kika zama yar Hannu ne. Duka minal ta daka mata tace banson ashar ke matsalata dake kenan. Zally tace kinga ni muje muyi yama sunan abin matan manya ? Minal tace me ?zaliha bude ido ta turanci. Dariya minal tayi tace tourism? Zaliha tace shi nake nufi Daga mu dafo abinci. Fita sukayi suka Duba ko ina sunata yaba Kyan gidan suka Duba kitchen akwai Kayan abinci Kamar na sati. Taliya suka daura sannan suka wuce parlour minal tace kawas canjo Maya muyi photon randa kika tare gidanki ko ba haka ba ? dariya zaliha tayi kamin ta wuce zata Shiga zaki minal tace tsafta na kara dankon abin…. Kin gane ai. Zaliha tayi murmushi ta shige tasan love minal kesan Cewa amma saboda su sahir na wajen yasa ta fake.
Bayan ta Shirya cikin Riga da wando hotuna suka sha abinsu sunyi kyau sosai domin minal ma Rolling gyale tayi.



Idan naga comments daya wa Toh za’a sami update dayawa.
Ina kaunarku sosai😘
Takuce karamarsu babbarsu
Don Allah kuyi voting
miss untichlobanty💕
14th January, 2020
MASU COMMENTING INA GODIYA ALLAH YA SAKA DA ALKHAIRI NA GODE DA KAUNA.
MASU VOTING KUMA NA GODE ALLAH YA BARMU TARE KU DAURE A DINGA COMMENTING10
YAN LABE SANNUNKU TUNDA NI BAN GANKU TA HANYAR COMMENT KO VOTING BA AI BAZAN GANEKU BA
ASHA KARATU LAFIYA
Bayan sun gama hotunansu su sahir ma sukace a watsa musu haka ko akayi suka dinga selfies masu kyau tunda yanzu bazai yiwu a dauki hoton ba dama sahir ne ke daukansu.
Abincin su suka dibo harda su sahir suka zauna a kasa suka lafci jellof din taliyarsu. Safwan ne ya zauna a cinyan minal tare da rungumeta yace aunty minal kakci yabu dani dan Allah, ina conki. Brother kaima kana conta ko ? Daga kai sahir yayi. Murmushi minal tayi tace nima ina sanku kuma bazan rabu daku ba kunji yaran albarka. Safwan yace aunty minal ni a dakinki zan kwana. Safwan yace brother ka manta daddy Cewa yayi mu dinga ce mata mommy? Zaro ido sahir din yayi yace hakane fa na manta ne. Hira suka cigaba dayi abinsu kamin bayan sunyi sallan magrib suka Koma gida.
Tambayansu minal tayi ko sunada home work su kace mata ai sunyi Hutu Al Qur’an ta dauko ta zaunar dasu tace su karanta mata har zuwa Inda suke sai ta kara musu.+
Safwan ne ya kalli sahir yace yaya sahir wannan din diccinayi (dictionary) ne?
Hararansa yayi yace dictionary akace. Nazari ya fara yi saboda tambayan Dan uwan nasa kamin yace nima ban saniba sannan ya kalli minal yace momy ai mu bama karanta dictionary a makaranta.
Kallon mamaki minal ke binsu wato Suna nufin basu masan Qur’an ba?
Shafa kan sahir din tayi tare da murmushi tace wannan ba dictionary bane. Wannan littafin addini musulunci ne. Kar duniya babu littafi me tsarki da muhimmanci irinsa kuma yanada anfani ga rayuwar mu baki daya. Da badan shi ba da abubuwa sun tabarbare mana shi yake nusar damu abinda ya dace muyi.
Kallon kurulla suke mata da alamu Suna shanye information din ne. Safwan wato karamin yace momy kinaso kice min shi Kamar guide ne?
Tace good boy you are smart shi din guide ne.
Jinjina kai yayi yace aiko mommy Idan haka ne Daga yau kullum sai na kayantashi kuma Nayi alkawari zanyi aiki daci dadai gwaigwado.
Sahir yace nima haka na miki alkawari momy.
Dadi minal taji sosai ganin yadda yaran ke son karatun addini kuma itama tayi alkawari zata yi dai dai gwargwadon ta wajen koyar dasu.
Shaking hannunsa tayi tace Toh zamu fara haddacewa yanzu zanga Wanda zai Riga haddacewa duka kuma banida burin daya wuce Idan kun haddace in koya muku fassaransa sannan zamu dinga yin saura littafai sau 2 a sati sauran 5 days kuma na al Qur’an ne.
Dadi sukaji safwan yayi saurin rarumar Qur’anin ya bude Jade fuska yayi yayinda minal ta karba tace safwan my boy yara basa taba Qur’an izu sittin kaji. Yace momy menene izu 60 kuma? Tace zan fada muku yana Qur’an yake amma dai izu sittin shine complete Qur’an oya Ku gyara zama mu fara.
Nan fa minal ta fara musu Daga suratul fatiha amma abinda ya bata mamaki shine har sun haddace Bismillah da aya uku. Idonta har cikowa yayi da haiwaye na tausayin yadda rayuwarsu ta kusa tabarbarewa saboda ba’a nuna musu addini ba dukda ko Suna da kai me Kyau. Lallai tabbas akwai abinda Allah ke nufi dasu daya hadasu fatanta dai Allah yasa alkhairi ne.
Sahir ne yace Toh momy me yasa aka rubuta kur’anin bada English alphabet ba. Tace saboda bada English aka sauketa ba an sauke ne a larabci. Safwan yace Arabic kenan tace eh yace amma ai ni ban iya Arabic alphabet ba lokacin da nacewa daddy na ya koya mana sanda muke London yace bayada anfani a garemu kuma bayida lokacin mu muje uwar mu ta koya mana kuma da mukaje muka sami mommy mukace ta koya mana tace bata iya ba.
Jikin minal ne yayi sanyi taji ta tausaya musu. Dukda batasan labarinsu ba tasan sun Shiga gararari gunjin kukan da taji ne ya dawo da ita Daga tunanin da ta shiga. Ganin su tayi rungume da juna Suna kuka.
Safwan yace wallahi dadynmu baya sonmu ya tsanemu kuma momyn mu ma ta tafi ta barmuuu😭😭😭 rungumesu minal tayi tare da basu hakuri sannan tace karsu zamu ai suma iyayensu ne ita da zakiyya momynsu ne kuma yazeed dadynsu ne.
Sallah ta koya musu tare da fada musu with time zasu koyi komai da akeyi a cikin sallah Karfe 9 tayi musu wanka tana cikim shafa musu mai yazeed ya Shiga fuskan shagwaba yayi mata yace kin barni ni daya yarannan sun kwacemin ke. Dariya tayi tace gaba daddy karatu fa mukeyi yazeed yace haba? yara na Ku tabba kun maida hankali kunji. Mommy kizo muje daki.
Tace daddy ka shirya sahir toh saboda mu tafi da wuri tunda shi na shafa shi. Cuku cuku yazeed ya dinga yi da kayan har minal ta gama Shirya safwan sai dariya suke masa safwan yace daddy kanaso inyi maka karatun da mommy ta koyamin? Yace eh kamin muji karanta mai yayi sahir ma yayi yace good good very good for my sahir and safwan. Ku kwanta Kuyi bacci. Safwan ne ya rike hannun minal tare da mata puppy eyes yace momy dake zan kwana. Yazeed ne ya lallabasu tare da musu alkawari kamin su tashi Daga bacci minal zatazo kamin suka hakura.
Koda suka Koma daki suna rufe kofa yazeed yayi hugging minal tare da fadin i missed you baby. Murmushi tayi tace me too.
Zaunar da ita yayi a bakin gado sannan ya mata godiya akan yanda ta rike amanan su sahir.
Murmushi ya mata yace sweetheart rufe idonki. Zan baki surprise.
Rufe idon tayi can yace open your eyes tana budewa ya mika mata form karba tayi ta Duba taga na jamb ne Dana WAEC da NECO tsalle ta daka ta rungumeshi tare da fadin Alhamdulillah zan Koma makaranta.
Dadi yaji aranta yaja kumatunta yace baby girl da Nasan komawa makaranta zai saki wannan farin cikin da na mayar dake tun randa na auroki.
Karatunsu su kayi bayan sun cika form sannan suka kwanta yazeed na fada mata zai tafi wani mission yaso ace da ita zashi amma bazai yuwu ba saboda rananda zai tafi ranan za’a fara WAEC shagwaba ta dinga yi masa har sukayi bacci.
Da sassafe taje ta tashesu safwan sukayi sallah sannan suka Koma bacci.
Dawowa tayi ta kwanta around 7 ta daura breakfast tare da hada na Yan hospital. By 10 kowa ya gama shiru anci breakfast sannan suka hadu a parlour domin tafiya asubiti su Mashkur sai santin abincin suke.
Yazeed ne ya nufi kofa ya juyo ya tabbatar kowa bata kallonshi sai ya kashe wa minal ido tare da blowing kiss abinda bai saniba shine kowa yana fakonsa Dan haka aka fashe masa da dariya ya Daga kai ya fice yana mai danne dariyarsa.
Fans Kiyi hakuri wallahi na zama busy daya wa ne shiyasa chapter din babu yawa love you all
Ga channel Dina na YouTube fatan zakiyi subscribing.
https://www.youtube.com/channel/UCjE7XttaGFjEBamBPDRNCbg
Takuce karamarsu babbarsu
Miss Untichlobanty 💕Hospital din dasu ayush suke suka fara zuwa nanma likitan yace baza’a iya moving dinta ba saide nanda Dan wani lokaci yazeed yace karka damu wannan da kake gani ya kware a fannin shiyasa na kirawoshi yazo har kasannan so he can take care of her condition. Doctorn yace mr yazeed are trying to say mu bazamu iya aikin mu bane ? Yazeed yace ba haka nake Nufi ba. Inaso be dai ayi moving dinta hospital da take akwai komai and tight security. Dr yace ok I will try my best domin keyi moving dinta amma yanzu Kam mashkur yace can I check on her? Dr. Yace that’s against the rule tunda ba a hospital dinnan kake aiki ba sannan permission da aka baka is only restricted to (iyakarsa)FIRST CLASS MULTI SPECIALIST ne idan ba under emergency ba wato bukatar gaggawa.
Yana gama fadin haka ya wucesu tare da shigewa office dinsa dama saga dakin da ayush ke kwance ya fito.
Kebewa gefe yazeed da mashkur sukayi Dan yau ba’a taho da luku guy ba.
Acewar yazeed ya zauna ya angonce.
Kuskus suka fara mashkur yace nifa ban yarda da likitan nan ba. Idan ba haka ba ya za’ayi yace baza’a iya moving coma patient zuwa wani hospital ba alhalin she is out of danger?
Wanda akwai risk ma shine idan za’a fitarta waje kuma shima za’a iya. Yazeed yace ni dama can bai kwanta min arai ba so abinda zamuyi mu dauki abunmu mu mayar gida sai ka kuka da ita sauran sai a barsu a hospital Dincan ko kaga za’a ragewa my zakiyya wahala ma.
Mashkur yace haka zamuyi nan suka sanarda mom tace hakan ma yayi Dan kallon da likitan ke Mata bai kwanta Mata ba domin kallon banza take Mata na yan iska domin akallon da yake Mata babu alamun aure yake sonta dashi.+
Ran yazeed ne yayi mugun baci Dakyar suka lallabashi ya huce. Koda suka fadawa dr din tuburewa yayi aishi Sam Baza’a fitarda ita daga nan ba yazeed ne yayi kwalarsa tare da yarfa mai tafi sanda bakinshi ya fashe yace na baka 30min a shirya komai domin mayar da ita gida. Zamuyi arranging komai kaji ko? Da sauri ya daga kai yazeed yace maza maza go to work.
Kafin minti 30 an shirya komai sannan aka hadasu da nurse yazeed yace bayaso zasu iya kula da ita sannan zasu dauko nurse daga asubitin da suke zuwa wato FIRST CLASS kuma kabilar China ce ma.
Aiko haka akayi bayan an mayar da ita gida tare da nurse dinta akace mom da minal su zauna a gida ujili ujilin yayi yawa. Minal ce ta lallabo zakiya akan taje tayi su Wanda ta shirya taci su abinci ba musu tayi koda ta fara cin abinci kawai sai ta fashe da kuka a tsorace minal da yaranta sukayo kanta suna tambayan lafiya tace tunda nake ban taba cin abinci mai dadin wannan ba saide abin takaicin ni ko abinci ban iya dafawa ba amma yarinya kamarki ta iya sai yanzu nake nadamar rayuwar da nayi a baya dadina daya Danayi nadama run lokaci bai kuremin ba yake yar uwata amina shin zaki koyamin rayuwar zaman aure? Daga kai minal tayi zakiyya ta kuma cewa shin zaki koyamin addini na? Minal tace da izinin Allah sauko wa kasa tayi ta rike kafafun minal tana fadin na roke ki da Allah ki yafe min duk cin mutuncin da na miki.
Dagota minal tayi ta sauri tana fadin babu abinda kikamin Wanda naji haushi ma na yafe miki tun da dadewa Allah ya yafe mana Baki daya daganan suka rungume juna cikin farin ciki. Mom dake sama tana kallonsu ta share guntun kwallarta yayinda su sahir suka fara tsalle da waka suna fadin mommy da mommy sun zama kawaye!
mommy da mommy sun zama kawaye!!
Dariya su minal sukayi kamin zakiyya ta share kwallarta taci gaba da cin abinci can tace toh yanzu kamin komi ya kankama mu fara karatun me zaki fadamin Wanda idan na rike bazan tabe ba.
Murmushi minal tayi tace idan akace Allah ya hana Kaza ko annabi ya hana toh karkiyi komin dadinsa domin zaki iya mutuwa kina aikatashi akwai situation da idan kamar Ansaki kiyi ok a kasheki toh idan fada akace kiyi sai ki fada amma niyarki ta kasance a tsarkake idan ko aikatawa akasa ki kiyi misali kisa to karkiyi gara a kasheki saboda ta iya yuwuwa Wanda akasa ki kashe din rayuwarsa tafi taki anfani ma al’umma toh kinga gara ki mutu da ya mutu kinga kenan Kamar kin ceci Ranshi ne kuma kinyi shahada tunda kasheki akayi. Manzon Allah (SAW) yace Duk Wanda ya cecin ran mumini Kamar duniya ya ceta sannan duk Wanda ya kashe mumini toh kamar ya kashe duniya ne baki dayanta.
Ajiyan zuciya zakiyya tayi tace amma na gode Allah ya saka da khairi Niko zanyi riko da wannan shawara taki su sahir sukace muma zamuyi. Rungume su minal tayi tace Allah ya muku albarka zakiyya ma rungumesu tayi baki daya harda minal.
Karan fashewar glass yasa su tsorata suka kalli inda sautin ya taho………
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀
Su yazeed Suna zuwa hospital suka wuce ward dinsu. Gaishe da ummie suka Shiga yi suka samu Dr Muhammad ma na ciki. Gaisawa sukayi sannan suka wuce room din da aka ajiye Jennifer. Tayi baki dukda ko dama ba wani hasken arziki gareta ba.
Dudduba su heart beat dinta yayi yaga Is normal sannan some part na brain dinta ya fara functioning she can hear and understand but she can’t react.
Dan haka yaja hannun yazeed suka fice yace dude gaskiya addua dinku is very strong ka duba kagani ummie ta tashi and there is a chance Zan iya tashar da Jennifer dinnan. All I need is mu fada Mata wani Abu dazaiyi shocking dinta back to reality tunda dama shock ne yasa ta shiga coma.
Yazeed yace ai da nasan shine zai farkarta da nayi tun da dadewa mashkur yace it might work Nacema ba guarantee na baka ba.
Suna shiga dakin yazeed ya kausasa Murraytare da cewa lukman kuyita dukanta harsai ta tashi ta fadamin Wanda yasata ta zuba mana poison.
Dukan abubuwa suka farayi Kamar dai ana jibgan mutum. Can yazeed yace sa bindiga ka harbe min ita yayinda yake kallon mashkur Wanda ke masa thumbs up alamun tana reacting. Belt yazeed ya ciro ya dakarkare ya laftawa dayan empty gadon dake dakin ki kake Tauuu kamar karan bindiga atake ta Mike tana shure shure daganan tafara tana fadin kayi Hakuri sir ! Karka kasheni I promise na manta ! Ka Tausaya karka kasheni. Har ta hada gumi saboda tsoran mutuwa mashkur yace calm down Kinji wani kararrawa ya dannan before 1min sai ga nurse ta shigo yace ta samo ruwa da sauri ta matso ta kawo ta bata tana mamakin yadda Jennifer ta tashi domin a nasu analysis da sukayi sai nanda 3 months zata farka. Lallai mashkur yasan aikinsa Allah ya gani tun rananda ta fara ganishi taji ya kwanta Mata aranta amma yanzu kam sonshi takeyi.
Bayan Jennifer ta natsu suka zauna a gefenta take ta fara tsurewa kwantar Mata da hankali yazeed yayi ya nuna cewa ba abinda zaiyi Mata. Tambayan duniyannan sun Mata wa yasata amma ta kasa tunawa atake mashkur yasa akayi dakin duba kwakwalwa da ita koda ya duba yes ta Sami memory lost amma kuma babu abinda ya Sami kwakwalwarta dazaiyi causing memory lost din. Wannan Abu shi ya daure masa kai abinda bai sani ba Kuwa shine tsafin da akayi Mata shi ya hanata tunawa kuma bazata taba tunawa ba koda kuwa zataga Wanda yasata aikinne haka yazeed yanaji yana gani ya hakura ya barta danshi tausayi ta bashi ga guilty feelings dake damunshi Dan a ganinshi saboda dukanta da akayi ne yasa ta rasa some part of memory dinta .
Dukda cewa tayi kokarin ta kashesu still baiji dadi ba. Haka suka kama hanyan gida jiki a Sanyaye.
Na sadaukar da wannan page ga dukkan masoya na Allah ya barmy tare
Takuce karamarsu babbarsu
Miss Untichlobanty 💕
18th January, 2020.Ajiyar zuciya dukansu suka sauke ganin ba wani serious Abu bane, glass ne ya fashe
Can bakin kofa kuwa zaliha ce tsaye ido a waje saide su basa ganinta saboda kofar ba a wangale take ba kadan ta bude zata shigo kamin tayi arangama da abin mamaki takowa minal tayi ta karaso wurinta.
Mutsittsika ido zaliha tayi minal tace ke lafiyar ki? Yawu ta hadiye tace don Allah tasheni minal, tasheni yadda kika saba tashina Idan ina baccin la’asar Baccin asara.
Dakarkarewa minal tayi ta yarfa mata tafi a gadon baya. Botsarewa tayi tace kai kede wallahi hannun ki a haka laushi amma a jikin mutum yanda kasan gaskami. Wai Dan Allah da gaske zakiyya ce ta rungumeki. Murmushi minal tayi tace gashi ko kin gani.
Jinjina kai zaliha tayi tace Allah mai iko me yin yadda yaso.
Zakiyya ce ta tako har wajen su tace me ake ci babu ni? A ah minal kice Amarya ya ce a tafe.
Mika mata Hannu zakiyyan tayi tace Assalamu alaiki.
Zaliha tace waiye huhu kai jama’a.
Dagaske gaisawa zaki yi dani zakiyya? Murmushi tayi tare da rungumeta tace hug din ma yafi.+
Tsurewa zaliha tayi ta kalli minal tace ke Dan ub*nki yi min bayanin abinda ke faruwa ban gane ba. Me kika mata? Karkice min wani abin ya sami kwakwalwarta.
Dariya zakiyya tayi tace ba abinda ya sameni Allah ne kawai ya nunamin Gaskiya Kiyi hakuri da zagin launin fatarki da takeyi duk lokacin da muka hadu. Girgiza kai zaliha tayi cikin rashin gaskata abinda ke faruwa tace ba Komai ya wuce ai.
Hawaye ne ya zubowa zakiyya tace ina ma ace Inada zuciya irin taku wacce takeda girma kuma ashirye take ta yafewa kowa.
Murmushi minal tayi tace ai zaki iya kawai danne zuciyar zaki yi sannan ki tursasata kuma kinsan shi hakuri jigo ne na rayuwa,gishirin zaman duniya ne Idan babu shi Toh rayuwarka da lami. Sannan kome ya faru da mutum ya daukeshi a matsayin kaddara mai kyau ko Mara kyau.
Jinjina kai zakiyya tayi tace kuma ai inna laha ma’assabirin.
Shigowa ciki su kayi dukansu, suka bags da hira yayinda su sahir suka tafi playing room da aka basu.
Can minal tace kash! Ni har na manta Ashe mom tace naje ta bani tsarabata. A take zuciyar zakiyya ta dunkule, fuskarta ya canja zafi takeji saboda tayi wasa da damarta minal ta kanannade komai amma sai tayi Saurin dannewa Dan tanason ta kyautatawa minal KAMIN SU RABU.5
Bayan minal ta haura sama suka cigaba da hiransu saide zaliha ta lura Kamar wani Abu na damunta sai ta share Dan batason ta banbarowa kanta Dan har yanzu bata gama yadda zakiyya ta canja ba. Koda ta isa mom tace my daughter sai yanzu Daga kai minal tayi tare da yin yake. Mom tace ya na ganki haka Kamar wani Abu na damunki, so zauna kinji ?
Zama minal tayi mom tace ina jinki minal tace mom a Gaskiya aunty zakiyya ta canja sosai kuma ni shedace sannan Nasan tayi nadama kuma abinda ta aikata yana damunta mom why not ki kirata mu raba kayannan tare Dan na lura sanda nave kina ne mana zamu raba kaya yanayinta gaba daya ya canja idonta ya ciko da kwalla wallahi tausayi take baniii😭😭 kawai sai minal ta Barke da kuka
Mom kam a zuciyarta tunani take anya zakiyya ba wata manufa bace da ita ? Dubi yadda tasa yar mutane ta damu a kanta Allah dai yasa da gaske ne.
A fili kuwa Cewa tayi haba aminatu manya mata miye abin kuka share hawayenki ki kirata. Da gudu minal ta fita ta kirata sai Washe baki take. Mom kam mamaki take Wai bata kishi ne? Lallai yazeed yana fama.
Zakiyya najin minal tace mom tace tazo taji wani dadi a ranta atake ta tashi cikin farin cikin suka hau sama akabar zaliha da jimami kamin ta bisu sama bayan tasa tala ta share glasses din daya fashe dama ginger juice tayiwa mom.
Koda suka Shiga har kasa zakiyya ta tsuguna ta gaida mom. Amsawa tayi tana kara mamaki da gaskata maganar minal Dan tun jiya zakiyya ta nemi afuwarta amma bata yadda ta tuba ba sai yanzu Dan da ace wani abin takeda shi a zuciya girman kanta bazai bari ta tayi abinda takeyi yanzu ba.
Amsawa tayi tare da Cewa zoki zauna a gefena mana daughter. Rarraba kayan suka farayi kamin zaliha ma ta Shigo ta jonasu bayan ta gaida mom.
Sari biyar ne sai normal Indian attire 12 ta bawa zaliha sari daya da set 2 sannan ta raba sauran ma zakiyya da minal.
Daki suka koma minal ta fara koyawa zakiyya girki kuma ta mYarda hankali sosai tana kota dukda ba’a rasa kusa kurai ba. Daidai lokacin su yazeed suka dawo a tare minal da zakiyya suka rungumeshi suna. Mai sannu da zuwa sandarewa yayi na Dan wani lokaci saboda bakon lamarin daya gani cikin gidansa.
Yau inada ta’alim yanzu haka a boye nake typing sorry ba yawa amma I promise to make it up to you gobe Insha Allah.4
SADAUKARWA CE GA MASOYA BAKI DAYA ALLAH YA BARMU TARE TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💕
20th January,2020.Inda mamaki na kashe mutum da yau yazeed ya mutu ganin yadda ya Tatar da matan nasa kasa boye farin cikinsa yayi hakan yasa ya sunbaci goshin s
Duka biyunsu saide ya lura akwai wani Abu a idon zakiyya wadda ya kasa gane alkhairi ne ko tsiya fatansa dai Allah yasa zaman lafiyan ya dore.
Su safwan ne suka rugo a guje Suna fadin daddy saura mu tare da juya masa gefen kumatun nasu. Janye jikinsa yayi Daga na matan nashi kamin ya tsuguna ya rungumesu tare da sumbatarsu. Sallama Mashkur da lukman sukayi hakan yasa minal janyo hijab dinta dake hannun kujera yayin da zakiyya tayi kitchen domin a can tabar hijab dinta. Aiko sai gata da zumbulelen hijabi.
Sakan baki yazeed yayi Dan bai gaskata abinda yake gani ba. Mashkur ne yace uhm su mai iyali manya.
Safwan ne ya lura da gaba daya hankalin shi baya Kansu gashi ya saki baki. Inda yake kalla yaji kamin yayi dariya kasa kasa yasa Hannu ya rufewa yazeed bakin tareda fadin daddy kuda zai Shiga bakin ka. Sai lokacin yazeed ya kallesu tare da Cewa muje muci abinci ko.
A tare su minal suka Shirya Komai yayinda zaliha da lukman Keta rafkawa juna harara. Min ta lura da haka.
Zakiyya ce ta fara zuba abincin. Ta zubawa su sahir da yazeed the next one Mashkur ne minal tace aunty kawo kawai. Zakiyya tace barshi in zuba. Murmushi minal tayi tace ai yanzu ma kinyi kokari kallon yazeed tayi tace kasan Cewa yau aunty zakiyya ce tayi mana girki? Yace haba shiyasa naji kamshin ya chanja. Kuce zakiyyan nawa chef ce. Kallon minal yayi da alamu maganar ta tabata kishin ya motsa yayi da zakiyya ke murmushi minal ko taci gaba da zuba abincin. Taci gaba da cewa nikam ina yiwa Allah godiya daya hada ni da mata Wanda babu yasu ga kyau ga iya girki. Nikam ban Masan wace tafi wacce ba.+
Murmushi dukansu biyu su kayi. Abincin yakai baki ba laifi yayi dadi amma yasan babu macen da zata kara da minal dinshi wajen dafa abinci.
Ajiyan zuciya ya sauke yace Ashe haka dama adalcin keda wahala Idan ka yaba daya sai ka yaba dayan? Wannan shine adalci a magana. Hmm Toh faa Gaskiya da aiki a gaba na.
Minal tana isowa kan zaliha dake gefen lukman Wanda Keta dangwalarta Dan ya gano ba abinda ta tsana Kamar tsokana Dan haka ya mayar da ita abin wasa. Tace kash na manta bamu kira mom ba. Bari kawai nakai mata daki zally zuba naki ki zuba na habibin ki.
Wani kallo ta aika mata kallon Idan na kamaki Allah ya jikan ki.
Gwaliyo ta mata kamin ta dale sama abinta. Zubawa zaliha tayi badan ranta yaso ba yayi da lukman ya kashe mata ido. Aiko ta kara cika amma ba yanda ta iya sai yake takeyi.
Yazeed ma ya gano dalilin minal na yin hakan. Cinye abincinsa yayi yayi wa zakiyya alamun ta sameshi a daki.
Bayan mintuna sai gata zaunar da ita yayi a bakin gado yace my zakiyya agaskiya Nayi farincikin yadda na dawo na samu gidana yau gashi kinyi Shiga ta addini kin zama mata ta gari bakisan yadda nakeji a zuciyata ba wallahi. Na rokeki da Allah karki canja halinnan. Matsowa yayi zai sumbaceta ta kauce. Kallon yayi da alaman lafiya? Mikewa tayi tace bana sallah. Kamin ta fice. Jinjina kai yayi yace tooh? Anya kuwa?
Zakiyya ko tana fita dakinta ta fada gado ta soma kuka aranta tana fadin ka yafeni yazeed amma inaso in manta dakai. Inaso in daina sanka shiyasa bazan yarda mu dinga karfafa alakarmu ba ka yafemin. Rayuwar auren mu na Dan wani lokaci ne.
Koda minal ta dawo bata kalli Inda su zally suke ba Dan tasan sakamakon. Dakin yazeed ta nufa har ta tura kofar sai wani tunani yazo mata what if yana tare da zakiyya ne. Memakon tayi knocking Dan rashin wayo sai ta leka ganinshi tayi yana shan magani hakan yasa ta Shiga tare da warcewa da Sauri. Duba sunan maganin tayi taga bata gane ba hakan yasa ta fara karanta uses dinsa kokarin kwacewa yazeed yayi amma ya makara domin ta karanta kuma ta gane Cewa maganin rage karfin libido ne. Ranta ne ya back idonta ya kada yayi ja. Cillo masa maganin tayi tare da fadin me wannan? Kace maka me wannan ? Tuni hawaye ya fara zubowa tace haba ya yazeed me kake shirin wulla mu ciki yanzu da ace mom ne taga wannan me zata dauka? Ace kanada mata biyu amma kanashan maganin rage sha’awa. Ka taba zuwa wurina na hanaka hakkinka ne? Daga murya tayi tace NACE KA TABA ZUWA WAJENA KA NUNA KANADA BUKATA NA HANAKA? Me kakeso ka nunawa duniya yakai mijina? Shin bamukai ka kusancemu bane? abin tausayi yazeed ya Koma dan yaji kunya yadda kasan da uwarsa na masa fada. Ya matso ya riko hannunta idanunsa sun cicciko yace ba haka bane na dauka bakisan wannan abin bane ni kuma banason na kawo miki shi lokaci daya kar Nayi gaggawa. Harararsa tayi tace a da ba amma banda yanzu domin kan mage ya wa…..
STORY CONTINUES BELOW

Bata karashe ba yazeed ya cafkota ya hade……… Su take ta tsorata saboda yadda yake mata Dan ita batasan yadda akayi ta zake haka ba Daga zaliha ta daurata a network din yadda abin yake ko gama koya mata batayi ba sai tayi azarbabi?
Tsoro sosai taji ganin yadda yazeed ya Koma ba sai kafarta ya fara rawa ba take ta fara kukan Neman agaji sakanta yazeed yayi yace you see! Kingani ba? Ba aje ko ina ba kin tsure. Tsitstsilla ido ta fara tare da Cewa ban Shirya bane cikin in ina.
Yazeed yace okay kawai ya Shiga ban daki da gudu ta fice kirjinta na lugude cabdi anya kuwa zata iya yadda taji ance idan bakayi wasa ba in akayi first night wasu har dinki ake musu. Amma ita har yanzu abinda bata gane ba shine me takeyi har yake causing dinkin? Cabdi bari dai ta nemi shawarar zaliha. Koda ta fito a wargaje hijab a yamutse ta samu lukman na jawa zaliha kumatu yayinda take bige hannunshi. Ganin minal ta dawo yasa yayi pecking kuma tun zaliha yace Toh honey na wuce harara ta aika masa tare da fadin da na rike ka ne. Fice wa yayi yanajin dadin yadda yake tsokalarta ko ba Komai hakan ma yayi masa dadi.
Tunani ya fara yi Kamar yadda ya saba na yanda zai Sauri ayush tun sanda aka makala masa zaliha amma yau Allah da ikonsa kawai sai yaji ransa na baci. Bayason ko tunaninta yayi.
Murmushi ya saka tunowa da irin kallon da zaliha ke binshi dashi lokacin daya fito yace Gaskiya yarinyace. Kai amma fa auren yaran ma da dadi. Shege yazeed Ashe chilling yake shiyasa kullum zaka ganshi makale da matarsa.
Daki minal taja zaliha ta mata highlight akan abinda ya fara bawai dalla Dalla ba sannan ta tambayi ya zatayi? Janyo kunnanta zaliha tayi ta rada mata wani Abu zaro ido minal tayi tace anya zan iya? Zally tace Ras ma kuwa saide in baki gwada ba.
Hararta minal tayi tace shegiya sai Sanin sirrin kula da miki amma ba’a aiki dashi. Kinyi asara, ni ba wannan bama Wai a ina like Sanin abubuwan nan ne? Zaliha tace mutum da salularsa a WhatsApp mana a irin groups hakannan kinsan sai kaga dama zakayi misusing phone. Kinsman wasu su suke jawa Kansu duk abinda ya samesu. Minal tayi ajiyan zuciya tare da Cewa hakane Nide ki hada lambata a lintsima ni Dan baza’ayi babu ni ba. Zaliha tace angama matar oga. Dariya su kayi kamin suka shige wata hirar.
Yazeed ko wanka yayi ya fito ya rasa yadda zaiyi da ransa rana zafi inuwa kuna.
Bayan sallar isha’i zakiyya ta hada golden morn tana sha yazeed ya Shigo. Ajiyewa tayi agun ta haura sama abinta shikam kallo ma yake binta dashi. Dakinshi ya wuce abinsa koda yaje Abu yagani cikin bargonsa karasawa yayi yaga minal ce ke bacci tabe baki yayi yace uhm matsoraciya kawai.
Wanka yayi abinsa ya Shirya kamin ya kunna game yana bugawa abinsa. Tashi juyi tayi hakan yasa bargon yadan zame taga Ashe bra ne ajikinta take ya juya kai tare da Cewa kul yazeed barta tadan huta zuwa ka dawo Daga mission dinka wata zuciyar tace amma kai sai ka cutu ? Yana cikin wannan zazzafar muhawara da zuciyarsa minal ta bude ido gashi tayi ta zauna kawai ta ganta ba kaya ihu ta kwalla ai super daya yayi yasa Hannu ya toshe mata baki yace ke lafiyarki kuwa? Zazzare ido tayi ganin Daga shi sai boxers itama kusan yanayi daya suke amma Idan zata tuna ai da kaya ta Shiga dakinnan kamin bacci ya kwasheta kallon window tayi taga duhu hakan yasa ta fincike hannun yazeed tayi saurin dauka tare da fadin waiyo banyi sallah ba. Kunya ne ya kamata tayi saurin shigewa toilet tare da yin dahara sannan tayi alwala. Bath robe ta saka kamin ta fito domin ta gano na kowa ya sheka mata tsiyarnan ba illa zaliha kuma zata rama.
Kayanta ta dauka ta Shirya kamin tayi sallah. Koda ta idar kin hada ido tayi da yazeed. Murmushi yayi ya rufe laptop din Nasa kamin yazo ya tsuguna a gabanta. Sunkuyar dakai kasa tayi ya dago da fuskarta yace me na sunkuyar dakai Dan tureshi tayi a wasa tace ni kunya kake sani ki kasaka kaya.
Dariya ya kyalkale dashi yace Idan wani ya ganki zai dauka wata salihar baiwa ce nanko wani abin dakika sani koni ban sani ba.
Kwanciya tayi akirjinsa tana rufe ido da hannun ta Dan dariya yakeyi mata yana shafa kanta. Cikin shagwaba tace Dan Allah ka dena ni kunya kake sani ji. Cakulkuli ya fara mata tun tana nokewa har ta fara dariya. Cakulkulin itama ta masa kamin ta mike da gudu nanfa suka fara guje guje pillow ta dauko tana kwala mai tare da Cewa banaso aiko kaimi ya kara wajen yi mata cakulkuli tana fading waiyo zanyi fitsari cikina. Shikam dariya yaketa yi. Dukansa ta fara yi dakyau da pillown shima ya dauko wani Daga nan aka Koma pillow fight abin dai gwanin ban sha’awa sanda suka faffasa pillown gaba daya dama guda 4 ne yazeed daya kalli dakin yaga yadda ya wargaje saboda wayo yace uhm bari inje in yin kallon mikewa yayi zai gudu tayi saurin cafko wandonsa ta janyosa tare da saurin rude koda tace babu Inda zaka sai Mun gyara dakinnan. Fuskar abin tausayi yayi mata taja hancinsa tace oga babu wannan maganar fa. Nanfa suka dukufa ka’in dana’in suka gyara dakin. Sai haki suke yazeed ya baje a gado. Minal ta dauko takarda ita ma ta fada gado jagab. Miko masa takaddar tayi yace haba uwar karatu ai ma huta na yau ko bakiga yadda Muka gaji bane. Jinjina kai minal tayi alamar yadda Dan itama dama ta gaji tace ya batun tausar fa yace barshi kawai shima. Murmushi tamai ta rungumesa kamin ta kwanta a wurinta. Tace Saida safe yazzy baby. Matsowa yayi yace ke madam tashi.
Zama tayi yace akwai matsala tace name fa? Yace ni bana iya bacci Idan babu pillow tace Toh bari in dauko ma a daki na ta fadi hakan tana kokarin sauka Dan ta dauka da gaske yake. Riko hannunta yayi yana mata wani munafikin murmushi yace haba mutuniyata ace duk aikinnan da kikayi kuma sai na baki wahalan dauko mina pillow? Zo ki kwanta abinki tace Toh ya zakayi kayi Baccin? Yace kwanta kede ki gani tana kwanciya ya kwanta a kirjinta dariya tayi tace zama kayi bayani. Da ka fadi kanka tsaye kace kanaso ka kwanta a jikina ba ka tsaya noke noke ba. Murmushi kawai yayi Kamin yace Allah ya miki albarka tace Ameen da alamu bacci na Neman saceta. Hannunsa ya daura a cikinta yace my minal inama ace yanzu haka akwai Dan Babyn mu acikinki mu rayu dukanmu harda su auntynki cikin farin ciki Dan dariya yayi idonsa fal da kwalla domin yana matukar son ya samu haihuwa yace ace Ku haihu rana daya kuma Ku haifi Yan uku uku. Jin shiru bata kwafso masa wani kwaba ba yasa ya kalli fuskarta yaga ai tana wani duniyan sumbatar ta yayi kamin ya kwanta bayan ya musu addu’a yana Rokan Allah ubangiji ya azurtashi da yaransa na kansa.
Kiyi hakuri nace zan muku update jiya kuka mini shiru afwan banida lafiya ne Kamar yadda wasunku suka sani amma yanzu dai na samu sauki kuma da izinin Allah jibi zan muku update.
Longest chapter ever Dan haka nima inason sweetest comments
Don’t forget to vote as well.
Love you all😘
Miss untichlobanty💕
22 January, 2020Zakiyya kam koda ta gama kukanta fitowa tayi domin ta dauki golden morn dinta amma sai taga abinda akasha har wuce rabin Wanda ta dama kuma Idan zata iya tunawa cokali 3 tasha, tabe baki tayi tace may be ban lura bane shiyasa.
Shanyewa tayi kamin takai kitchen. Dakin da ayush take ta shiga ta duba ta sannan tayiwa nurse saide safe saide ta lura kamar akwai abinda ke damun nurse din amma sai ta basar.
Koda ta koma daki taga 2 missed calls from summy wannan friend dinta yar lesbian.
Calling back tayi ringing 2 ta dauka gaggaisawa sukayi tayi Mata Jaje sannan ta sanar Mata cewa mom dinta batada lafiya jibi zatazo ta dauketa sai ta duba ta. Zakiyya tace toh amma sai ta fadawa yazeed.
Koda gari ya Waye registration nasu jamb da WAEC and NECO akayiwa minal bakinnan har kunne. Bayan sun dawo minal tana Yan tattare tattare a dakinta sai ga zakiyya. Gaisawa sukayi tace toh mu fara ko. Minal tace toh bari na gama Dan tattare tattare nan. Hannun zakiyya tasa sukayi tare bayan sun gama suka nufi toilet minal tace toh tayi Mata alwalar yadda ta iya ta gani sai ta Mata gyara.
Abinda ya bawa minal mamaki shine ta iya tace Mata to ai kin iya ma. Murmushi kawai tayi akayi Salah ma gyara kadan aka Mata. Bayan sun gama har su azkar minal tace toh aunty zakiyya duk kin sani ma ai gyaranki kadan ne. Murmushi tayi tace thanks to my father lokacin da muke yara…..+
Wani mutumi ne me kimanin shekaru 45 tsaye a tsakiyar parlourn gidanshi da alamu an bata masa rai duba da yadda yaketa huci kofar wani daki ya kalla tare da cewa ummi! Zakiyya! Idan na shigo dakinnan zaku gane kuranku. Wata budurwa me kimanin shekaru 15 ce ta fito tana zumbure zunbure. Wani kallo ya bita dashi yace kede ummi kinji kunya babbar banza kawai ke bakisan cewa Ilimi shine gatan mace ba da makarantar boko ne kinfi kowa rawar kai wato shine kika fara hurewa yar uwar taki kunne ko.
Kauda kai gefe tayi tare da zura hijabin islamiyarta. Yarinya me kimanin shekaru 11 ne ta fito tare da cewa abba kayi hakuri hijab Dina na rasa. Murmushi yayi yace ba komai AI nasan ki zakiyya ta badai himma ba wajen karatu dama ke na sawa me sunan mamana ba wannan babbar kwabon ba. Kallon ummi yayi yace Allah ya shirya ta tabe baki.
Mota suka shige ya nufi islamiyarsu. Koda suka isa yace toh ummi Allah yasa muga alkhairi wannan karan. Indai sakamakon nan da zaku karbo yayi kyau to zan sayo miki wannan takalmin Kema zakiyya Allah yasa kinyi maintaining position dinki. Ameen tace cikin ajin dadi kamin ta dauki Jakarta. Naira biyar biyar ya basu yace ga wannan ku rike ko? Godiya zakiyya tayi tana mai jin dadi yayinda ummi ta yatsine fuska ta karba sannan ta fice ba ko godiya.
Suna shiga ummi ta finciko zakiyya tare da lafta Mata tafi tace shegiya irin ke yarinyar arziki shine harda wani godiya ko toh saina fadawa mommy dama nice me sunan maman mommy ba ke ba. Hankadeta tayi ta fadi tare da gurje hannu. Kuka ta fara yayinda ummi tayi shigewarta cikin clique dinsu Dan itace leader suka nufi aji ana shewa.
Mardiyya best friend din zakiyya ce ta zo ta dagota tareda bata hakuri suka wuce ajinsu suma. Kuma duk abinda ke faruwa ummi na kallo yatsa ta cije Dan haushin mardiyya takeji wai ita ke mayar da kanwarta yar kauye. Murmushi tayi saboda wani makirci data hado musu.
Koda su zakiyya suka shiga aji tana ganin Umar ta fara murmushi tana sauke kai ita a dole sonshi take. Shima dai a nashi bangaren hakane saide ko magana basu tabayi yi wa juna ba. Sai satan kallo. Ganin tana dingishi yasashi zuwa wajenta da sauri ya riko hannunta tare da cewa zakiyya me ya sameki. Kunya ne ya rufeta ta kasa magana. A hankali ta janye hannunta ta zauna a tabarma Dan lokacin ko private school ba ko wanne keda benci ba. Benci 5 a ajin 2 na Mata 3 na maza.
STORY CONTINUES BELOW

Kunya ne ya kama shi amma ya make yayinda mazan ajin suka hau tafi matan kuwa suka cika suka bates Dan haushi. Umar kyakkyawa ne saurayi Dan shekara 15. Ba yan ajinsu kadai ba hatta yan gaba dasu crushing suke akansa.
Daidai lokacin aka kada kararrawa domin al’ijtima(assembly). Kamar kullum yauma zakiyya ce ta daya. Bayan an tashi har bakin kofa Umar ya rako zakiya. Sallama sukayi sai Noke noke take yace zakiyya! Tace na’am yace inasonki. Kallonsa tayi taga da gaske yake kawai sai ta fice a gurje cikin jin kunya. Mota ta shige abbansu yace mamana ya sakamakon naku? Ta Miko masa albarka yasa Mata kamin tace wannan farin cikin Anya babu wata a kasa kuwa. Girgiza kai tayi tace babu.
Sanda suka jira ummi kusan 15 mins kamin ta fito kawaye sun Mata ca ta ko ina.
Gida suka nufa suna isa ta fice yayinda zakiyya ta fito a hankali abbansu ya lura da tafiyarta yace zakiyya lafiya dai ko ?me ya Sami kafanki Sosa kai tayi alamun karya zatayi tace faduwa nayi murmushi yayi Dan yasan ba haka bane kuma ummi nada alaka da wannan amma sai ya basar. Bayan sun shige ciki yace ta Kira masa ummin.
Kiranta tayi nan ma sanda tasha dunguri kamin ta fito. Kememe ta tsaya Akan mahaifin nasu. Tafi uku ya lafta Mata a jere sanda tayi adungure sallar mage kamin ya hau jibgarta.
Ihu ta fara tana neman dauki. Hakuri zakiyya ta fara bawa baban nasu tana kuka domin duk wulakancin da ummi ke Mata tana sonta.
Mommy dake sama tana baccin asara ne ta sauko tana fadin me zan gani haka Alhaji banson wulakanci. Dan bakasan zafin haihuwa ba yasa kake jibgar min yarinya ko? bakasan wahalar da nasha ba saide kaga na dirosu shine zaka…….. itama mari ya yage Mata yace ke badawiyya ni ba mijin tace bane inada iko da gidana karkiga na daga miki kafa ko Nemi ki kawomin rainin hankali. Duk ke kika janyo yarinyar nan bata ganin kan uban kowa da gashi. Wallahi ko kiyayeni. Yana kaiwa nan ya fice domin an fara kiran salla.
Daki uwarsu tasa zakiyya dake ta kuka saboda batason taga iyayenta na fada ta jibgeta. Tun tana kuka har ta dena.
Washe gari ta tashi jikinta duk yayi tsami haka ta shirya suka tafi boko. Umar na tsaye a bakin gate domin both boko da islamiya makaranta daya suke zuwa. Ganin yanda jikinta yayi birtsi birtsi yasa ya jata lungu hankalinshi a tashe yace my zakiyya ya haka? Me ya sameki? Kuka ta fashe dashi kamin tace yayarta ne ta Mata hakan lallashinta yayi ta yi har sukayi missing first period. Dukda cewa ya fita da aji daya a boko hakan bai hanasu zama tare ba. Haka yaci gaba da kula da ita a kwana a tashi har akayi hutu. Allah ya taimaka dukkansu iyayensu nada Karfi Dan haka suke waya ta land line ko kokuma su rubuta letter soyayya suke me tsafta kowa yana fatan idan sun girma suyi aure. Cikin Hutun kullum sai ummi tayi kokarin fita amma uban ya hana haka ta hakura saide Rama da Tasoma yi da alamu akwai abinda ke damunta.
Bayan sun koma islamiya da sati 2 aka Koma boko.
Suna shiga makaranta zakiyya ta tafi wajen farouq yayinda ummi ta nufi bayan ajinsu.
Wani matashi kamar Dan shekaru 17 ne yazo ya sameta ya tara afro a kannan harda sarka tana ganinshi ta rungumesa. Yace my baby! Wannan sati 3 da akayi a hutu bakiji yanda na keji ba kamar nayi hauka. Nan fa suka yi ashararancin su sai lokacin break suka koma cikin yan aji. Nan fa take cewa ina hilwa akace Mata ai hilwa tunda tayi ciki ubanta ya cireta makaranta cika baki ta dinga yi tana cewa Ai itakam ubanta bai isa ba. Nan ma yan clique din tasu staff room suka nufa ko wacce ta nufi wajen nata akayi zina aka kwashe kaya daga gaban annabi. Kuma a cikin staff room din kowa na kallon kowa bayan an gama wannan kuma Mata suka koma wajen Mata maza ma haka. Abin kazanta da kayan Allah wadarai. Matsalar da suka samu shine sun rufe kofofi da ko ina amma sunbar guda biyu.
1. Kofar Allah sun manta da cewa yana ganinsu a duk inda suke.
2. Akwai wata yar karamar window wacce basu rufe ba kuma duk abinda sukayi akan idon zakiyya da mardiyya. Shiyasa tun daga Ranan Ranan zakiyya ta tsani duka biyu kuma yana daya daga cikin dalilin da yasa bata bawa yazeed hakkinshi.
Bayan Sati biyu lokacin birthday din zakiyya saura 1 week. Umar da mardiyya kullum sai sun hadu suna shirye shiryen yadda zasu Mata surprise saide kash. Ummi ta kewaya ta nuna Mata amanarta Suke ci. Tun bata yarda ba har ta fara yarda domin duk sanda suka labe suna magana da tazo sai su canja abin na damunta. Ana saura kwana gobe birthday dinta tana zaune tana addua Allah ya taimaka Mata ya kawo Mata dauki ummi ta shigo. Dariya ta fashe dashi tace ke banziya ce wayace miki Allah zai jiki ko ya ansa addu’ar taki? Babu ko daya farouq dinki da mardiyya sunacin amanarki kuma ba dainawa zasuyi ba gobe ki ritsasu kawai duk sanda kika shiga matsala ba zuwa zakiyi ki shinfida sallaya kina addua ba aikin banza kike ai action kawai zaki dauka.
Da haka da haka ummi ta cirewa zakiyya son Allah a zuciya Ta gurbata Mata tarbiyya. Washe gari kuwa zakiyya tana zuwa ajin da ummi ta fada Mata ta Sami farouq yana taba kirjin mardiyya dukda ko kayansu yananan komai normal.
Nan take ta fara cewa ba ita basu sunci amanarta wa ya mutu wa ya tashi sannan ta fice tana kuka wiwi. Abinda bata sani ba kuwa shine wannan ajin da suke ciki nanne meeting point din duka yan ajinsu before aje school hall inda suka ara daga wajen makaranta domin yin Partyn.
Kan farouq ne yadau zafi ya fice bai ma san inda yake tafiya ba mota yayi ciki dashi kuma akan idon zakiyya domin taga sanda ya fita ta biyo bayansa. Da gudu ta antayo tana zuwa ta janyosa jikinta tana kiran sunansa dakyar ya bude bude idonsa. Kuka take sosai can ya fara magana kamar haka: “zakiyya kisani cewa tun kina nursery 3 nake sonki kuma har yau ban daina ba. Benci amanarki ba ki tambayi kawarki me mukeyi yan ajinku da ajinmu ma shaidu ne. Inaso ace mun girma……” tari mai jini ya sarkesa dadai lokacin mardiyya ta karaso domin taga fitowar zakiyya sunansa ta fara Kira tare da cewa mai ta samesa kuka kawai zakiyya keyi tare da nadamar yarda da abinda ummi ta fada Mata tayi. Magana yaci gaba dayi “naso ace na aureki amma bai yuwuba inasonki wallahi ina… ” kasa karashewa yayi tare da Kamewa can ta saki jikinsa da alamu ya sheka. Ihu ta fara kwallawa hakan shi ya janyo hankalin students aka fara fitowa me gadi na kokarin hanasu akayi sama dashi. Kuka zakiyya keyi harda shidewa mardiyya na tayata.
Aranta Addua take tana cewa Allah indai Kaine Allah ka dawomin da farouq Dina jin shiru yasa ta yarda da maganar ummi. Allah sarki anan ummi ta daura ta akan keken bera.
Tun daga lokacin idon zakiyya ya bude ta bankare itama abin kuwa ya kara karfi ne bayan ance an nemi mardiyya an rasa. Tundaga lokacin ta sauya saide dukda haka bata taba yin zina ba.
Bayan watanni aka gano ummi nada ciki. Hakan yayi sanadin zuciya mahaifinsu ta buga. Hajiya badawiyya kuwa tasa aka barar da cikin. Wasa wasa islamiyar ma suka watsarta bokon ma zakiyya ce ta karashe ummi daga ss2 ta tsaya.
Koda zakiyya ta gama bada labarinnan ta jikawa minal Riga da hawaye. Lallashinta minal tayi kamin suka cigaba da sabgoginsu.
Koda zakiyya ta tambayi yazeed bai hanata zuwa gidansu summy ba domin dadi yaji atleast ta shiryu.
Jibi nayi saiga summy ta tazo daukan zakiyya aiko suka wuce gidansu su summy tunda suka shiga zakiyya yaji hankalinta bai kwanta ba. Drinks aka kawo Mata tasha kadan daganan summy tace “Muje ko? Tana dakinta ne” binta zakiyya tayi a baya haka dai har suka isa zuwa dakin suna shiga summy ta rufe kofa tare da wulli da key din. Kallonta zakiyya tayi tace ban gane ba Menene kuma haka? A zafafe sumaiya ta hada bakinta Dana zakiyya atake zakiyya ta shiga wani yanayi saboda drink din data sha………
TOH FA! SAI KU BIYONI A CHAPTER NA GABA DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA A TSAKANIN SUMAIYA DA ZAKIYYA.
NA GODE SOSAI DA HAKURINKU NA RASHIN JINA 2 DAYS. INA MATUKAR YINKU IRIN TOTALLY DINNAN.
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
miss Untichlobanty 💕
26th January, 2020.Rufe ido zakiyya tayi sakon da sumaiya ke aika Mata na ratsa and then it click to her Cewa wannan abin zunubi babba.
Babu shiri ta hankadeta tare da cewa me haka sumaiya ina maman taki take? Dariya summy ta sheke dashi tace shegiya ni. Ji muryarki yadda kike magana kamar yar kwaya tsabar jarabar Dana tado miki, wa yace miki inada uwa?Matsowa tayi kusa da ita tana yauki tare da shafo Fuskar zakiyya tace haba my zaky basai mun tsaya muna ja inja ba. Mari zakiyya ta yarfa Mata tace kin bani kunya wallahi am ashamed ashe ke fasika ce ban sani ba?kazama,dakikiya kuma jahila? Ke nayi miki kama da yar iska ne? Dariya summy itama tayi tace hmmm lallai ma zakiyya bakisanni ba.
Marinta ta Rama tare da cewa ince ke wayaiya gaki matar manya ko? Kiyita dressing kina bude tsiraici, toh kin budo ni kuma na gani kuma ya min,kuma sai na samu. Tsaki zakiyya taja ta dauko key din da summy ta ajiye ta bude kofar tana kokarin fita summy tace me zakice idan nace kina sa kafarki wajen dakinnan zaki rasa uwarki.
A zafafe zakiyya ta juyo tace ke banson hauka kina jina ko? Karki kuskura kisa uwata a shirmennan naki. Dariya summy ta fashe dashi da kaji amon sautinta babu imani a cikinsa. Tace uhmm su hajiya zakiyya manya!dariya ta kuma fashewa dashi sai lokacin zakiyya ta lura cewa summy ta girmeta sosai,sannan ko dacewa basuyi a matsayin kawaye ba. Zuwa yanzu daga skin tight sai bra ne a jikin summy Wanda zakiyya bata ma San yaushe ta cire kayan ba. Kallon jikinta yayi taga hijab dinta ne ya yamutse.
Kauda kai tayi daga kallon summy dake tunkarota hannunta rike da tablet, nuno Mata video call ne. Mamanta ne a daure a wani store ta jigata sosai da alamu duka aka Mata bakinta har yau yake tsiyayarwa. Tace zakiyya ki taimaka ko me sukeso kiyi musu. Zasu kasheni ke daya zaki iya cetona. Ki taimaka ko biya musu bukatarsu ! Karki tuna abubuwan danayi miki a baya nasan ban kasance uwa ta gari a gare ki ba. Nayi miki alkawari bazan sake ba zan nuna miki soyayya ta uwa wacce ko wacce a diya ke bukata…+
Lokacin zakiyya ta Dade da jikewa da hawaye itakam ta shiga uku tana tsaka me wuya ta bangare daya ran mahaifiyarta dayan bangare kuwa hakkin Allah. Shiru tayi tana tuno maganganun da tayi da minal wata kila zata samu mafita a ciki.
Summy tace kamin na kirga 3 ki yankee shawara. Bindiga aka saita Akan mommy take ta fara cewa don Allah Allah zakiyya dan Allah.
Summy tace 1…………. dogon nazari zakiyya ta fara shin mommy ta cancanci ta sabawa Allah saboda ta cecota? Idan ma ta ceceta akwai probability cewa bata tuba. Toh amma uwa ce fa uwa?
Summy tace 2………. yanzu idan tana cikin sabawa Allah ita da mommyn suka mutu dukansu fa ? Asara bibbiyu kenan. Kai Anya kuwa momy ba so take ta danna kaina a ruwa ba in mutu ina madigo ta mutu tana mushrika? Ajiyan zuciya ta sauke tunowa da yadda mahaifiyar Tata ta dinga bin bokaye har kwanciya tayi dasu duk saboda ta hana mahaifinsu yi Mata kishiya.
TAUUUUUUU !! Taji hakan yasa ta tsorata sosai ta saki tablet dake hannunta summy tayi saurin cafewa tare da cewa ke ya haka zakiyi min asara. Kallon cikin wayan tayi tace wow ji yadda kwakwalwarta ya fito. Don Allah ku fasamin cikin ko naji dadi a raina. Saukar bullet kakeji tace ku cire hanjin ku saka roba zan aikashi wani gur koda ta juyo ta kalli inda zakiyya take tuni ta sume. Tabe baki tayi tace ke kika jiyo dama nima ba bukatarki nake ba. Wayarta ta dauko ta danna Kira ringing 4 yayi kamin aka dauka. Tace hmmm AI tayi taurin kai Dan haka dayan option din mukabi. Allah keson ya ceci Aurenta. Kyaci tayi tace wallahi madam naso ace ta bada hadin kai na rakashe kuma wallahi na saita camera din yadda zai daukemu dakyau da kawai sai mu rife fuskana my sambadawa mijin. Tsaki aka ta dayan bangaren tare da cewa barta hakan ma ya isheta zamuyi tunanin wani abin. Dariya ta kyalkyale dashi tace zakiyya wallahi ko kinki ko kinso sai kin rsbu da yazeed.
Summy tace ma ya zamuyi da ita? Tace Kira su kyankyaso kice su dauketa su yar a wajajen gidanta amma karsu karasa saboda kinsan security din wajen. Suyi using wayanta suyi contacting din wani yazo ya dauke ta sai su ajiye Mata a wajen. Summy tace okay amma kamin a mayar da ita zan iya ……… kingane AI.
STORY CONTINUES BELOW

Ta dayan bangaren tace ke banson shashanci ku miyar da ita nace bakisan inada kishi ba ko? Sgagwaba dummy ta fara tace kai my luv kishin ruwa fa zan mayar kinsan yanzu bakyanan kuma kinsan yadda nake. Ajiyan zuciya madam din ta sauke tace wallahi kamar kinga zuciyata nima na takura da bakyanan amma soon😉kinji ko? Summy tace okay sannan suka kashe wayar.
Haka ko akayi aka yarda zakiyya tare da kiran number din minal saboda shine last call dinta. Nan fa minal ta diburbuce gashi yazeed ya tafi aiki. Ta dinga kiransa baya picking saboda yana meeting. Gashi duk sojojinsa da ta sani ya tafi dasu kuma bataso ta fadawa mom hankalinta ya tashi. Fitowa tayi Joshua yana ganinta yace ma barka da fitowa tace yauwa so nake ka kaini……….
Nan ta kwatanta masa yace ya gane,haka ita da tala suka dauko zakiyya niki niki, sojojin zasu sa Masu hannu tace su barshi tala ma ta isa. Bayan sun dawo suka kaita dakinta daidai lokacin yazeed yayi calling back. Dauka tayi tanata kuka hankali yazeed a take ya tashi tun kamin ta fada mai matsalar. Tambayan duniya yayi Mata tace sai ya dawo zata fada mai. A Emergency ya dawo gida daga shi sai luku. Koda ya iso already idonta ya kumbura,riko hannunshi tayi har dakin zakiyya salati ya fara tare ta cewa me ya sameta haka ya naga goshinta a fashe? Bayanin abinda ta sani minal tayi. Take ya bada order yace a duba anguwar gaba daya daga sunga basu yarda da mutum ba a kamoshi kawai ko Waye sannan ya Kira dr Muhammad. Bayan ya dubata yace firgici ne yasa wutanta daukewa, amma zata iya tashi at any momen…… bai karashe ba sukaji ta fashe da kuka kanta sukayo baki daya. Yin duniya anyi taki yin magana kuma taki daina kuka saboda a firgice take.
Gaba daya ranan dakyar suka karashe, hatta su sahir ko wasa basuyi ba kowa cikin damuwa jugum. Mom kam kasa magana tayi.
Akwana a tashi yau sati daya amma a yan uwan zakiyya babu Wanda ya bugo tunda dama mommyn ta rabasu da Dangin mahaifinsu, danginta ko babu Wanda zakiyya ta sani idan ba ayush ba itama zata can jibge banbancinta da gawa kadan ne. Rayuwa kenan yau Kaine gobe waninka yanzu duk yadda take fantamawa jibi yadda cikin kankanin lokaci DUNIYA tayi Mata atishawan tsiya.
BAYAN WATA HUDU
Rayuwa ta warware ma jeedmar family,minal ta gama zama jarabawarta har admission ya fito tayi su registration in 2 weeks time zata fara zuwa makaranta. Tsakaninta da yazeed kuwa komai ya daidata kuma suni cewa daga ya dawo zata bashi hakkinsa a matsayin welcome gift. Yaune kuma rananda yazeed zai dawo daga mission din daya tafi Kamata yayi ace sun dawo tun last week amma lukman ya Kira yace wani Abu zai tsaida su sai this week. Gidan ya kacame sai aiki ake oga yazeed yayi wata daya baya gida. Ayush had yau shiru kakeji mashkur kuwa ya nemi transfer gaba daya zuwa Nigeria inda ya hada hannu da yazeed suka siye hospital din. Su ya Abubakar ma an saka ranan aurensu kuma yanzu haka saura wata daya Dan haka sunata shiri,Abin saide hamdala.
Su zaliha lamarinsu ba’a cewa komai domin lamarinsu kara gaba yakeyi a kullum sukanyi fada yakai sau 3……..
Minal ne ta fito da gudu hannunta rike da wani container cike da cakes yayinda su sahir ke binta a baya suna cewa mommy zamuci mommy zamuci
Dariya zakiyya ke musu daidai lokacin zaliha ta shigo tana murmushi tace ku kuma lafiya haka kuketa gudu. Rugowa sukayi wajen zaliha sukace yauwa aunty black beauty dan Allah kicewa mommy minal ta bamu cake. Fuskan abin tausayi zaliha tayi Mata tace haba mommy minal bazaki bamu cake din ba? Dariya zakiyya ta fashe dashi tace kede zaliha anyi babbar banza. Guda daya minal ta dauko zata raba musu zaliha tace me kike nufi uwar rowa don Allah mu ki bamu muci mu koshi minal tace ananne kuma kikayi karya daddaya San Baku. Jiniya suka juyo hakan yasa suka firfito waje dukansu mom harda saurinta itace a gaba. Koda motocin suka tsaya ido suka zura domin ganin yazeed dinsu farinciki kuma jagoran gidansu saide me lukman ne ya fito rike da sandar guragu(crotches), ambulance din hospital ne ta shigo aka bude bayanta tare da sauko da gawa take mom ta zube a kasa ba tare da tashirya ba yayinda jiri ya dauki minal itama ta zauna zakiyya kam an fara zama customer din masifa da tashin hankali dan haka sankarewa tayi……….
😢 kai jama’a ban gane ba yazeed,yazeed ya mutu a filin yaki? Waiye huhuu !!!😭😭
Domin samun cigaban wannan labari ku sabarbado comments tare da sharhi masu tarin yawa.
Wannan page sadaukarwa ce ga fateema tafeeda Allah yabar kauna sis.
Lovelies karku damu indai mutum yanayi comment yadda ya kamata toh zan saudakar masa da page
Takuce (shesshekan kuka) KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💔
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.sauko da modern keken guragu wato wheel chair akayi, kofa aka bude aka aka ciro yazeed aka daura akai gaba daya jikinsa bandage ne. Haaaaaah ! Kowa ya kara firgicewa. Firgicinsu na yanzu yafi na sanda sukaga gawa suka dauka yazeed ne, Kai sukam Allah ya duba musu. Daga sun fita daga sannan matsalar sai su fada wancan. Innalillah wa inna ilaihi raji’un shine abinda suketa maimatawa da gudu minal ta rugo tanaso ta fada jikinshi ta rungumeshi amma ba hali saboda jikinshi baki daya ciwone. Dakyar mom ta Mike idanunta sai anbaliyar hawaye suke tace my son? Me zan gani haka? Kaine kuwa ? Ji yadda ka koma. Hawayene ya gangarowa yazeed minal tasa hannu ta goge zakiyya ko tama kasa yin komai kawai kallo take yayinda zaliha ta karasa kusa da mijinta jiki ba kwari riko hannunshi tayi tace ahhh! Ta hararesa kasa kasa tace kaide anyi rago ka duba yazeed jarumi. Turbune fuska yayi yace a haka kika aurenin dai kinga ko bakida bakin magana.
Da badan yanayin da ake ciki ba da babu abinda zai hanasu yin fada. Ciki suka dunguma baki daya batareda sunbi ta kan gawan ba Wanda ya kasance na Joshua.+
Tarairaya da kula kam yazeed yashashi a wajen ahalinsa cikin Kan kanin lokaci duk an since bandage din jikinsa na wuya da hannu ne sukayi saura. Kwance yake kan gado yana anfani da wayana da dayan hannunshi sai ga minal ta shigo niki niki da kayan abinci zakiyya na biye da ita zakiyya ce ta taimaka masa ya zauna minal tace ya yazeed(bata kiransa da yazzy baby a gaban zakiyya) kasan me? Murmushi yayi yace a ah. Tace nayi maka pancake. Murmushinsa ne ya kara fadada yace a lallai yau zanci abinci dayawa.
Zakiyya tace ni kuma zobo na maka yace masha Allah nikam Dan gata ne. Murmushi suka mai kamin suka zuba abincin da zobo zakiyya ce ta zauna a gefensa tana bashi yayinda minal ke masa tausa Kamar yadda dr ya uemura saboda har yanzu baya tafiya dan haka zama waje daya zai iya ja mai matsala.
Dadi yakeji sosai a ranshi sanda yaci ya koshi yayi nat kamin yace na koshi.
Zakiyya tace AI ni mamaki ne ma ya isheni wai yaushe ka fara cin abinci dayawa minal ya nuno yace aunty minal ne ta koyamin ya fadi hakan kamar yaro. Dariya suka mai kamin taja hancin minal kallon juna suka tsayayi. Zakiyya ta lura da hakan aranta tace ya Allah karka raba masoyannan ya Allah ni kuma ka bani Wanda zai nuna min soyayya fiye da wannan. Ganin abin ba karau ba yasa ta tattare kwanukan ta fice dasu tare da rufe musu kofarsu.
Can mutaneku suka farga dubawan da zasuyi sukaga har ta kwashe kwanikan ta fice. Hannun minal yazeed ya riko ya daurata a cinya yace my minal kenan kinsan nayi missing din lips dinki ko ? Murmushi tayi tana Dan sauke kai tace nima domin ta dan rage jin kunyarsa. Pecking lips dinta yayi yace minali na, tace na’am yazzy baby yace akwai wata magana da nake so muyi. Tace ina jinka yace inasonki kuma kema kin sani saide kaddara ta Riga fata domin bazan danne miki hakki ba. Ki saurareni da hankalin fahimta inaso ki sani wannan Abu daya sameni daga Allah ne, hankalinta ne ya fara tashi ganin yana shirin kuka. Shafa kanshi tayi alamun yaci gaba yace ba… zan iya biyawa mace bukatarta balle ta kai ga a Sami rabo. In hankalin minal yayi dubu toh ya tashi amma sai ta dake tace innalillah wa inna ilaihi raji’un!kayi hakuri insha Allah komai zai daidata. Riko hannunta yayi yace inaso ki amince na rabu dake ki samu wani miji kiyi aure domin ko a musulunci zamanmu akwai matsala. Rungumeshi tayi kam tana kuka tace wallahi idan ka kara tunanin rabuwa dani saina falls maka Mari ko da haihuwa ko babu ni zan zauna dakai har abada. Kuka take sosai domin ta tausayawa yazeed saboda yasan yadda yake burin samun haihuwa. Kuka tasha sosai kamin yazeed yace taje ta kiramai zakiyya.
Koda zakiyya taga idanun minal tun daganan tasan akwai matsala cikin tashin hankali tace minal me ya faru? Fada kukayi?girgiza kai kawai tayi kamin tace yana kiranki sannan ta wuce dakinta.
Sallama zakiyya tayi ta shigo amma me? Yazeed ma dai a wargaje take tunani ta fara to kodai sakan minal yayi?
Jiki babu kwari ta karasa ta zauna. Bayani ya Mata yadda yayiwa minal amma batace komai ba can ta sauke ajiyan zuciya tayi salati kamin tace faduwa ce tazo daidai da zama domin kuwa nima ba Dade inaso inzo muyi magana dakai. Bazan boyeta ba tunda nake dakai ban taba gane cewa banasonka ba saida na shiryu,shi yasa ko jini banson hadawa dakai,ashe duk zamannan da muke kudinka da family name nakeso. Da badan kuskurena ba da yanzu kaga jininka domin ni ke Shan magungunan hana haihuwa a baya koda aka Sami kuskure ciki ya shigeni zubarwa nayi. Ina rokonka sa ka yafemin kusa kurai ba bazan kara ba. Tana kaiwa gabannan ta fashe da kuka hawaye ne ya silalo wa yazeed. Indai hakane toh fa zakiyya ta cuceshi amma ya zaiyi ? Dole ya yafe Mata tunda tayi nadama. Paper da Niro ta miko masa tare da cewa na gode da irin soyayyar daka nunamin. Tabbas baka tauyemin hakki ba kuma kikayi tunanin zan rabu dakai Dan abinda ya sameka ne ah ah zan rabu dakai ne saboda na cutar dakai kuma Allah ya kawo me kula dakai kiyimin izini in rubuta takaddar tunda kai hannunka da matsala. Gyada Mata kai yayi yace sau daya ya sake gyada kai. Abin abin tausayi rungumeshi tayi sukayiwa juna dogon sumbata kamar karsu rabu amma dole ta rabu dashi saboda ta kuntata mai dayawa yanzu itama gara tayita dakon sonshi a boye tunda ta nuna batasonshi kuma karya take dukda ko tanason dukiyarshi a baya suna shima tana sonshi. Kawai de ta biyawa son zuciya ne tare da hudubar Sheridan.
Haka ta fito wujiga wujiga ta shiga nata dakin itama sai kuka. Ashe haka zafin zawarci yake? Yanzu shikenan batada aure? Anya batayi kuskure ba kuwa? Ranan ko abinci bataci ba.
Koda yan uwa sukaji lamarin abun Baiyi dadi ba. Barin ma su inna yanda suka nuna kulawa domin da ace wasu iyayen ne rufe ido zasuyi wuce sai an sako musu yarsu, amma su cewa sukayi tayi Wanda yayi Mata idan tanaso ta zauna indai bazata cutu ba.
Wata rana zakiyya tana kokarin fita aiki domin yazeed ya bata manager of art and designing na company din kaya. Sanye take cikin Arabian gown tayi rolling domin yanzu shine dressing dinta. Tana sauri bata Ankare ba sukayi gware da Jamal Wanda keta sauri shima Dan yanzu shi da lukman ke managing companies din yazeed hakan yayi sandiyyan zubewan files dake hannunshi. Tasa hannu zata kwashe shi ma yasa hakan yasa ya riko hannunta a take suka hada ido. Wani yanayi ya fara shiga domin tun kamin yazeed ya auri zakiyya yake sonta domin shi yanason Mata masu kwalisa da wayewa (ba wayewar data sabawa addini ba) tuni boyayyar soyayyar ta yunkuro. Zakiyya kam wani bugo zuciyata yayi Wanda abin ya bata mamaki domin bata taba jin irin haka game da Jamal ba.
Kallon hannun nasu dake hade Dana juna tayi shima ya kalla da sauri ya saka tara da Sosa kai ya bata hakuri. Hakurin itama ta bashi kamin ta fice domin duk wani second da takeyi a wajen bugun zuciyarta karuwa yakeyi.
Koda ta fita motanta kin tashi yayi gashi tayi latti sauran motocin kuma duk sanyi kura saboda hunturun sanyin nan da muke fama dashi, wabi sonja tasa ya wanke Mata tana tsaye sai duba lokaci take Jamal yace kinyi latti ko? Zo muje tare in yaso sai a kawo miki motan kinga dai this is your first week at work. Badan ranta yaso ba haka ta shiga suka fice.
Shiru Motan ya dauka Jamal nason ya Mata magana amma ya rasa mai zakice can yace madam zakiyya yau kinyi kyau. Murmushin take tayi tace na gode dukda ko deep down taji dadi amma ba wannan bane a gabanta. Can yace dan Allah in tambayeke mana tace ina jinka yace wai shin yaushe zaki kara aure idonta ne ya ciko da kwalla Wanda Jamal ya lura dashi hakan yasa yace kiyi hakuri bansan tambayan zai bata miki rai ba. Girgiza kai tayi tace AI babu laifinka daganan kowa yaja bakinshi yayi shiru har suka isa kowa ya wuce office dinsa.
Akwana a tashi yazeed ya daina aiki da keke ya fara using sanda sannan ko ina na jikinsa ya warke sai abinda ba’a rasa ba. Zaune yake kan gado yana nazarinsa minal ta fito daga wanka daga ita sai towel yace my beautiful wife wish…. tare da kashe Mata ido daya sarai ta gane me yake nufi amma tace you wish what. Janyota yayi yace DA SO SAMUNE mu raya sunnah nida ke a daren yau. Murmushin karfafa guiwa tamai tace komai yanada lokaci AI . Shafa kanta ya fara yace yau nayi magana da mashkur kuma yace akwai wani dr daya sani may be he can help, a Germany yake so get ready jibi zamu tafi. Tace okay Toh mikewa tayi ta fara cire masa kaya domin shima yayi wanka. Tsokanarta yake yana fadin iye matar yazeed kefa kiba ma kikayi abinki kamar kazar gona ok? Turo baki tayi tace wallahi karka kara cewa inada kiba idan ba haka ba tam. Yace idan na kara menene hukunci na? Ashararan wasa tamai tace kara ka gani.
Lokacin daga shi sai boxers yayinda take tsaye a tsakanin kafafunsa hannayenta zagaye da wuyansa tunda ta gama cire masa kayan. Gyara zama yayi yace minal yar lukuta. Pecking lips dinsa tayi tace wannan hukun ci da dadi yake kice in yita fada. Ya a
Sake cewa minal mama lutiya wannan Karan kumatunsa tayi pecking, maimatawa yayi Aiko ta fara masa cakulkuli tana cewa wannan shine ainihin hukuncin garin sai ya Rama ya tube Mata towel aiko tayi saurin gyara tare da cewa waiyo. Dariya yayi yace kwantar da hankalin ki ko duka matan duniya zasuyi tsirara babu abinda zan iyayi a halin yanzu. Murmushi kawai tayi kamin ta taimaka mai ya shiga toilet din jacuzzi ya shige abinsa da wandon shi yace ta tsaya a waje ya cire sai ta karba tunda ita uwar kunya ce.
Koda ta karba ta jiya zata fice ya janyota ta fantsama cikin ruwan sannan ya cire towel dinta dayasha ruwa yayi firo dashi. Kokarin tashi takeyi yace bara in zuba ido dakyau kina mikewa inga bulus kinga yanzu rose dinnan da muka zuba akai ya rufa miki asiri. Kuka ta fara mai………
KSI JAMA’A WALLAHI NA GAJI.
MASU KUKAN MUTUWAN YAZEED SAI A DENA KO ?
ME ZAKU IYA CEWA GAME DA ABINDA YA SAMU YAZEED?
SHIN KUNA GANIN ZAKIYYA DA JAMAL ZASU DACE?
DAGA KARSHE WANNAN PAGE SADAUKARWA CE GA Ummuanwar01 , deey_jah,ummasuwaid and sadydanhauwa nagode da comments dinku sauran ma naku yananan tafe2
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💕
31st January,2020.Kuka ta soma mai tace kai yazzy na wannan fa ba adalci bane,fuskar yara ya Mata yace sorry my love kawai inaso muyi wanka tare ne. Turo baki tayi tace ni yanzu gaka fa sanyi nakeji. Lips dinta na kasan ya kamo ya tsotsa,murmushi tayi tare da rufe fuskarta a kirjinsa. Shima murmusawa yayi tare mai sauti. Dagowa tayi ya dangwali hancinta yace wa yaga minal Dina a kasar waje. Dariya tayi tace kyau kenan.
Haka sukayi wanka suka fito suka shirya tace yazzy baby yace na’am tace in the next 2weeks birthday Dina ne fa yace haba? Tace eh yace wow ok.
Zaliha zaune a parlour tana kallon zee world taga an mayar Mata tashan ball. Kicin tayi da ido tare da juyawa aiko kamar yadda take tsammani luku ne a tsaye a bayan kujeran da take. Murmushi yake sakar Mata da ka gani kasan na neman magana ne.
Tsaki taja tare da cewa menene haka ni ka miyar min bakaga ina kallo bane ? Shafa gemunshi yayi kamin ya jewayo ya zauna a gefenta tare da riko hannunta. Fincikewa tayi tana aika masa harara janyota yayi zai rungume ta Mike a take tana mai kallon sama da kasa tace wai me kake nufi ne? Kallonta kawai yakeyi kamin shima ya Mike matsowa ya farayi a take gabanta ya fara lugude saboda wani Abu da ta gani a idonsa. Ko wani takunsa daya tare da zuciyarta yake bugawa jin ta hadu da bango gashi kirjinta na gogan na luku yasa gumi karyo Ma ta. Hannu tasa a kirjinsa jiki babu kwari zata hankadeshi amma ta kasa. Hannunsa daya yasa ya kamo nata duka biyu tareda likawa da bango a take ta hadiyi wani yawu kutt. Gaba daya ta tsure ta rude ta kidime sai zazzare ido take numfashinsa ke sauka a fiskanta har ya hade goshinsu. Dayan hannunsa yasa ya riko fuskarta tareda fara shinshinar wuyanta. Ido ta rufe ta ruf yayinda take juya kai gefe domin bashi dama. Jin ya tsaya yasata bude ido. Kallonta yake yana kunshe dariya aiko suna hada ido ya fashe da dariya baya ya fara yi yana dariya harda kama ciki tareda nunata. Cikin dariya yace dubata kin dauka wani abin zan miki sai anyi magana ki bude bakin cakwaikwaiwa kice bakyaso na. Harara ta zabga mai kamar idonta zai fita tare da tsaki ta wuce bangan bangan ta fada daki tareda buga kofa. Kan gado ta fada ta fara chatting ko ta huce haushi ji take kamar ta kamoshi tayi masa dukan tsiya.+
Bayan ya gama kallon ball dinshi ya shiga dining area babu abinci kitchen ya shiga shima yaga empty.
Knocking yayi har sau uku amma ba’a amsa ba hakan yasa ya Shiga kai tsaye kwance ya sameta tayi bacci a ruf da cikin tana chatting messages sai shigowa yake kwanciya yayi luf Akan bayanta tare da zura hannunsa ya rungume kunkuminta. Cikin bacci taji Abu me nauyi ya danneta hakan yasa ta bude ido badon taso ba Dan mafarkin sulaiman dinta take wai har sun haifi yara.
Kamshin turaren lukman da taji shi ya tabbatar Mata da cewa shine ba kowa ba. Kokari juyawa tayi amma ina linzami yafi karfin bakin kaza.
Yace my wife ina abinci na tsaki taja tace ban dafa ko kaga alamun nayi girki ne? Nifa la takuramini ehe maida bakinka kace kowa yayi rayuwarsa yanzu kuma zaka wani zo kana likemin. Wata bazawarar Dariya yayi yace hmm bakida dama nide yanzu ba fada naso nema ba so nake ki dafa mana abinci. Dariya ta sheke dashi dashi tace idan naki fa sai ayi kaka?
Yace ki ki yi din kiga ikon Allah tace toh baza’ayi ba. Zip din Riga ya fara bude Mata tace me hakan bai kulata ba ya fara balle Ma ta bra yace ince bazakiyi ba tace waiyo kayi hakuri dan Allah zanyi wallahi zanyi yace good for you. Rufe Mata yayi ya rufe zip din kamin ya ciccibeta tana wantsal wantsal bai direta ko ina ba sai kitchen a gaban gas cooker yace fara harararsa tayi tace toh ba sai na hada kayan ba lo kanka zan dafa? Hade rai yayi yace baki daddara ba ko? Janyota yayi da karfi ta fadi jikinsa take ya fara kissing dinta a zafafe tun tanajin sugar har taga ba haza ta fara kuka. Shikam yama mance Dan kokarin bude Mata zip ya fara karan kuka data kara shi yasa ya dawo sense dinsa saketa yayi tare da goge bakinsa sannan yace na baki 10mins ki dafo min abinci ki kawomin. Da sauri ta girgiza kai yace good kamin ya fice yana murmushi itako gaba daya ta tsure da sauri ta daura indomie. Tana cikin zubawa a tukunya yace saura minti 2. Ta sake rikicewa hade hannu biyu tayi a gaban gas cooker tayi kneel down tare da cewa kayiwa Allah ka dafo na shiga uku waiyo. Lukman dake labe yana Mata video sai dariya. Itako hawaye take tana yarfa hannu tace noodles ka taimaka ka dahu kar ya dawo waiyo na shiga uku.
Koda ta kawo yace kinyi lattin minti biyu 2 rau rau tayi da ido tace kayi hakuri abincin ne bai dahu ba. Yace hmm zanyi tunani juyawa tayi zata tafi ya make mazaunanta ta jiyo tana kallonta da mamaki yace ko zaki Rama ne da sauri ta girgiza kai tana shigewa daki tace Allah ya isa na kamin ta rufe dakin da sauri Dan mugun tsoron lukman ta farayi.
Minal kuwa karatu ta koyawa yaranta kamar kullum yanzu har sun haddad izu biyar sannan sunyi Rabin hakkul Mubin su usulus Salasa ma duk sunyi nisa azkar ma haka.
Wajen zakiyya taje suka sha hira abinsu domin yanzu sun zama aminan juna. Minal tace nikam ina Jamal fa ya kuka kaya? Murmushi zakiyya tayi tace hmm ai in fada miki………..
Zakiyya zaune a office taji anyi knocking amsawa tayi tare da bada izinin shigowa ba tare da ta dauke idonta daga kan screen din system dinta ba. Zama yayi a daya daga cikin kujerun dake gabanta,kamshin turarenshi shi ya sanar da ita cewa Jamal ne ba kowa ba hakan yasa ta dago suna hada ido ta masa murmushi. Gaisawa sukayi yace ya aikin ? Tace Alhamdulillah gashinan muna fama. Mikewa tayi domin hado masa tea sai binta yake da kallo har ta gama, ahanyarta na kawowa tayi Tuntube da rug din dake shinfide a office din cup din ya fadi ya fashe ita kuma ta fada jikinshi kallon kallo suka tsaya yi kamin tayi saurin mikewa tana fadin astagfirullah am sorry. Gaba daya tama rikice rashin sanin abin yi yasa ta sa hannu ta fara dauke kwalaben amma kamin jamal ya hanata har ta yanki kanta.
Yace subhanallah tare da rike yatsan yana fadin wa yasaki ? Da kin Kira anzo an miki AI dubi kinjiwa kanji ciwo itakam bata masan yanayi ba Dan kawai kallon yanda ya kidime take tare da yadda yake motsa bakinsa. Kai Anya baifi yazeed kyau ba kuwa( Nace a ah hajiya ta kede kawai so ya rufe miki idanu) tissue yasa Mata kamin ya tisata har company clinic dukda ko tayita magiya ai ciwon ba babba bane amma fa deep down dadi takeji kamar ta mutu.3
Dariya minal ta sheke dashi tace kina wuta mutuniyata kamin suka tafa minal tace ni fa na matsu ayi aurenku fa. Zakiyya tace ke😳! Rufamin asiri nace miki muna soyayya ne? Dariya minal tayi tace saima kin fada toh wallahi ko fans din KURUCIYAR MINAL aka tambaya sunsan cewa kina sonshi. Fans ko karya nayi?2
TOH ANAN ZAN DASA AYA MASOYA SAI KU AMSAWA MINAL TAMBAYARTA.
ME ZAKU IYA CEWA GAME DA LAMARIN ZALIHA DA LUKMAN?
YA LABARIN AUREN SU YA ABUBAKAR ? KU BIYONI A SANNU TARE DA COMMENTING DOMIN SAMUN AMSOSHIN TAMBAYARKU.
WANNAN PAGE SADAUKARWA NE GA NAMECY ALLAH YABAR KAUNA.
KARKU MANTA TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
miss Untichlobanty 💕
2nd February, 2020Haka duka dinga musu daga karshe zakiyya tace taji ta yarda ta dan fara sonshi amma kar minal ta fada ma kowa.
Da daddare minal na dakin yazeed tana hada kayan tafiyansu domin karfe 2 dare jiginsu zai tashi yazeed yace baby kin taba hawa jirgin sama girgiza kai tayi yace tab ai kina hawa ki fara tunowa da Allah Dan idan ba ragewa da addu’a kukayi jirgin kifawa zai daku yayi adungure sallar mage. Zaro ido tayi tace kace Allah? Dariya yayi yace zan miki karya ne? Girgiza kai tayi kayansa ta hada masa kaf shiko ya cigaba da game dinsa can yaga kamar bata saka nata kayan a box din yace a wani akwati zakisa kayanki ne girgiza kai tayi jiki a sanyaye. Alamu ya Mata da tazo, ta taho kafafunta na hardewa. Zaunatta yayi a tsakanin kafafunsa yace ya akayi ? Danshi yama manta da cewa ya tsokaneta dazu.
Muryata na rawa tace na fasa tafiya ne. Tace kamar ya kin fasa tafiya ? Me yasa? Kuka ne ya kwace Mata tace ba kai kace jirgi zaiyi adungure sallar mage dani ba? Dariya ce taso kwacewa yazeed amma ya matse kwantarta yayi a jikinsa yace ai ba kowani lokaci bane yake kifawa sai idan masu zunubi sunyi yawa a ciki, bakiji nace kiyi addua ba? Kallonsa tayi tana goge kwalla tace nidai gaskiya bazan shiga ba kawai mu fasa tafiyannan. Zaro ido yayi yace ku fasa kuma? Idan mun fasa toh ya batun babies dinmu ? Alamun tunani tayi yayinda yaketa kunshe dariyarsa. Tace toh ka tafi kai daya, turo baki yayi yace dama bakya sona? Girgiza kai tayi tace toh tare zamu tafi. Wani kwalla ne ya sake tsiranyowa daga fuskarta har tausayi ta bawa yazeed. Haka ta hada kayanta tana kuka dan gani take daga daren yau sunanta gawa. Tunanin zucin da take ne ya baiyana. Tace oh su nima an zama labari, Dariya ce ta kufcewa yazeed yayi saurin mayar da ita tari.2
Haka suka kwanta tare da saita alarm din karfe 12:00am minal kam ta kasa rintsawa sai juyi take tana lissafa abubuwan alkairin da tayi wanda take iya tunawa,ajiyan zuciya ta sauke tace da sauki ma ko na mutu ina sa ran shiga aljanna. Yazeed yana Jinta domin shima baiyi bacci ba Dan sai nuku nuku take a jikinsa ga ruwan hawaye dake jika masa Riga. Haka alarm ya kada suka tashi suka shirya minal sai kuka take tana fadin ni banason injeeee😭😭! Koda sukaje yiwa mom sallama taga yanda idon minal ya kumbura tace lafiya ko bakida lafiya ne? Shiru tayi tana tsittsilla ido kamar mara gaskiya yazeed yace cikinta ne yadanyi Mata ciwo amma gashinan dai yanzu tasan warke. Mom tace toh Allah ya kara sauki a ya stare hanya haka kowa ya taso akayi musu rakiya har airport bayan anyi clearing dinsu kamin su wuce ne minal ta kebe da zakiyya. Suna shiga toilet din zakiyya tace lafiya minal tace don Allah zakiyya kin taba shiga jirgi ko? Zakiyya tace sosai ma kuwa wani abin ne? Tace wai da gaske ne yanayi ‘kolin ‘koli da mutane ya ‘kwala da kasa. Zakiyya tace wa ya fada miki? Idonta ne ya ciko da hawaye tace yazeed ne. Zakiyya ta gane franking dinta yayi shiyasa tace ehhh toh bai fiya yi ba amma dai id…..
Kuka mai karfi minal tasa hakan ya hana zakiyya karashe maganarta, nan fa tahau lallashi ana cikin haka yazeed ya Kira wai suna inane? za’a fara boarding.
Koda suka zo kasa kasa da murya zakiyya tayi tace Allah kaide yazeed bakada Kirki dubi yadda kabi duk ka ruda yar mutane. Dariya yayi kasa kasa tace zakiyya kenan babu ruwanki media kice na tuna miki da sanda na tsoratar dake akan tsaka. Dariya sukayi a tare tunowa da yadda zakiyya ta rude lokacin hannu ta daga zata makeshi kamin ta tuna da cewa ba mijinta bane. Hakan yasa dariyar fuskassu ta dauke murmushi tayi tace Allah ya kiyaye hanya make sure idan zaku dawo ku dawo da mai dadi, ku tafi ku biyu ku dawo ku uku. Jinjina kai yayi yace da izinin Allah daga nan ya kamo hannun minal suka wuce.
Koda fa minal taga jirgi da girmansa sai hankalinta ya kara tashi. Cije wa ta fara yi yazeed yana janta yace ke menene haka wai? Hawaye na dawafi a fuskarta tace nace na fasa, wallahi na hakura. Dafe kai yayi yace AI ba komawa yanzu kina komawa za’ace ke yar boko haram ce. Tace toh ai ni matarka ce kuma ai soja bazai zauna da yar boko haram ba. Yace toh ai karin matsala kenan cewa zasuyi na kasheki a take kawai a huta kuma kinsan bazan iya ba kinga za’a ce mun hada baki sai akashemu duka biyu kinaso a kashemu? Tace a ah yace toh maza muje haka suka shiga kirjinta na duka dib! dib!! dib!!! dib!!!! dib!!!!! dib!!!!!!
STORY CONTINUES BELOW

Kadawa cikinta yayi koda suka zauna tace inane toilet dan Allah ? Nuna Mata yayi tayi using tana shirin fitowa taji ana announcing za’a tashi babu shiri ta fito kamin ta karaso sit dinsu wani ya kamata kurrrr! Cikinta ya bada sauri Allah ya taimaka Dan ma class dinsu babu mutane dayawa da ace irinsu economy suka shiga da an Sami matsala ai. Wani zubin auren me kudin ma nada dadi.
Zama yayi tare da riko yazeed ‘kam ‘Kam a tsorace tace yanzu zai tashi ko? Yace eh,habawa jin sautin engine din jirgi take wani fitsari ya matsota. Yazeed yace kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru. Tafiya jirgin ya fara tace kai ashe ma kamar mota ne naketa jin tsoro, window ta kalla taga still suna kan kwalta tace toh amma ya muke tafiya Akan kwalta bayan kuma n……… tashin da jirgin ya farayi yasa minal kasa karashe maganarta kara riko yazeed tayi tana karanto duk addu’ar da tazo bakinta.
Wata budurwa daketa kallonsu tun dazu sai dariya take. Koda jirgi ya daidaita a sararin samaniya budurwa tace kai gaskiya sister kinada abin dariya sai kace yau kika fara hawa jirgi? Hannu yazeed yasa yana goge wa minal hawaye kamin yace baby na kede kinji kunya,minal jam turo baki tayi tareda yiwa wannan budurwar gwaliyo tace kede kice kishi kike bakida mijiiiii
Wani saurayi dake gefen budurwar ne yace my love rabu da ita da alamu bata ganine. Kallon yazeed yayi yace nikam wannan kamar captain yazeed ko? Murmushi yazeed yayi yace nine,musabaha sukayi kamin suka dan fara hira kamin kace me tuni sun saki jiki sun fara hira saurayin me suna Ahmad yace kamar yadda muka fada muku mu sabin ma’aurata ne so zamuje honeymoon ne yazeed yace aiya mu medical treatment zamu je daga nan sai mudan huta. Matarsa mai suna ameera tace gaskiya kanada kunada kirki sosai. Daganan kowa yaci gaba da sabgar gabansa. Minal tace wai ina sojojinka ne ko an hana musu Visa ne murmushi yayi yace aisu military ne so zasu iya fita amma da guda daya na taho idan naje can zasu bani na kasarsu. Tace da wa muka taho toh ? Yace kiyi guessing tace Joshua? Yace kin manta ya mutu? Tace Ezekiel? Yace nope Ezekiel ai yaje kauyensu tace toh ni ban sani ba. Murmushi yayi yace da lukman na taho ihu tayi tace da luku da zaliha mukazo? sauran mutanen dake wajen suka kallosu danma duka duka su 10 ne.
Zaunar da ita yayi yace ke Shashasha bakisan a cikin mutane muke ba ? Sannan ko kin manta da cewa jirgi ne da kike kokarin tsayawa tace au na manta ne.
Ameera tace lafiya take ihu? Minal tace albishir yamin shiyasa kamin suka cigaba da magana tace toh ya basu zauna tare da mu ba yace saboda wasu sun rigamu kinga babu dadi ace anyi cancelling saboda a bamu a rashin Adalci ne ko? Ta daga kai yace yanzu suna business class idan mun sauka zamu hadu.
Surutu taci gaba da mai har bacci ya dauketa. Gyara Mata kwanciya yayi kamin ya kunna film abunsa.
ALHAMDULILLAH!
Anan na kawo karshe littafin KURUCIYAR MINAL da fatan an karu kuma an fadakartu.
OUR YAZEED
1
OUR MINAL

*Valentine’s* *Day*
Is a jaahiliya( *Ignorant)*
Roman festival,
which continued to be celebrated until after the Romans became *Christian* .
This festival became connected with the saint known as *Valentine* who was sentenced to death on *14* *February* *270* *CE* . The kuffaar still celebrate this festival, during which immorality and evil are practised widely.
The *scholars* have issued fatwas (lectures) stating that it is haraam to celebrate Valentine’s Day.
*Shaykh* *Ibn* ‘ *Uthaymeen* (may Allaah have mercy on him) was asked:
In recent times the celebration of Valentine’s Day has become widespread, especially among female students.
It is a Christian festival where people dress completely in red, including clothes and shoes, and they exchange red flowers.
We hope that you can explain the ruling on celebrating this festival, and what your advice is to *Muslims* with regard to such matters;
May *Allaah* bless you and take care of you Aameen🤲.
He *answered* :+
Celebrating Valentine’s Day is not *permissible* for a number of reasons.
*1* – It is an innovated festival for which there is no basis in *Islam* .
*2* – It promotes *immorality* in the name of love
*3* – It calls for hearts to be preoccupied with *foolish* matters that are contrary to the way of the righteous
May *Allaah* be pleased with them Aameen🤲.
RECAP…..
Surutu taci gaba da mai har bacci ya dauketa. Gyara Mata kwanciya yayi kamin ya kunna film abunsa…….
Koda jirginsu ya iso tashinta yayi tunda ba halin ya dauketa, ta departures’ door suka fito suka fito suka hango cars gida biyu ga wani ya daga carbon paper an rubuta captain yazeed abdulmajeed wajen motan suka nufa nan sojoji sula Sara masa direct hotel din da zasu sauka akayi dasu minal da zaliha an saki baki yayinda luku ke cin magani dan yanzu baya sakar wa zaliha fuska.
Akwana atashi anyiwa yazeed aiki kuma its successful. Nan fa su minal aka rikice nesa yazo kusa. Dakyar da dubara akayi abin, kunya duk ya isheta Dan gani take kowa yasan abinda ya faru.
Wasa wasa yau watansu 3 a Germany amma shiru kake ji babu ciki babu alamarsa ga yazeed yabar aiki jingim kuma next week za’ayi bikin kara masa girma wato ya zama major general yazeed abdulmajeed Umar.
Haka suka tattara ya nasu ya nasu suka dawo mom duk ta damu saboda tanason taga jikokinta kamin rai yayi halinsa tunda batasan sanda zata tafi ba.
Koda suka dawo Nigeria har anyi auren laila da ya Abubakar da kuma zakiyya da Jamal ba tare da bata lokaci ba. Yanzu haka laila nada cikin wata da sati biyu daya ma minal da fari ta dau abin wasa amma da taga cikin Laila abin yadan fara damunta amma ganin ai ba’a wani Dade ba yasa ta kwantar da hankalinta, yazeed na lura da ita kaf amma ya zuba Mata ido.
Shiri suketa yi yayinda minal da zaliha keta yin fada akan lallai sai minal tayi kwalliya yayinda ta dage cewa bazata yi ba.
Zaliha tace kinsan Allah idan dai bazakiyi kwalliyar nan ba zamuyi fada ? Bakisan cewa za’a dauke ki a camera bane ga yan jaridu da gidan talabijin dukzasu zo minal tace tunda ba gasar kyau za’aje ba bazanyi ba kuma ai miji akewa kwalliya ba ƙartin banza dawofi ba. Kuma ni ance miki zanje ne dan adaukeni? Zanje ne Dan mijina. Dauko gyalen da zatayi rolling tayi Dan kayan da tasa baya bukatar hijab ta dau Jakarta ta fice dan zaliha ta bata haushi.
STORY CONTINUES BELOW


A bakin kofan side dinta tayi kicibus da yazeed ciccibarta yayi yana fadin wa ya tabamin baby na? Dauke kai tai tana kumbura yace my minal fishing harda ni ne? Sharesa tayi bai dirar da ita ko ina ba sai dakinsa, dakyar yashanyo kanta suka sha romance ganin yana neman zurfafawa yasata guduwa.
Haka akayi bikin Karin matsayi akayi su pictures kowa na farin ciki aka watsesaide kash basusan cewa nanne farin matsalar su ba.
Yazeed kwance kan cinya minal a parlour suna kallon wani Indian series tsabar abin tausayi minal batasan sanda ta fashe da kuka ba dariya yazeed keta Ma ta wai ta jona Shaun asararru masu yiwa film kuka sai turo kanshi take tana ya tashi tunda abin hakane daidai lokacin luku ya tsindumo babu ko sallama sai haki yake da alamu gudu yayi. Yace ina wayarka inara kiranka baka daga ba? Yazeed yace ba wannan yafi muhimmanci ba, wa ya baka izinin diro min cikin bangare ba ko sallama. Tsaki lukman yaja cikin haki yace kai dalla share wannan bakas……. bai karashe ba yazeed yakai masa naushi tsabar kishi. Minal tayi saurin rikeshi tare da kallon luku tace ya akayi? Yace government tasa an rufe gaba daya account din yazeed saboda ana zargin wai ya hada baki da yan siyasa anacin kudin kasa sannan bazai iya sayar da kadarorinsa ba ma atakaice de har company yanzu duk NASA ne amma suna under government so he does not have a say a kansu har nanda 3 months Abu daya aka barma daga gidannan sai ka zabi mota daya. Yanzu haka EFCC suna bin cike kuma you can’t use your passport kamar kasan ba kuma baza’a baka Visa bama koda emergency har sai 3 months ya cika.
Yazeed ya zama shock ma dan shi baya ko irin kai wa yan siyasa ziyara da akeyi balle ya saci kudi daga jin magana akwai tuggu a ciki. Bakinsa na rawa yace menene hadin companies din mahaifi na da za’a saka a ciki ? Luku yace saboda idan ta tabbata gaskiya zai zama na gwamnati wai shine hukuncin ka.
Yace ya batun Wanda na bayar dasu ga families Dina? Luku yace eh wannan basu da harka dashi tunda yanzu ba naka bane ajiyan zuciya ya sauke tace atleast munada yadda zamuci abinci maza ka hada meeting da uncles Dina baki daya on Saturday, Luku yace sure kamin ya fice.
Gumi ke tsattsafowa yazeed domin ba dukiya daya rasa bane ta dameshi yadda aka bata masa suna bai ji ba bai gani ba. Rungume sa minal tayi tare da kwantar dashi a kirjinta tace yazzy baby karka damu komai zai wuce is part of kaddarar mu.
Haka yaci gaba da basa baki har yayi bacci a kirjinta sai alaokacin ta lura da yadda hawayensa ya kika Mata Riga. Ajiyan zuciya ta sauke kamin tayi nata kukan Dan ta daure ne kar ta karya masa guiwa.
🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹🍀🌹
🤣Darius take shekawa abinta tare da cewa kai nifa shegiyace duk wadda ya taboni toh shida kwanciyan hankali sun raba kafa kamar aljanna da wuta.
Mummunin Alhajin da take zaune a cinyarsa ne ya sheke da dariya yace kaji shegiya wai dama kinsan akwai wuta da aljanna kike wannan tsiyar? Hade rai yayi Tace me kake nufi? Daidai lokacin wayanta yayi ringing ta dauka tace ya akayi ta dayan bangaren akace gaskiya fa madam mugu(bokanta) yana korafi cewa idan dai bazaki dinga zuwa yana biyan bukatar sa ba to saide ko dinga aiko da jarirai uku idan ba haka ba ku ɓaɓe. Tsaki Taja tace ni rabani da jarabarsa ban iyawa ga warin da yake zan karo ma 500k a samo Karin jaririn akai masa. Ta dayan bangaren akace hakan ma yayi.
Daga nan ta kashe wayan Alhaji yace amma baby wai me suka miki hakane kika tsanesu da kike kashe irin wannan kudi? Murmushin rashin imani tayi tace hmm bazata gane ba. Yace ada na barsu ganin abokin hamaiyar tawa ya mutu amma yanzu Dana hadu dake sai naji dole ma in ga kayansu musamman yanda dan ke nema yafi uban yin nasara.
Sauka tayi daga cinyarsa tare da fara safa da marwa a dakin tace kiyaiyar danake musu tafi Wanda kafirai keyiwa annabi na samesu fiye da yadda na tsani mutuwa ta kai Alhaji bari kaji idan har zanga sun kaskanta sun wahalu a duniya toh wallahi babu ja in ja na yarda in shiga wutar jahannama indai sun wahala. Banida matsala koda kuwa za’a haɗa ni da shedan a wuta a matsayin roommates.
Jinjina kai yayi kamin ya tattaro ya harhado tumbinsa ya Mike yaje ya rungume ta ta baya yace yanzu ne na haɗ da macen data dace wacce bata tsoron ta baci indai saurinta zai cika gaskiya wannan jawabi naki ya kara sa min kaunarki a zuciyata.
Juyawa tayi tace Allah Alhaji na? Yace kwarai ma kuwa yanzu yadda zamuyi dasu Dan nima a shirye nake tsanani dai ace wuta za’a samu toh ni ALHAJI TUKUR GADON ƘAYA na bada ticket din aljanna ta Dan in kuntata ma ahalin ALHAJI ABDULMAJEED UMAR. Dariya suka fashe dashi tace kaga mu hanzarta domin na koma gida daga nan suka shiga aikata ashararancin su.2
WANENE ALHAJI TUKUR GADON KAYA? WANI ATTAJIRIN MAI KUDI NE WANDA SUKAYI TASHE TAREDA ABDULMAJEED WATO BABAN YAZEED INDA YAKE DAUKE DA MUGUN HASSADA MA ABDULMAJEED SABODA YA FISHI YIN NASARA.
DA FARI JEEDMAR A BAUCHI SUKE DA ZAMA TAKURAR DA TUKUR GADON KAYA YA MUSU YASA SUKA KOMA GOMBE NAN MA YA BISU,SUKA LULA ADAMAWA,YA BISU SUKAYI KANO, YA BISU SUKAYI, SOKOTO LOKACIN AN HAIFI YAZEED AMMA YA BISU NAN MA SAI SUKA KOMA ABUJA TOH ANAN NE SUKA ZAUNA NA SHEKARA 4 KAMIN YA SAKE BIYOSU SUKA KOMA KADUNA ANAN NE AKAYITA TA KARE TUNDA ABDULMAJEED DIN YA MUTU BA SHIKENAN BA? TOH ASHE
DAI BAI HAKURA BA GASHI KUMA YA SAMU WACCE TA FISHJ DAUKAN ZAFI LAMARIN SAI YADDA ALLAH YAYI.
Ina mai lallashin ku na rashin jina da kuka yi abubuwa ne suka Dan taso min da fatan za’a min uziri?
Shin me zaku iya cewa gameda batun Alhaji TUKUR GADON KAYA? Ya kuke ganin lamarin nan zai kaya a tsakanjn su ?
Shin in karar da littafinnan da wuri ko kuma acid gaba da gashi?
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU wato
Miss_untichlobanty 💕
14th February, 2020
Don’t forget to vote and shareSauri minal keta yi tana tsallake steps da bibbiyu saboda lattin da sukayi domin yau jirginsu zai daga zuwa Abuja inda zasuje baban jeedmar group kuma anan ne za’ayi meeting din tallafawa yazeed kamin government ta wankesa.
Bude Mata kofa kurtu yayi ta shige luku ya finciki mota. Ba bata lokaci jirginsu ya daga sai federal capital territory of Nigeria.
Koda suka isa yazeed bai tsaya isa gida ba direct jeedmar group ya nufa. Sunayin parking ya fito cikin kwarjini da haiba yana takunsa mai daukan hankali gwanin ban sha’awa. Dukda cewa a cikin damuwa yake hakan bai hana kyawunsa fitowa ba.
Ezekiel da lukman kawai aka bar masa a matsayin escorts dinsa, sai masu gadin gidansa shima an rage wasu daga cikin su. Haka masu yin hidima duk an rage masa kuma duk munafurcin Alhaji tukur gadon kaya ne.
Tun daga bakin kofa ake gaishe sa tare da buda hanya yana zuwa bakin kofan shiga kofan yace “new individual detected please wait ……” scanning iris dinsa yayi kamin yace “welcome president it is nice of you to visit kindly put your thumb”
Saka thumb din nasa yayi take kofar ta bude masa gaba daya directors sun jeru Dan haka yana shigowa suka bi bayansa.
Files suka fara miko masa ya daga musu hannu alamun not now. Suna shiga gaba daya uncles din nasa suka Mike Yana zama suma suka zazzauna. Yace good day to you all ! As we already know we are here to discuss…….. nan ya musu bayani ya sanar dasu duk abinda yake wakana sannan yace zasuyi signing contract before abubuwa su wartsake masa zasu dinga bashi 10% percent na ribar da suka samu idan companies dinsa suka dawo zai biya su.+
Abinda ya basa mamaki shine yanda sukayi caaa! Sukace Sam Sam basusan wannan labarin ba. Daga karshe ma watsewa sukayi ba’a gama meeting din ba hakan yasa ran yazeed ya baci kuma ya tabbatar da cewa hatta dan uwan ka zai iya cutarka sannan sai ka shiga matsala zaka gane masu sonka. Fita yayi suka tafi ainihin family house dinsu dake central area, ba’a cewa komai domin yafi na Kaduna kyau masha Allah tabarakallah.
A parlour ya samu minal ga abinci an kawo Mata amma ta kasa ci tayi jungum jungum. Umma hanifa dattijuwa ce kuma me aikin su yazeed ne tun suna Abuja ganin batada kowa na dangi sai Allah yasa koda zasu bar Abuja basu sallame ta ba, sai suka barta taci gaba da zama a gidan tana gyarashi kuma ana biyanta kudinta har yau sannan ba ita kadai bane akwai maids guda goma.
Gaishesa sukayi kamin suka watse, gaisawa sukayi da umma hani kamin ta basu waje saboda ta fahimci suna bukatar hakan.
Riko hannun minal yayi zuwa daki duk ta kagu taji yadda aka kaya suna shiga tace da fatan komai lafiya? Ajiyan zuciya kawai yayi, hakan yasa ta fahimci me yake nufi baki ta basa kamin ta dauko musu abinci cikin Muryan shekiyanci yace bazai ci ba yasani ko akwai poison a ciki ta masa pancake kawai kuma hakan akayi.
Kwanciya yayi bayan yayi sallar azahar ta ja masa bargo kamin ta koma kan couch ta fara nazarin yadda lamarin zai bille. Zaro ido tayi tare da murmushi alamar idea tazo Mata hakan yasa ta nufi jakar yazeed ta dauko paper da pen ta fara rubuta list. Sallan la’asar da aka Kira yasa ta tasheshi tana mai cigaba da rubutu. Saukowa yayi tare dayin bismillah yaga ta nata rubutu baibi ta kanta ba yayi alwala ya fito still tana rubutu.
Sansadowa yayi ya warce papers tare da cewa me ki keyine baby. Turo baki tayi tare da kokarin kwace paper dinta canja hannu ya fara yi sanda ya bata wahala kamin ya bata. Yace list din menene wannan? tace list din kayan abinci ne. Dafatan akwai space a group building yace eh tace masha Allah daga gobe zamu fara saida snacks and desserts sannan zamu dinga yin contract na abinci. Murmushi kawai yayi sannan ya tashi ya fice da sauri domin idonsa ya ciko da kwalla kar minal ta gani. Ita ko jikinta yayi sanyi ta dauka idea dinta ne bayaso hakan yasa ta yaga papern sannan ta fada gado ta fara kuka. Ace mijinta yana matsanancin hali kuma bazata iya taimaka wa ba?
Yazeed kam kukan farin ciki ne ya kama sa da nadaman yadda ya dinga treating dinta, Allah yasha dashi da ace ya sake ta da yayi babban asara. Komawa yayi yaga tana kuka yasa yayi saurin karasawa bakin gadon tare da fadin baby na lafiya kuma juyawa yayi ya kalli kujeran da suka zauna yaga ta yaga papern. Da sauri ya kwaso su kamin ya dawo gefenta ya zauna tare da fadin ya haka ? Me yasa kika yaga mana plan din? Cikin shessheka ta tashi tare da cewa na dauka bai maka bane ace kana da kudi kana da group ince maka ka fara saida abinci dukda cewa quantity da quality me kyau ne kuma naga cewa ba’a daukan shawaran Mata.
Murmushi yayi ya goge Mata hawaye tare da cewa wa yace miki na Rena shawaranki ? AI sana’a bata kadan albarka kawai ake nema. Batun shawara kuwa kin fini karfin tunani ma amatsayinki na mace. Murmushi tayi tace Allah? Yace kwarai kuwa mata ta sannan ya rungume ta.
Pieces din paper din ya bata kamin ya fita ya karbo glue ya like musu takardan sannan ya janyota suka baza shopping din kayan abincin su Dan da zafi zafi ake dukan karfe.
Gidan radio da talabijin aka sanar AI kan kace me wannan sun Sami order yafi dari saboda ana matukar son yazeed. Minal sanda ta tsorata ta fara darewa tana ganin bazata iya ba yazeed yace karka damu zasu dinga Tahowa da masu aikin gidan su sai su dinga tayata, kuma ai shima yananan.
Haka suka dawo gida sunyi likis ranan da wuri suka kwanta 9pm a gado ta musu.
Kirrrrrr!kirrrrr!kirrrrrr!
Tsaki minal taja tare da sake shigewa jikin yazeed. Bacci sukayi bayan sunyi sallan subh sai suka saita Alarm din 6:30am suka saita dan shirya tafiya aikin su akan lokaci, badan ranta yaso ba ta tashi suka shirya sai jeedmar group sai dadi takeji.
Direct area dinsu suka tafi bashida girma; office 3 ne a ciki ba manya sosai ba sai kitchen da reception. Aiki suka fara minal da yazeed na girki saura na packaging da branding. Sallah da cin abinci kawai suke tsayawa yi. Masu delivery nata yi. Ga orders 3 na biki yazeed in yayi aiki sai ya dawo ya goge wa minal gumi sai yaci gaba. Haka suka yi ta yi har yamma tukunna suka tafi gida gaba daya sunyi likis wanka da ruwan zafi sukayi, tare da sallah da cin abin ci. Sai gado a kwana a tashi cikin sati daya aiki ya fi karfin Dan mutum ga riba sun tara sosai kawai sai suka siya engine. Sosai sukayi dedicating time dinsu suna aikin su.
Mutane kuwa ganin abin da akayi wa yazeed ba’ayi masa adalci ba gashi an kasa proving komai, an duba account summary dinshi da kuma information na company transactions dinshi duk kudinshi daga company dinshi ne albashinsa ne kawai from government.
Dan haka mutane suka fara zanga zanga cewa dole a sake masa dukiya tunda yana taimakon talakawa.
Zaune take akan kujera tana juya wa tare da busa shisha. Wani number ta Kira tace maza kuyi aikin ku da fatan mutanen sunzo? Akace yes ma tace don’t make a mistake……
Order phone din su yazeed aka Kira ya dauka nan akayi placing order na birthday party abincin 25 people.
Aka hada aka kai bayan 2 hours sai ga police wai abin cin da aka kai is poisonous kawai suka rufe shagon take yazeed ya Kira yan NAFDAC yace ya sun duba abincinsu ba’a basu number ba police yanzu sunzo sun rufe musu aiki.
NAFDAC suka ce gasunan zuwa after 30min sai ga su. Yazeed yace ga yan sandan can suna jira they should talk to them, shugaban tawagar tafiyar NAFDAC din yace it’s true abincin is poisonous. Yazeed yace toh me yasa suka yi musu register a baya ? Sukace ai Sam basuyi musu register ba sannan sukace ma yan sandan a tafi dashi cell dukda cewa military officer ne ai yayi laifi sannan bulldozer zata zo ta rushe part din ko kuma ya bar wa government yace ai ba nasa bane mallakin matarsa ne Dan haka basuda right akai. Sojoji ya Kira har Wanda gwamnati ta kwace masa sanda suka zo sai ga jama’a ma sun iso, domin live komai ke faduwa ga yan jarida rututu.
Sojoji da mutane suka kewaye yazeed mutane sukace ba’a isa a rushe wajen ba yayinda sojoji sukace ko abar maganan ko su bude wa yan sandan da nafdac wuta. Atake aka fara yada jita jita wai yazeed shi ke supporting din terrorism wasu kuma nacewa ya hada kai da yan boko haram ne.
Back up na 20 cars aka aiko ma yan sanda yayinda sojoji ma suka karo back up, kaucewa mutane suka fara yi Dan sunga fadan yafi karfinsu. Shugaban yansanda na lokacin ne ya zo shima sai ga shugaban sojoji ma .
Cikin isa shugaban yan sanda yazo ya danko hannun yazeed wai zai wullashi a mota minal tayi kukan kura ta raba hannun su tare da cin kwalarsa ta yarfa masa Mari 3 masu kyau. Sama yan sanda suka harba tare da saita ta da bindigogi amma ko gezau batayi ba sojoji ma suka harbi sama suka saita shugaban yan sandan sukace ana taba minal sunanshi sorry.
Huci minal keyi tare da kara matse damkar da tayi masa har yana ƙaƙarin amai , kawai wani Dan sanda mai rawan kai ya saita ta tauuuuu! Kakeji.
MASHA ALLAH! DONT FORGET TO FOLLOW ME, VOTE AND COMMENT AND INA BUKATAR ADDU’AR KU MUN KUSA FARA EXAMS
THANK YOU! TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
miss Untichlobanty 💕
23rd February, 2020.RECAP
Back up na 20 cars aka aiko ma yan sanda yayinda sojoji ma suka karo back up, kaucewa mutane suka fara yi Dan sunga fadan yafi karfinsu. Shugaban yansanda na lokacin ne ya zo shima sai ga shugaban sojoji ma .
Cikin isa shugaban yan sanda yazo ya danko hannun yazeed wai zai wullashi a mota minal tayi kukan kura ta raba hannun su tare da cin kwalarsa ta yarfa masa Mari 3 masu kyau. Sama yan sanda suka harba tare da saita ta da bindigogi amma ko gezau batayi ba sojoji ma suka harbi sama suka saita shugaban yan sandan sukace ana taba minal sunanshi sorry.+
Huci minal keyi tare da kara matse damkar da tayi masa har yana ƙaƙarin amai , kawai wani Dan sanda mai rawan kai ya saita ta tauuuuu! Kakeji.
CONTINUATION
Shiru wajen yayi tsit kowa yana register din abinda ya faru.
Faduwa minal tayi akan guiwanta tare da rike hannunta da aka harba. AI nan kakejin dau!dau! An sakewa Dan sandan nan bullet biyu a hannu.
Nan fa shugaban nafdac ya fara hadiya yawu tare da kokarin zamewa ya gudu, wabi cacuma sojoji suka masa sukace ko ya fadi gaskiya ko yaji ba kyau. Tsilli tsilli yayi da ido Dan yaga mutuwa a gabansa. Nan fa ya fara in ina,wani soja me zafin rai me suna musa ya gwabje sa da bindiga atake ya soma bayani cewa kudi aka biyasa ya fadi hakan.
Akace wa ya biyasa yace Alhaji tukur gadon kaya ne. Nan take ya basu registration number tare da bada hakuri yazeed yace ai dole a tsigeshi nan fa ido ya Rena fata m, haka ya dinga bada hakuri yana nuna nadamar da yayi sanda yazeed ya tabbata ya wahala yace yaji ya tafi zaiyi tunani amma fa hakan batayi wa Musa dadi ba Dan haka yasa shi lungu ya dan jijjibgesa ya sauya masa halitta kamin ya barsa.
Asibiti aka kai minal da Dan sandan nan jina jina nanfa magana ta lafa, chief of police din yace a masa afuwa ba laifinsa bane na yan NAFDAC ne da sukayi musu karya kuma munafiki harda shi a ciki.
Haka dai magana ta watse aka sasanta toh anan ne mutane suka sake tada kayar baya akan a sakewa yazeed dukiyarsa.
Shugaban yan sanda yana zaune a office gadon kaya ya kirashi yace asan yadda za’ayi da mutanen nan dake zanga zanga. Nan ya Kira yan sanda 3 yace a saki teargas a wajen zanga zanga. Daya daga cikin su mai suna lieutenant sabir murya kasa kasa cikin girmamawa yace :sir! This is totally dishonest and unfair, some police are the cause of the negative views people have on us. If not for dishonesty these people did nothing wrong, they did not temper with government property neither did they go against the law. They are just practicing a peaceful riot. To tell the truth me and my people will not participate in this (yallabai wannan fa rashin gaskiya da rashin adalci ne, wasu yan sandan su ke jawa wasu bacin suna,idan ba rashin gaskiya ba mutanen nan basu taba kayan gwamnati ba basu yi wani Abu da ya Saba doka ba, peaceful riot sukeyi Dan haka shi bazai sa yaranshi suyi ba.)
Mari chef of police din ya wankawa lieutenant sabir kuma yace yaje shi bayan kwana 3 ya dawo ya karbo dismiss letter. Yace shidai da ayi aikin rashin gaskiya dashi gara ya rasa aikinsa.
A bangaren su yazeed kuwa bayan an cirewa minal bullet din ta farfado yazeed yana bata shayi sukaji hayaniya a hall din asibiti,saukowa minal ke kokarin yi daga bed dinta yazeed ya kwantar da ita kuka ta fara masa wai tanason ta gani dan haka ya dauketa suka fito Dan sandan nanne suke cakwakiya da sojoji zasu tafi dashi Dan ya harbi matar oga yayinda yake kuka yana fadin bashi ya harbeta ba. Yazeed yace a dakata. Tsit kowa ya yi yazeed ya iso gaban shi yace :kace ba kai ka harbeta ba? Da sauri gyada kai yazeed yace idan na gano kai ka harbeta wani hukunci zan maka yace a tsire ni.
Yazeed yace a kai bullet din da aka harbeta da kuma bullet din bingigarsa a duba su shi kuma kar a tafi dashi a mayar dashi daki aci gaba da kula dashi.
Koda aka Dubo bullet din ba na bindigar sa bane nan yazeed ya fara tunanin yadda zai gano na waye tunda yan sanda ke duba wannan kuma yan sandan ba mutuwa dashi sukeyi ba.
STORY CONTINUES BELOW

A kwana a tashi minal ta warke yau aka sallamo su kuma basu fadawa kowa abinda ya faru ba especially mom saboda kar hankalin ta ya tashi.
Marhaba umma hani tayi musu tare da sauran masu aikin inda sukayi musu jaje. Su nason minal sosai saboda kirkin ta.
Washe gari zabe dan haka yazeed yace wannan shekara bazasuyi Zane ba saboda tsaro kar a kuma kawo musu hari. Sabon president yana zuwa ba tare da bata lokaci ba yasa akayi dismissing case din saboda ya gano rashin gaskiya kawai akeyi. Anan ne yazeed yayi resigning.
Mr. President yayi bakin ciki na rashin jami’i mai gaskiya da amana Dan haka ya hada masa taron bankwana a wajen taron ne aka Kira yazeed domin yayi jawabi cikin jawabin Nasa ne yake cewa zai koma ya kula da hard work din mahaifin sa kuma insha Allah daga ranan har tashin kiyama baya fatan shi ko wani a zuri’arsa su kara involving kansu da government business kawai zasuyi kuma individually zasu dinga taimakon kasarsu ba sai sun tsunduma kansu a cikin ba idan an nemi gudun muwarsu toh zasu bayar. Idan sunga ana Abu da ya Saba doka toh zasu yi magana.
Kuka jama’a keyi wiwi! Anan taron ne akayi presenting award of excellence ma yazeed as the BEST MILITARY PERSONNEL of the year. It was a heart touching moment,box daya na tissue paper na karad saboda kuka anan ne nima aka bani award Dina as THE BEST FICTION WRITER of the year. Muka ci abinci muka sha sannan muka watse ana ma juna fatan ALKHAIRI.2
Washe gari da safe suka lulu suka dawo Kaduna domin yazeed yayi shirin fara aiki as JEEMAR GROUP PRESIDENT yayinda minal taga cewa ya kamata su ciyar da almajirai domin godiya ga Allah Dan haka asabar din data kewayo ta Nemo tsofi 20 aka fara girki. Manya manyan tukunya fiye da lamba hamsin guda 20 aka daura kenan ko wacce tsohuwa 1 tukunya 1, yayinda aka biya ko wacce dubu hamsin kuma anyi haka ne Dan a taimaka ma tsofin ma.
inspection minal tazo yi yayinda take testing ana bude tukunya farfesun kaji ta hau kakarin amai. Dannewa tayi ta dandana ai take ta fara amai ba sassauci nan hankalin tsohuwa ya tashi itakam kashinta ya bushe.
Kowa ya rude ya rikice aka samo likita ta dubata tace yuzu dai she can’t say amma tana suspecting ciki ne da ita dan haka aka bata pregnancy test tube aikuwa positive. Nan shagali ya karu murnane ba’a cewa komai, tun daga ranan minal batada aiki sai cin gurasa da zogale.
BAYAN WATA 7
Minal zaune akan gado ta mimmike kafa bakin nan cike da gurasa da zogale yazeed shigo ya zauna a gefenta,daura kafafun nata yayi a cinyan sa yana Mata tausa saboda sun Dan kumbura yace mummy gurasa na shirya sai tafiya turo baki tayi tace daddy zogale ka tafi dani Dan Allah yace a hakan? AI idan na kaiki can zaki wahala ne gara nan akwai mom kuma ai bakuyi hutu ba karki damu yanzu zakiga weekend din ya kewayo na sake dawowa kinji? Tace Tom shikenan Allah ya tsare ya kuma kare yace ameen.
Saukowa tayi dakyar tare da kanka kwanta me kwabon zogale yazeed ya ja kumatun ta yace nikam Allah ya tunamin ranan haihuwar ki, irin wannan ci da kike yi zaki rakanin ma kina cin zogale cikin mamul mamul da baki tace babu ruwanka.
Fitowa sukayi tibi tibi suna dariya har ya shige mota bayan sunyi sallama ya sauko ya rungume ta tare da kissing gurasa da zogale (cikinta) yace bye bye my little babies da big baby dariya suka fashe dashi kamin ya shige motan suka wuce yayinda minal ta koma cikin gida.
…………………….
Zaune take a kan gadon dakinta yayinda take hango duk abinda ke faruwa a farfajiyan gidan, aani Luna da tafarfasa zuciyar ta keyi kamar tayi hauka haka takeji. Fincike drip din dake hannunta tayi yayinda ta yage riganta jiyoyin kanta sun tashi cikin huci tace nayi regretting aurennan da nayi auren banzan nan da nayi shi ke hannu kusantar ka masoyi na yazeed. Ke kuma sh*giya sai na hallakar dake da wannan tsiyar dake jikin ki sannan ta naushi gini Wanda har jini sanda ya fito daga hannun ta inda ta lashe tare da cewa na rantse da jinin nan sai na kasheki.
WA IYAZU BILLAH!
Toh masoyana Rabin raina, a halin yanzu dai ba baku satan amsan wacece ita. Shin a ganinku wacece ita? Duk Wanda ta canka zanyi dedicating Mata next chapter.
Me Kuke ganin zai faru a gaba?idan kika canka zan miki kyautar chapters guda 3 a jere.
Shin labarin nan yazo karshe ko da saura?
Ina tsimayi amsoshin ku. Domin inyi muku wani update yau ina bukatar 30 comments 50 votes.
Karku manta kuyi tagging kawayenku domin su karanta sannan kuyi sharing lungu da sako domin wani ma ya samu.
Karku manta kuyi following Dina @miss_untichlobanty ta haka ne zan gane masoya na, na gaskiya.
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU wato
Miss_untichlobanty 💕
11th march,2020
RECAP
Zaune take a kan gadon dakinta yayinda take hango duk abinda ke faruwa a farfajiyan gidan, wani kuna da tafarfasa zuciyar ta keyi kamar tayi hauka haka takeji. Fincike drip din dake hannunta tayi yayinda ta yage riganta jiyoyin kanta sun tashi cikin huci tace nayi regretting aurennan da nayi auren banzan nan da nayi shi ke hannu kusantar ka masoyi na yazeed. Ke kuma sh*giya sai na hallakar dake da wannan tsiyar dake jikin ki sannan ta naushi gini Wanda har jini sanda ya fito daga hannun ta inda ta lashe tare da cewa na rantse da jinin nan nawa sai na kasheki.
CONTINUATION
Jiki na rawa nurse din dake kula da ita tazo ta riko hannun ta dake zubda jini cikin harshen turanci tace ina rokon ki ki barni in koma kasar mu kar wata rana su gane ba a coma kike ba su kasheni dama ance yan ta’adda ne bakaken fata. Mari ta falla Mata tace ki iya bakin ki. Hawaye nurse din ta fara tace maza goge hawayen nan sannan kika sake wani ya gano me ake ciki ni da ke ne. Kamata ma yayi ki ji dadi ana biyan ki ba tare da kinyi aiki ba.+
Cikin kuka nurse din tace idan yanzu suka shigo suka ga hannun ki da ciwa ta yaya zan fara bayani? Hankade ta tayi Tate da zama bakin gado tace gyara min hannu na.
Jiki na rawa kamar mazari haka nurse din ta fara dressing hannun nata. Itako tunani take a ranta kamin tace ni ayush nayi alkawari indai bazan samu yazeed ba toh babu mai samun sa kuma wad……
Ringing wayanta ya fara hakan yasa bata karasa maganan ta ba ganin goje love na yawo akan screen din yasa ta jan tsaki tare da dauka cikin murya my zaki tace my love! Ta dayan bangaren goje yace wifey wai yaushe zaki tashi daga jinyan karyan nan ne ? Nayi missing dinki fa.
Murmushi mai sauti tayi tace soon karka damu sai anjima banason su jiyo ni bye zan kashe wayan ne.
Wani tsaki taja tare da fadin kaina aikinka ya kusa karewa. A bangarenshi kuwa tunanin yadda zai kashe ayush ne da tayi taking control ta masa handing over.
Bokanta ta Kira sukayi kus kus Wanda nima banji ba. Tace shikenan ko da akwai wani Abu. Ta dayan bangaren boka mugu yace wannan aikin babba ne dan haka ina bukatar ki samo fatan farjin mace sabon gawa zan miki wani hadi sai kisa a cikin jikinta,ki tabbata kin tura sosai tace zan iya bayarwa ayi? Boka yace ko da wasa, da kanki zakiyi!
Tace naji matsalata dakai ka fiya tsauri, dariya ya sheke dashi tace dadi na fa? Tace aikin ka ba wasa.
Dariya suka sheke dashi mai ban tsoro Wanda yasa cikin nurse kadawa da daukan ruwa dukda cewa batamin yaren tasa ba abin arziki ake kullawa ba.
Ƙwanƙwasa kofan dakin da akayi yasata kwantawa yayinda nurse din ta lillika mata fake drip da sauran su.
Bude kofan tayi zakiyya ce ta shigo ta zauna a bakin gadon tare da shafo kumatun kanwarta tana Mata kallon so, kamar kullum yauma sanda ta tamabayeta yaushe zaki tashi? Hawaye ne suka dinga zirya a idanunta.
Bayan aani lokaci tace ma nurse din zata tafi nurse dai nata gyada kai ne Dan banda film bata taba ganin irin wannan mugunta ba.
Ayush kam tunani ta lula bayan zakiyya ta fita. Juyi tayi tare da tuno sanda ta fara haduwa da goje.
FLASH BACK
Kamar yadda kuka sani zakiyya ta kasance me kokari,makaranta daya suke zuwa har ayush toh saide zakiyya tafi ayush da aji daya.
Ayush a rayuwanta babu Wanda take mutuwan so kamar Farouk saurayin zakiyya hakan yasa take Mata hassada, gashi ta fita kokari tana karban kyaututtuka.
Yau ta kasance ranan rufe makaranta kamar kullum zakiyya ce tazo na daya, yan ajin su ayush din suke ta tsokanan ta wai itace dakikiyar family din baki daya shiyasa ko turanci bata iya ba lokacin. Da gudu ta fice tana kuka bata ganin inda take tafiya. Cin karo tayi da marka mai goro da Sigari tayi Mata bari nan fa marka tace ta biyata, ita kuma batada kudi. Hayani ne ya kaure, karkashin wani rumfa goje yace ke marka wai me kike ta daga makokoro ne? Tace wannan banziyar kwailar ce ta yi mini bari, karki ga kinje makaranta ki nemi ki kawomin ranin hankali ta karashe tana cin kwalar ayush.
STORY CONTINUES BELOW

Sauri ayush ta kara tana mai kara tsanan duniyannan saboda azzalumai sunyi yawa a cikinta.
Lokacin shekarun goje 20, wulla ma ta kudin yayi tare da riko hannu ayush har cikin rumfan suka zauna. Yace yan Mata ya sunanki? Tace Aisha yace wow! Kina da saurayi ta girgiza kai. Yace me yasa kike kuka toh? Abinka da shashasha nan tazauna ta tsara masa bayani shikam sai binta yake da ido. Sigari ya bata yace ta zuka aiko ta kware sai tari take yace ta sake gwadawa a haka har ta zuke daya tuni ta fara jin ta a sama duk damuwan ta sun tafi.
Tun daga ranan suke ture turen letter domin a garinsu take hutu. Wasa wasa ta fara son shi hakan yasa lokacin da ya baiyana Mata soyaiya ta Amince kai tsaye. A haka ya dinga Mata kalamai inda ya nuna Mata yana son jasancewa da ita amma ba’ayi musu aure ba a gida dan haka sukayi aure a boye. Hakan yasa koda tace zata zauna gidan yazeed baiso ba amma tunda kudin yake bukata ai shikenan.
END OF FLASH BACK
Hawaye ta goge tare da ci gaba da tunaninta sannan taji haushin kanta na yin soyaiya da lukman kawai Dan ta kusanci yazeed.
Message din plan dinta tayi ma goje kamin ta fara shirye shiryen fita.
Zakiyya kuwa tana fita daga dakin ayush dakin ta taje ta shirya sannan ta nufi dakin minal domin ta kaita antenatal kamar yadda suka Saba. Taimaka Mata tayi ta shirya sannan suka nufi dakin mom sukayi Mata sallama.
Ayush kuwa direct gidan goje taje ta karbo shantun da bokan yace a bata Wanda tayi mai text ya karbo sannan suka tafi operation area. Text bokan ya Mata na yadda zatayi domin bukata ta biya.
Zakiyya tana cikin kuka mota kayansu yayi faci fitowa tayi domin taga me ya faru aka doke Mata kai wani powder aka hurawa minal daga nan bata kara ganin komai ba.
Ahankali zakiyya ta fara bude idon ta amma me ganinta tayi daure a kujera likimo tayi Dan taga Wanda ya kamosu. Aiko ayush da goje suka shigo suna dariya ko a jikinsu. Tashinsu sukayi zakiyya tama kasa magana saboda tsananin mamaki kawai kuka takeyi.
Tsk.tsk.tsktsk shine abinda ayush ta maimata kamin tace my darling sister are you surprised? Zakiyya tace me muka miki ? Idan na miki wani Abu ne me yasa zaki azabtar da mai ciki? Fuskar tunani tayi kamin tace may be me cikin da cikin suma sun min laifi ne.
Tunda muka taso kike samun duk abin da kike so, ni fa? Banida komai. Iyayenki sunfi nawa kudi kin fini Ilimi, malamai suna sonki, Kin Sami farouq,kin Sami yazeed,kin Sami kudi,nayi kokarin rushe farin cikinki amma a banza.
Ba kashe farouq,na tabaki da yazeed, na koma boutiques dinki,nayi abubuwa da yawa aciki harda hatsarin yazeed amma me yanzu ma kin samu wani miji ga kina rike da mukamin da nakeso kinga dole ne na salwantar dake. Idan har bazan Sami abu ba toh babu Wanda ya isa ya samu.1
Ke kuma, ta naushi bakin minal sai jini, kece dadi miji ko? Kowani lokaci kiuita like masa toh yau ne na karshe. Doke kan minal tayi da sanda take ta sume sannan ta dauko garin dake cikin shantun ta raba biyu kamar yadda boka mugu ya umarce ta.
Rabi ta zuba a tulun yayinda ta barbarda Rabin a tsakiyar kan minal Rabin kuma ta zuba a shantun ta jijjiga sai ta fasa. Sannan ta taka da kafar hagu. Kallon zakiyya tayi tace bakiyi mamaki ba Dana barki kike gani? Nayi haka ne domin kisan abinda ke wakana saide bazaki iya yin komai akai ba, Wannan shine hukuncin ki.
Yanzu haka your dearest mom tabi duniya don yanda na fasa shantun nan haka kwakwalwarta ta rushe sannan kishiyarki zata manta komai, zata dawo kamar yanzu aka haifeta. Kowa zai manta da ita banda ke da ni da mijina da boka na da………
Kofa ne ya bude sai ga mummy (maman zakiyya) ta shigo, zaro ido zakiyya tayi hawayen dake zubowa a idon ta suka tsaya cak tace mummy dama baki mutu ba, colin samun Kwarin guiwa tace mummy help us ayush ta haukace,ni ban San wannan ba mummy ba ayush din my bace. Zama mummy tayi yayinda ayush ta rungume ta tana fadin mummy saura kiris kiyi missing kuwa.
Bakin zakiyya na rawa tace tare kuke aiki ? Mummy tace what do you expect?look young lady idan ma baki sani ba ki sani ayush ce kadai yata ke da yayarki a gidan marayu na dauko ku meaning maman su safwan ma is not your biological sister that is you are all alone.
Zakiyya tace mummy me yasa zakiyi min haka? Mummy zakiyyan ki ne fa! Mummy…… yatsa mummy ta daura Mata a baki tace ya isa please no complaints. Riko hannun ayush tayi tace baby go ahead. Wani allura suka soka Mata a take ta zama paralyzed.
Mummy tace dont forget after three three months zakina yin wani okay? Tace okay mummy. Ya batun gidan anyi settling komai ? Tace yes nasa anyi photoshopping pictures din the guy is an American so ya iya aikinshi sannan umma hani ma bazata iya musa duk wani Abu da zamu ce ba tunda boka yayi mana maganin bakin ta.
Ayush tace wow mama na you are too great wallahi,naga pictures din. Nuna Mata tayi tace wow bazaka tana cewa hada hotunannan akayi ba. Tunba wannan da muke yara ba. Let’s hurry up mu kama hanyan Abuja nasan yazeed ma I mean bro yazeed ya suma already muje kamin ya tashi.
Dariya mommy tayi tace sh*giyar yarinya wai bro yazeed kamar da gaske, suka fashe da dariya. Zakiyya tana gani kuma tana ji amma banda ƙyafta ido babu abinda zata iya yi.
Ko hawaye saide idonta su ciko. Wheel chair suka daura ta goje ya turata ya fitar da ita. Sannan suka fitar da minal ma.
Dadai maraba gaban karo international market suka yarda minal suka barta kwance Shabe shabe kamar macacciya……….
IS ANOTHER UPDATE
KOWACCE TA TOFA ALBARKACIN BAKINTA.
KUN TABA TSAMMANIN AYUSH CE MUNAFUKAR?
YA ZATA KAYA NE WAI? INA TSIMAYIN COMMENTS DINKU.
KARKU MANTA KUYI VOTING SHARING SANNAN KUYI FOLLOWING DINA miss_untichlobanty
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💕
14th March,2020RECAP
Zakiyya tana gani kuma tana ji amma banda ƙyafta ido babu abinda zata iya yi.
Ko hawaye saide idonta su ciko. Wheel chair suka daura ta goje ya turata ya fitar da ita. Sannan suka fitar da minal ma.
Dadai maraba gaban karo international market suka yarda minal suka barta kwance Shabe shabe kamar macacciya……….
CONTINUATION
Cikin garin Abuja suka shiga inda suka nufi gida direct yayinda ayush ta tafi hospital saboda already an kirasu cewa yazeed is unconscious.
Koda ta isa asibitin dakin da yazeed yake aka kaita, kwance yake cikin kayan asibiti, fuskarsa tayi fayau ya Dan rame kadan. Baki ta tabe tare da yin murmushi tace soon I will be ruling everything sannan ta Sami waje ta zauna.
…..
Ummu Amina ce ta fito daga gidan ta damuwa dauke a fuskarta ta shiga makwabtan su. Sallama tayi uwani ta amsa tare da yi Mata barka da zuwa gaisawa sukayi a tsatstsaye uwani tace ummu amina haryanzu yarannan shiru Anya lafiyar su kuwa ? Dan tsanani kwana uku suke dawowa gida amma yanzu dubi satin su daya ba ko labarin su. Ummu amina tace ai shiyasa nazo mu fita mu nemosu, Dan garin habujan nan tsoro yake bani masu kudin nan yawanci yan shan jini ne balle yaran mu sun fito daga kauyen habuja yanzu sai a rudesu ga maraban nan badai mutane ba. AI muna samun su kawai tisa keyarsu zamuyi mu tafi Suleja ko ya kika ce? Uwani tace nima dai haka nake gani amma zan shawarci me gidana, Allah dai ya shirya mana zuri’a. Ummu amina tace ameen. Nan uwani ta zaro mayafin ta suka baza cikin gari domin neman ‘ya’yan su wato sabi’u da lado.+
Uwani dai itace mahaifiyar lado yayinda ummu amina take mahaifiyar sabi’u Wanda ake Kira da sabi nigga. Ummu amina batada burin daya wuce ta haifi dariya mace tasa Mata amina saide Allah bai bata ba sai da daya data Haifa wato sabi niga Wanda ya Santo mata alaƙaƙai, dahaihuwar sa gara babu.
Yan jihar nasarawa ne amma a maraba suke zama, sai lokacin noma yayi suke komawa nasarawa su noma doya sai su dawo su siyar.
Shi da lado basuda aiki sai yawo a garin su daki wancan,su sari wancan, su ƙwace kudin wancan, ayi bangar siyasa dasu, su tsokano yan sanda. Kullum dai cikin matsala suke gashi suki aure. Toh ko zasuyi ma wa zai basu yarsa?
🌹🍀
Hadiri ne ya hadu baki kirin, sai tawa da cida ake yi hakan yasa ummu amina da uwani labewa a zauren wani shago aiko ruwa ya barke ba kakkautawa.
Ruwa daya fara dukanta yasa ta bude idanun ta da sukayi Mata nawi. Gaba daya jikin ta ciwo yake Mata dakyar ta zauna kawai sai ta fashe da kuka domin gaba daya ji take zuciyar ta mata nawi ga bakin ciki da takeji. Kokarin tuno wani Abu tayi amma taji dib banda sunanta ba abinda ta sani kamar yanzu aka cillota duniya. Jin motsi a cikin ta yasata kallah, me zata gani cikin da ita. Toh fa anan ake yinta.
Tunani ta fara wai shin hatsari tayi ne? Cikin waye? Tana ma da aure? Su waye iyayenta? Waye mijinta? Daga ina take? Ganin babu amsa yasa ta kara fashewa da kuka. Tsananin kukan da take yasa hankalin su uwani yayo kanta. Ummu amina tace Allah sarki wancan mahaukaciyar kyakkyawa ko wani azzalumi aka samu ya dirka mata ciki ? Ga ruwa na dukanta ka bibiya yunwa ma takeji yasa ta kuka. Uwani tace har ta bani tausayi amma yanda kika ganota da kyannan kika bibiya hamshakiyar karuwa ce. Ummu amina tace kai nide ban yarda ba, uwani li fadi ALKHAIRI ko kiyi shiru. Bari in dauko ta in shigo da ita kasar rumfannan kar abinda ke cikin ta ya lahanta.
Nufo minal din tayi jiki na rawa Dan tsoron kar mahaukaciyar ta rufeta da duka. Daga dan nesa nesa tace baiwar Allah, minal tana dago kanta cak, ta tsaya da kukan lokaci daya taji kaunar ummu amina ya kamata babu bata lokaci ta fara kokarin mikewa. Taimaka Mata ummu amina tayi ta Mike a take ta rungume ta. Tare da kokarin fadin umma ? amma me sai taji ta kasa magana. Jan hannun ta ummu amina tayi ta kaita kasan rumfan. Haka aka gama ruwa tace mu tafi ko ? Ummu amina ta kalli minal tace toh baiwar Allah mu zamu tafi ki tafi gida, kema ki tafi gida kar zazzabi ya rufe ki. Riko hannunta minal din tayi uwani ta yarfa tare da fadin sake Mata hannu Dan Allah. Kema ummu amina laifinki ne daga ganin mutum waike uwar taimako ko? Haka uwani ta rufe ido tanata masifa wai ummu amina ta fita shiga harka da ba’a gaiyace ta ba.
Ummu amina kuwa fadi take haba uwani ki bari ko abin ci mu bata mana, mai ciki fa abin tausayi ne.
Minal kam yunwa takeji ga sanyi, haka ta dinga karkarwa ga zazzabi daya rufeta. Tashi tayi ta fara tafiya ga jiri dake dibarta. Wani suya spot ta gani taje gefen wajen ta tsaya sai hadiya yawu take tana kallon yanda mai ke diga daga jikin naman. Wani guntun biredi aka bata aiko ta hau mamuka har tana ƙwarewa.
Kowa idan ya gama cin abinda zaifi sai ya bata guntun. Mai suya dai abin ya fara bashi haushi dan haka ya cika yayi fam saura fashewa.
Former lieutenant sabir (Wanda ya rasa aikin sa na dan sanda saboda yace bazaiyi rashin gaskiya ba)ya siyo doya Wanda za’ayi breakfast a gidan da yake gadi ya hau babur dinsa kawai yaji yana marmarin suya hakan yasa ya tsaya tukuban da minal ke gefe. Haka aka kawo mai yana ci yana kallon ta, ji yake kamar ya San ta amma da ta fara tunani sai kansa ya fara ciwo kawai sai yaji ya kasa ci saboda kallon naman da take ta yi.
Mai tukuba kam ganin kamar saboda ita sabir ya kasa ci yasa shi fara Koran ta kuka ta fara masa tana cijewa Dan bata koshi ba ya fara hankadeta. Sabir ne ya saka masa tsawa. Kwalarsa ya damka rate da fadin kai wani irin wawa dabba ne? Bakasan Kima da darajar mace bane, bakaga ciki ne da ita ba zaka na hankade ta? Ko muharramar ka ce da zaka taba ta?
Duk cakwakiyar nan da ake yi minal bata sani ba Dan har taje ta dauki naman da sabir ya bari ta fara ci. Sabir kuwa lura yayi da bata wajen hakan yasa ya saki mai nama ya juya daidai lokacin kuwa ta danna albasa a baki. Murmushi kawai yayi ya zauna a gefenta. Yace ya sunanki? ƙuri tayi da ido tana kallonsa,murmushi ya sake Mata yace yunwa kike ji? Ta daga kai daidai lokacin wayarsa tayi ringing.
Yace hello hajiya. Tace sabir ina ka tsaya ne yace ganinan dawowa daga nan ya kashe. Tashi yayi tare da cewa yar uwa sai gobe ki? Murmushi tayi ta daga kanta. Daga nan ya dale babur dinsa ya wuce itama daukar ledan ta tayi ta fara tafiya. Tana cikin tafiya ta taka kaya hakan yasa ta tsalla ihu.
Ashe daidai ginin yan shaye shaye ne lado yace tattabara daga sama gasassa.
Sabi ne yazo ya sunkuce ta bai ajiye ta ko ina ba sai cikin ginin. Kuka ta fara musu ga zafin kayan da takeji lado ne ya ajiye kwalbar giyan dake hannunsa ya fara zare belt. Baya baya ta fara yi daidai lokacin Allah ya taimaka Mata aka dauke wuta dan haka area din gaba daya yayi duhu. Kwalbar ta raruma ta kwalawa ma wani sannan ta Mike ta fara bin gini aiko ta taka kwalba. Toshe bakin ta tayi tana fita aka kawo wuta hakan yasa suka bita a guje ashe sabi nigga ta kwalawa kwalbar.
Gudu suka dinga yi kamin ta samu ta labe a lungu sai haki take taji an dafa kadar ta juyowa tayi suna hada ido ta zaro ido tare da kwala ihu…
I know that wasu haushin abin da ya samu minal sukeji. Hakuri zakuyi labarin ne yazo da haka.
Su o o har ankusa zubda kwalla saboda tausayin minal.
Karku manta kuyi VOTING,COMMENTING tare da following Dina sannan kuyi SHARING da followers dinku domin kar a basu labari
ONE LOVE💋
Miss Untichlobanty 💕
28th March,2020.RECAP
Kwalbar ta raruma ta kwalawa ma wani sannan ta Mike ta fara bin gini aiko ta taka kwalba. Toshe bakin ta tayi tana fita aka kawo wuta hakan yasa suka bita a guje ashe sabi nigga ta kwalawa kwalbar.
Gudu suka dinga yi kamin ta samu ta labe a lungu sai haki take taji an dafa kadar ta juyowa tayi suna hada ido ta zaro ido tare da kwala ihu…
CONTINUATION
Ba kowa bane illa sabi nigga, aiko ya wanka Mata wani jahilin Mari Wanda ya sata faduwa ba tare da bata lokaci ba.
Dariya ya sheke dashi harda rike ciki, hakan ya bata daman rarumar dutse ta tashi a hankali sannan ta kwala masa.
Ihu ya saka yayi da ta fita a guje tana mai tallafo cikinta Wanda ke Mata zafi a halin yanzu.
Sauran yan daban ne sukayi saurin karasawa wajen sabi’u sakamakon ihun sa da sukaji. Tambayan sa suka fara yi lafiya ? Ya nuna musu hanyan da minal tabi. Biyu daga cikin su ne suka bi hanyar yayinda lado ya tsaya, ya tallafa masa ya tashi sannan ya fara kokarin kaishi gida.+
Minal gudu ta sharara har sanda kafar ta suka daina gudu kamin ta Sami zauren wani gida ta shiga. Itacen girki ta gani a jibge gefe guda dan haka taje ta jingina a jiki babu bata lokaci tayi bacci dukda ko a jikinta tanajin akwai abinda ya dace tayi Wanda batayi ba.
🌹🍀
Yazeed bai bude idanun sa ba sai wajajen karfe Goma na dare. Akan fuskar ayush suka fada ta sakar masa wani murmushin munafurci tare da fadin brother sannu da tashuwa. Kallon ta yayi da alamar tambaya yace brother? Tace eh karka damu dama likita yace min zaka iya manta wasu abubuwa so karka damu, San baka dukkanin information da kake bukata. Jinjina kai yayi alamun toh yana kare Mata kallo Dan shi bai ma yarda da ita ba yace wacece ke? Murmushi tayi tare da zama a bakin gadon sa ta riko hannun sa. Dan janyewa yayi tace karka damu ni muharramar ka ce,ni kanwarka ce, your baby sister ka tuna? sakan jiki kadan yayi yace toh me yasa aka kawo ni nan? Tace saboda tun sanda mahaifin mu ya rasu kake cikin damuwa hakan yasa kake samun wani ciwon kai me tsanani Wanda yakan sumar dakai wani lokaci ko ya sabbaba maka manta wani Abu toh wannan karan da alamu alakarka da mutane ka manta.
Jinjina kai yayi domin maganan ta kama kwakwalwar sa. Yace munada mahaifiya tace eh tana gida yanzu kaga hotanta. Ta fadi hakan tana mai nuna masa wallpaper wayanta. Hoton su ne su hudu, shi da ita da mummy da umma hani. Yace toh ai Mata biyu ne wajen waccece ita? Tace me kwalliyar nanne mana. Wancan kuma umma hani ce nanny din mu. Ajiyan zuciya ya sauke yace bani ruwa insha, Darius tayi kamar shasha tace au na mance na tsaya ina maka surutu. Murmushi kawai yayi tare da karbar ruwan yasha.
Nan dai taci gaba da masa bayanan karya shi kuwa Allah sarki bai sani ba sai shiga yake tare da rike komai da take fada masa.
🌹🍀
Gidan mahaukata sukasa aka kai mom bayan an haukatar da ita. Mai kawo abin ci ne tazo tana wulla musu hara ta iso dakin mom Wanda yake na karshe. Tana kallon mom taji kamar ta Santa kuma lokaci daya taji mahaukaciyar ta kwanta Mata a ranta. Wulla Mata nata abin cin tayi mom taso ta dauka ta kyalkyale da dariya kamin kuma tace na gode.
Fara co tayi tana yamutsa fuska da ka ganota kasan bata Saba shan wahala ba. Tsayawa kallonta tayi kawai sai taji hankalinta ya kwanta da mahaukaciyar. Bude dakin tayi ta shiga sannan ta rufe, a take mom ta fara ja da baya tana fadin karki matso kusa dani! karki matso kusa dani! Matar tace kwantar da hankalin ki ba abin da zan miki.
Zama tayi a gefenta kawai sai mom ta fashe da kuka. Matar me suna senior hauwa tace me aka miki kike kuka? Mom tace ɗa na, zasu cutar min dashi! Senior hauwa tace ina yake kuma yaya sunan shi? Shiruuuu mom tayi kamin tace nima ban sani ba, na manta sannan ta sake fashewa da kuka.
Rarrashin ta senior hauwa tayi haka sukayi hirar su dukda cewa wani lokacin mom din takan Mata hauka amma dukda haka tana zargin wani Abu tana ganin haukan mom din ba haka kawai bane.
STORY CONTINUES BELOW

🍀🌹
Washe gari da safe aka sallamo yazeed kuma har wannan lokacin ayush tana like dashi, mummy ne tazo tayi musu oyoyo, taci ado ta kashe saurin dankwalin shaddar nan, gwala-gwalai ta ko ina abin nema ya samu.
Daidai lokacin wayan ta yayi ringing hakan yasa tayi excusing kanta kamin ta haura sama. Goje ne ke kiran ta, tace baby ya akayi ne? Yace lafiya kalau wifey dama so nake mu hadu tace okay no problem ka sameni a Sheraton hotel, royal suit daki na uku yace ba matsala sai mun hadu.
Motar luku ne suka ta iso suka fito suna cewa ina president? Wai attack dinka ya tashi ko? Nan sukayi masa jaje domin suma an juyar da kwakwalwar su sannan suka koma side dinsu, kuma a daidai lokacin ne su zakiyya suka shigo ita da Jamal. Yazeed yayi shaking hannun Jamal yace gou are Jamal ko? Jamal yace yup ashe baka manta ba. Dariya yazeed yayi yace ai little sis ta fadamin tace idan naga balarabe toh shine cousin Dina jamal. Jamal yace tabbas kuwa amma ka daina damun kanka, uncle ya tafi babu abinda yake bukata sai addu’ar mu. Mummy ta fara share kwalla kamar da gaske.
A halin yanzu dai abinda suka nuna ma duniya shine baban yazeed ne ya hada jini da larabawa saboda kimanin yazeed da kuma Jamal idan ba haka ba ai mummy yar najeriya ce futuk dan haka basuda explanation shi yasa suka hado wannan karyar tunda dai a zahirin gaskiya mom ce balarabiya kuma sun batar da ita.
🌹🍀🌹🍀
Koda su lado suka karaso layin su godiya sabi’u yayi masa tare da cewa ya tafi gida shima zai wuce haka suka rabu suna shirya yadda zasuyi mugun sabawa minal idan suka sameta.
Yana raba hanya haka ya shigo har ya wuce sai yaga kamar akwai wani Abu da bai Saba gani ba a gefen itacen mahaifiyar sa. Rakani kashin sa (Nokia) ya ciro ya haska sai ya tuna ashe gari ma ya waye kalla yayi dakyau yaga minal kwance tana bacci hankali kwance. Yace daidai kenan wato kin tagaiyara ni shine ke kuma zaki kwanta kiyi bacci ko? Toh gashinan Allah ya kawomin ke har gida. Dariya ya fashe dashi Wanda yayi sanadiyyar farkawar ta babu shiri ta fada cikin gidan daidai lokacin ummu amina ta sauke kunun sayarwar ta tana kokarin dauko su mukubur din ta na tuyar kosai taga mutum ya fadi Mata gida salati ta rafka yayinda minal ta buya a bayanta. Daidai lokacin sabi ya fado cikin gidan yana fadin ina take ? Ina ta shiga? Ummu amina tace lafiya zaka biyo yar mutane ku fadomin cikin gida da sanyin safiya? Yace kalli, ummu kalli goshina. Wannan yar iskar ce taji min.
Kallon ta ummu amina tayi tace a ah yar nan Dama kece? Sabi yace kin Santa ne? Tace ai jiya da muka fita nemanku ni da uwani, sai aka fara ruwa anan muka hadu da ita.
Kai miko min kujerar can ta zauna, yace tashin hankali ai indai ni zan dauko kujera ta zauna saide ta mutu a tsaye. Ba rantse da wallahi idan na shiga na fito bata bar gidan nan ba, zan muku hauka. Yana fadin haka ya banka dakin sa ya shiga. Ummu amina tace dadin abun nice uwar ba kai ba, daga nan ta shigar da minal daki ta zaunar da ita ta bata kunun sannan tace Mata ta shirya su tafi kasuwar gwanjo ta siyo Mata kaya, ta daga kai alamun toh nan dai ummu amina ta gane cewa minal bata iya magana.
Haka suka tafi kasuwa ta zabo Mata kala 5 masu arha da rahusa sannan suka dawo gida. Koda suka dawo sabi bayanan dan haka ummu amina tace ma minal tayi wanka ta shirya sai tazo ta karbi kosai a kofan gida.
🌹🍀
Yazeed yana zaune a dakin sa, ayush tana hada masa shayi yace little sis banida Mata ne? Ajiyan zuciya ta sauke tace Allah tayi Mata rasuwa bayan ta haifi safwan. Shiru yazeed yayi kamin yace safwan din ɗana ne? Ayush tace eh shi da yayan sa safwan. Murmushi yazeed yayi yace no wonder nakeji kamar ina missing wata ashe marigayiyar Mata ta ce. Ina yaran suke? Tace sun tafi school is already 8am fah. Yace kikace nine president na jeedmar group ko? Tace ofcourse bro Yace toh gobe zan cigaba da fita aiki. Tace okay but bro kasan ban Dade da dawowa daga karatu ba and you said zaka bani GM kace zaka shirya papers din kuma sai wannan abin ya faru. Yace no problem tomorrow zaki iya fara fita kece general manager na advertisement department. Tsalle ta daka tare da rungume shi tace thank you brother, ya shafa kanta yace you are welcome sweetheart. Kanshi ne ya Sara jin kalmar sweetheart hakan yasa ya rike kansa. Tace bro lafiya yace nothing ki turomin sahir da safwan din idan sun sawo in gansu. Dariya tayi tace kaji ka fa bro wai ka gansu. Sai kace irin an siyosunnan yace toh ai na manta shiyasa. Dariya kawai tayi ta fice, tana fita daga side dinsa ta daka tsalle tare da fadin yes! Komai yana tafiya yadda nake so.
…….
Ummu amina tana cikin tuya minal ta fito ta zauna a gefen ta, Murmushi ta Mata tace har kin fito kenan? Minal ta daga kai kosai ta zuba Mata ta fara ci tana Mata hiran yadda takeson Allah ya bata diya mace. Tace sai gashi Allah ya bani ke, kinason ki zama diyata? Minal ta daka kanta.
Abinda basu sani ba yan anguwa duk sun taru, labari ya ratsa ko ina akwai sabuwar budurwa kyakkyawa a gidan ummu Amina kuma tana da ciki. Saurayi dake siyan kosan ne yace ummu amina wai a ina kika samo wannan kyakkyawar budurwar? Ummu amina tace kai banason maganar banza diyar nan tawa ce da na Dade ina rokon Allah ya bani ya kawo minaita har gida, kuma harma ina sa ran samun jikoki. Sunan ta Amina.
Kallon minal yayi yace wow nide minal baby zan dinga kiranta sannan yayi kokarin riko hannun minal din. Wani irin kallo ta banka masa tare da Jan dogon tsaki tana mai yin kicin kicin da idanu.
Yace tofah, ummu ai baki sanar dani cewa amina taki batada kunya ba ashe uwar tsiwa ce. Wani kallo minal ta aika masa ta ajiye kosan a gefe ta dafa kasa ta Mike. Wato za’ayi cakwakiya kenan, daidata tsayuwarta tayi ta dunƙule hannu wata Mata dake keken abinda ke faruwa ta window tace tooo, ashe aminar ba ta arziki bace wannan aminatun yar jagwal ce.
Take kan minal ya Sara ‘aminatu yar jagwal’ ke Mata yawo akai kamin ta yanki jiki ta fadi.
Nan fa…nan fa…nan fah. Au ashe ruwan biro na ya kare shiyasa na kasa ci gaba da labarin😁
Karku manta ku latsa tauraron dake kasa sannan kuyi COMMENTING hakan ne zai nuna min tsananin kaunar da kuke wa littafin nan da ma mai littafin da kanta.
Follow me on miss_untichlobanty
One love 💋 from your KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💕
30th March,2020RECAP
Yace tofah, ummu ai baki sanar dani cewa amina taki batada kunya ba ashe uwar tsiwa ce. Wani kallo minal ta aika masa ta ajiye kosan a gefe ta dafa kasa ta Mike. Wato za’ayi cakwakiya kenan, daidata tsayuwarta tayi ta dunƙule hannu wata Mata dake keken abinda ke faruwa ta window tace tooo, ashe aminar ba ta arziki bace wannan aminatun yar jagwal ce.
Atake kan minal ya Sara ‘aminatu yar jagwal’ ke Mata yawo akai kamin ta yanki jiki ta fadi.
CONTINUATION
Mikewa ummu amina tayi tana rafka salati tace na shiga uku aminatu lafiya? Fallawa saurayin Mari tayi tace kai ilu me kayi Mata? Uwani ta Kira ta taimaka Mata suka shiga da minal cikin gida.
Sabi yana karyo kwana yaga taron mutane, baya baya suka fara ja lokacin da suka lura yana tunkaro su. Ashar ga danna yace kai me kukeyi anan wajen? Yaran ne suka ruga da gudu yayinda samarin suka watse suna gunguni su kuwa Mata yan tasha yan gulma suka dinga Watso magana ta batanci. Matar nan dake leke ta window tace kai sabi’u bamason iskancin banza, kai da uwarja bakuda aiki sai hada tarzoma. Yatsa ya nuna Mata yace ke talatu billahillazi la ilaha illa huwa idan kika kuma kirana sabi’u zanci… tam.+
Kofar gidan su ya bankade da kafa har sanda ta karye ya shiga tun daga zaure yake dannawa mahaifiyar sa kira. Ummu! Ummu! Ummu! Tace kai wai lafiya kake Kira na haka sai kace kana bina bashi dalla ka fice kaje ka tuya mini kosai banson shirman banza.
Yace ummu ba nace kar na dawo na samu yarinyar nan a cikin gidannan ba? Tace tunda kai ka haiho ba. Wallahi sabi idan baka fice ka toya kosan nan ba zan fito daga dakinnan in ci maka mutunci. Uwani tace waikai sabi bakada tarbiyya ne? Mahaifiyar ka tana magana kana mayar Mata yace ke uwani babu ruwanki, kuma idan rashin tarbiyyar ne ai gara akan danki.
Juyawa yayi ya fice yana fadin mutane sai shisshigin masifa ko uban me ya kawota gidan oho. Kuma wallahi idan ba’a cire wannan yarinyar a gidannan ba zan muku hauka zan muku bari.
Koda ya fito zama yayi a kujeran yana suya yana banbami wai tsabar an rainashi za’a hadashi da suya. Wallahi babu abinda zai hanashi ketawa minal rashin mutunci.
🌹🍀
Safina! Safina!! Safina karki fita a gidannan nace ko. Wacce aka Kira da safina ne ta ja tsaki tare da kada kai tayi ficewar ta.
Motar kawarta dake jiranta a bakin kofa tayi shigewarta tare da cewa babe yau Sheraton zamu je. Kawarta me suna rafisa tace kamar kinsan zuciya ta Dan naji ance this week akwai guests sosai. Figar Motan sukayi bayan sun sake kida kamar a club.
Suna cikin tafiya rafisa ke cewa gaskiya babe mum dinki bata kyauta miki ace big girl kamarki bazata iya using mota ba? Haba this is not right. Tsaki safina taja tace kede bari ai wata rana saina gaurawa wannan matar Mari.
Reception suka Shiga lokacin da suka iso hotel din nan suka tambaya kuma aka sanar dasu cewa yau akwai baki sannan ma ana party.
Nan suka tafa tare da biyan kudin daki saboda kar a hanasu shiga.
Daki Dali suka fara bi suna kafa kunne idan sunji alamun namiji ne kadai a dakin sai suyi knocking idan an bude sai sugani, idan Dan hannu ne shi da kansa zai musu tayi idan ko ba Dan hannu bane sai su basa hakuri suce batan kai sukayi.
Saide fa yau da matsala Dan basu samu customer ba gashi anfara complain cewa wasu Mata na damun baki.
Shawara suka Yanke idan suka duba room dinnan ba customer toh zasu nufi wajen party ne.
Knocking sukayi ba’a bude ba har suna shirin wucewa sukaji alamun motsi hakan yasa suka gyara tsayuwa tare da sake budo wasu bangare na jikinsu. Ana budewa suka saki murmushi amma me zasu gani ayush ce ta bude kofar. Wani kallo take binsu dashi da yake itama safina tanaji da kanta harara ta mayar Mata. Aiko babu bata lokaci ayush taci kwalarta tare da wulla ta chiki daki. Sauri rafisa tayi itama ta fada tana kokarin ceto kawarta yayinda itama safina ta ci kwalar ayush nan fa dambe ya kaure tsakaninsu suna zagin juna uwa da uba.
Ganin abin yaki karewa yasa goje shiga tsakani tare da fadin wai sweetheart me ya hadaku fada ne tsawa ta daka mishi tare da cewa banza munafuki wato abinda kakeyi a bayan idona kenan ko? Wato kanada wasu yan Mata ko? Safina tace ke munyi miki kama da kananun karuwai irinki ne? Wani kallo ayush ta Mata kamin yace ke shegiya ki iya bakinki wannan din miji nane. Kai kuma…. ta juyo tare da sake kallon goje saide kamin taci gaba yayi saurin cewa haba wifey hotel dinnan fa ke kika kama kuma nasan zakizo toh meyasa zan kirawo yan Mata? Sannan da banida gaskiya bazan bari ki bude kofa ba saide ni in bude ince musu su jirani ko wani Abu. Tace ehhh kuma fa hakane amma ya akayi cikin duk dakunan hotel dinnan sukazo dakinnan? Yace tayaya zanyi na sani? Kallon Safinan tayi tare da cewa karamar ka….. safina ce tayi saurin cewa wallahi kina karashe wa saina tsinka miki Mari. Karuwa tana bin maza ne dan kudi Niko ina binsu ne Dan biyan bukatata. Ni safina Usman nadabo nafi karfin kudi wallahi.
STORY CONTINUES BELOW

Ayush tace what ke yar gidan Alhaji Usman nadabo ne? Safina tace kwarai kuwa. Murmushi mai sauti ayush ta fara tare da fadin yar uwa ai bakiyi bayani bane da wuri, toh amma me yasa kika zabi wannan harka bayan dukiyan da babanki yakeda shi? Tabe baki safina tayi tace wannan harka ta ce babu ruwanki. Ayush tace hmm malama safina kenan ai yanzu batun rigima ta kare a tsakanimu ai mun zama yan uwa dariya rafisa dake kefe tayi tace kai jama’a duniya juyi juyi anayi inajin dadi kamar ba yanzu kuka gama fada ba. Ayush tace kinga babu ruwanki ehe, kawai kina nema ki shiga tsakanin yan uwa.
Safina tace malama ya da sauri haka yaushe na zama yar uwar ki? Ayush tace kede bar wannan sanar dani ansar tambayan ki. Tabe baki tayi tace saboda kawai in biya bukatata. Ayush tace toh kiyi aure mana. Safina tace lokacin da nakeson ayimin AI ba’ayi ba yanzu ko ban bukata Dan na Saba da maza dayawa guda daya bazai isheni ba.
Dan tunani ayush ta shiga yanda zata rike safina Dan idonta akan kudin mahaifinta ne. Aikuwa sai ta tuno lokacin da zakiyya ke raki akan jarabar yazeed hakan yasa tayi saurin cewa idan kuma na samo miki Wanda yakeda komai har wannan fa? Safina tace ai babu bata lokaci zan bar bin maza.
Ayush tace rest your case hajiya ta kin samu bani numbarki kawai. Sharing number dinsu sukayi suna ta jin dadi kowa bukatarsa zai biya sannan suja rabu.
Koda safina ta koma gida carko carko ta Sami iyayenta. Baban ta na ganinta ya daka Mata tsawa ke me sunan mama daga ina kike? Nace cabdi,wannan shine ihu bayan hari. Turo baki tayi tace daddy wai kaima irin momy zaka zama ne? Yace shashashan yarinya ayimin shiru. Wallahi idan baki fito da miji nanda 3 months ba babu ni babu ke. Bubbuga kafa ta fara tare ta haye sama tana fadin lokacin da nace ayimin cewa akayi banida kunya yanzu kuma za’a dameni. Mum dinta ne tace idan kika bari na sameki wallahi zan ballaki.
Kallon Alhajin tayi tace Alhaji kaga abinda nake fada ko lokacin da kake bata ta, tazo tace tanason aure kace Sam sai tayi karatu saboda tayi taking over business dinka. Toh gashi yanzu ita auren ma baya gabanta.
Zama yayi tare da sauke ajiyan zuciya yace hajiya ki yafemin na lalata rayuwar diyar mu guda daya tak. Maganin hawan jininsa ta Nemo masa duba da yanayin sa tasan zai bukace su.
Minal kuwa tana bude idonta tace idan baka da hankali tabani kaga ikon Allah.
Ummu ce tace ke amina tu magana kikayi koko kunne nane sai alokacin itama minal tayi magana hakan yasa ta rungume ummu tanajin dadi.
Ummu tace aminatu yaya sunanki na asali? Minal tace amina ne kuma banda sunana babu abinda nake tunawa. Ummu tace kenan bakisan me cikin jikinki ba? Ta daga kai. Ajiyan zuciya ummu ta sauke tace ina kyautata miki zaton mutumiyar kirki amma da alamu kinada zafi. Nikam zan ajiye ki idan har kika haihu ba’a nemeki ba toh zan aurar dake, kinaso? Minal tace ni banason a rabani da ummu na. Ummu tace karki damu ko gidannan bazaki bari ba.
Fita tayi tare da karbar tuyanta a hannun sabi tana fadin shege ja iya abin arziki amma bakayi da tuyar kakemin kana samun albarka befi maka ba? Tashi yayi yana fadin ko ki karbi wannan abun ko na barar da komai. Kuma na dauki naira dari biyu tace nide karka sake kayimin shaye shaye da kudi na. Yace ke kika jiyo tare da bazata cikin gari.
🌹🍀
Safwan ne da sahir suka shigo dakin yazeed da gudu suna fadin daddyn mu ya jikinka? Murmushi yayi tare da rungume su lokaci daya suka kwanta mai hakan yasa babu shakku ya yarda cewa yaransa ne.
Ayush ne ta shigo tana fadin kai kuyi ahankali kunsan daddyn ku bashida lafiya.
Dariya sukayi sukace daddy kaji aunty ayush ko? Wai muna damunka ? dariya yayi tare da cewa yaushe yara na zasu dameni?
Ayush ne tace brother akwai abin da nakeson in fada maka. Gyara zama yayi yace kaga dai yanzu 7 years kenan da rasuwar mummy sufwan ya kamata ka kara aure ko Dan su. Jin Jina kai yayi yace wannan gaskiya bari zan Nemo musu mummy, kunaso ko? Suka daga kai da sauri tare da fadada murmushin su amma dai sahir abun bai kwanta masa ba.
Ayush tace AI na samo maka kanason ka hadu da ita? Shiru tayi kamin yace
KO BAN GANTA BA NASAN ZABINKI YAYI DON HAKA ZAN AURETA!
GENG! GENG!! GENG!!!
Cabdi akwai cakwakiya fa jama’a.
Me zaku iya cewa gameda CHAPTER dinnan? Ya kuke ganin za’a kaya ne wai.
Karku manta kuyi VOTING tareda FOLLOWING Dina.
Ina matukar kaunarku! Daga taku KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty 💕
5th April, 2020.
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.RECAP
Ayush ne tace brother akwai abin da nakeson in fada maka. Gyara zama yayi yace kaga dai yanzu 7 years kenan da rasuwar mummy sufwan ya kamata ka kara aure ko Dan su. Jin Jina kai yayi yace wannan gaskiya bari zan Nemo musu mummy, kunaso ko? Suka daga kai da sauri tare da fadada murmushin su amma dai sahir abun bai kwanta masa ba.
Ayush tace AI na samo maka kanason ka hadu da ita? Shiru yayi kamin yace
KO BAN GANTA BA NASAN ZABINKI YAYI DON HAKA ZAN AURETA!
CONTINUATION
Akwana a tashi kamar wasa auren yazeed da safina saura sati daya cir. Lokacin da iyayen safina sukaji sunyi mugun mamaki da lokaci daya ta fitar da miji amma basu kawo komi a kansu ba ganin Wanda zata auran mutumin arziki ne ba sha ka tafi ba. Ayush sai rawar kai ake yayinda yazeed ko zaiyi auren ne saboda yaransa Dan shi yanzu ba mace bace a gabansa.
Minal zaune a parlourn ummu suna shan rake taji kamar mararta yadan murda. Dakewa de tayi taci gaba da hira can sai ta fara jin fitsari amma abinda ke damunta shine ta kasa yi Dan ta kewaye yakai sau 10. Ummu run bata lura da zirya hardai abin yayi yawa hankalinta ya dawo kan minal. Koda minal ta zauna ummu tace yar nan ince lafiya dai ko naga sai zirya kike murmushi minal tayi tace ba komai. Abinci ummu ta zubo musu sukaci minal ta dau kwanon zata wanke ummu tace ta barshi itako ta dage tsugunawa tayi ta fara zuba detergent babu shiri ummu ta Mike ta karba tare da fara wankewa daidai lokacin sabi ya shigo yana fito. Wani ashar ya danna tare da dauke minal da Mari har sanda ta fadi kasa Wanda ya janyo tsananta Mata nakuda. Yace bansan cewa ke yar dakikiya bace sai yau idan ba hauka ba ya zakiyi ki saka uwata aiki. Tau! Tau! Kakeji, ummu ta daukesa da maruka har biyu tare da mangaresa.+
Hankalinta ne ya iyo kan minal saboda ihun data tsala nan fa ummu tasa ya Kira Mata uwani sukasa minal a daki. Yanda sukaga yini haka suka ga dare, daidai an fara kiran sallan asuba Allah ya albarkace su da……..
Yan biyu Mata yan cukul cukul gwanin sha’awa,dadi ummu ta dinga ji kamar jikokinta na gaske kankace me makota da munafukai da yan tsurku anata shigowa domin ganin yara. Kowa na tofa albarkacin bakinshi. Saide an fara tuka tsiya da minal ne lokacin da akazo wankan jego tace ai Sam batasan da zance ba saide tayi da kanta haka aka hakura aka barta tunda ba halin ayi Mata karfa karfa.
Sati na kewayo wa aka sha suna daidai gwargwado, inda aka samu sahla da zayyana.
Kuma a wan an rana ne aka daura auren ango yazeed da amaryarsa safina. Har yan kawo amarya suka gaji suka watse ango shiru. Su sahir ne suka shigo suna murna suja rungumeta suna fadin mommyn mu, sannu da zuwa. Yake tayi musu tana Dan tutturesu a dabarance yayinda a ranta take cewa kai indai yarannan kamannin uban su suja dauko toh lalle na jefi tsuntsu biyu da dutse daya.
Dalewa tsakiyar gadon sukayi suna tsalle ta daka musu tsawa tsirata sukayi ta nuna musu kofa sidif sidif suka fice suna kallon juna. Bayan sun fita Safwan yace mommyn nan batada kirki. Sahir yace maybe kawayenta ne suka bata Mata rai. Rugawa sukayi da gudu abinsu ko a jikinsu.
Shiru shiru yazeed bai shigo ba har bacci ya dauki amarya a wajen. Mutuminku ko tun da aka daura aure ya shige dakinsa ya kwanta Baku kara jin duriyar sa ba yanaji aka kawo amarya aka gama bidiri aka wuce tsaki yaja tare da kwanciya haka kawai yakejin haushin kowa dake tare dashi a lokacin ji yake kamar ba shi ba.
Minal kuwa tsakar dare zayyana ta tashi ta fara musu kuka aka bata mama anyi yin duniya amma sai kuka basu suka rintsa ba sai bayan asuba yayinda sahla ta dinga bacci kamar gawa.
BAYAN SHEKARU 8
Dauke shi da Mari safina tayi tare da cewa wallahi sahir idan baka fice mun a daki ba zaka Rena kanka idan ba rainin hankali ba da ban yini ba zaka ganni ne? Tsabar munafurci zaka wani zo wai gaisheni? Kuma saura inji ka fadawa wa ubanku ni da kai ne mangajesa tayi tare da fita ta kunna TV a parlourn sama tare da kure murya kamar cinema.
Mummy ne ta fito tare da cewa haba safina irin wannan murya sukace cinema? Ki rage muryar tv din mana. Tafiya mummy taci gaba dayi amma me ? Sai safina taja tsaki juyowa mummy tayi tace je safina karkiga ina daga miki kafa ko nemi ki kawomin hauka a gida kinaji na ko toh wallahi idan baki kiyayeni ba zaki sani aikin banza da wofi. Mikewa tayi tare da cewa ke tsohuwa dakata kiji….. mummy ne ta datse ta ta hanyar cewa uwarki ne tsohuwa.
Daga hannu tayi zata wanke mummy da Mari ayush tayi caraf ta rike hannunta sannan ta yanka Mata Marin. Dariya ta sheke dashi kamin ta tattare zanyi nanfa suka zage dantse suka casu suns zagin juna ayush na fadin dama a karuwancinki na barki kikayi yayinda safina ke fadin ai yafimin zama da wannan Dan wahalar Wanda tunda mukayi aure sau daya ya rike hannuna.
Mummy ne tayi kokarin rabasu aka mangaje ta, ta doke kai da gini ashar ta danna tare da cewa yasin babu abinda zai hana Dana sakinki. Dariya safina tayi tace wai danki, ke bakiji kunya ba ? AI shekarata 2 a gidannan na gano ba danki bane. Kuma da kike zancen saki AI gara zawarci da aurennan saide babu inda zani yadda na wahala na shekaru 8 wallahi kuma bazakuji dadi ba. Kuma wata shegiya tace zata fada masa taga ikon Allah komawa tayi ta zauna akan kujera sai haki take sanadin fadar da sukayi tare da turo Dankwali gaban kai.
Cikin tsoro mummy da ayush ke kallo juna jamin sukayi wuf sula shige daki tare da yin kuskus.
🌹🍀
Abangaren su minal kuwa ta auri sabi saide dukan yau daban na gobe daban ga ummu amina bata da lafiya wannan dalilin kadai yasa minal bata gudu da daga gidan ba.
Zayyana da sahla ne a kofar gida, sahla na yar carafke yayinda zayyana ke yar gala gala akan hanya. Yaran anguwa babu Wanda ya isa ya taka idan zaka taka kuma ka wuce toh dole ta mareka haka yara ke kin zuwa aike saboda ta kasa ta tsare tijararta yafi na mahaifiyar ta.
Da daddare minal da sabi sukayi wani fadan hakan yasa ya zaro wuka zai kokuwa suka fara yi har suka bige lantarkin su. Hankadesa tayi ya fada aiko akayi rashin sa’a ya fada akan wukar ihu ya saki hankan ya tsoratar da minal sosai babu shiri ta dauki sahla wacce take shiru shiru kuma batada kuzari tare da tashin zayyana cijewa ta fara yi minal tace idan baki Mike mun tafi ba gobe zaki mutu babu shiri tarigasu isa bakin kofa tafiya sukayi sosai cikin daren wajajen karfe 3 jiri ya dauke minal ta suma tsabar tashin hankali ga tsoron kisa, ga daukar yarinya gashi yanayin da tabar jikin ummu Anya kuwa ta Mata adalci, iya ta dauketa lokacin da batada kowa kamar nata tayi Mata komai amma da abinda zata saka mata dashi kenan? Kai amma yaranta fa tunda dukda ba ita ta kashe sabi ba ita za’a daurawa balle ansan basa jituwa. Ga ummu kuma rai a hannun Allah hawan jini ya addabe ta.
Jijjigata suka fara yi suna kuka suna kiran sunanta wani ya haskosu da tocila tare da cewa kai! Su waye a wajen ne? Matsowa kusa yayi ganin kamar yara ne. Haska Fuskar minal yayi cikin rawar baki yace YAR UWA? KECE?
KO SHIN WANENE WANNAN MUTUMIN? TAMBAYAR MAI SAUKI CE AMMA DUK WANDA YA ANSA TA TO CHAPTER BIYU NA GABA DUK NASHI NE SHI DAYA.3
TEASER/CIKIN CHAPTER NA GABA: minal zata hadu da yazeed………
MASHA ALLAH, AYI MIN AFUWA JIYA KUN JINI SHIRU, SAFGOGI NE SUKA SHIGEMIN GABA.
DEDICATED TO @MYNEWFANS.
GOODNEWS: their will be another update today by 5pm insha Allah stay tune.1
DON’T FORGET TO VOTE AND COMMENT.
ONE LOVE FROM
Miss untichlobanty 💕
10 April, 2020.
RECAP
Jijjigata suka fara yi suna kuka suna kiran sunanta wani ya haskosu da tocila tare da cewa kai! Su waye a wajen ne? Matsowa kusa yayi ganin kamar yara ne. Haska Fuskar minal yayi cikin rawar baki yace YAR UWA? KECE?
CONTINUATION
Gumi ne ya fara tsatstsafo masa cikin tashin hankali ya sake furta yar uwa? Ashe rai kanga rai? Daukarta yayi tare da cewa yaran su biyosa. Zayyana tace ka San mu ne? Ina zaka kai mana ummin mu? Bai kulata ba har suka iso gidansu dakin mahaifiyar sa ya kaita.
Ummu sabir tana cin goronta taga ya fado da mace da yara tace kai dannan, me zan gani haka? Yace ummu nasan bazakiso ba amma ki daure ki danne zuciya kinga matata ma tabar gidannan ne sandiyyar ki. Kwata kwata bana iya zama da mace saboda ke ki daure kibar wannan baiwar Allah ta zauna ko na lokaci kadan ne tsaki taja tace kar ka fice da wadannan Ababa a daki kaima sai in tsine ma. Hawaye ne suka cika masa idanu jiki a sanyaye ya juya ya fita tareda kaisu dakin matarsa. Kwantar da minal yayi sannan ya yaiyafa Mata ruwa. A hankali tace ruwa, ruwa.+
Ruwa ya dauko ya ba ma zayyana yace ta bata sannan ya fita ko zai samo abinci. Garzayawa yayi ya koma gidan da yake gadi ya sanar dasu abinda ya faru, nan suka bashi abinci da wasu surutu sukace yakai ma minal din.
Koda ya dawo minal har ta Dan ware nan ya basu tare da ficewa sallar asuba.
Bayan ya dawo minal tayi masa godiya harda hawaye kamin yace niko kamar na sanka. Murmushi yayi yace Dan uwa ne fa. Shiru tayi ta gama nazari bata gano wani Dan uwa ba. Nan sabir ya labarta Mata yadda akayi aiko ta dinga yi masa godiya.
Dakin mahaifiyar sa ya leka ya sanar da ita zai koma bakin aikinsa. Dauke kai tayi tare da fadin da fatan tare zaku tafi? Yace haba baba kiyi hakuri mana zasu bar gidannan amma yanzu ki daga musu kafa. Naji kawai tace hakan yasa shi sauke ajiyan zuciya harda godiya sannan ya fice.
A hanyarsa ko tunanin halin mahaifiyar sa yake ita indai harka ba ta kudi bane to baza’ayi da ita ba. Tunda ya rasa aikinsa ya kasa gane kanta. Haka ya isa gurin aiki hankalinsa ba a kwance ba.
Samu yayi gidan anata shirye shirye ya tambayi me bayin flower me ke faruwa ne ? Me bayin flower yace bakasan cewa yau diyar Alhaji na biyu zata dawo ba? Sabir yace ikon Allah gaskiya naji dadi. Mai bayin flower yace cab lallai an barka a baya kace kaji dadi? Wannan yarinyar bata ganin kowa da gashi a tsakiyar ka. Sabir yace kaga malam, ni banason gulma. Sannan ya koma bakin aikinsa.
A gida kuwa sabir yana fita mamar sa ta fito ta samu sahla da zayyana a bakin rijiya runa dibar ruwa. Warce gugar tayi tace Dan…… wa ya Baku izinin shan ruwa a gidannan? Zayyana tace ishi mukeji. Tace kinci ….. sahla cikin muryarta na abin tausayi tace kiyi hakuri. Idonta sun ciko da hawaye .
Minal ce ta fito tana kokarin bada hakuri kawai ummu sabir ta adungure kan sahla kan kace tak ta fada rijiyar. Wani irin kara ta saki ta fara ihun neman taimako mutane ne suka shigo aka cirota kamar gawa kokarin ceto ta samarin sukeyi amma minal gani take kamar kasheta zasuyi hakan yasa ta karbi yarta ta wuce suka fice a gidan Allah wadai mutane sukayi da irin halin ummu sabir sannan suka fice.
Tana tafe batasan inda take wulla kafarta ba Dan ji take kamar tana dauke da gawar yarta ne duba da yanayin sahlan. Zayyana ne taja hannunta ta zaunar da a bakin wani gini tace ummi ku zauna anan bara in kawo mana ruwa.
Tafiya ta fara bata masan inda zata Sami famfo ko rijiya Dan sun fara shiga cikin Abuja, pure water kuwa sai ka siya.
🌹🍀
Yazeed ne zaune a office yana shan tea sai ya tuno cewa yanada meeting kuma personal assistant dinshi bai tunatar dashi ba cikin bacin rai ya Mike tare da danna kararrawar neman sa Wanda yayi sanadiyyar faduwar wayansbi ya fashe. Shiru yaji har minti biyu suka wuce hakan yasa ya Dan sassauto tare da tunanin ko baya kusa ne. CCTV footage na office dinsa ya duba amma me? Bacci take harda yawun bacci. Wani tafasa ya farayi baisan sanda ya jefi gini da wayarsa ba. Babu wasting time personal assistant yasan inda dare yayi masa. Yayinda yazeed ya fice domin Nemo wani waya dukda ko zai iya sawa a kawo masa amma duniyar yanzu sai ayi connecting wayan yanda za’a iya samun muhimman abubuwa.
STORY CONTINUES BELOW

Zayyana na tafe hannunta rike da naira 10 da aka taimaka Mata dashi har ta iso wajen traffic. Wata mota ta gani booth dinshi a abude kawai taje da gulma wai zata rufe kudin ta ne ya fada ciki Dan haka ta shiga zata dauka. Tafiya motar ta fara yi sanadiyyar hannu da aka basu. Nan ido ya Rena fata tayi ihu har ta gaji amma me motar ya kure sauti Dan haka bayaji dadin abun ma booth din a bude Dan haka tana shan numfashi. Cikin gari suka shiga nan fa ta saki baki tana kallon ikon Allah.
Abinda yasa mutane kuwa basu ganin ta saboda a kwance taje kuma booth din bai wangale sosai ba da mai motar zai gani ta mirror ya rufe. Jin an tsaya yasata buya a cikin rigar mota.
Aikuwa baifi second uku ba securities suka duba booth din inda suke ce masa malam you are careless fa, kana bari booth ba’a rufe ba ko? Dariya hausar securityn ya bawa zayyana. Kunshewa tayi yayinda suka rufe masa booth din amma bai rufu ba nan suka gane cewa hook din ya baci ne sannan suka barshi bayan sunmai warning.
Ciki ya shiga ya yayi parking sannan ya fice bayan kamar minti biyar sai ta fito. Kokarin karanta abinda aka rubuta a sama tayi. Shoo….s..ho? Kai sho…pi..re.. a ah ri ne. Sho…pi..ri..te….
Dariya ta kyalkyale dashi tace kai ni banza ce wallahi ashe shoprise ne toh ko me yasa suka rubuta shoprite oho.
Wasu family masu yawa ne zasu shiga ta shige cikinsu suka shiga tare nan fa ta fara ciyar da idonta abinci. Officials idan sun ganta sai su tambayeta ta harshen turanci itako dayake kwakwalwar kamar na uwar ne sai kawai tanuna wani waje tace can sai ta hudu. Su kuwa basu gane ba duba da kayan jikinta sabi ne masu kyau Wanda aka bawa sabir ya basu kuma tanada harke dukda cewa batakai mamanta ba sai suke Mata ganin ajebo.
Tana cikin tafiya ta iso wajen na’urori(gadgets) sakan ido da baki tayi tana kallo cikin karamar muryata ta yara tace kai jama’a kaga wayoyi masu kyau ba irin na ummi ba. Bara in dauko Mata wancan.
Juyawa tayi taga wani ya fito mutane biyu na binshi a baya. Sai taji ana sanarwa da turanci tabe baki tayi tace ko me suke cewa oho.
Wallet din mutumin taga ya fado da alamu bai lura ba Dan haka ta dauka budewa tayi taga kudi har ta juya da gudu tanajin dadi sai ta tuna abinda minal ta fada Musu “misalin abinda ba naki ba kamar wuta ne, shin zaki dauki wuta balle kici?” Juyowa tayi da gudu ta fara binshi tana uncle! Uncle! Uncle!
Yana tafe yanajin anata uncle amma bai dauka dashi akeyi ba. Jin ana uncle me kaman larabawa yashashi tsayawa tare da ganin wake damun mutane da ihu haka. Wata yarinya ce ta tsaya a gabansa tana haki. Cikin ƙufula yace ehm? Lafiya? Cikin yatsine fuska irin na ka renamin wayo zayyana ta kama kunkumi tare da cewa kaji min mutuminnan fa. Kama rasa abinda zaka ce min sai uhm lafiya? Karka kaga shekarana 8 karfi gareni. Nausa hannu da kafa tayi yayinda tayi murmushin gefen baki yace calm down little girl me kikeso. Tace ni ba little bace fa ehe yace okay big lady (babbar mace) inajinki, uncle yana sauri. Kauda kai tayi tare da miko masa wallet dinsa shafa aljihunsa yayi yaji babu. Murmushi ya danyi ya karba tare da shafa kanta yace godiya nake boss lady 5k ya miko Mata ta karba ta jujjuya yadau ta Rena ne sai yaga ta dauki daya ta dawo masa da sauran tace daga gani manyan kudi ne Dan haka kwalli daya ma ya isheni a madadin wadannan ka mayar dani wajen ummi na. Murmushi yayi yace angama boss lady muje ko sannan ki rike wadannan din ma na baki.
Washe baki tayi tace ba gode sannan ta riko hannunshi suka fito. Mota suka shiga nan ta fada masa abubuwa Sheda data rike a kanta na inda tabar minal yace boss lady wannan wani irin kwatance ne babu sunan anguwa sai sunan wani gini ta ina zan gane. Driver dinsa yace na gane wajen sir yazeed yace muje toh. Suna cikin tafiya tace kai gaskiya uncle motar ka nada kyau. Yace Allah ko boss lady? Nikam ya sunan boss lady. Cikin jin dadin zancen ta gyara zama tace sunana zayyana zaka iya cemin zayya, kaifa uncle yaya sunanka? Yace sunana uncle yazeed. Tace naji dadin ganinka uncle yazeed. Hirarsu suka cigaba dayi har suka iso tace yauwa tsaya anan gasucan bude kofa tayi ta sauko tare da cewa uncle na gode sai wata rana yace haba boss lady bakyaso inga mommyn mu ne? Tace nk no no mummy na kyakkyawa ce sai da kudi ake ganinta. Rugawa tayi a guje zai bita secretary dinshi yace sir mutanen nan sun iso suna meeting hall kuma kai suke jira and masu neman aikin personal assistant dinka sun hadu for interview hakan yasa ya hakura tare da sa ran zai dawo domin meeting din is important yaso ace ya kalli Fuskar maman amma ta bashi baya da alamu mutanen dake cikin motar gefenta ke mata magana.
Zayya tana isa taga wasu yan Mata suna fadin baiwar Allah ya haka zaki zauna da yarinya me bacci a titi kina kuka dauke kai tayi ganin sun takura yasata cewa ta mutu…. zayya tace me?! Ummu me kike cewa sahla ta mutu? Har idonta ya ciko da kwalla ya fara zuba faduwa tayi a guiwanta ta matso kusa da ita tace kanwata karki barni Dan Allah. Daya daga cikin yan matan ne tace karkice ta mutu muje gida a kawo likita ya duba ta dai tana da rai.
Mikewa minal tayi cikin fitar hayyaci tace kin tabbata tana raye baiwar Allah karki sakamin rai fa.
Sai a lokacin suka kalli fuskarta take suka ja da baya baya sunan fadin wayo Allah mun shigesu. Nafeesa tace aunty me nake gani haka?
GENG GENG GENG ME YASA KUKE GANIN SUKA TSORATA? SANNAN YAYA RAYUWA ZATA KASANCE? DONT FORGET TO VOTE, COMMENT AND FOLLOW ME.
DEDICATED TO Ramatu326611, aishatu_humairah, and zeemeen092
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU wato
miss Untichlobanty 💕
12 April, 2020.RECAP
Zayya tana isa taga wasu yan Mata suna fadin baiwar Allah ya haka zaki zauna da yarinya me bacci a titi kina kuka dauke kai tayi ganin sun takura yasata cewa ta mutu…. zayya tace me?! Ummu me kike cewa sahla ta mutu? Har idonta ya ciko da kwalla ya fara zuba faduwa tayi a guiwanta ta matso kusa da ita tace kanwata karki barni Dan Allah. Daya daga cikin yan matan ne tace karkice ta mutu muje gida a kawo likita ya duba ta dai tana da rai.
Mikewa minal tayi cikin fitar hayyaci tace kin tabbata tana raye baiwar Allah karki sakamin rai fa.
Sai a lokacin suka kalli fuskarta take suka ja da baya baya sunan fadin wayo Allah mun shigesu. Nafeesa tace aunty me nake gani haka?
CONTINUATION
Nafeesa wacce bazata wuce shekaru 18 ba tace aunty me nake gani haka? Me aunty bushra keyi anan ba yanzu muka barota a gida ba? Dakata, y
anzu na gane abinda sabir ke fada dazu Allah sarki ashe da gaskiyarsa
Mintuna kadan da suka wuce
Sabir na komawa gida ya iske wannan labari haka yadan bi sawu amma bai gansuba cikin tashin hankali ya nufo gidan da yake gadi domin su taimaka a sanar a gidan rediyo, talabijin da sauran su.
Acan kuwa……
“Oyoyo aunty Bushra sannu da dawowa” nafeesa wato feena ke fadin haka yayinda ta rugo a guje saura kiris ta fadi a beni sanadiyyar karar motan da taji. Wata budurwace ta fito daga ciki tana yarfe gashinta dake kan farin fuskarta tare da gyara tabarau din dake manne a idonta murmushi ta saki lokacin da ta sanya kanwarta nafisa a idanunta. Rungume juna sukayi feena na turo baki cikin shagwaba tahau magana…+
Amma wani hanzari ba gudu ba na kasa saurara balle har na rubuta abinda take fadi domin nifa ba kowa nake gani a tsaye ba sai minal cikin kananun kaya saide wannan tafi minal kiba da kirji sannan minal ta fita gashi da tsayi.
Sauran yan gidan ne suka fito suna Mata marhaban. Ana cikin haka sabir ya shigo duk ya hada gumi yana fadin hajiya wannan baiwar Allahn ta gudu daga gida sabod……..
Maganarce ta makale masa a makokoro cikin rawar yatsa yake nuna bushra yace yar uwa me kukeyi anan sannan ina yaran. Wani kallon ka renamin wayo ta mai tace (Dan Iska me ka kirani yanzunnan?) what the fuck did you just called me? Baki ya bude zai bada amsa amma bai samu dama ba sanadin Marin data yanka masa. Mahaifiyarsu ce ta riko ta tare da cewa ke bushra bakida hankali ne zaki daki namiji? Kuma ya girmeki? Banason rashin tarbiyya, au abinda kika koyo a turan kenan? Toh bari mahaifinki ya dawo zakiga ikon Allah.
Hakuri suka bawa sabir Wanda ya kasa yin komai yayinda tayi tsaki tayi wucewar ta. Fadawa tayi a kujera, tayi ciro da takalman kafunta tare da cewa (ji wani mafari mara kyau)what a bad start! Aunty jalila kanwar wacce takeda shekaru 32 maman su tace gaskiya bushra kin bani mamaki menene haka? Ya zaki Mari sabir? Mutumin kirki ga gaskiya kuma…. datseta bushran tayi ta hanyar cewa aunty kuyi min uziri ku siyomin icecream keda feena, kaina ciwo yake zamuyi magana anjima. And please ku zaku siyo kar a bada sako ma driver ko wani kazamin.
Tabe baki aunty jalila tayi kamin ta shiga daki tana fadin aiki ya sameki sannan ta shirya suka fice tare da cewa yarta shameela wacce take sa’ar su zayya ta zauna ta sakawa bushra ido idan tayi wani Abu ta sanar Mata. Ita kuwa abin nema ya samu saboda rawar kai gareta.
Hakuri suka sake bawa sabir sanda ya bude musu gate yace ba komai sannan suka fita suna cikin tattauna halin da ta dawo musu dashi feena tace la aunty kinga wata baiwar Allah zaune da yarinya a hannu ga za’ayi ruwa kuma dai nan ba wajen bara bane. Haka kawai aunty jalila taji tanason ta tsaya dukda yadda zamaninnan ya baci.
Magana sula fara Mata amma taki ta dage kanta balle ta kulasu sai kuka take ana cikin hakane zayya ta dawo……
CIGABAN LABARI
Ajiyan zuciya minal ta sauke tana mamaki da akace akwai me kama da ita. Feena tace aunty zo kiji, cikin kunne ta fada Mata wani Abu sukayi yar shawara.
Tsugunawa tayi a gaban minal tace kinga yanzu ruwa za’ayi kuma da alamu bakida wajen zuwa me zai hana ki biyo mu. Girgiza kai tayi tare da cewa ni yanzu bazan yarda da kowa ba ku barmu ni da yara na kawai mu mutu.
Aunty jalila tace wannan wacce irin… kasa karashe wa tayi sanadiyyar ruwan daya tsinke zayya ne fara rokanta akan su bisu kawai kar ruwa ya halaka yar uwata. Badon ran minal yaso ba tabisu.
Yazeed kuwa suna cikin tafiya ruwa ya balle Abu na farko da ya fado a ransa shine boss ladynsa. Ganin hankalinsa bai kwanta yasa yace su juya koda ya koma yaga wayam haka yanaji yana gani ya hakura.
………..
Suna shigowa gida suka sassauko a motar da sauri suka shiga ciki saboda ruwa yayinda akabar feena da zayya suna dauko ledan icecream. Shameela na ganinsu tace mummy wallahi kina fita aunty bushra ta sa ya sabir aiki wai ya goge Mata takalma….. aunty jalila tace yanzu tana ina? Tace tana dakin mama.
A waje kuwa daidai zayya ta juya ta hango wani kamar ta sanshi amma ta share batayi magana ba taci gaba da yiwa feena hira suna dariya suka shiga ciki.
Surutun da shameela keyi na ya tsaya lokacin da ta lura da minal dake bayan jalila. Kallon saman beni tayi ta kuma kallo minal sai ta bazama a guje tayi sama cikin haki ta bude dakin mama taga bushra a cikin dakin sai ta kallo minal, ta sake kallo Bushra ta kalli minal kawai sai ta fashe da kuka.
Waiyo umma(abinda take kiran mama dashi) na shiga uku na haukace. A tsorace mama da bushra sukayo kanta suna fadin lafiya ? Nuno minal tayi da yatsa aiko minal da bushra suka hada ido.
Kallo kurilla sukewa juna yayinda mama ke fadin ke jalila me nake gani haka? Murmushi tayi kamin ta fara fadawa mama yadda akayi. Mama tace no wonder sabir ya Kira bushra da yar uwa ya dauka itace ashe…. wani tunani ne ya fado Mata bata karasa zancen ba tace ke dakata hakan na nufin itace Wanda ta gudu yake neman ta. Ke shameela je ki Kira mana sabir, da gudu ta fita a bakin kofa sukayi karo ita da zayya. Tsaki taja kamin ta fice zayya ta bita da kallo. A lalle za’ayi cakwakiya bata sanni bane kar taga nan gidansu ne babu abinda ya dameni wallahi wulakanci zan Mata kar taga gidansune.
Ganin kallo yayi yawa yasa feena tambayarta ko ta Santa ne? Tace a ah.
Haka dai sabir ya shigo ya roki afuwar su sannan aka duba sahla inda aka tabbatar tanada rai saide a halittarta bata juran wahala.
Minal da bushra dai basu cewa wa juna komai ba har dare yayi sukaci abinci. Ba ciki na ciki, minal ta kasa gaskata akwai me kama da ita yayinda bushra kejin haushi ya za’ayi ita da take ganin tanada kyau ace wata banziya gayyar talauci tana kama da ita har ma ta fita kyau.
Wasa wasa lokacin na tafiya safina hargutsa gidan yazeed baki daya. Yayinda sahir ya tafi cambridge university karatu safwan kuwa yace a kasarsa zai makale babu inda zashi danshi Dan baba ne.
Bayan shekaru 6
Da baya baya yake ja idonsa cike fal da tsoro kamar kulya a lungu kafarsa na mazari Dan yasan kashinsa ya bushe tunda ya sake ya jefi zayya da ball.
Gefe kuwa yan team dinsu ne tsaya suna cika suna batsewa. Kirbashi ko ta soma tun yana ihu har ya daina da alamu ya suma yarda shi tayi ta juya zata tafi ogan team din cikin harshen turanci yace ke kina tunanin kin daki banza ne ? juyowa tayi suka hada ido.
Ido cikin ido suka fara nufo juna gaba daya daliban da suka taru suna kallo baya baya suka fara yi Dan sunsan yau za’ayi world war na 3…..
Don’t forget to vote, comment and follow me. I repeat vote and comment ooo.
DEDICATED TO: aysherahmaddanlami
Love you all💋❤
Miss Untichlobanty 💕
14th April, 2020.OH WAI YANZU COMMENT DIN MA AN DENA.
RECAP
Ido cikin ido suka fara nufo juna gaba daya daliban da suka taru suna kallo baya baya suka fara yi Dan sunsan yau za’ayi world war na 3…..
CONTINUATION
Naushi ya kawo Mata ta kauce, caraf tayi ta riko shi tare da basa one blow seven die. Haka dai ta hadesu duka su goman ta basu kashi.
Principal ne yazo kanshi ya bata sammacinta lokacin da aka dawo daga wasa.
Cikin takunta na maza ta shigo dakin taron Dan malamai gaba daya sun taru, cikin harshen turanci tace malamai sannunku sannan ta dauke kai.
Ajiyan zuciya principal Solomon ya sauke tare dacewa zayyana meyasa? Meyasa bakyajin magana ko kadan? Ke wace irin matamaza(tomboy) ce? Mun baki hutun hukunci (suspension) yadi Akirga,hukuncin Karin lokacin tashi (detention) kuwa yana cikin jadawalinki. Kinsani a Bisa ka’idar makarantan nan ba’a duka tunda international school ne Dan haka mun yanke shawara zamu mayar dake dayan branch dinmu Wanda babu musulmai,babu hausawa, babu yan kasarnan saide yan wata kasa.
Tunda principal din ya fara magana ta saka earpiece a kunnenta dan haka koda ya gama godiya tayi ta karbi paper da ya bata sannan tayi ficewarta aji ta koma ta zauna a kujerarta Wanda ke karshen aji sannan ta fara shirgar baccinta. Girgiza kai malamin yayi kamin yaci gaba da bada darasi.+
Koda aka tashi sanda sukayi fada da shameela akan ta bata musu lokaci zayya bata ce kala ba sanda shameela ta gama zayya tace bana taba Mata saboda ragwaye ne sannan ta wuce abinta.
Suna dawowa suka samu kowa da kowa a parlour barka da zuwa aka musu mama na zaune a gefen daddy wato Alhaji mansur mainasara, yayinda aunty jalila ke hararan kanwar shameela wato nana saboda tayi roko.
Bushra aka tisa a gaba akewa fada akan yadda ta rufe ido Sam wai ita sai mai kudi zata aura. Ga yadda take wulakanta talakawa kuma hakan matsala ke haifar musu ita da minal.
Ko ina idan minal taje neman aiki sai ace ba ita bace tayi wulakanci a waje kaza ? Sai a koreta komin rantsuwar da zatayi, yayinda ita kuma bushra ake cewa an ganta a waje kaza da shiga ta mutanen arziki. Shiyasa kullum sai sunyi fada.
Daidai lokacin minal ta sauko tana sauri tace bye bye everyone (kowa da kowa ) ni na fita inada interview Alhaji mansur ne yace haba minal ni zakibi ta tawa da kin bari na miki hanya kin samu aikinnnan cikin sauki. Girgiza kai tayi tace no daddy nafiso insha wahala in Nemo da kaina zanfi daraja aikin. Murmushi yayi yace kuma hakane kinci wannan yar uwar taki ita ba aikin za’a nema Mata ba ko yi Mata za’ayi bazata karba ba nide nayi asarar kudin karatu . Mikewa bushra tayi tana fadin haba dady tunda wannan imposter (me satan kamannin wani) tazo gidan nan ka dena sona komai akayi minal, minal, minal,minal.
Dariya yayi yace yaro man kaza ai sai ki yi aure ko kinga ba sai kinganta ba balle ta baki haushi. Kema.. ya fadi hakan yana kallon minal ya kamata ki samu miji ki sake aure tunda dai a asibiti ance babu abinda ya samu kwakwalwar ki malamai ma sun duba ki ance ba komai ko akwai abinda kikeji. Tace a ah kawai de idan suna duba ni sai in fara ji na tuna komai da sungama kuma sai na sake mantawa gashi kuma ko nayi kokarin fada kasawa nake.
Ajiyan zuciya yayi yace Allah dai ta kyauta. Fitowa tayi sabir na labe domin ya tabbatar ba bushra bace Dan batason ko ganinsa tayi acewarta.
Ganin ya tabbatar minal ne yasa yazo suka gaggaisa sannan ta fice bayan ya Mata addu’ar Allah ya bada sa’a.
Ba’a Dan Jima ba sai ga bushra ta fito itama buya yayi a bayan flower zuciyarsa na lugude.
Tuka motan ta take tanata sauri Dan tayi latti motan dake gabanta ne ya tsaya ba tare da bada alama ba aiko sukaci karo kau.
Iska ta furzar tare da saukowa ta cika tayi fam. Shima (yazeed) fitowa yayi kannensa dauke da bluetooth tare da fadin zan kiraka ta harshen larabci sannan ya kashe.
STORY CONTINUES BELOW

Masifa ta fara yi masa baka ganine? Ya zakayi muna cikin tafiya ka tsaya? Ba tare da ya ce komai ba ya nuna Mata traffic light. Rufe ido tayi tare da shafa fiskanta tace kayi hakuri ban lura bane na….. datseta yayi ta hanyar cewa banida lokacin wannan ki bani business card dinki cikin harshen larabci Dan shi ya manta domin waya yake da Jamal lokacin da abin ya faru.
Tace mene? Ya sake cewa nace ki bani katin kasuwancin ki ko bakyajin larabci ne ? Sarai taji abinda yace amma tasan rainin wayo ne kawai irin na mai kudi yana Nigeria yace bai iya hausa ba? sai tace la ban iya ba, banaji, ka gane me nace, la Arabic, la okay? Mota ya koma ya dauko wayarsa tare da daukan hotonta sannan ya karbi wayan hannunta yasa numbarsa ya Kira. Tace kai dalla malam ka bani wayata ko bakaji ne? Nace ka bani wayata ko? Mika Mata yayi still ta larabci yace yanzu inada hotonki inada numbarki zan kiraki mu tattauna kudin gyaran. Purse dinta ta dauko ta ciro passport dinta ta bashi tace ga hoto na maza goge hoton da ka dauka. Karba yayi yasa acikin suit dinsa sannan ya shige mota kan tayi magana yaja abinda saboda an basu hannu. Tace kai, kazo ka goge hotonnan wallahi. Tsaki taja ta shige motar ta duba madubi tayi Dan ta gyara wuyan hijabinta sai taga ashe man bakin ta ne ya baci. Naushin steering tayi tare da cewa Allah ya hadamu kaga ikon Allah sannan ta wuce.
Aiko taci interview kuma ta samu aiki a jeedmar group a department din ayush….
Da yamma da ta dawo gida ta samu an taru a parlour kowa yayi jungum jungum an kafe zayya da ido zama tayi tana me fadin lafiya? Letter da aka bawa zayya aka miko Mata ta karanta abinda ke ciki kamar haka.
“Letar sauya makaranta
Duba da yadda daliba zayya mainasara ta addabi makaranta saboda rashin jin ta, da yadda take fada da maza. Hukumar makaranta ta yanke shawaran mayar da ita dayan cibiyar mu Wanda ke wajen gari kuma makarantar kwana la Alla zatayi hankali.
Idan har iyayenta basu yarda da wannan hukunci ba toh saide a gafarcemu domin bamuda wata zabi da ya wuce mu koreta .
Mun gode ~~
Saka hannun makaranta

Mikewa minal tayi tare da riko hannunta suka shiga daki,dadi ne ya kama shameela yau za’a daki zayya yayinda cikin daki kuwa minal tace zayya na fahimceki domin nima nayi abinda kikeyi yanzu haka, yau dinnan ma naso in daki wani amma yanzu na girma, bawai ina karfafa miki guiwa bane saide banason ki dinga taro fada, amma kuma karki zauna a cuceki kinji? Kuka ta fara yi tace mummy ni gaskiya a cireni daga makarantar banason rabuwa dake, minal tace karki damu ni inaji a jikina ALKHAIRI ne kuma zan dinga kawo miki ziyara duk karshen wata sannan zan canja miki sabuwa waya ma, washe baki tayi tace da gaske? Minal tace sosai ma kuwa na samu aiki yau. Ihun dadi ta sake shameela dake kasa tace yes a kara Mata Alhaji mansur yace je banson shashanci fa. Zayya ne ta sauko tana fadin grandpa mummy ta samu aiki! mummy ta samu aiki! Murna aka taya minal yayinda da aunty feena da aminiyarta deena suka ja minal daki cikin kaguwa sukace sis a wani company ne tace a jeedmar ne sukace what?! Mene? A jeedmar? Deena tace wow! Naji ance president din kyakkyawa ne, feena tace dama nice saide abinda na karanta idan na samu aikin dakyar idan zan dinga ganinsa. Minal tace nima sai akace muku ganinsa zanyi ko Dan shi naje yin aikin? Dariya suka kyalkyale dashi sunata bata labarin yazeed.
Bayan Sato biyu
Zayya ne rike da akwatinta tsaye a bakin makarantan su tana kare masa kallo kai amma an rena wa bakaken fata, wato shine su akayi musu nasu local amma dubi wannan branch din kamar a turai, itakam rashin ji yayi Mata rana. Bude kofofin hancinta tayi ta shaki iska tana sakan murmushi kamin ta shiga. Bawa idonta abinci take sosai Dan jinta take kamar a kasar waje. Gaba daya yan makarantan ke binta da kallo abinka da turawa da yan China su Korea ne, Italia ne Thailand ne yan turkiya dukdai gasunan suna al’ajabi domin sunsan ba’a kawo bakar fata makarantan su.
Cikin harshen turanci suke magana dan haka tace menene kuka kafa min ido? wata baturiya me suna halsey tazo cikin zumudi ta rungume zayya tace bakuwa a makarantar mu, sannunki da zuwa sunana halsey kuma zanso mu zama aminai, nasan ma kin yarda Dan haka mu aminai ne zo muje. Ta fadi haka tana janta.
A wani hostel kike? Wani daki?
HALSEY

Zayya tace dakata mana, da farko dai yaushe nace na yarda mu zama kawaye? Abin tausayi tayi tace bakyasona ne? Dariyar zayya tayi tace dalla gyara fuskarki ni ki rakani wajen principal. Zayya tace yay naji daidai muje….. rike hannu sukayi suka nufi office din principal. Knocking sukayi suka shiga suka samu principal dinsu yar kasar Australia. Murmushi tayi musu tace ku shigo mana sannan ta kalli zayya tace da alamu kece zayyana mainasara ko? Tace nice ma. Wani paper ta bata. Photo copy ne na student information tare da su hostel ajujuwan da zata dinga shiga da sauransu. Godiya tayi principal din ta bata uniform tana fadin principal Solomon ya ce bakida tarbiyya sai an miki tsauri ni banga alamun haka ba. Halsey tace kwarai kuwa principal, kawata tanada mugun kirki ga hankali sosai ma kuwa, mun gode, muje ko ? Ta fada tare da janta suka fice.
Halsey tace menene wannan wai a kanki, zayya tace shi aje Kira hijab, halsey tace me aikinsa to? Tace saboda rufe kyawun mu domin shine mutunci (modesty) bakyajin zafi? Zayya tace kin fiya tambaya gaskiya zan amsa miki rakani daki.
Halsey tace muga paper din, ihu ta kwalla lokacin da taga cewa dakinsu daya tace dakin mu daya muje! muje! muje! Unpacking kayan zayya sukayi halsey na fada Mata duk wani information da ya dace ta sani da yar iskar makarantar tasu.
Wayanta halsey ta dauko suka dauki selfies. Daddare zayya ta dauko diary dinta ta fara rubutu:
MONDAY– 6 JUNE
Yau nazo sabon makaranta na kuma wallahi kyau gareshi gashi nayi kawa mai suna halsey saide akwai wata banziya wai ita vanessa amma zanyi maganinta idan ta shiga sabga ta.
Don’t forget to VOTE, comment and share love you all.
Miss Untichlobanty 💕
15th April, 2020.RECAP
Wayanta halsey ta dauko suka dauki selfies. Daddare zayya ta dauko diary dinta ta fara rubutu:
MONDAY– 6 JUNE
Yau nazo sabon makaranta na kuma wallahi kyau gareshi gashi nayi kawa mai suna halsey saide akwai wata banziya wai ita vanessa amma zanyi maganinta idan ta shiga sabga ta.
CONTINUATION
Halsey ne tace zayya ki tashi muje muci abinci, zayya tace okay tare da rufe diary dinta suka fita. A layin siyan abinci ma haka aka dinga kallonta itako babu abinda ya shafeta.
Cikin dare suna bacci sukaji ansaki key a kofar dakinsu za’a bude. Textbook zayya ta dauka yayinda halsey ta dauki takalmi. Zayya ne ta bude tare da rafka ma Wanda ke bakin kofan textbook ashe hostel incharge ce ta kawo musu roommate dinsu me suna “na yeonsil” yar southern Korea ce.
Washe gari aka fara karatu zayya da taga ba gane komai take ba kawai tayi kwanciyarta.
Mafarki ta fara yi wai gata a kwace sanye da kayan snow white sai ga yarima yazo ya sumbace ta murmushi tayi ta fara bude idonta a hankali amma me tana bude idonta ta soma ihu tsabar muninsa.
Aiko ihun ta kwalla a gaske tana mai goge bakinta da tufarda da yawu bai tsaya a ko ina ba sai fuskar malamin su yayinda kowa ya tsura Mata ido.
Detention ticket (tikitin ladabtarwa) aka yanka Mata, cikin harshen hausa tace kai nikam na shiga uku tun ranar farko zan fara shiga detention? Malamin nasu Dan Korea ne yace kimin shiru kamin yaci gaba da darasi.+
Lokacin break suka shiga ban daki domin gyara kwalliyar su kamar yadda kukasan al’adar farin fata. Watsawa fuskarta ruwa tayi tare da sauke ajiyan zuciya tace in tambayeki mana halsey.
Idan mutum yayi mafarkin Dan sarki me hakan ke nufi? Halsey tace me kukayi dashi a mafarkin? Dan Sosa kai tayi tace kawai rike hannu mukayi. Tunani halsey tayi tace nide ban gane ba. Yeonsil dake kan shadda idan ta fadi ko wani kalma sai tayi nishi tace hakan na nufin zaki hadu da masoyinki a gaske. Juyowa sukayi su duka biyu suka kalli kofar ban dakin da take sai ki kake fatatata ta saki zawo.
Zayya kuwa gira daya ta daga ta ce WAYE SHI?…….
Bayan an tashi gaba daya zayya tayi sneaking ta fita daga makaranta ta siyo popcorn tana tafe tanacin abinta. A hanyarta na dawowa makaranta tayi Tuntube ya zube hakan yasa ranta ya baci ga su halsey na kiranta wai tayi sauri ta dawo kar a gane batanan. Tuno baki tayi tana tafiya tana kwallo da duk abinda ke gabanta.
Sahir ke take totir din motansa me budadden sama kawai yake Dan ya samu yancin watayawa babu speed limit a Nigeria shiyasa ma yaki fitowa tare da safwan.
Zayya kuwa wani gwangwani ta gani a gabanta cikin nauyin zuciya tayi shot dashi bai fada a ko ina ba sai goshin sahir aiko ya daki streetlight Wanda hakan yasa ya fara habo yayinda taci gaba da tafiyarta tanaji kamar tayi kuka.
Fitowa yayi tare da daukan gwangwanin dadin abun hanyar babu kowa. Yace hey! Ke ! Ke me UNIFORM! Juyowa tayi cikin harshen turanci yace bakida hankali ne? Tace kai kuma waye kai? Yace waye ni? Mamallakin wancan motar tare da nunawa da yatsarsa. Tace toh sai akayi yaya? Me alakata a ciki? Ta fadi haka fuskarta na nuna alamun rashin fahimtan inda ya dosa
Iska ya furzar tare da nuna Mata gwangwanin yace ke kika jefar da wannan? Tace bani bace. Yace amma ke kikayi kwallo dashi ko ta daga kai. Cikin masifa yace kaji karamar yar iska kin dauka lamarinnan wasa ne? Saura kiris ki kasheni !
Itama cikin daga murya da canja Fuskar abin tausayi zuwa yatsine tace me kake nufi ? ai ba da gangan nayi ba. Kuma wallahi ka fita daga idona na rufe Dan yanzu haka raina a bace yake.
STORY CONTINUES BELOW

Yace dalla dubata ni zakiyi wa barazana? Yanzu abar wannan magana zuwa anjima. Ya zakiyi da motata?
Fuskar kulya tasa adan shagwabe tace da alamu kai Dan masu kudi ne, abar maganan kaji? Yace kai ni warin talauci ma nakeji. Kasa kasa tace koma dai menene banza me mako kawai. Yace me kika ce? Tace karka damu zan biya kudin gyaran nawa ne? Yar bazawar dariya yayi yace kinsan nawa ne kudin motan nan kuwa?
Tace nawa ne? Murmushi yayi yace bar wannan zancen, tunda ke daliba ce zan miki ragi muyi 50 50 ki bada rabi in bada rabi. Tace nawa kenan yace ki kawo dala dubu Goma $10,000. Ido ta zaro tare da Jan numfashin da bata shirya ba tace mene? Yace bakiji ba? Cewa nayi $10,000. Tace la ga yan sanda nan sunzo ma. Juyawa yayi yana juyowa yaga wayam ta arce iska ya nausa tare da fesar da iskar. Yana shirin juyawa yaga wallet dinta. Dauka yayi yaga student ID card dinta a ciki yace hmm zamu hadu sannan ya shige mota.
🍀🍀🍀Zayya tana kwance a hostel tana bacci taji Karan motan yan sanda ta cikin speaker sukace zayyana mainasara you are under arrest kiyi saranda ko mu miki karfa karfa, kin dauka zaki rusa masa mota ki tsira ne? Da sauri ta leka window aiko motocin yan sanda ne guda 10 gaba daya sun saita window dinta da bindiga. Shugaban yaci gaba da cewa bazaki iya arcewa ba kiyi saranda kawai ko muyi harbi sauri tayi ta rufe window ta hanyo hularta da akwatinta sai ruwan bullet kakeji aiko ba shiri ta kwanta luf.🍀🍀🍀
Vibration din da wayanta yayi yasa tayi firgigit ta tashi daga mafarkin da take tare da sauke ajiyan zuciya ta goge gumin da ya tsattsafo Mata tare da kara wayar a kunnanta tace hello ? Ta dayan bangaren yace NINE! Tsaki taja tace me kuma kakeso yace AI bamu gama da case dinmu ba. Cikin tsiwa tace wani case kuma Bayan an wuce wajen? Tsk ince nabar muku makarantar Dan haka ka dena takura mini kaji ko? Ta karashe tana mai daga murya. Kallon wayan yayi kamin yace lafiyarki kuwa? Ko kan da matsala ne? Tace kai Aminu Yusuf kanason ka mutu ne? Yace Aminu Yusuf? Waye shi? Nifa SAHIR YAZEED ABDULMAJEED UMAR ne.
Tace mene? SAHIR YAZEED ABDULMAJEED UMAR? hmm waye kai? Yar murmushi yayi yace nine mamallakin Lexus dinnan da kika bata ko ince kika rusa. Zaro ido tayi tare da zare sim din wayar ta fara kukan shagwaba.
Bayan Sati daya minal da feena sun fito shopping kawai sukaji ana sanarwa wai customers suyi hakuri su fita baban mutum zai shigo. Minal tace wallahi babu inda zani ko shugaban kasa ne zai shigo, yo menene za’a wani shiga hakkinka. Ince duk Abu zamu siya? Feena ne tace nide yaya minal kinga tafiya ta minal tace jeki.
Yazeed yana cikin shopping din inner wears dinsa Dan baiyarda a siyo masa saboda kar a cutar dashi. Yaji kamar karan takalmi coge ta dayan bangaren kewaya wa yayi yaga wata macece amma bayanta yake gani tana siye siyenta. Body guard dinsa ne yace malama ke kurmace da za’ayi sanarwa a fita ke ki zauna a ciki kin wani dibo hijab kamar….. yazeed ne ya daga masa hannu yace karka zagi hijabi domin yanada muhimman ci a addini amma mafiya yawa Mata basusan da hakan ba Dan haka ka daraja mai hijabi balle ma irin su Abuja ai sai an daure za’a saka shi.
Murmushi tayi jin zantukan yazeed hakan yasa ta juyo domin taga waye sannan raji dalilin da yasa sai mutane sun fita zaiyi siyaiya amma me tana ganin yazeed ne tace wow! Daidai kenan dama kere na yawo zabo na yawo wata rana zasu hadu. Wato shine Dan wulakanci ranan nan ka dauki hoto na mai makon kace min man baki na ya baci wato ga shashasha ko?
Jin hayaniya yasa manager yazo dubawa ganin minal ke fere yazeed yasa yace security ku fita da ita hannu yazeed ya daga musu. Itako sands tamai tastas ta hankade keken siyaiyar nata wa manager sannan ta kalli yazeed tace kaikuma karka bari mu hadu a karo na uku mtsww, Sannan ta fice tana cika tana batsewa.
Feena ne tace yaya me ya faru, kauda kai minal tayi tace ashe wannan Dan renin hankalin daya Dakar mini mota na ne. Feena tace kina nufin yazeed abdulmajeed ne ya daki motar ki? Waiyo dama nice. Tsaki minal tayi tace ya akayi kikasan cewa banzan yazeed dinku ne? Feena tace da farko dai wasu yan nata ne naji suna cewa shine. Ba biyu kuma ba banza bane me kudi ne kuma…. minal ne ta datseta ta hanyar cewa karma ki fara banasonji kar kunnena suyi ciwo.
Yazeed kuwa a hanyarsa na zuwa gida ya Kira secretary dinshi yace ya batun personal assistant dinnan kowani department sun bada sunan masu hazaka? Secretary din yace eh yazeed yace this time around ni zanyi musu jarabawan da kaina Dan na gaji da canje canjen P.A dukansu kasalallu ne basa son aiki ko kadan.
Washe gari minal tana zuwa office aka miko Mata letter dinta akan cewa vacancy ne na PA din president kuma tana cikin masu hazaka idan tanaso toh karfe 10 am taje floor na Goma sha biyar wato na karshe anan zataga sauran abokan aikinta masu neman mukamin.
Karfe 9:45 ta shiga lifter domin zuwa floor din, ba kowa yake zuwa haka kawai ba sai da dalili Dan haka bata taba hawa nan ba. Lambobin ta duba taga daga floor na 14 ya tsaya. Fitowa tayi ta tambayi yadda ake zuwa sama aka nuna Mata wasu lifts guda biyu bata lura da rubutun dake sama ba kawai ta shige daya gani tayi tsarinshi daban ne harda kujera tace ikon Allah mutane da securities ne suka fadin wait! Dakata amma ina ta Riga ta danna top floor Dan haka ya rufe. Hankalin kowa ya tashi yau karamar ma’aikaciya ta shiga lift din president! Securities har wani zawo zawo sukeji.
Tana Isowa floor din ta fito abinda ta fara haduwa dashi shine secretaryn yazeed da wata assistant dinshi sun minke hannu kowa yana jira yaga wacce ta kawo hayaniya cikin building din. Harara assistant sin ta aika Mata yayinda secretary yace malama juya ki karanta saman kofan da kika fito. Karantawa tayi taga an rubuta PRIVATE ELEVATOR wato na musamman ne. Murmushin jin kunya tayi kamin tace yi hakuri ina sauri ne ban tsaya na karanta ba. Dan murmushi yayi yace ba komai amma ki kiyaye tace insha Allah.
Layi tazo tahau ta tsaya taga kowa sai gyara kwalliya ake tace wadannan ko lafiya sukewa tsoho kwalliya? Sunayensu aka fara Kira ko wacce ta shiga sai ta fito tana kuka, Kazan kuwa jiki a sanyaye suke fita sunan minal aka Kira ta shiga tana fargaban wani tambaya akeyi da yakesa mutane kuka da mutuwar jiki.
Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki haka ta shiga saide kujeransa ba ita yake fuskanta ba baya ya bata wato yana kallon gari ne tunda ofishin nasa bangare daya glass ne. Cikin kakkaurar murya kuma kamar ya gaji da yin maganan yace idan akwai jagwalgwalon da kuke Kira kwalliya a fuskarki toh ki fita ko jarabawar baza’a miki ba idan ko babu to kalli gefenki na dama. Babu musu ta aikata hakan kujerace akai akwai laptop da kuma files guda 10. Yace kalli agogo karfe nawa ne? Tace 11:50 yace mun rasa soft copy na wadannan files da kike gani Dan haka so nake kamin karfe 12:30 ki sake typing duka idan kuma bazaki iya ba toh KEMA GA HANYA!
HHHH TYPING IS NOT EASY! KARKU MANTA KUYI VOTING, COMMENTING DA KUMA SHARING.
NAJI WASU SUNA CEWA SUN ZAMA CONFUSE PLS KU FADAMIN ABINDA YA RUDAR DAKU DOMIN AYI MUKU BAYANI.
ONE LOVE💋
miss Untichlobanty 💕
16th April, 2020.RECAP
Cikin kakkaurar murya kuma kamar ya gaji da yin maganan yace idan akwai jagwalgwalon da kuke Kira kwalliya a fuskarki toh ki fita ko jarabawar baza’a miki ba idan ko babu to kalli gefenki na dama. Babu musu ta aikata hakan kujerace akai akwai laptop da kuma files guda 10. Yace kalli agogo karfe nawa ne? Tace 11:50 yace mun rasa soft copy na wadannan files da kike gani Dan haka so nake kamin karfe 12:45 ki sake typing duka sannan banason kuskure ko daya idan kuma bazaki iya ba toh KEMA GA HANYA!
CONTINUATION
Kallon files din tayi sannan tayi nazarin lokacin da aka bata indai aikin kwanciyan hankali zatayi toh kana bukatar awa biyu amma a kasa da awa daya akeson ta gama. Zama kawai tayi ba tare da tace mai kala ba, mamaki be ya kamashi da yaji karar keyboard. Ko shi da yakeda saurin aiki yana bukatar awa daya amma mace tayi tunanin zata gama a kasa da minti 55 ? Taurin Kaine kawai na Dan Adam.
Ganin saura mata minti hudu yasa shi yin murmushi faduwa dole. Itako garin sauri ta fice daga wajen Allah ya taimaka tanayi tana saving kokarin komawa tayi dukda ta cire rai saboda akwai file daya a gabanta amma me? Sai taga ga files dinnan gaba daya da me kuskure da Wanda yazeed din ya gyara wato wahalar banza yake basu daga karshe goge aikin zaiyi? Lallai ma mutuminnan. Ai in yasan wata baisan wata ba kaji tsohon nan fa ! Kofar file din tayi sai ta saka kuskure guda 1 daya saboda kar ya gane agogo ta kalla saura Mata second Goma sha biyu ta dannan control-save tace na gama. Yazeed dake Abu cikin wayarsa Dan ya sakankace faduwa zatayi ya kalli lokaci saura second 8. Abu biyu ne suka dira masa a lokaci daya mamaki da kuma kishi, yace karaso ki zauna. Hakan akayi amma me? Yana juyowa suka hada ido take annurin fuskarta ya dauke yayinda a nitse kamar yau ya fara ganinta yace miss mai nasara can you tell me why you want to be my personal assistant? (Ko shin zaki iya fadamin dalilin da yasa kikeso ki zama personal assistant dina?) Tabe baki tayi tace personal assistant na president ba naka ba tunda bansan kai bane president din, amma yanzu da na sani….. mikewa tayi tace kaga tafiya ta gobe zan kawo takardan barin aiki. Har takai bakin kofa yace dakata ms (miss) mainasara! Da alama sanda kika saka hannu a takardan aiki baki karanta ba? Ka’idar mu shine dole mutum yayi aiki damu a kalla na shekara 1 idan ba wani laifi yayi aka koreshi ba. Kinga bisa wannan dole kiyi aiki anan batun mukami kuwa nine me komai anan Dan haka no zan zabi Wanda naga dama ya zama kaza ko kaza. Daga gone office dinki ya dawo nan, banason latti! zaki iya tafiya.+
Washe gari lokacin free period sai surutu ake a ajin su zayya kaya kaya yayinda ta turo baki tayi jugum kamar ka dangwaleta tayi kuka.
Halsey da yeonsil ne suka zo sukace zayya wai ba yau bane 1 year anniversary dinku keda saurayinki? Ba yau zaizo ba? Ajiyan zuciya ta sauke tace jiya muka rabu sukace mene? Meyasa?
Kuzarinta ne ya dawo Mata a take tace kai kubar wannan zancen kunsan mota Lexus? Yeonsil tace nidai ban taba shiga cikinta ba amma na taba ji. Zayya tace kina ganin nawa za’a kashe domin a gyara Dan karamin kurjewa a jikinta? Ta fadi hakan tana gwada kankantar da hannun ta?
Murmushi me kyau halsey tayi tace ke gajiya me kika aikata? Cikin San yarda magana tana wasa da yatsarta tace bani bace kawata ce. Halsey tace a kudin kasarku akalla dubu dari! Zayya tace haa ? Yeonsil tace zaifi sauki ka biya jikinka.
NA YEONSIL

STORY CONTINUES BELOW

Kifawa zayya tayi cikin harshen hausa tace na banu na lalace. Bayan an tashi akayi assembly na karshen sati Wanda yayi daidai da karshen wata kuma bisa al’ada duk karshen wata dukan fito bakin makaranta susha iska na minti talatin yayinda za’a tabbatar an kewaye waje da masu tsaro saboda masu guduwa. Yauma dai hakan akayi cikin jindadi su zayya suka fito suna yar hirarsu yeonsil tace la kyautar cupcake ake bayarwa acan naga an taru? Kafin ta sugmfe baki zayya tayi nisa AI suma gudun suka saka domin baza su ki bati ba.
Isarsu keda wuya suka kutsa taro sukaga an lillika fefofi ne rubuce a jiki ba komai bane sai: ZAYYANA MAINASARA KI FITO YANZUNNAN! Yagewa ra fara yi rana fadin wani Dan iskan ne yayi wannan?
A gefenta taji muryasa da bazata manta ba yace manyan Mata yaushe gamo? Kinyi kyau fa. Tsaye yake a jikin gini yayinda ta jingina kafarsa daya ya shafa bakin gashin dake kwace a kansa tare da sake Mata wani munafikin murmushi.
Murmushin yake tayi masa rare da cewa hi wato sannu. Gaba daya yan matan ne suka fara “awwn!” “Kyakkyawa!” “Waiyo dama yace yana sona” da maka mantansu. Abinka da Wanda yayi karatu a turai sankamarta yayi ya daura kafada nan yan Mata suka fashe da ihun hakan yasa hankalin securities yayi kansu Wanda ya bashi daman sata a mota yayinda tabar yar Mata suna zubda yawu aminanta kuwa suna mamaki.
Tafiya suke tana tunanin zuci “wai ina zai kaini ne?” Taji yace what a beautiful (kai yau rana mai kyau ce) ba karamin kyau zaiyi ba idan akaje ofishin yan sanda ko makabarta. Farce ta fara ci cikin abin tausayi kamar marayan bera tace Dan Allah karka kasheni. Yar budurwar dariya yayi yace bazan kasheki ba abinda zakiyi kawai ki bani $10,000 ko kuma mu karasa. Maganar yeonsil ce ta fado Mata, cab wallahi babu yadda za’ayi ta biya da jikinta.
Yadda kasan marayan Dan akuya haka muryatta ya koma tace nifa talaka ce yar makarantar secondary ne ajin manya. Banida kudi. Yace hmm! Da alamu dai nafa bakida hanyar biyan kudin barnar da kikayi ko? Kirjinta ne yace dam amma ta gyada kai murmushi yayi yace ba matsala.
Restaurant ya kaisu tare da ajiye Mata wani paper a gabanta yayinda ya bararraje kamar a parlourn gidansu.
Yace sign it ( saka hannu aciki ). Tace menene wannan din? Yace karanta mana, dala dari ko wace Rana Dan haka zaki gama biya a kwana 100. Kinga 100×100=10,000.
Lekawa tayi taga an rubuta ENSLAVEMENT AGREEMENT wato yarjejeniyar bauta turo baki tayi tace wannan rashin adalci ne fa. Yace rashin adalci? Toh shikenan sai in karbi kudin daga waje mamanki. Ya fadi hakan yana zaro wayarsa tace barshi barshi zan saka hannu.
Ta daura bairo kenan tace kodai kokari kake ka…. sai ta shiga tunanin ya siyar da ita a gidan giya wani kurma ya ceto ta ya aure ta. Saurin girgiza kai tayi tace bakida lafiya yan Mata ko kyau ma bakida shi bari in fada miki. Tace anji dai! Yace ni kiyi sauri yunwa nakeji. Signing tayi ya karba ya ninke ya ajiye kamin yace student ID card dinki kuma sai mun gama yarjejeniyar tukunna zan baki dai lokacin abincin su ya iso dadi ta fara ji cikinta har sauti yake bayarwa sai taga an jerasu baki daya a gaban sa turbune fuska tayi yayinda yaci koma biyu a jere kamin yace banacin abinci da bayi na. Wullo Mata atm yayi yace kije wani shagon kusa ki nemi Dan abin ci da ruwa saura kici dayawa ki gani.
Wani restaurant ta shiga tayi ordern abinci kala kala Wanda yakai mutane Goma suci su koshi.
………..
Washe gari minal ta rubuta Letar daukan hutun kwana 3 wai za’ayi Mata tiyata na appendix. A gaske kuwa so take ta shirya kanta yanda zata iya danne bacin ranta ta huce idan taga yazeed.
Zayya kam titsiyeta yeonsil, halsey da sauran aji sukayi, a ina kika samo hadaddan gayen? Gashi da kudi ga kyau da alama yanada Ilimi cewan halsey. Yeonsil tace kode mafarkin ki ne ya zama gaskiya? Zayya tace to AI shi ba yarima bane da alamu dai kyakkyawa ne kuma yanada kirki.
Ihu yan ajin suka sake kamin ruwan tambayoyi ya fara zuwa kamar haka, tun yaushe kuke tare? A ina kika hadu? Wani makaranta yake zuwa? Inane gidansa? Me da me kukayi?
Murmushi tayi tare da gyara zama tace restaurant ya kaini ya siya min icecream har yace zai zama bawa na, sai mukayi yawo a Lexus dinsa sai yakaini gida ta karashe maganar tana murmushi kamar da gaske. Halsey ne tace kinada message. Karba tayi taga sahir ne.
Bandaki ta shiga tana rufewa gabadaya yan ajin suka lika kunne a kofa. Kiranshi tayi kamar yadda ya umurta yace ba nace kina ganin kirana ki dauka ba? Tace yanzu na fito daga aji. Yace naji maza kizo gidana yanzu tace mene? Yace abinda kikaji. Tace ina da sauran aji daya fa kamin a tashi bai amsata ba yace Gidana yana kallon makarantar ku ta gefen dama. Tace Anya kai musulmi ne kuwa? Kizo yanzu kawai yace kamin ya kashe wayarsa. Tace hello! Hello ! Ihu ta kwalla kamin ta naushi kofar ji kake ruuuu! Gajab gaba dayan su dake bayan kofar suka zube. Tafiyan maza ta fara Su halsey suka biyota sunajin dadi cikin ƙaguwa sukace zayya! Ke zayya wai cewa yayi kije gidansa? Halsey tace lokacin yayi! Riko hannunta sukayi cikin bada karfin guiwa sukace zayya mu zaki iya kinji? Yarfesu tayi tace ka dalla ku matsamin ni bansan me kuke magana akai ba.
Cikin tsohon dakin ajiya ta shiga ta window akwai inda ya fashe dama ta nan take fita kuma akwai tsani (ladder) dan haka ta fice.
KAKA KARA KAKA CABDI HMM DA FATAN DAI KUNA NISHA DAN TUWA ? WANI HANZARI BA GUDU BA ZAN CANJA SUNAN LITTAFIN DAGA KURUCIYAR MINAL ZUWA (WAI KOWANI AURE IRIN NAWA NE?) YAYI KO BAIYI BA ? IDAN KUNADA WANI SUNA A ZUCIYARKU TOH KU SANAR DANI ZANYI FARIN CIKI.
DON’T FORGET TO VOTE, COMMENT, SHARE AND FOLLOW ME miss_untichlobanty LOVE YOU ALL
Miss Untichlobanty 💕RECAP
Cikin tsohon dakin ajiya ta shiga ta window akwai inda ya fashe dama ta nan take fita kuma akwai tsani (ladder) dan haka ta fice.
CONTINUATION
Bayan ya kashe wayarsa ya kalli bakinsa Abdulhameed Wanda bashida buri saide yayi waka yace Abdul huy ya ka tsareni da ido ne? Abdul yace lamarinka sai kai yanzu kuma wata chika ka samu ? Yace shege mutumi na ka sanni dayawa. Wallahi wata yar secondary ce, Abdul yace kai daga samun freedom sai barna ? Kasan dai a turai baka isa ba.
Dariya suka fashe dashi Abdul yace bara inyi gaba ko? Sahir yace yeah zan biyoka nima sannan suka rabu.
Ringing bell din tayi ta security TV dinsa ya fada Mata password din. Tana bude kofar wani gajeran wando ne ya fara Mata sallama. Da ta kalli parlourn ba’a cewa komai gaba daya sai a slow. Ciki ciki tace hello, murmushin mugunta ya Mata yace hi tare da sake Mike kafa akan kujera yace nasan kin fahimci me nakeso kiyi ko? Tunburo fuska tayi kamin yace ni zan fita yanzu idan kin gama kawai kija kofar zai rufu shi da kanshi saura kimin kauyanci tace ance maka mu talakawa ne? Yavmce to ko kawai na Kira iyayenki ne. Jifarshi tayi da jakar makarantar ta tace dallah jeka.
Yana fita ta warware gyalen ta tare da daure sa akai. Aiki take tana wake wakenta tare da rawar hauka Dan ba iyawa tayi ba sanda ta gyara komai tas tayi ciye ciye da barnace barnace har su gym room dinshi ta shiga tayi tabe tabe. Magazines din Abdul ta samu na yan Mata model. Nan ta fara kwaikwayar yadda sukeyi tana murkude murkude ta ture ture. Allah sarki batasan akwai CCTV camera ba.+
…………
Bayan kwana biyu, yazeed ne ya shigo, sai gaisuwa ake wullo masa har ya shige office dinsa Dan tsayawa yayi ganin cewa minal bata fara zuwa aiki ba tun jiya tunda kujeranta babu kowa.
Cikin zafin rai ya zauna a kujeran sa ya Kira Jamal yace ya batun personal assistant Dina ne? Jamal yace bros kayi hakuri mana AI Hutun jinya ta dauka,yazeed yace tun kafin ta fara aiki kuma kuka bata? Toh banason irin haka. Jamal yace baza’a sake ba amma me ke damunka? Ajiyan zuciya ya sauke yace kaide bari. Jamal yace Matsalar safina ce ko? Kawai ka sausage Mata mana tunda kai bazaka kusanceta ba. Yazeed yace AI matsalar daga ita ne tunda ta nuna kanta afili na sanar Mata wannan baya gabana ganin ta damu tun auren mu bai shekara ba nace gaea mu rabu tace Sam dole na zauna da ita. Toh ya kakeson nayi? Hmm ganinan zuwa office dinka ma tattauna.
Bayan kamar minti 10 Jamal da minal suka shigo suka samu yana waya bayan ya gama. Cikin fara’a cikin harshen turanci Jamal yace yallabai,wannan itace ms mainasara,PA dinka.
Murmushin manya yazeed yayi cikin harshen larabci yace naji dadin sake haduwa dake murmushi tayi tace nima haka Jamal ne ya kalleta yace yanaji turanci da kuma hausa so kidinga yi masa magana dawa dannan shi kuma ya amsa yadda yaso.
Yazeed ne cikin harshen turanci yace naji ance an miki tiyatar appendix ko? Murmushi tayi yace shin gefen cikinki na daman ya warke gyada kai tayi tace yayi kyau haka akeson ji amma appendix a gefen dama yake.
Yawun rashin gaskiya ta hadiya,amma ta maske. Yace excuse me ko? Inada appointment yanzu, so sai na ganku a reception din anjima. Yana fita minal ta sauke ajiyan zuciya. Jamal yace ms mainasara kun taba haduwa ne bayan na interview? Tace a ah kawai a elevator ne mukace gaisa. Jamal de bai yadda ba amma ya share. Tace to wai me yasa aka zabe ni? Yace ya zanyi in sani bayan shida kansa ya zabeki.
Kallonta yayi daga sama har kasa yace Partyn yau a haka zakije? Kide tuna yaune. Sannan ya fice tace yan kamfaninnan a rikice suke dazu yace reception yanzu kuma party. Allah kyauta.
Bayan ta koma gida ta bude walk in wardrobe dinta tayi ta dirje ta dauko farin abaya anyi masa kwalliya da golden hakan yasa ta dauki Jaka,takalmi da komai golden.
Zaune take gefen yazeed tunda PA dinshi ce. Yace ms mai nasara akwai wani party da zaki ne bayan wannan ? Tace mene? Oh eh wallahi yau birthday kawata ne. Aranta ko tace ni wai wani iskanci ne yasa bazai wa mutane hausa ba saide turanci da larabci? Tunaninta ne ya datse sanadiyyar maganar sa yace kinyi kyau kuwa a cikin kayan nayi mamaki.
Tace thank you. Yace zai tafi daidai kuwa da mission dinki na yau. Tace mission kuma? Yace emm, kinga wadan can mutane masu farin neck tie. Kallonsu tayi tace wadan can biyun ko? Yace kwarai larabawa ne amma sunajin turanci Dan haka karki nuna kin iya larabci. Abokan gasar mu ne akan hayr deal kuma sultan wato mai hayr (company) yazo wajennan so nake ki jiyo akan meeting dinsu. Tace kana nufin inyi leken asiri zanyi? Ya zanyi ince ban iya larabcin ba? Yace amma AI ranan nan kinyi pretending ko? Tace ranan nan ai….. wata baturiya ce tace yazeed dama kazo? Daf da kunnen minal yazo yace zaki iya kamin ya wuce wajen baturiyar.
Tafiya wajen mazan can ta fara yi amma hankalin ta yana kan yazeed tana gungunin yadda ta sata aiki. Karo taci da wani ta zuba masa juice din dake kofin hannunta balarabe ta gani a gabanta hakan yasa ta fada bashi hakuri ta yaransa sai a lokacin ta lura sune Wanda zatayi aiki a kansu. Tambayarta sukayi da fatan bataji ciwo ba tace ah ah. Wucewa sukayi yayinda ta dauko wayanta ta rambatsawa yazeed Kira. Dauka yayi ba tare da yace Mata komai ba tace na kwafsa? Yace mene ? Tace nayi magana da larabci ya zanyi? Yace ke wannan ta shafa mi dace document din ma idan ta kama. Sanna ta kashe wayarsa tace kan bala’I sannan tayi kwafa.
Wajen larabawan taje suna hira sai dayansu yace ko waye wancan yake magana da jeedmar president? Dayan ne yace AI babu Wanda yasan shine president din anan idan bamu ba. Dadin ta ma mu zamuyi gasa ne da balarabe irin mu ba wani banza Dan Nigeria ba. Dariya tayi tace amma wani hanzari ba gudu ba naji ance janar ya fiku shiga wai gaskiya ne na biyun ne yace inji wa? Ai mun masa wani tarko. Ba farkon ne ya nasa alamun yayi shiru tayi dariya tace karku damu ba aiko ni akayi ba balle ba bada labari na farkon yace kin tabbata? Tace kwarai. Nan suka saki baki suka juye Mata komai ita ko ta shanye tas sannan ta tura masa ta message.
A hanyarsu na dawowa yace ms mai nasara kinyi kokari. Banyi tsammanin zaki iya samo Abu mai muhimmanci irin wannan ba. Tace wannan kuma Cibus dinsu ne. Yace cibus? Me wannan kuma tace kuskuren su ne wannan.
Yace gaskiya ne a kasuwanci faduwar wani ribar wani. Kinada wata baiwa na yaudara da Allah ya baki. Tace mene yace hmm yabo ce daga gareni. Tace waima…..
Wayanta ne yayi ringing ta fara nemansa tana dauka ya datse tace hello? Hello? Yazeed yace saurayinki? Tace babu ruwan ka wannan personal ne.
Kiransa(saurayin ta) tayi amma a kashe sake Kira take a karo na uku. Yazeed yace idan har ya kiraki sai kuma ya kashe, kika kira baya dauka toh akwai abinda yake boyewa.
Tace akan wani hujja kuma kake fadin haka? Yace na fiki sanin namiji idan kuma baki yarda ba ki sake gwadawa. Daidai lokacin motar da aka basu ta tsaya a company din. Cikin turo baki tare da dauke kai tace zaka iya sauka, bama bukatar shawara a wajen Wanda yakeda da tarun yan Mata amma babu soyaiya na gaskiya ko daya.
Sauka sukayi dukansu biyu yana fadin soyaiya ta gaskiya? Shin menene wannan soyaiya da kike batu akai? Purse din dake hannunta ta Dan buga a kirjinsa tana mai fadin tau sannan ta hure kamar da bindiga tayi harbi tace kaji kamar an harbi zuciyar ka da harsashin bindiga kasan wannan yanayin? Yace harsashe ko ? an taba harbina da bindigar gaske.
Jinjina kai tayi tace ba shakka naga alama AI karara. Toh bari kaji soyaiya ta gaskiya wato true love shine zuciyoyin mutum biyu su hade su zam daya, kuyi farin ciki tare ku taimaki juna yayin da aka shiga matsala wani Abu makamancin wannan.
Yace babu wani Abu kamar wannan. Tace akwai! Yace toh yana ina? Kirjinta ta dafa tace nan. Yace okay toh amma ms amina me yasa ko wani lokaci na kallesu babu alamun farin ciki tattare dake? Jumm tayi da fuska ya Mata yar karamar murmushi yace muje muci abinci sai ki wuce. Yake ta masa cikin gatse tace na gode amma saurayi na zaizo zance gashi har isha’i ta kusa, Sannan ta harareshi ta wuce.
Murmushi yayi kawai ya girgiza kai Dan dariya ma ta bashi gida ya koma ayush ta taro shi gaisawa sukayi tace brother ni har yanzu baka fadamin dalilin da yasa baka tafi dani Partyn nan ba, wai ma da wa kaje? Yace da PA na naje. Cikin shagwaba Tace ina kishi fa. Yauwa brother dama cewa nayi mai ze hana zakiyya ta dawo cikin gidannan da zama maimakon dakin baya. Yace wacece zakiyya kuma? Tace kaide da mantuwa kake. Zakiyya yar gidan umma hani mana yace ba matsala Ai sai ta dawo nan. Haka ayush tasa umma hani ta dawo da zakiyya cikin gida duk lokacin smda umma hani ke son tace zakiyya ba yarta bane sai ta kasa. Duk lokacin da zata fadi gaskiya kuwa sa farfadiya ta dauke ta.
Bayan minal ta dawo bata cire kayan jikinta ba tana jiran amude sairayinta amma shiru har bacci ya dauke ta saide taki yarda da cewa shima anarta yaci kamar sauran samarin ta.
Washe gari tana shigowa floor dinsu taci karo dasu yazeed secretary dinshi ne yace ms mina da alamu hiran jiya yayi dadi tunda birthday din saurayin ki ne. Kwal….datseshi tayi ta hanyar cewa rike zancenka, ko ganin fuskarsa banyi ba. Sannan tabi bayan yazeed tana mai murkutsa baki.
DA FATAN DAI YANA MUKU DADI DUKDA CEWA YA KUSA KAREWA?
DON’T FORGET TO VOTE,FOLLOW,SHARE AND COMMENT
ONE LOVE💋💋
Miss Untichlobanty 💕RECAP
Washe gari tana shigowa floor dinsu taci karo dasu yazeed secretary dinshi ne yace ms mina da alamu hiran jiya yayi dadi tunda birthday din saurayin ki ne. Kwal….datseshi tayi ta hanyar cewa rike zancenka, ko ganin fuskarsa banyi ba. Sannan tabi bayan yazeed tana mai murkutsa baki.
CONTINUATION
A gidan mai nasara kuwa maman su ne tare zaune suna hira da bushra take cewa bushra ya kamata kema fa ki fara aikinnan kinga yar uwar ki minal….
Bata karashe ba sanadin bata rai da minal tayi tace ba yar uwata bace.
Maman tace munji kinga dai yanzu a jeedmar take aiki ya kamata kema ki nemi aiki. Zama tayi tace mom jeedmar kikace fa. Tace eh shi mana. Tsaki taja tace dama nasan ba’a sona ya za’ayi a nema Mata aiki anan ni a hanani ? Mama tace kinaji tace uta Zata Nemo aikinta yanzu zakice an nema Mata.
Tace babu yadda za’ayi ta samu aiki saide in jikinta ta bayar. Sahla yar biyun zayya tace AI uwar mu ba irin su oo bane. Cikin mamaki dukansu biyu suka kalleta. Bushra ta Mike zata daketa tana fadin keda ko usili bakuda shi sahla tace kina duka na zan fada ma daddy duk abinda kika ce akan ummi na, wallahi karkiganni shiru shiru banda kyau Dan haka bazan juri zagin uwata ba daganan ta shige daki.
Sallama aunty jalila tayi shameela na biye da ita. Tace yar karamar kanwata lafiya kike haki haka. Mama ne tace ma shameela taje wajen feena a daki zasuyi magana da mamanta. Amma kun Santa da gulma Dan haka labewa tayi.+
Sahla ce ta bude kofa ta hangota Dan haka ta Nemo zare a hankali tasa Mata a jiki. Ihu ta kwalla kowa ya fashe da dariya ashe suna sane da ita.
Aunty jalila tace mummy ga me aikina fa shekarar 5 muna tare sai yau kuka hadu. Sai a lokacin umma ta lura da kyakkyawar matar dake tsaye a baya tana kalle kalle yayinda take zubda kwalla. Mama tace baiwar Allah shigo mana lafiya kike kuka? Zauna anan gefena.
Zama matar tayi suka gaisa umma tace lafiya dai ko? Matar tace kawai gidanku ya tunamin ra rayuwata ne. Nann ta labarta musu rayuwar ta amma ta kasa fadan family name dinta. Yin duniya akayi ta kasa fada ko ymta kwatanta inda za’a samesu. Matar nan ba kowa bace illa MOM mahaifiyar yazeed. Security dinnan ce ta taimaka Mata ta fitar da ita daga gidan mahaukata.5
🌹🍀🌹🍀
Ya Abubakar zaune da matar sa laila da yaransu guda biyu a parlourn su inna sun kawo musu ziyara.
Tunda dama ta rasa kowa nata tun kamin su mance komai yanzu a nasu tunanin ita Marai niyace gaba da baya domin ko sun mance da wani Dan uwanta goje Wanda ya kasance miji ga ayush idan Baku manta ba.
………..
Direct company ya nufa wajen baban sa ya samu minal da yazeed da secretary sunata aiki. Shigowa yayi babu knocking suna hada ido da minal yaji kamar akwai alaka mai karfi a tsanin su. Baisan yadda akayi ya gaishe ta ba.
Yazeed yace kai secretary taba min goshin sa ko bayida lafiya ne? Dariya yayi yace lafiya nake. Secretary tace ms minal wannan shine sahir, future president wato babban Dan yazeed. Murmushi tayi masa tace nayi farin cikin ganinka zama yayi a gefenta yace na fiki farin cikin ganinki. Yazeed yace kai banson shirme tayi kama da sa’ar la ne. Wato dama abinda ake fada min gaskiya ne ? Muje. Sahir yace ina zamu? Yazeed yace gidan ka.
Wani kulululu yaji a cikin sa, take yayi kokarin kawar da maganan amma yazeed yace Sam kallon minal yayi yace muje ko? Sahir kuwa Message ya turawa zayya akan ko bata gama ba tabar gidan,Amma me rana can tana shirme.
A cikin mota sahir ya matso jikin yazeed cikin kunne yace daddy dama PA dinka ce matar ka. Yace me kakeso kace ? banason kwane kwane. Yace dadi na dakai saurin gano ni so nake ka AURETA. Mangare shi kadan yazeed yayi Yace hmm yaro man kaza kaida kakeda mummy safina me zakayi da sabuwar mahaifiya? Kaga dai safina.. hannu sahir ya daga masa yace bana bukatar ji. Dariya yazeed yayi yace wai me yasa bakason safina ne? Duk maganar nan da suke minal bataji.
STORY CONTINUES BELOW

Cikin daga murya kuma hawaye na zuba a idonsa yace saboda bata son mu, ta tsanemu ra wahalar damu…..nan ya fadi duk abinda ke cikinsa rungume sa kawai yazeed yayi. Ashe kangin da yaransa suka shiga kenan ? Toh lallai zaiyi maganin safina. Zaiyi maganin ta ne ta kasa kasa yadda tayi masa zalinci kasa kasa.
Hakan kawai minal taji kamar ta rungumeshi dukda cewa bata San shi ba.
Daidai lokacin suka iso gidan suna bude kofa sukaci karo da zayya tana wakar hauka tana rawa da mop. Yazeed ne ya kalli sahir yace me yarinyar nan take a gidan ka? Yace daddy aiki takemin.
Ita dai minal idan ba kuskure tayi ba toh bayan yarinyar yayi Mata kama Dana yarta zayya.
Murda kunnenshi yazeed yayi yace aikin kaniyar ka? Zukekiyar buduwa ce zata maka aiki? Hmm daidai kenan fadamin address dinta gobe goben nan zamuje gidan su. Yace me kake nufi dad? Yazeed yace auren ta zakayi kuma dole ne ba shawara nake baka ba. Sahir yace zan AURETA da sharadin zaka auri PA dinka. Minal kallon bakada wayo tayi ma sahir shi kuma ya Mata abin tausayi.
Shiru yazeed yayi tunda sun sha wahala a baya ya kamata ya auri wadda suke so wata kila zaiji sauki sauki. Kuma ai ms mina ma ba laifi tana burgesa. Wani lokacin ma dariya take basa.
Yace naji amma naku za’a fara sahir yace ina ? Naku dai ai cikin satinnan nakeso ayi. Minal tace nace na yarda ne? Gefe yazeed ya jata yace nasan kinji abin da yace dazu? Na Dan wani lokaci ne kawai tai maka min zakiyi in koya ma safina hankali zan biyaki.
Hararsa tayi tace banason kudin ka saboda sahir zanyi Dan karamin dariya yayi yace fadi gaskiya dama na Dade da gane kina crushing murmushi kawai tayi ta girgiza kai. Ashe dama mr yazeed yanada kirki? Cabdi za’ayi ruwa da kankara.
Wajen sa suka dawo sukace mun yarda ihun dadi ya sake Wanda yasa zayya juyowa tana fadin waiyo barawo!barawo! Bara…. bata karashe ba sanadin hada ido da tayi da minal. Tace um… ummi? Minal tace zayya?a tare suka tambayi juna me kikeyi anan?
Yazeed da sahir ma suka hada bakin wajen cewa kunsan juna ne? A tare suka sake cewa yata ce da kuma mamata ce.
Yazeed da sahir suka kalli juna kawai sai suka sa dariya. Maganar ido sukayi irin mutumi na a gida daya zamuyi aure fa.
Zayya ne ta kalli yazeed tace uncle? Kallonta yayi na Dan sakanni yace idan ba kuskure nayi ba boss lady ce ko? Tace uncle ashe baka mantani ba? Yace ina fa?
Wannan karan minal da sahir ne sukace kunsan juna ne? Nan zayya ta fada Mata ai shine Wanda ya taimaka musu lokacin nan godiya minal tamai. Haka kawai taji hankalinta ya kwanta da auren shi da zata yi koda zasu rabu batada asara dukda cewa babu rabuwa a lamarin ta ma.
Zayya kuwa tanajin cewa sahir Dan uncle ne ta yarda zata auri sahir ko ba komai zata bawa shameela haushi.
Haka sukaje bayan kwana uku suka nemi aure kuma cikin sa’a aka basu. Feena sai dadi takeji yayinda shameela da bushra kamar zasu fashe.
…….
Suna shigowa yazeed yace kowa da kowa ya taru a parlour akwai babban albishir. Cikin jin dadi kowa yazo umma hani ma haka ta turo zakiyya ta fito da ita Dan yanzu ta daina kokarin fadan gaskiya Dan bazata iya ba.
Maman ayush kamar da gaske tace son ya akayi ne naga kanata jin dadi ? Murmushin sa ne ya fadada haka kawai gaban safina ke lugude.
Ayush tace brother na kagu yi sauri ka fada mana mana yace da farko dai sahir zaiyi aure. Murmushi ne ya fadada a fuskar kowa safina kuwa cikin ranta tace toh sai akayi uwar yaya? A baiyane kuwa yake tayi tace finally Dana ya girma,Ko ba kai bafa. Murmushi yazeed ya Mata aranshi kuwa yace zaki San kin taba ni.
Zakiyya ma dadi takeji cikin ranta harda tsalle amma bazata iyayi a zahiri ba.
Yazeed yace na biyu kuma nima zanyi aure! Tsit parlour yayi ko allura ne ya fadi za’a ji karar ta. Safina tace kan bala’I toh ba a gidannan ba. Na rantse da Allah baka isa kayi aure ba harni za’a wulakanta? Ni safina. Cabdi! Hawaye ne ya zubo a idon zakiyya domin tunawa da yadda tayi wa yazeed lokacin da zai auri minal har yau tana nadama.
Yazeed yace ke a suwa? Mummy da ayush ne sukace fada Mata dai. Mummy tace aure dole bari kiji da na dole ya kara aure. Tafawa ita da ayush sukayi suna nuna kiyaiya karara. Yazeed ko mikewa yayi yana fadin asabar me zuwa daurin auren bayan wata daya za’ayi na sahir lokacin ana hutun makarantar su yarinyar. Kallan safwan yayi yace toh Alhaji saura kai ni da sahir munyi namu.
Sama ya haura sahir yabi bayansa safwan yace kai ku jira ni mana shima ya haura aguje yana tambayar Dan uwan sa sanda suka fara soyaiya bai sani ba.
Safina kuwa wani fadan suka kafa a kasa yayinda umma hani da zakiyya sukejin ransu wasai.
Koda suka shiga daki umma hani tace zakiyya naji dadi sosai da shugaba zai kara aure kefa kinji dadi? Kyafta ido tayi. Umma hani tace nasan kema kinsan gaskiya shiyasa ke daya nake iya tattauna wannan maganar ba tare da wani Abu ya sameni ba shiyasa na nayi nazari sai nake tunanin kodai lamarin nan akwai sihiri? Kyafta ido ta sake yi tace to indai haka ne zan Nemo ma shugaba magani. Shin kema sihiri aka miki ? Zakiyya bata kyafta ido ba tace ba sihiri aka miki ba? Ta kyafta ido tace ikon Allah.
Yau ta kama asabar ranan daurin aure kuma tun daga ranan da su yazeed sukayi tambaya minal bata sake fita aiki ba shirye shirye kawai ake dukda cewa ba wani shagali za’ayi ba.
Sahla ne ta shigo ta zauna a gefen minal da zayya tace ummi wai aure zakiyi ki barni anan ? Minal tace nima banaso in barki amma karki damu zan tambayi miji na idan ya yarda sai kizo mu zauna tare ko? Zayya tace AI ni akafi cuta ranan Monday fa zan koma makaranta.
A bangaren ango kuwa yasha shaddar sa ruwan madara sai kamshi take sha dukda ya haura shekara 40 hakan baisa kyawunsa ya dishe ba idan ma baka lura ba toh zaka dauka har yanzu Dan talatin da wani Abu ne.
Kirari aketa zuba masa yana ta kara kudi kamar bayaso. Yaransa na biye dashi gefensa kuwa Jamal ne sai ma’aikatansa Wanda suke shiri kamar su ya Abubakar. Luku kuwa bai samu zuwa ba saboda shi ke kula da company dinsu dake Cairo dan haka shida matar sa zaliha suna can saide kash gaba daya sun manta da minal. Akan sadaki dubu 100 aka daura auren saide ana gamawa kan yazeed ya Sara salati ya fara yana ganin dishi dishi sannan ya tuna komai da komai kamin ya fadi kasa a sume. Kamin kace tak, Jamal da safwan da sahir da duk wani Wanda aka yi masa tsafin sun zube a kasa hankalin jama’a ya tashi. Nan akayi ciki dasu aka kaisu part din daddy Dan nanne babu mutane.
Mom kuwa kamar yar gida haka ake Mata taci leshinta fess sannan ba’a wani sata aiki sosai. Suna zaune a dakin mama ana hira irin ta manyan Mata mom tace wai ni kam WANENE angon ne naji ana an daura auren Amma banji sunan sa ba. Mama cikin fadada murmushi tace yazeed ABDULMAJEED Umar ne atake mom ta Mike tana fadin shine wallahi shine. Akace shine me? Tace Dana shine Dana. Daidai lokacin bushra ta shigo dakin tana fadin mama ayiwa kawayen wannan yar rainin hankalin magana su fita a daki na. Yau kwanana biyar bana nan daga dawowa za’a bata min rai? Mom tace minal me kikeyi anan? INA YAZEED?
DON’T FORGET TO VOTE,FOLLOW,SHARE AND COMMENT YOUR THOUGHTS
LOVE YOU ALL💋
miss Untichlobanty 💕
20th April, 2020.RECAP
Mom kuwa kamar yar gida haka ake Mata taci leshinta fess sannan ba’a wani sata aiki sosai. Suna zaune a dakin mama ana hira irin ta manyan Mata mom tace wai ni kam WANENE angon ne naji ana an daura auren Amma banji sunan sa ba. Mama cikin fadada murmushi tace yazeed ABDULMAJEED Umar ne atake mom ta Mike tana fadin shine wallahi shine. Akace shine me? Tace Dana shine Dana. Daidai lokacin bushra ta shigo dakin tana fadin mama ayiwa kawayen wannan yar rainin hankalin magana su fita a daki na. Yau kwanana biyar bana nan daga dawowa za’a bata min rai? Mom tace minal me kikeyi anan? INA YAZEED?
CONTINUATION
A saman ido take kallon mom kamin tace dalla dubata, wacece ke kuma da zaki wani kirani da sunan wancan yar rainin hankalin ? Mama ne ta gwabe Mata baki yayinda mom ta fita ta nufi part din da aka ajiye su ko da ta shiga wajen yazeed ta nufa mama na biye da ita. Rungume shi tayi tana kuka tana fadin yaro na ka tashi, mahaifiyar ka ta dawo gare ka. A firgice ya bude idon sa yana fadin minal! Minal ! Mama ne tace a cewa sabir ya Kira minal.
Dakin sabir aka je amma me kwance shima aka samesa shame shame dan haka aka ciccibo sa aka hada dashi. Kururuwar kawayen amarya akaji suka fito a rikice akace faduwa tayi ko? Suka ce taya akayi kuka sani? akace kawai su dauko ta su kawo side din lokacin yazeed ya tashi ya makale mamar sa kam kam babu abinda yake sai kwalla kamar yaro.
Daya bayan daya haka suka dinga tashi saide babu Wanda yace komai. Bayan wani lokaci baki suka watse yayin da kowa ya tashi ya war tsake. family ne zaune baki daya parlourn ya dauki shiru yazeed ya rungume minal kam babu ruwan sa da cewa ana ganin su. Shirun ne ya katse lokacin da zayya da sahla suka fado cikin ankonsu na lace sunsha kyau saide fuskar duk ta baci da hawaye sahla na fadin ummi wai da gaske uncle Dan gayu ne baban mu? Gyada kai minal tayi dadi suka faraji suna tsalle da rawa sai zayya ta tsaya. Sahla tace menene sis? Shagwabe fuska tayi tace kenan sahir yaya na ne babu aure a tsakanin mu? Da sauri ya janyota ta fado jikinsa ya rankwashe ta yace kaji ta a wajen. Ni ba Dan daddy bane amma yayi dauke ni a matsayin Dana tun muna yara, Kinji dadi? Washe baki tayi ta rungumeshi kam kam sahla ne tace sis Allah ya isa na. Kowa ido ya zuba ga mamakin da zayya ta basu ta makale sahir ita kuma wannan tana Allah ya isa? Ko na menene?+
Kafeta da ido sukayi cikin Sosa keya tace bafa komai bane kuke kallo na, idan ba neman magana ta ba shine zata je ta zauna a cinyarsa Dan ni banida saurayi ? Gwaliyo zayya ta Mata yayinda sauran suka rafka Salati cikin annashuwa sukace ikon Allah yaran zamani ba kunya ko kadan. Safwan ne yace nima fa zanyi Allah ya isan nan. Kallon yazeed da sahir yayi yace haba daddy da bros ku duba yanda kuka wani makale a jikin matan ku, kuka barni ni daya bayan kunsan cewa akwai wata zukekiya Baku fada min nima nayi wuf da ita ba? Dariya aka masa.
Alhaji yace yanzu dai ayi mana Karin bayani domin an barmu a duhu. Yazeed ne yayi ajiyan zuciya ya sassauto rokon da yayi ma minal yayi kudubatul Haja sannan ya nuna mom yace ABBA…. wannan da kake gani itace mahaifiyata, minal ya nuna yace wannan kuma matata ce kuma ga yarana na kamar yadda kuka sanar dani. Sahir da safwan kuwa tun kamin wannan Lamari ya faru ba daukesu a matsayin yara na. Sun kasance yaran marigayiya yayar tsohuwar Mata ta zakiyya kuma matar Jamal a yanzu. Ya fadi hakan yana nuna Jamal yace Jamal kuma Dan kanin mahaifiyata ne.
Yace akwai aminiyar minal tare wato zaliha da kuma aboki na lukman suna kasar waje amma na tabbata yanzu haka suma sun tuna komai dukda cewa dama basu mantani ba matata suka manta. Sai kuma akwai Wanda har yanzu yake Kaduna toh shima dai bai mantani ba matata ta ya manta.
Alhaji mansur yace toh naji bayanin ka amma me hadassa wannan mantuwa naku ? Yace wannan ne banida amsa bansa ko akwai Wanda ya sani ba….yauwa sannan a gida akwai mahaifiyar zakiyya da kuma kanwata ayush Wanda na dauka kanwata da mahaifiyata ne. Ture shi minal tayi cikin zafin rai tace ko sunan su ka kara Kira ban yafe maka ba. Shin bakasan cewa wannan tsohuwar kalakin ba mahaifiyar zakiyya bace mahaifiyar ayush ce? Ko baka San cewa ayush ce tasa kuka mantani ba? Ko bakasan cewa ita taso ta haukatar maka da mahaifiya ba har ta kaita gidan mahaukata. Shin baka gane cewa dukiyar la takeso ba? Shin bakasan hassada da San abin zuciya su suka sakata aikata wannan aiki ba? Shin bakasan cewa shedan yana alfahari da
Ita ba? Wannan tsinanniyar ko taro za’ayi shedan bai samu halarta ba idan taje an gama. Lokacin da ta kawo nan kuka take sosai janyota jikinsa yayi yana bata hakuri. Zaburowa tayi ta zauna tace ina zakiyya? Karkace min sun kasheta? Yace tananan saide kuma bata iya yin komai ko kinsan dalilin hakan tace allura suke yi Mata. Jiyoyin kan Jamal sunyi tashi zuwa lokacin idon sa sunyi ja mikewa yayi akayi saurin rikosa yace ku barni ku barni inje in kashe wancan shaidaniyar matar wallahi sai na kasheta tunda ta bakasa min Mata.
STORY CONTINUES BELOW

Yazeed ne ya kwalla masa Mari sai a lokacin ya shiga haiyacin sa yazeed yace kana tunanin ban fika jin haushi ba ? Ka duba yadda aka rabani da matata da yara na. Ka duba yadda aka yi wa mahaifiyata da yadda sukasha wahala muma kayi tsammanin zan barta ta mutu cikin sauki AI Sam Sam sai ta yabawa aya zakinsa tukunna. Sai na gasa Mata aya a tsakiyar ka. Kamin in bata kashi sannan na kasheta murus. Dukda ko ranta yana jikinta amma zata zama bata da maraba da gawa.
Sai a lokacin ya sassauto yace toh menene plan dinka kamin yayi magana wayarsa tayi kara dauka yayi yace ta dayan bangaren ya Abubakar yace inlaw nasan dai kaima ka tuna ko? Yazeed yace eh yanzu haka ma muna tare ya Abubakar yace dukda bansan me ya faru ba banda manta yar uwa na da nayi nasan cewa akwai matsala tunda duk shekarun nan da suka shure ban taba jin zancenta ba na tabbata bakwa tare.
Yazeed yace karka damu zamu zo muyi muku bayani yace AI mun hutar dakai yanzu haka muna airport address kawai zaka bamu. Yazeed yace toh shikenan zan maka text yana sauke wayan tun kamin a tambayeshi waye yace musu ahalin minal ne suka iso. Alhaji mansur ne yace nikam na zama Dan gata Allah ya bani iyali masu yawa sama ta ka.
Dariya akayi mama tace ma sahla taje tace masu aiki su kawo abinci. Tana fita safwan ya gyara zaman hular shi yace ni yanzu ban masan wa zan tambaya ba daddy yazeed ko ABBA mansur. Akace me kakeso ka tambaya. Dan Sosa kai yayi yana murmushi yace wallahi batun yar uwar zayya nan ne sahla idan babu damuwa inaso a dinke mu. Muryar inna suka tsinkayo tana fadin a dinke mu sai kace atampa ? Assalamu alaikum!
Dariya sukayi kamin aka amsa inna ta kama kofa ta tsaya tace kash duk fuskokin ban banesu ba sai na yan kadan ko za’a yi mini Karin bayani? Minal tace inna ta kizo kenan za’a fara.
Waigowa inna tayi tace ja’irar yarinya ji yadda kika zam babbar mace ashe makalewa kikayi ajikin miji shiyasa ban ganki ba. Alhaji mansur ne yace gaskiya yazeed dukda har yanzu ban Sami daman sanin tsohuwar nan ba da alamu za’a dama da ita. Inna ne tayi kicin kicin da ido tace wacece tsohuwa? Nan da kake gani na zam nake zan iya sake aure Goma nan gaba Baba ne yayi gyaran murya yace da fatan kina sane da cewa har yanzu ban mutu ba? Ya Abubakar ne yace inna bude mana hanya mu shiga tunda naga alama bakida niyan shiga balle ki zauna.
Shigowa sukayi minal tana ta washe baki ganin ta kasa hure dadin yasa ta Mike da gudu ta rungume iyayenta da yan uwanta wato ya Abubakar matarsa da kuma deejah kanwarta. Zayya ne tace hehehe ashe abin gado ne sai nayi Abu ace na fiya shirme. Inna tace kaji min yar banza daga gani ba sai an fada ba ke jikata ce saboda babu abinda kika bari na uwarki.
Zayya tace cabdi Allah ya kiyaye ki zama kakata, wani yaro mai kamar shekara bakwai yace dama AI kakar mu ce me za’ayi dake ? Ko ba haka bane daddy? Ya fadi haka yana kallon ya Abubakar.
Introducing kansu sukayi deejah shekara biyar da suka wuce tayi aure amma sai yanzu ciki ya zauna saboda tanada budaddiyar mahaifa. Ya Abubakar kuwa yaran sa biyu aziza sai mukhtar.
Sahla ne tayi sallama ta shigo masu aiki biye da ita dauke da abinci. Ci sukayi suka sha nan inna tace nikam kar kuce min yan biyu minal ta Haifa Dan wannan sahlar da zayya take ko wa kama suke. Zayya tace ba komai na miki uziri kakus tsufa yasa kika manta sunana.
Inna tace dallah yi mana shiru. Wai shin wannan Alhaji a dinke da Wanda Wanda ja’irar nan ke zaune a cinyarsa su waye ? Yazeed ne yace baki gane yan jikokin naki ba ko? Ai sahir da safwan. Inna tace Allah sarki sahiru da safwanu ashe rai kanga rai? Safwan yace zaki fara ko ni tun ina yaro kike damu na da wani safwanu. Safwan akace tace kai karkayi min lala ta mana banfa hakura da tangaran Dina da ka fasa ba.
Yazeed yace ai safwanun naki ma batun auren sa da sahla yake kika shigo, tace Dan banzan nan ne zai auri yarinyar kirki? Ke kuma zayyanatu idan baki sauko ba sai na mangare ki. Sauka tayi daga cinyar sahir tana turo baki sahla tayi Mata gwaliyo. Tace ummi kin ganta ko….
Sallama sukaji kasa kasa bushra ta shigo inna tace a ah me zan gani haka? Ke ya akayi kike kama da yata? Baba ne yace AI kya bari mu amsa sallamar ta shigo ko? Shigowa tayi taje gefen Alhaji tace daddy Dan Allah kayi hakuri ka yafeni ban taba sanin aure na da dadi ba sanda naga anayin na yar uwata minal, Dan allah ku yafeni kuma na yarda ka aura min duk Wanda kaso bani da damuwa.
Yafe Mata kowa yayi daddy yace batun na aura miki Wanda naso bai taso ba ki naimo miji dai amma kafin nan ya kamata nasani SHIN KIN TABA YIN ZINA A YAWACE YAWACEN KI?
DAN! DAN!! DAN!!!
NIDE BABU RUWANA, WAI SHIN WA KUKE GANIN ZAN BAWA BUSHRA NE? WACCE TA FARA CANKA NEXT CHAPTER NATA NE.
SHIN WANI HUKUNCI KUKE GANIN YA DACE AYIWA AZZALUMAN CIKIN LABARIN NAN?
NOTE: INSHA ALLAH ZANYI KOKARI MU GAMA LITTAFINNAN KAMIN RAMADAN DA IZININ ALLAH DAGA NAN SAI IN GANI KO ZAN SAKE RUBUTA WANI LITTAFI.
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU WATO
Miss Untichlobanty 💕
22nd April, 2020.DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.
RECAP
Yafe Mata kowa yayi daddy yace batun na aura miki Wanda naso bai taso ba ki naimo miji dai amma kafin nan ya kamata nasani SHIN KIN TABA YIN ZINA A YAWACE YAWACEN KI?
CONTINUATION
Shiru parlourn ya dauka kowa ya tsime yana jiran Ansar da zata bayar girgiza kai tayi hakan yasa kowa ya saki numfashin da basu San sun rike ba.
Alhaji yace toh masha Allah ai abun yazo da sauki. Mikewa tayi zata tafi inna ta kalli bushra tace uwani baki ga baki bane? gaishesu tayi zata fita sabir yace ABBA inada magana.
Daddy yace toh muna jin ka. Yace dama idan babu matsala ni naji na gani inason in aure ta. Kallonsa kowa yakeyi daddy yace ka tabbata ? Yace eh. Daddy yace toh ke kinji kina sonsa? Tace ABBA indai ya maka nima yamin daddy yace toh kai sai ka turo manya ko? Yace ABBA AI banida su yaya mace kadai gareni. Daddy yace toh fa toh yanzu yaushe kake ganin za’a daura auren? Caraf bushra tayi tace yanzu ma yayi. Salati inna ta rafka tace riko sai jalla jalalu. Toh AI shikenan.+
Atake a wajen aka daura auren akan Rabin albashin sa wato 10K yazeed ne yace ni kuwa kamar na sanka ko? Yace kwarai kun sanni. Ai nine…………
Bayani ya tsara masa yazeed yace Allah sarki Allah ya tsare na gaba ya saka maka. Sabir yace no wonder lokacin da naga yar uwa naji kamar na San ta.
Daddy ne yayi ma mama magana a kunne fuskarta ya Dan canja amma da ta kalli mom sai ta sauke ajiyan zuciya ta gyada kai alamar yarje wa.
Kallon yazeed yati yace Alhaji yazeed idan BAZAKU damu ba naga auren nan gwanin ban sha’awa zan so nima inyi wuf da mahaifiyar ka.
Dariya kowa ya fashe dashi abin kamar a wasa suma a zaman nan aka daure su Alhaji sai washe baki yake yi wai shima a dole ango.
Sahir ne yace toh wai nifa ban gane ba naga sai overtaking akeyi anata aure aure toh kawai ayi namu a huta mana zayya tace kasan dalilin da yasa nake sonka? Girgiza kai tayi tace saboda kanka yana ja sosai. Maketa inna tayi. Akace toh marmarza sahir da safwan ku ciro duk abinda ke aljihun ku ku ajiye. Daga nan aka daura auren daddy yace a Nemo nana da kayai lemo ayi yar karamar shagali.
Inna ke ta kokuwa da cinyar kaza Dan ya Abubakar yace kakus kawai ki hakura da naman nan kin tsufa fa sai kin cire hakori kizo ki hanamu bacci da daddare. Dariya aka yi tace haba mai gida (yaron me sunan baba ne) harda kai ake haduwa aci mini mutunci?
Safwan yace kakus karya kikeso yayi?
Yazeed ne yayi gyaran murya yace inada magana yanzu dai zan bar kowa anan domin banaso ayush tasan cewa mun dawo hankalin mu Dan haka daga ni sai matata sai sahir da safwan da iyalan su ne zamu tafi Jamal kaima zamu tafi tare tunda dama tun da a gidan mu kake amma kar kayi kuskuren nuna kauna ko tausayi ga zakiyya sauran kuma abar mana ni da ita(wato minal).
Sai bayan la’asar sannan suka nufi gida bayan anyi hotuna ran kowa wasai duniya tayi musu dadi.
🌹🍀🌹🍀
Ayush zaune da uwar ta a parlour hankalin su kwance suna kallon film Dan basu da Aiki sai kallon fina finan horror da vampire da BL da GL da sauran su.
Safina ne ta fito taci leshi tana taku jikin nan yana motsawa ta ko ina tace an dai ji kunya. Duk wannan shagali da kuke dazu harda tara kawaye aikin banza ne Dan ko ajikina bari kuji. Kitchen ta shiga ta dauko madara da Kofi.
Sallaman su yazeed yasa hankalin su yayo bakin kofa. Dum dum kirjin su ke bugawa. Cikin tsoro ayush ta hau bari ganin minal biye da yazeed. Mummy ce tayi kokarin cewa son har ka dawo kenan ? Ashe ma tafe kake da amaryar.
STORY CONTINUES BELOW

Murmushi yayi yace mummy ga inlaw dinki. Ayush ya kallah yace sis ya kika ga matar tawa? Cikin yake tace wow gaskiya tana da kyau. Safina kuwa kasa tsayuwa tayi hakan yasa tayi wuf ta koma daki.
Tana rufewa ta sauke ajiyan zuciya tace kan bala’I wannan AI ta kera ni a komai da alamu ma na fita shekaru, ya zama dole na dage idan ba haka ba da matsala.
A waje kuwa ayush ne ta riko hannun minal ta zaunar da ita yayinda take lura sosai da yanayin yazeed amma taga babu sauyi. Sahir ne yace aunty my baki ga amaren mu bane?
Dariya tayi amma da ka ganta kasan a firgice take tace kuma karde auren aka daura yau ? A ah ya naga safwan ma da wata me kama da matarka? Yazeed ne yayi caraf yace AI kinsan dama yar matan tawa zai aura kuma yan biyu ne yaranta sannan itama tanada twin sister(ya fadi hakan ne domin ya kawar musu da shakku tunda yanzu akwai bushra ko suna tunanin minal ne zasu daina)
Mummy tace masha Allah kace kawai ruwan jikoki yan biyu za’a dinga min? Murmushi yayi irin yaji kunyannan.
Ayush tace sis ya sunanki cikin duniyar da kai minal tace nana. Ayush tace masha Allah nana sannunku da zuwa family din mu.
Yazeed yace toh mummy bari mu shiga daga ciki tace toh ba matsala Dan albarka.
Suna wucewa ayush ta rugo da gudu har tana Tuntube ta zauna a gefen mummy tace mummy minal ce fa. Djngure Mata kai tayi tace kiji banziya ba mugu yace daga ta aure shi zai tuna komai ba ? Ke banda shashanci bakiji yan biyu bace ba ma? Kuma yaran nan nata ai sunyi shekara 18 (su zayyan sunada girman jiki hakan ne ya cika musu ido)
Ke kinsan tabar gazar da mukayi musu bazasu yi mana da sauki ba da sun tuna ayush tace wannan gaskiya ne. Amma dai zan sa musu ido sosai.
Umma hani ce ta fito tana fadin naji hayaniya karde har sun iso ina bayi? Ayush tace toh sannu munafuka sun iso sai akayi yaya? Umma hani tace Allah huci zuciyar ki shugaba ta tambaya kawai nakeyi.
Mummy tace dallah ki koma daki ganin ki kadai yana sa ni inji kamar zanyi amai.
Simul sumul ta koma tana shiga tace ma zakiyya sun iso fa kuma ina ji a jikina wahalar mu ya kare.
A dakin su yazeed kuwa suna rufe kofa ya kara rungume ta. Kawai sai ya sake Mata kuka cikin mamaki tace haba kai kuwa da girmanka? Yace kewarki nayi sosai.
Murmushi tayi tace in fada maka wani Abu kallon ta yayi yace me ? Jan hannunshi tayi ta zaunar dashi a bakin gado ta kwantar da kanta kirjin sa tace “YAZZY BABY” wannan karan ita ta fara hawaye shi kuwa cewa yake sake fada inji tace yazzy baby yace banji ba Dan Allah maimai ta. Tace yazzy baby Kankameta yayi yace Allah ya isar mini da aka rabamu.
Kuka take masa harda majina yace toh sarkin shagwaba kin girman ma baki canja ba ko? Ni dagani in cire babbar rigan nan. Tace indai ins tare da kai toh bazan taba girma ba kuma har mu mutu kai yazzy baby na ne. Sumbatar goshinta yayi yace me ya samu zakiyya? Hawayen fuskar ta goge kamin ta zayyano masa abinda ya samu zakiyya take ya Kira mashkur ya fada masa shi kuwa yace AI wannan me sauki kaza zaku siya ku canja Wanda akeyi Mata dashi shikenan zata warke yazeed yace toh mun gode sosai yaushe zaka zo? Yace gaskiya ba rana saide ku ganni kawai.
……..
A dakin su sahir kuwa suna shiga ko ina kayan sa ne da ya watsar yau da safe fara tattare dakin zayya tayi tana babatu tace kaide wallahi anyi kazami, la duba dakinka kamar bola sai an…….
Finciko ta yayi ta fado jikinsa yana kallon bakin ta yace waye kazamin? Turo baki tayi tace toh ba kai bane kake….. kasa karashe tayi sanadiyyar peck da ya Mata a lebe. Zaro ido tayi tace dama halsey ta fada min ashe gaskiya ne ? Cikin rudewa yace me? Tace wallahi shocking naji. Tsaki yaja ya raba jikinsa da nata sannan ya fada ban daki tace kai ka jiyo bani yadda muyi Abunnan har sai nayi shekara 18. Batasan ya jita ba Dan haka yace mu zuba mu gani.
……….
A dakin su sahla kuwa ashe kunya kunya nan a fili ne amma tafi zayya sanin me takeyi dukda ko itace usaina. Safwan kawai daga Dan tabata kadan ganin yarinya ne yanaso ya daga Mata kafa kawai ta kama masa wasu irin salo da badan ya dage ya kwaci kansa ba da ya rasa sallah magrib.
Bayan Isha’I kowa da kowa zaune a dining room, mummy ta kwala ma umma gani Kira fitowa tayi da sauri minal ta kafe da ido tana mamaki ko itace ko ba ita bace. Murmushi ta Mata wanda ya tabbatar Mata da itace.
Minal tace sannu baba umma hani tace yauwa sannu sunana umma hani. Murmushi minal ta sake yi mata. Mummy tace kicewa masu aikinnan su kawo mana abincin….
Juyawa tayi tana tafiya tana waige hakan yasa minal ta kashe Mata ido alamun ita ne bayan ta isar da sakon hajiya wajen zakiyya taje ta fada Mata. Hawayen jin dadi zakiyya ta fara dukda basu tabbatar da cewa minal bace Dan da ita ne da tabbas za’ayi tashin hankali.
Wajajen karfe Goma yazeed yace ma minal uwar yanzu ayush ke fitowa shan shayin dare daga nan sai tayi kallo Dan haka kiyi naki bangaren plan din. Sannan part dinnan da mutum ya doso shi ake alerting Dina….. haka ya faf fada Mata sabon tsare tsaren gidan sannan ta fita ta zuba mai a kofan side din zakiyya da mummy domin ko wani side part biyu ne dashi.
Wato side daya asali na mom da late ABDULMAJEED ne kuma shine mummy da ayush ke ciki. Sai na sahir da safwan sai kuma na minal da yazeed sai na guest har guda biyu.
Komawa tayi daki suka kunna CCTV footage din suna kallah.
Ayush kuwa fito wa tayi da niyar tasha shayi tayi leken asiri sannan tayi yanda zatayi ta hanasu yin wani Abu. Saide me ji tayi wani Abu ya kwashe ta sannan ya adana da kasa.
A daki kuwa gani sukayi ayush ta fito cikin satin rigar bacci tana latsa waya. Suu mai ya kwasheta ya direta a gefe ihu ta fara waiyo kwankwaso na brother! mummy! Ku taimakeni haihuwa tazo min babu ciki.
Dariya su minal suka fara minal tace gaskiya mu fita Dan inga plan b ido da ido camera dinnan ba dadi. Yace duk abinda kikeso shine burina masoyiya ta.
Fitowa sukayi kowa da kowa ana fadin lafiya ? Itako sai fadi take ku tayani gani kwankwaso na yananan? Kokarin dagata mummy da minal sukayi amma ta like da floor. Yin duniya akayi a dagata Abu yace Sam mummy tace saide mu Nemo wuka sai a yaga pant dinki sai ki tashi shikenan.
Kuka ta fara wiwi tana fadin waiyo Allah na mummy na shigesu! Mummy tace menene? Tace bazaki gane ba mummy! Tace toh menene? Tace shikenan tawa ta kare waiyo!waiyo!waiyo Allah na yasin banida Dan kamfai (pant)mummy tace na shiga uku ni salamatu yau za’ayi tonon salala.
Yazeed yace ma su sabir su koma daki zayya da sahla kuma su tsaya. Bayan sun shiga dakin yazeed yace sis kajama kawai za’ayi miki a cireki idan ba haka ba kuma toh saide ki kwana anan gobe likitoci suzo da karafuna a banbareki. (Yace karafuna ne Dan ya bata tsoro)
Tace wa ? ni shegiya inji Dan daudu kawai ku cireni. Zayya da sahla ne auka rike hannu yayinda mummy da minal suka rike kafa akayi sama da ita a lokaci daya.
Tace la ha’ila ha illallahu shikenan! Kun kun kasheni. Waiyo Allah sun kwaye min mazaunai.
Umma na sun kwaile min mazaunai naaaaa😭😭😭
OKAY BARI NA DAN DARA KADAN NE😁😁🤣🤣 DA FATAN KUN MURMUSA KUMA KUNYI DARIYA A WANNAN CHAPTER?2
INA FATAN DUK SANDA KUKA TUNA KUYI MURMUSHI HAR BAYAN RAMADAN INDA ZAMU CIGABA DA GASAWA AYUSH GYADAA A TSAKIYAR KA YAYINDA MU KUMA ZAMU DARA DOMIN MU KARE LITTAFIN MUNA MASU ANNASHUWA DA FARIN CIKI.
INNA TANA MIKO MUKU GAISUWA TA MUSSAMAN TARE DA WASHE BAKINTA DA HAKWARA SUKA SOMA ZUBEWA😁😁
KUYI VOTING DA COMMENTING SANNAN KUYI SHARING DOMIN WASU MA SU DARA.
KAUNATA GAREKU BUHU BUHU❤❤
Miss Untichlobanty 💕
DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA YARINYAR CE TAYI MIN FYADE
WANNAN GAJERAN LABARI NE DAYA FARU A GASKE. BAN CANJA SHEKARUN YARINYAR BA KO ALAKA BA,AMMA NA CANJA SUNA, GARI DA KUMA ANGUWA.
LUBABATU YARINYACE YAR SHEKARU 5 KACAL WADDA TA FARA DA TABA MA BABBAN SAURAYI DAN SHEKARU 27 JIKI KAMAR DA WASA ABU YA GIRMAMA. SHIN WAI ME ZAI FARU NE? KO ALJANU NE DA YARINYAR? BUKATAR DA NAMIJI A SHEKARU BIYAR BA ABINDA MUKA SABA JI BANE. SAIDE AYI AIKIN KARFA KARFA TOH FA ANAN ITACE TAYI.RECAP
Tace wa ? ni shegiya inji Dan daudu kawai ku cireni. Zayya da sahla ne suka rike hannu yayinda mummy da minal suka rike kafa akayi sama da ita a lokaci daya.
Tace la ha’ila ha illallahu shikenan! Kun kun kasheni. Waiyo Allah sun kwaye min mazaunai.
CONTINUATION
Mummy ne ta fado dakin su umma hani duk a rikice tana fadin umma hani zo ki taimaka kar yata ta tagaiyara,umma hani tace ni kuma ranki shi Dade? nida bani da kwakwalwa bansan me nake ba ta ina zan temaka wa wayaiyu yan boko abin tausayi mummy tayi tace haba ke kuwa AI an zama daya ko ba haka ba? Ki mance da baya ai duk rashin sani ne kinsan ance yafi dare duhu. Zo muje kinji.
Haka aka dauki ayush aka kaita daki aka kwantar da ita ruf da ciki. Mummy ta nemi ointment (man da za’a shafa ma ciwon) ta rasa shi sama ko kasa batasan su yazeed bane suka boye.+
Umma hani dukda batasan nake wakana ba tasan aikin su yazeed ne tace bari na hado wani abin na gargajiya a shafa Mata kamin gobe a siyo na malam bature. Ayush cikin kuka tace yi sauri Dan Allah kamin ta share majina.
Minal ne tace bara inje in taimaka Mata, mummy tace toh yi maza yar albarka. Umma hani tana shiga kitchen ta hau dariya tace kai wannan Anya kuwa ba hadashi akayi ba ? Dan baiyi kama da tsautsayi ba. A bayan ta taji minal tace aikin mu ne. Juyowa tayi adan tsorace tace hajiya barka dai minal kam zuwa tayi ta rungume ta tace umma hani nice fa me zaki wani ce mini hajiya. Gaggaisawa sukayi sama sama umma hani har da kwallar ta. Minal tace idan kin hada maganin ki saka wannan a ciki. Umma hani tace menene shi? Minal tace kallesu da kyau mana barkwano ne da gishiri sai kuma aboniki. Wannan kuma kiyi a hankali dashi domin karara ne wato garin a Sosa. Kawai kwabasu zakiyi da manja
Toshe baki umma hani tayi Dan kar tayi dariya tace Allah ya biyaku. Wannan aiki naku yayi daidai idan kuma numan taimako ko na menene indai zan iya zan muku. Minal tace mun gode! Umma hani tace yi wa kai ne.
Kawowa sukayi suka bawa mummy umma hani tace idan ya fara zafi kadan yana aiki kenan sannan yakan yi ma wasu kaikayi toh kar ki sake ki Sosa. sannan kowa ya fice kafa kunne sukayi a bakin kofa.
Ayush ta Dan hakura ta dena kuka har bacci ya fara daukarta taji an saka Mata wani Abu kamar acid babu shiri ta Mike tsaye kewaye dakin ta fara a haukace ta ma kasa komai saboda azaba. Sanda tayi kusan minti biyu sannan ta daka tsalle ta saki ihu. Kaikayi take Mata ba halin Sosa wa. Kai ganin abin ba sha yasa ta fara sosawa sai jini. Mummy tana karki Sosa aiki yake itako fadi take bazaki gane bane. Ya ge rigarta tayi ta shiga toilet kamar mahaukaciya tana Sose sose ta shiga ban daki. Kunna ruwa tayi taji ba sauki lamarin gaba yake kawai ta fito zata fice tsirara mummy ta rikota ta saka Mata hijabi.
Da gudu su yazeed suka buya itako ta Fito sai kitchen ta dauko cokali tana sosawa yana jini umma hani tace kai har ta ban tausayi wallahi. Minal ne tace baki San me tayi ba shiyasa kike fadin ta baki tausayi.
Daki suka tafi sukayi kwanciyar su sunajin daidai a ransu. Ayush ko yanda taga Rana haka taga dare. Gashi bazai yuwu ta zauna ba in ta kwanta kuma azaba. Gaba daya ta koma mahaukaciya a kasa da awa 24.
Washe gari ambulance yazo ya dauke ta yayi asibiti da ita anan su yazeed suka sami damage kwashe allauran da take ma zakiyya sannan suka canja da na magani.
Zayya da sahir ne suka fita shopping tunda gobe zata koma makaranta dama auren minal tazo da weekend kuma sai itama aka daure ta.
Yawanci kayan sawa ne suka sissiyo nata da nasu halsey. Chanji aka basu amma babu naira 50 sahir yace a barsa sai cashier tace ba matsala tunda tafe yake da kanwarsa kuma ansan Mata da cin chewing gum su dauki daya. Zayya ne ta harari matar tace nayi kama da kanwar sa? Sahir ya janyota tare da yiwa matar yake yace matata ce sannan ya janyota suka wuce. Daukan strawberry flavor sukayi sannan suka tafi gida.
Direct dakin sahla ta shiga babu ko kwankwasawa ta samu safwan yananan gashi yanayin su da matsala hakan yasa ta fice da sauri kamar wata shashasha tana basu hakuri. Sosa kai take Dan kanta ya daure har ta shiga part din ta. Ganin idan taci gaba da tunani wahalar banza zata sha yasa ta fada kan gadonta tana mai sauke ajiyan zuciya bayan ta ajiye ledojin a kasa.
Yazeed ne ya tare sahir kamin ya haura sama yace sahir zo zauna mana. Zama yayi yace daddy ina wuni? Yace lafiya ya kuka kwana jiya? Yace lafiya Alhmdllh yazeed yace toh yayi kyau daga ina kuke ne? Yace wallahi mun Dan je siyo abubuwa ne gobe zata koma makaranta. Yazeed yace yayi kyau da fatan ka shirya ma next plan ? Sahir yace na shirya yazeed yace naga kana kallon sama bi matar ka bazan rike ka ba dariya yake ya tashi ya haura.
A daki ya sameta kwance akan gado yace wifey ya naga kinyi jungum jungum? Juyawa tayi tace karma kayi tunanin ni zan yarda. Yace me fa? Tace barshi kawai a wuce page din.
Yace oya dauko mana kayan muyi arranging a akwatin ki.
Dauko wa sukayi suna jerawa ta dauko chewing gum din boyewa tayi a bayan ta ta masa gwaliyo tace bazan baka ba.
Yace yarinya kinyi kadan kokarin kamawa yayi ta kautar cuku cuku suka fara yi kamar wasa Abu ya koma dambe sai dariya take. Gudu suka fara yi a tsakiyar dakin wayarta yayi ringing tace ka tsaya a inda kake idan ka matso ka kwace kayi cuce kuma ka zama ragon namiji.
Tsayawa yayi ta dauki wayar sahla ce ke kira tana dauka, ihu ya daki kunnenta. Cikin masifa amma a wasa sahla tace sis kede anyi yar wulakanci shine kika fado min daki babu sallama babu knocking ko? Yanzu gashi kinsa ya fita ma. Zayya tace iye sannu Sara me farar takashi gashi blue gashi jaja jaja.
Wai ke me miji dadin abun nima inada shi dallah in bakida Abin fada zan kashe waya ta. Sahla tace AI ko baki fada ba ansan kinada miji ji yadda kikewa mutane haki aci dadi lafiya. Zayya tace ba haka bane ba fa kawai….. sahla tana dariya ta datseta ta hanyar cewa kawai me? Sis babu boye boye sai anjima.
Zayya tace kash anyi banziya wallahi. Sahir ne yace gwamma kin shanyani anan fa. Kamin ta ankare caraf ya kwace yana shirin budewa idonsa ya fada kan wani rubutu….
Mika Mata yayi yace kinsan ni mijin kirki ne gashi na baki amma kar kici sai tare da kawayenki gobe. Tace me yasa yace saboda ki zama kawar kirki. Karba tayi ta sumbaci kumatunsa tare da shafa kansa tace good boy sanda bata ma lura da tayi hakan ba taci gaba da jera kayan ta.
Yana fita yayi dariya yace yan Matana aci chewing gum lafiya yana Mata dariyar mugunta. Itama a bangaren ta yana ficewa tace sai kace ban sanka ba kawai zan yarda cewa ka hakura. Hmm nasan so kake kabi dare ka cinye dan haka gadi zanyi sannan tayi ma kofar gwaliyo.
A asibiti kuwa……..
Shin ok me yasa sahir ya fasa cin cingam din?
ANAN ZAMU DASA AYA FAH. A BAYA NACE ZAMU TSAYA DA UPDATE HAR SAI BAYAN RAMADAN AMMA SAI WASU SUKA NUNA CEWA PAGE DAYA BAZAI HANASU IBADA BA KUMA SUN KASANCE SUNFI YAWA FIYE DA WANDA SUKE GANIN YA DACE A TSAYA HAKAN YASA NACI GABA AMMA UPDATE SAI BAYAN KWANA UKU UKU.
DON’T FORGET TO VOTE, SHARE, COMMENT AND FOLLOW ME.
miss untichlobanty 💕
26th April, 2020.RECAP
Yana fita yayi dariya yace yan Matana aci chewing gum lafiya yana Mata dariyar mugunta. Itama a bangaren ta yana ficewa tace sai kace ban sanka ba kawai zan yarda cewa ka hakura. Hmm nasan so kake kabi dare ka cinye dan haka gadi zanyi sannan tayi ma kofar gwaliyo.
CONTINUATION
A asibiti kuwa ayush tasha plasta a mazaunai sannan kar ta dinga zama saide kwanciya ko tsayuwa. Tafiyar ma gwale gwale takeyi Kamar yar kaciya. Wayarta ta dauko taga missed call aciki harda na Dan iskan mijinta wai ya dawo daga Mali. Tun shekaru biyar da suka wuce ya tattari tarukucensa ya tafi neman Mata ta da harkar gabansa da sunan kasuwan ci saida ya kwaso kanjamau tukunna ya lallabo ya dawo.
Bayan sun kammala wayar ne taga cewa wata number ta Mata missed call Kira tayi bugu biyu aka dauka tare da fadin barka da war haka hajiya ayush ashe de baki canja lamba ba.
Ayush ne tace wai wa ke magana? Dariya akayi ta dayan bangaren tace hehehe su ayush manya shekaru nawa ne har kin manta da SUMAYYA? Ayush tace wace sumaiya kuma? Tace summy de guda da kika sani yar lesbian yanzu kuwa magajiya ce.+
Dafe goshi ayush tayi a ranta tace mutum na fama da wata matsalar sai wata ta kunno kai. Daidai lokacin mamata ta turo kofa ta shigo dakin da take hakan yasa ta dawo daga tunanin da ta shiga tace toh summy kike ko wa ya akayi? Summy tace ya akayi? Lokacin da na yi miki aiki ba cewa kikayi idan kin samu dani za’a raba ba? Jini shiru yasa na share na bar kasona tare da ke a matsayin ajiya yanzu ko fatara nake babu kasuwa sosai Dan haka so Nike ki bani. Ayush tace turo account number ki. Summy tace ance miki cikin sauki zan karba na wuce AI wallahi gidan da kike nan zan zauna kima San yadda zakiyi ki shigar dani ayush ta kunduma ashar tace bara in kashe wayar muga tsiya. Summy tace wallahi ko bakar magana kika kara yi min wallahi sai na zo na miki tone tone.
Iska ayush ta fesar tace naji zanga yadda zanyi sannan ta kashe wayar baki daya.
Mummy tace waye ne? Ayush tace waye kuwa banda wancan yar iskar wai ita summy. Mummy tace wacece kuma summy? Tace wannan yar iskar de wacce tayi min aiki akan zakiyya tayi kokarin kwanciya da ita. Tattaunawa sula ci gaba da yi na yadda zasu tsere daga tarkon summy.
Da daddare zayya tana kwance ta rufe Rabin jikinta da bargo taji sahir ya shigo, likimo tayi tana kallonsa yaje wajen Jakarta kamin ya dawo ya kwanta. Bayan minti biyar ta tashi da sauri ta duba chewing gum dinta yananan wani paper ta gani Wanda batasan dashi ba ta dauka. Muryarsa ta jiyo yace finally zan rabu da alakakai dama Dan daddy yayi aure na aureki badan raina yaso ba. Gabanta ne ya fadi hannu na ruwa idonta ya ciko da kwalla tace sakina kayi? Yace duba ki gani ko guda nawa ne sannan yayi kwanciyarsa ko a jikinsa.
Kafarta na rawa ta dosana mazaunanta akan gado ta bude paper ido shame Shame da hawaye ta karanta kamar haka.
“Zayya manyan Mata gara ma ki tashi Dan nasan ba bacci kikeyi ba fadin cingam kikeyi. Karki dauka Dan na aureki contract din mu ya kare dole ki karashe. Dan haka so nake yanzu ki hadomin shayi.”
Tana gama karantawa tayi kicin kicin da ido duka ta kawo masa ya kauce yana dariya ta ƙwale hannunta. Kafa tasa ta turesa daga kan gadon ya fadi fatt a kasa tace idan na ganja a gadon nan sai na cire ma idanu kuma bazan hado shayin ba. Kwanciya tayi a tsakiyar gadon ta juya masa baya. Murmushi me sauti yayi yace idan nan da minti biyar ya cika banga shayi na ba kinsan student ID card dinki yana gurina? Kaiwa zanyi lost and found na makarantar ku ince a club din hotel na samu kamin ya karashe maganar har ta isa bakin kofa. Yatsar tsakiyar hannu ta nuna masa wato alamar f*ck you sannan ta fita tana shiga kicin ta samu sahla da safwan a bakin fridge suna lobewa tsaki taja tace dalla malamai ku tafi dakinku. Saa ne tace sis Allah ya isa kin kalle min kirji zayya tace dadin abun shekara daya da ya wuce ma tare muke wanka dukda an hanamu sannan taci gaba da harkar gabanta.
Washe gari Monday wato litinin aka sallamo ayush. Koda ta dawo su zayya sun tafi makaranta. Direct dakinta ta wuce amma me tana shiga ta fara jin kukan jarirai hakan yasa babu shiri kafa a faffale kamar baba ari Dan wasan hausa ta fito da gudu ta koma mota tace summy tuka muje wajen mugu, maza kaini wajen boka mugu Dan wallahi akwai matsala ya taimaka min dama na Dade banji daga gareshi ba.
Bayan tafiyar awa biyu suka iso lokacin ayush tayi lubus Dan ba zama sai kwanciya a karkace shima. Taimaka Mata summy tayi suka shiga ta baya baya suna gafaran ku dai subhanallah sukaji ana fadi ayush toh kuji wata sabuwa ko batan kai mukayi bokan yana ganinta ya ganeta yace aishatu dakata daganan idan har kinsan da mummunar Niya kikazo Dan ni Allah ya shirye ni. Ayush tace taimaka boka taimaka…… datseta yayi yace ke ni ba boka bane ni yanzu gardi ne na makarantar allo….
Datseshi tayi ta hanyar cewa ni mugu duk wannan zance da kake yaushe ma nakeda imani balle na kama sunnar na bar bidi’a? Yace ke ba sunana mugu ba Salmanu nake atakaice ni me sunan salmanul farisiy ne. Tace toh koma wa kake ba salmanu ba nide taimaka wallahi kukan jarirai nakeji a daki na yace AI saima kin fara ganinsu AI duk Wanda muka yanka ne nima nan da kike ganina ina fara jin su na tuba Dan na gano an Sami matsala kiyi gaggawar tuba wata kila Allah yasa kiji kamshin rahama koda baki ganta ba. Kuka ta fara tace kash ba wani taimakawa da kake sai rura wutar ke sumaiya muje. Mikewa sukayi suka fita tana nazarin inda zata Sami sabon boka.
Koda suka dawo sumaiya tace toh ko wani aiki nayi miki za’a kara da kudin sa fa ayush tace ba matsala. Tana shiga ya leka dakin amma har yanzu kukan jarirai take ji haka ta kankame hannun summy har tayi bacci. Summy ne ta Sami mummy ta fada Mata abin da ya faru.
Cikin mamaki mummy taje dakin tana kalle kalle amma bataji komai ba tace ka bibiya kalle kallen film ya janyo Dan gobe sai tace taga kurwa.
Yazeed kam cewa yayi bazashi aiki ba yana makale a gurin minal yayi ma Jamal waya cewa a nemi gurbi a bawa sabir me gadi aiki sannan ya kashe wayarsa cikin hakane sukaji hayaniya ta bayan Window dinsu ta kasa lekawa sukayi suka ga ayush ne da wata amma da alamu ayush a firgice take. Minal har tana Tuntube ta kunna CCTV footage din suka kalli komai.
Minal tace na Sami idea! Yazeed yace na me fa? Tace tunda dai bisa alamu aljanune suke bibiyarta dole zasu hanata bacci da daddare da rana kuma sai mudinga yi Mata kurwa tunda kaji dai abinda mahaifiyar ta tace kaga sun yarda akwai kurwa kenan. Kaga kawai kowa kallon tabbabiya zai dinga Mata daga nan zamu San abinyi.
DON’T FORGET TO VOTE,COMMENT AND SHARE.
LOVE YOU ALL!
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
Miss untichlobanty 💕
1st MAY, 2020RECAP
Minal tace na Sami idea! Yazeed yace na me fa? Tace tunda dai bisa alamu aljanune suke bibiyarta dole zasu hanata bacci da daddare da rana kuma sai mudinga yi Mata kurwa tunda kaji dai abinda mahaifiyar ta tace kaga sun yarda akwai kurwa kenan. Kaga kawai kowa kallon tabbabiya zai dinga Mata daga nan zamu San abinyi.
CONTINUATION
A makaranta kuwa zayya suna shigowa aka fara kallon sabon motan Dan ba’a sanshi ba saboda ba da wannan motan yazo ba a karan shi na farko. Ansiya musu sabin mota saboda sunyi aure. Kan kace me labari ya karade ai an kawo sabuwar daliba. Motan na tsayawa kowa yayi kur da ido amma me ? Zayya ce da sahir suka fito hannu sakale da na juna dukda ko mintsininta yakeyi.
Ta aika masa harara alamun zata Rama har hostel ya rakata sukayi sallama ashe yeonsil da halsey suna hangosu ta window Dan a second floor suke tana shigowa sanda gabanta ya fadi ganin mutane biyu sun kafeta da ido da sauri suka zauna da ita a bakin gado sukace dama a wajen mr handsome kikayi spending weekend dinki bayan kin sanr da mu cewa auren mamanki zakije? Tace da farko dai addinin mu ya hanamu kwana a gidan saurayi na biyu kuma labarin dogone zama suka gyara sukace mun shirya ko zai kaimu Isha’I. Dungure kansu tayi tace ajin fa sukace ki mana alkwari zaku bamu tace an gama sannan suka shirya suka wuce.
Bayan sun dawo daga aji ta labarta musu yadda akayi tass har inda aka daura auren shewa sukayi sukace mude ki bamu tsarabar my dauko ma kowa nata tayi daidai lokacin cingam ya fado yeonsil ta dauka dama ita uwar bari ce babu ruwanta ko me yazo fada kawai take tace la me nake gani anan ? Zayya tayi saurin warcewa tare da cewa bani chewing gum Dina.+
Tafawa sukayi halsey tace kai amma kin Rena mana AI baki cika alkwari ba tunda baki bamu labarin bangaren nan ba. Shine dan renin hankali muna gani condom baro baro kice mana cingam? Dan yamutsa fuska tayi tace con..dom? Halsey tace kwarai. Zaunarta sukayi tare da bata bayani filla filla. Kamar zakanya haka ta Mike ta danna masa Kira ringing 2 ya dauka cikin tsokana yace wifey kinyi missing Dina ne naga… kamin ya karasa tace idan na kara jin kalma daya daga gareka lahira zatayi bako. Wato da gangan kace na taho da wannan abar makaranta ko? Yanzu idan da principal ta gani me zance? Bari ma ka gani yanzu zanzo in sameka saina…..
Yeonsil ne tayi saurin karban wayan ta kashe suka sata a tsakiya. Dungure kanta yeonsil tayi tace kinada hankali kuwa ? Halsey ma ta dungure ta tace mijinki kike ma ihu? Yeonsil ta dungurota tace kuma Dan iskanci harda cewa zaki kasheshi? A tare suka dungure keyarta sukace daga yau abinda mukace kiyi shi zakiyi.
A gida kuwa ayush ta samu ta fito harda kunna kallo amma me abinda ya fara baiyana shine horror movie. Cikin tashin hankali ta saki remote tare da kashe socket din. Ta koma daki da gudu bata fito ba sai bayan magariba da yunwa ya sakota a gaba. Da sanda take takawa babu kowa a parlourn kuma akwai duhu a hankali ta kunna wuta.
Wani Abu taga ya gifta acikin kitchen din gabanta na dukan tara tara sansada ta shiga amma bataga kowa ba. Shayi ta fara hadawa kawai wuta yadauke kofar kitchen din ya rufu da karfi ihu ta tsala ta taho da sauri taja kofar amma a rufe kuka ta farayi sai taji ana dariyar mugunta a bayanta juyawa tayi kafarta na karkarwa batasan tana fitari ba cikin bari tace waye?
Muryarce tace Mata gani nan a sama tana kalla kuwa ta zube kasa sumammiya. Abinda bata sani ba kuwa shine basirar sahla ce tayi aiki domin ta iya Zane hakan yasa tayi zanen kurwa ta abinda ake cewa 3D.

Koda ta bude idonta a daki ta sameta babu kowa saide ba’a canja Mata kayan jikinta ba har ta fara zarni. Mikewa tayi jiri na Dan dibarta taji ance sannu a kujerar dake dakinta. Tana juyowa sanda kirjinta ya buga wata ce zaune da farin kaya irin na nurse a jikinta kwayan idonta kore manya manya da gani kasan da matsala murmushi ta sakewa ayush tace sannu da tashi madam nice me kula dake har zuwa lokacin da zaki warke. Yake ayush tayi matar tace kina bukatar wani Abu ne ayush tace eh fitsari zanyi. Kamata tayi ta taimaka Mata itadai ganin ikon Allah take domin bata taba ganin me irin halittar ba. Gabanta na faduwa ta shiga bandakin ta fara tsulawa kawai taga wuta ya mutu zabura tayi ta Mike tace nurse ke kika kashe wutan ne? Shiru sake magana tayi amma ba’a amsa ba hakan yasa da gudu ta fito ba tare da ta mayar da suturar ta ba tana haki tace mummy! Mummy!
A birkice mummy ta shigo tana fadin lafiya? Cikin tsinkewan numfashi tace ina…. ina take ? Mummy tace wa? Ayush tace nurse din. Mummy tace nurse kuma? AI babu wata nurse a gidannan. Cikin Dibir bir cewa tace mummy kice Allah. Tace zan miki karya ne aishatu? Tace mummy na banu wallahi aljanu da kurwa nake gani.
Dariya mummy tayi tace kiji min ke da wani zance wai aljanu da kurwa. Kode minyard ce ta fara tabaki kinga ni barni naje nayi bacci kema ki kwanta ta fadi haka tana juyawa rikota ayush tayi shikin kuka tace mummy na karki barni Dan Allah na shigesu mummy tace ke ayush banson sakrci ya kike Abu kamar yarinya ne ? Ni ki wuce ki kwanta gobe ma tattauna ayush tace inada sheda akwai kurwar a kicin muje ki ganta nasan wannan ma buya tayi idan babu zan barki ki kwanta.
Kitchen sukaje babu komai su yazeed har sun goge. Mummy tace kingani babu komai haba yar kirki. Kawai ke kike ganin cewa akwai wani Abu amma babu komai je ki kwanta kinji cikin sanyin jiki tace toh amma a dakinki zan kwana mummy.
Dakin mummy suka shiga hankalinta ya Dan fara kwanciya hakan yasa ta yanke shawarar shiga bandaki tayi wanka bayan mummy ta tabbatar Mata babu komai a ciki. Da dar dar tayi wankan amma bataga komai ba har ta fara tunanin toh ko da gaske babu komai kawai rudewa tayi? Gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta cikin kwana biyu kamar ana tsotse Mata jini. Duk tayi wani kwarshal da ita fuskar nurse dinne ya fado Mata a zuciya take fitsari ya tsargo Mata. Har ta gabatar tayi flushing amma maimakon ruwa sai taga jini. Juyawa tayi bayan ta rufe ido ta daura hannunta a kirji tace ayush karki damu ba gaskiya bane. A hankali ta bude idonta sai taga jariri anyi masa yankan wulakanci jini yana bulbulowa kamar daga famfo da gudu ta fice Dan yanzu ba ta ciwon jikinta take ba yanzu ta ranta take. Mummy tace ke lafiya kika fito kamar kinga mutuwa? Ayush tace idan kika fadin hakan ma yayi daidai domin naga mutuwar. Mummy wallahi ba tunani na bane yanzu nan naga……..
Labarta Mata tayi mummy taja tsaki tace ke ni kin fara fice mini akai inba iskanci ba yaushe katuwa irinki zata dinga wani gudun kurwa da aljanu? Na fara bacci na zaki wani fito da gudu ki tsinka mini gaba muje naga ni. Ayush ta shige bargo tana rawar sanyi tace bani kara shiga wallahi. Gobe dakin yaya yazeed zani Dan shi yana addu’a. Mummy tace ni kuma kafura ko? Toh nima na iya addu’ar ai babu abinda zai bani tsoro ayush de batace komai ba illa kara kankame bargo da tayi.
Mummy cikin dure duren ashar ta shiga ban dakin tana fadin wani shegen ne yake tsoratar min da yata? Aikin banza da wifi ashe ma matsorata ne kunsan dai ni ba gaba da gaba ba ko ta baya sai an shirya. Har zata fita taga brush din ayush dake jefe cikin sink. Girgiza kai tayi tana kaji shashashar yarinya. Bude famfon sink tayi ta wanke tace gashinan ruwa me kyau zata wani ce na jini ne. Kamin ta rufe bakinta ruwan ya koma jini. Murmushi tayi tace ka duba nima har tasa na fara gane gane. Rufe fanfon tayi dukda ko taga jini ne amma gani take kamar tunaninta be dago kanta da zatayi ta cikin madubi ta kalli wannan nurse din saide halittarta ta munana sosai anan murmushi tayi ma mummy tare da daga Mata hannu alamun hello sannan tace SANNUNKI!
Bude baki mummy tayi zatayi magana amma shiru kakeji ji kake jigib tayi ruf da ciki a gaban aljana tana. Waiyo! Waiyo ! Aisha! Aisha ki kawo Agaji ki taimaka.
Ayush ne ta leko kanta ta cikin bargo tace mummy ba komai fa karki damu shirme na ne. Mummy tace kiyi wa Allah kizo wallahi wannan shine fitsari na na 5 kenan kiramini yazeed yayi min addu’ar nan. Ayush tace AI kema kin iya kiyi kawai kamin ta rufe bakinta wani saurayin aljanu kyakkyawa har yafi yazeed nesa ba kusa ba amma kwayar idonsa Jajawur ne ya zauna a gefenta tare da daura hannunsa a bakinta yana Mata murmushi yace matata kiyi shiru kinji? Kirjinta na bugu ta gyada kai.
A bandaki kuwa mummy fadi “lakad ja’akum innaka innaka humaiya” wai ita ta dage addua take harda daga murya………
TO BE CONTINUED IN CHAPTER 94…….
SISTERS YA KUKE YA RAMADAN ? YA IBADA ALLAH YA BAMU LADANSA.
ME KUKE TUNANI GAME DA CHAPTER DINNAN ? SHIN HUKUNCIN DA NAYI WA SU AYUSH YA DACE DASU ?
KARKU MANTA KUYI VOTING DA COMMENTING TARE DA SHARING.
LOVE YOU ALL 💋
miss untichlobanty 💕
8th may, 2020.RECAP
Ayush tace AI kema kin iya kiyi kawai kamin ta rufe bakinta wani saurayin aljanu kyakkyawa har yafi yazeed nesa ba kusa ba amma kwayar idonsa Jajawur ne ya zauna a gefenta tare da daura hannunsa a bakinta yana Mata murmushi yace matata kiyi shiru kinji? Kirjinta na bugu ta gyada kai.
A bandaki kuwa mummy fadi “lakad ja’akum innaka innaka humaiya” wai ita ta dage addua take harda daga murya………
CONTINUATION
Haka kawai ayush taji ta kasa yin komai jikinta duk ya mutu ta kurawa wannan aljanin ido. Bayan wasu dakiku yayi murmushi yace mahaifiyar ki ta fita raki daga ganin yaya ta duk tabi ta rikice murya na rawa tace waye kai? Murmushi ya Mata yace ni mijin ki ne. Zaro ido tayi tace AI inada miji kuma kai aljani ne tayaya zaka aure ni? Riko hannunta yayi yace zo mu tafi gidan mu masoyiya ta.+
Kamar shashasha (dama shashashar ce) ta sauko daga gadon yace rufe idonki rufewa tayi. Taji kamar suna cikin iska bayan sakanni yace bude. Tana budewa ta ganta a wani kungurmin daji ta Dan tsorata amma ganin ya rike hannunta yasa ta Dan saki ranta tafiya suka fara babu jimawa ta hango wani dankareren gida kai kace ba duniya bace.
Murmushi tayi a ranta tace Allah me riko nikam abubuwa sunmin daidai ga miji kyakkyawa ga kuma dankareren gida. Murmushi me sauti aljanin yayi Dan yanajin duk tunanin nan nata.
Suna shiga cikin gidan kofar ta rufe gam sanda gabanta ya fadi juyawa tayi tare da kokarin bude kofar taji kyam Kyam ta juyo zata ma aljanin magana amma sai gata a kasa sumammiya saboda halittar sa ta asali da ta gani jibgege ne. Harshensa kamar na micijiya idonsa kore shar ga kaho, ga jela kai bazai kwatantu ba.
………
Zayya kuwa tsakar dare ta gudo ta nufi gidan sahir dama tana da mukullinta dan haka babu wani danna kararrawa ta danna kai ta shigewar ta.
Sahir yana bacci yaji ruwan sanyi sai jinsa kake a kasa fat! Ya fado. Mikewa yayi ganin zayya ce yace baby har kinyi missing Dina ne? Tace Allah ya kiyaye dama hukuncin abinda kayi min nazo ma kaga tafiya ta. Tayi ficewar ta kwafa yayi yace yarinyar nan sai na yi Mata seti tukunna.
A gidan Alhaji mansur kuwa zaman lafiya ake sosai mom da mama kamar yan uwa dukda ko kowacce tana da kishin ta amma sun girmi wannan AI su dai a barsu da kokarin birge Alhaji mansur ko da inna zasu koma tsokanar sa take wai daga yin aure har yayi kumatu ko kwana uku beyi ba.
A gidan yazeed kuwa minal ce tsaye gaban madubi tana taje gashinta. Yazeed ya fito daga wanka yazo ya tsaya a bayanta tare da karban cumb din. Murmushi tayi tace kana jiyo mutanen ka fa. Murmushi yayi yana cuku cuku da gashin yace na jisu saka rigarki mu kunna kallon mu. Tace kai bazaka sa ba? Murmushi kawai ya Mata yace zamuyi wasa ne anjima kadan. Girgiza kai tayi tana mamakin rashin kunya irin na mijinta. Tirare ta shafa sannan suka kunna kallo su.
Bayan mintuna sukaji knocking pause suka sa kuma suna daidai inda aljani ya fito ma ayush amma su basa ganin komai. Bude kofar minal tayi bayan yazeed yasa jallabiya. Summy (yar lesbian) ce minal tayi murmushi tace ki shigo. Shigowa tayi ta zauna a kujera kanta a kasa tace kuyi hakuri kun ganni war haka wani Abu na gani shine nace dole in fada muku shin nine ko kuma kun gani
DAN ALLAH KU MAIDA HANKALI NAN WAJEN KAR KU RIKICE ………
tace a CCTV footage Dina ina cikin kallon abinda ke wakana har na ga ayush tana magana ita kadai bayan ta sauko daga gadon kawai sai hotan ya dauke bayan sakan 3 ya kawo amma bata daki. Na duba kaf gidannan ban hanata ba kuma har bayin da mahaifiyar ta take na leka banga kowa ba. (bazata iya ganin aljanin a camera ba)
Yazeed ne ya duba nasu suma Abu daya ne ya faru hakan ya daure musu kai sosai minal tace karki damu kije ki Kwanta idan ma guduwa tayi San kudin ta zai dawo da ita.
STORY CONTINUES BELOW

Sigina summy ta Mata cikin tsokana yace wata ta kagu infita toh yanzu zan wuce. Tsaki minal taja tana dariya ta jefe ta da pillow tare da fadin ki rufe mana kofa de. Bayan ta fita jugum minal tayi yazeed ya riko hannunta yace karki damu komai yazo karshe da izinin Allah wahalar ki ta kare zo kiga wani Abu ya fadi hakan yana janyota jikinsa……….
ABINDA ya faru kuwa shine tun a can baya lokacin da alama su minal munafurci kasa kasa yazeed ya soma bjncike kamar yadda kuka sani Wanda hakan yasa ya zargi goje cewa shi ya saka musu kayan Maye abin sha Dan basuda wani makiyi sai shi. Garin binciko ne ya gano cewa goje (Dan uwan lailai matar ya Abubakar wanda har yaso ya Mata fyade Allah ya sha da ita.) yana auren ayush kanwar zakiyya abin ya bashi mamaki sosai. Hakan yasa ya hada one plus one dinshi yadda akasa lukman ya auri zaliha maybe shiyasa take daukan fansa hakan yasa ya zurfafa bincike Dan ya tabbatar kar yayi kuskure toh amma yana bukatar Wanda zai shiga jikinta ana cikin haka har wata rana summy tazo neman aiki amma babu vacancy.
Marainiyace daga ita sai mahaifiyar ta mara lafiya hakan yasa ta hakura da zama babbar mace ta nemi aiki a companyn yazeed. Sosai ta bawa Jamal tausayi yake bawa yazeed labari nan yazeed yace ya nemota akwai aikin da zata mai.
Koda tazo yazeed ya sanar da ita yadda zatayi ta shiga jikin ayush har ayush ta yarda da ita ta dinga bata mission sannan ya Mata gargadin kisa idan tayi kuskure tunda lokacin ko tunanin retire baiyi ba. Ita kuwa abin nema ya samu dama yar karya karya ce amma ba yar lesbian ba. Ta zama yar lesbian ba karya ne duk a cikin shirin yazeed Wanda minal ce ta bada shawara.
Numbar ta ya karba sai yaga ashe ma yana da ita. Numbar da ke chatting da zakiyya ne lokacin da zatayi tafiya. Yace menene hadinta da zakiyya? Tace kawai ita burinta ta dinga shiga cikin manyan Mata hakan yasa duk group din da akwai manyan Mata toh sai tayi karya karya ta samu ta shiga anan ta samo numbar zakiyya yazeed yace matarsa ce zakiyyan Dan haka tayi hankali.
Ana cikin haka ne har ayush din tasa summy tayi kamar tayi zina da zakiyya da sauran duk abinda ta sata yayinda take surfowa su yazeed rahoto su kuma sunata tara shedan da zasu bawa zakiyya si nuna Mata cewa yar uwarta ba yar uwarta bace kuma ba mutumiyar arziki bace saide kash suna planning su tona Mata asiri idan minal ta haihu ranan suna a Mata tsamo tsamo amma kafin sukai ga yin haka tayi musu tsafi.
Bayan sun warke kuwa gani sukayi tunda batasha jibgar gidan suna ba dole su Rama abinda ta musu kamin su Dan ka ta hannun yan sanda ayi kasheta tunda itama ta kashe jarirai.
Acikin gaba daya tafiyar rayuwar sun nan akwai muhimmin Abu da suka fahimta. KAYI KOMAI AKAN LOKACIN DA KAKE DA SHI DAN BAKASAN YA GABA ZATA KAYA BA KARKACE ZAKA JIRA WANI ABU, SANNAN DUK WAYONKA BAKA IYA TSALLAKE TSAUTSAYI DA AJALIN KA.
Abinda summy ta fahimta kuwa shine DUK LOKACIN DA KA DAGE SAI KA SAMU ABU TOH WAHALAR BANZA ZAKACI KO KA SAMU BE ANFANE KA BA KO BAZAKA SAMU BA. LOKACIN DA KA KOMA GA ALLAH KUWA IDAN YAGA DAMA YA BAKA ABINDA KAKE NEMAN A DUNIYAN KUMA YA KARA MAKA DA ALKHAIRI A LAHIRA. Matar da ta taimakawa mom tabar gidan mahaukata kuwa ba kowa bace illa mahaifiyar summy wayo sumaiya. Yazeed ya biya Mata kudin magani ta warke har ya nema Mata aiki amma bayan wasu shekaru ta rasu.
CIGABAN LABARI
safina asararriyar matar yazeed tana baccinta me dadi take jiyo hayaniya sama sama har ta farka jin mommy ce yasata yin tsaki tace tsohuwar nan zan Mata wulakanci wallahi bazar bazar ta shigo dakin mummy ta sameta shaman cikin fitsari tana mazari tsabar tsoro.
Tace tsohuwar munafuka ya akayi mummy tace kinga yar albarka safina taimaka ku ciro ni. Safina tace jibgegiya dake saide in jaki mummy tace nide cireni daga bayin nan kinji matar kirki. Tace badan halinki ba kawo hannunki. Sannan ta taimaka Mata gyara jikinta tayi sannan suka zauna a bakin gado yadda kasan shiri sukeyi tun da.
Cikin son jin labari safina tace wai ya akayi ina aishar? Mummy tace ke bar batun yar iskan nan ai yau na leko barzahu na dawo. Safina tace ban gane ba labarin tass mummy ta tsara Mata ta nutsu ta shanye tas sanda mommy ta gama tace kuma sai akace miki zan yarda? Kai mummy kin iya hado ta mummy tace nima ban yarda da ayush ba sanda na gani.
Yin duniya mummy tayi safina bata yarda ba daga karshe ma dariya ta sheke dashi ta koma dakinta. Ta kwanta tare da kashe wuta ahankali ahankali iska ke kadawa a jikin labule yana kara karfi kofofi da da taga ne suka fara kara ga bakin kura yana kadawa hajaran majaran. Ruwa mai karfi ne ya tsinke tare da cida daidai lokacin kuma yazeed ya sumbaci minal yayinda safina…………
😶😶😶BANCEWA KOMAI KAWAI KAR KU MANTA DA VOTING, COMMENTING TARE DA SANAR DA KAWAYEN KU SUMA SU KARANTA.
ALLAH TA VAR JAUNA SANNAN YA KARBI IBADUN MU BAKI DAYA.
Miss untichlobanty 💕
17th may, 2020.
Yin duniya mummy tayi safina bata yarda ba daga karshe ma dariya ta sheke dashi ta koma dakinta. Ta kwanta tare da kashe wuta ahankali ahankali iska ke kadawa a jikin labule yana kara karfi kofofi da da taga ne suka fara kara ga bakin kura yana kadawa hajaran majaran. Ruwa mai karfi ne ya tsinke tare da cida daidai lokacin kuma yazeed ya sumbaci minal yayinda safina…………
A bangaren ayush kuwa aljanin nan daureta yayi kullum zaizo ya sha jininta bayan azaba da yake Mata da wuta tare da bata tafashasshen ruwan diwa mai jini da azabar wari. Gashi bata ganin komai sai jarirai. Kullum tamabayar ta me tayi masa? Ganin ta dameshi yasa yace ke saurara kiji, nine aljanin da aka tura na mantar da kowa da sharadin duk randa suka sake yin aure zan rasa nawa auren ba wannan kadai ba matar tawa ni zan kashe da hannuna.
Dan haka yanzu na rasa matata, amarya ta a sanadin ki shiyasa ya zama dole ki zauna da ni.
Kuka ta fara yi tana bashi hakuri shikam ko ajikinsa. A kwana a tashi babu wuya har wata daya ya shude. Su minal sunje sunyi ma ummu amina godiya sosai na yadda ta kula da minal inda yazeed ya dauki main aikin da za’a Mata. Anan suka samu sabi’u wagon sabi ya makance. Ummu amina ke sanar dasu AI tun randa minal tasa kafarta tabar gidan yake kuka ashe yana sonta kawai haushin mijin da ya AURETA sannan ya wulakanta ta ahalin tana dauke juna biyu yakeji. Hakan yasa yake sauke haushin akan yaran.
Talauchi da yanayin rayuwa tasa yake dabanci amma deep down can cikin zuciyarsa mutumin kwarai ne. Yayi kuka har ya gaji har ya kasa controlling hawayen sa. Hakan yayi sanadiyyar makancewar sa cikin shekaru 4.+
A yau ne ta kasance an bawa su zayya hutu zata dawo gida yayinda sahla kuwa dama day takeyi Dan haka kullum zuwa taje ta dawo ne amma dai tare akayi hutun Dan makaranta daya ne.
Kuma a yau dinne LUKMAN da matar sa kuma aminiyar minal ZALIHA zasu dawo kasarsu ta gado wato NIGERIA. Saide su Allah da daya ya basu dukda cewa karami ne shekarun sa bakwai. Amma har yau fa jiya I yau ne kullum sai sunyi rigimar nan dai tasu.
Minal an cakare anci ado sai walwali take tana ta zirya tsakanin kitchen da dinning room zakiyya ce ta shigo da abun koyar tafiyanta Dan shekara 15 a zaune ba wasa bane. Mashkur yace suma gode Allah akwai hope zata iya taka kasa Dan yanzu leave shima ya dauka yazo zai Dan zauna da su yazeed a sake karfafa zumunta da shakuwa.
Hira suka fara ita da minal suna jimamin ko ina ayush ta shiga? Zakiyya tace ke ni bar banza AI wallahi ma taje Allah kiyaye hanya. Minal tace uhm uhm fa idan kuma taje ta bata rayuwar wasu yanda taso yi wa namu fa? Zakiyya tace kuma fa maganarki gaskiya ce toh amma… bata karashe ba sanadiyyar Umma hani da ta shigo da saurin ta tana fadin uwar daki akwai matsala banga hajiya ba. Minal tace ai hajiyoyin maki yawa garesu wacce ? Tace hajiya babba mana na duba…… hayaniyar da suka jiyo ta window din kitchen yasa ta yin shiru kamin suka fita.
Aikuwa mummy ce ta tattare zani tana sharar gudu kamar mota sharon.kai kace standby generator aka jona Mata ga security da masu aiki sunyi ca sai binta suke amma ta file musu.
Waje ta fice ta ari titi suna bin ta a baya. Ba komai take fadi ba sai kai jama’a ga mutuwa ga yan boko haram, ku gudu.
Irin yan acabar nan sun taru dama kawai sukaga Mata cikin kaya mai tsada harda sarkin gwal tana gudu tana fadin ga mutuwa shiyasa kafa me naci ban baki ba? Gudu suma suka fara, wasu nayi adungure su diro daga machine din suyi kolin koli su kwalu da kasa sannan su Mike su cijewa rigar su iska. Irin stop stop dinnan na yan napep suka wuce shugaban wajen sunan shi dogo me babban Riga.
Ana cikin cakwakiya da shi akan kudi ya sakami mai napep kenan zai nana da kasa yaga taron mutane ana gudu cuceshi kawai ake wani fiwt ! Fiwt ! Kakeji abinda akee fada yaji aiko ya sako mai napep din dam a kasa ya fita da gudu shine a gaba gashi yafi kowa tsayi rigar iska ta cikata ji kake fafar fafar baka ganin komai se babbar rigarsa yayinda yake sambado gudu zundum zundum.2
Inyamurai masu saida doya sukazo wucew inyamurar ka bajin hausa suke ba amma sunji Boko haram take suka bi ta Kan doya yayin da mamar su tsohuwa kafa ya hau mazari ji kake curr ta saki fitsari.
Haka suka dinga kwasar mutane, me shayi ne, masu kasa irin kayan marmari a titi ne…. sanda akayi gudu iya gudu aka gaji aka tsaya hutawa dogo yace wai ni wa ya gansu ne samrin nan sukace wannan hajiyar ce. Yace wai to ma a ina kika gansu ne? Dariya tayi tace zakusha mamakin inda na gansu. Cikin mafarki nagansu in fada muku. Ashar irin ta yan daba ya danna yace wannan matar ta ma raina mana hankali wallahi kai kuyi Mata na jaki.
Rufeta akayi da mugun duka matan inyamuran nan suka zage dantse suka kiranta kamar sun Sami sakwara. Akayi Mata ruf dubu aka jijjibge ta. A TAKUCE de daga nan itama tasan inda dare yayi Mata domin haukace wa tayi dalilin da yasa haukace kuwa shine saboda lokacin da za’a tsafin anyishi ne cewa in dai ayush tana raye mom din yazeed bazata taba yin hankali ba toh yau da safe ayush tayi gaba sanadiyyar cinye gaban ta da aljanin yayi domin satin ta daya a gidan wasu halittu masu Lama da kuda suka fara fitowa daga kasar ta suna cinye Mata fata. Atakaice de tayi mutuwar wulakanci iya wulakanci ga bata sallah ga shirka ga zalinci ai kowa ma yasan makomar ta.
A gida kuwa safina fadi take nikam yanzu komai nawa ne nayi baje baje kawai abinda yamin saura shine na fitar da wannan kucakar matar tasa. Waka take tana rangaji daure da towel zata shiga wanka saboda ance za’ayi baki kar su kawo Mata raini.
Bude bandaki tayi tana rangaji da juyi. Jijjiga tayi zatayi juyi, juyin ta ke da wuya santsi ya kwasheta ya hada da gini sannan ta fadi ta baya ta doke da toilet sit a take a wajen jini ya cika kwakwalwar ta sai barzahu. Allah yaji kan mu’umini ameen!
Motar su zaliha ne ta faka a cikin gidan su minal. Da sauri yaransu me suna kabir ya fito yana fadin wow daddy! Gidan uncle dinnan ya hadu. Kace ya ma sunanshi? Luku yace sunan shi uncle yazeed. Ciki ya shiga da gudu yana fadin kowa ya fito , king kabir yazo. Nine sarki kabir Dan lukman dariya minal tayi tana saukowa tace maraba sannu da zuwa Dana sarki kabir.
Alamun tunani yayi kamin yayi sauri ya riko hannun minal yace kece wannan kyakkyawa matar uncle handsome ko? Murmushi tayi masa sannan tace kaima AI kyakkyawan saurayi ne kabir Dina. Yace toh ya akayi kika sanni? Tace mommyn ka ne ta tura min hotonka.
Dadai lokacin su zaliha suka shigo rurrungume juna akayi aka Dan zubda kwalla abin ka da Mata. A one sitter zata zauna shima luku na yayi kokarin zama. Tureshi tayi shima ya ture ta. Ture ture suka soma kabir ya girgiza . Dan in da sabo ya Saba ya samu guri tare da fara latsa tablet dinsa yana shan alewa. Sahla ne ta sauko da tayi bulbul da ita tana dauke da juna biyu karami shekaran jiya suka San hakan fadi Dan samri Kaine kanin namu? Dago kanshi kabir yayi yace wow! Kaga mata kyakkyawa fara sol idan na girma yar ki zan aura.
Zaliha ne ta zauna a kujerar luku ya ciccibeta ya dagata shi ya zauna. Dariya tayi tace daidai kenan ta dake cinyarsa. Wani tunani ne yazo masa Dan haka ta kasa kasa ya fara tattaba Mata jiki ganin zai nemi ya tsinkata gaban yara yasa ta tashi kuma duka abinda sukeyi akan idon minal.
Sahla kam tuni game ya ‘bage tsakanin ta da mutumin ta kuma sirikin ta acewar sa fa kenan. Hira su minal suka kafa yayinda luku yace ina mutumina ne? Minal tace na barshi a daki yana shiryawa yaci ace ya sauko ma yanzu.
Daidai lokacin yazeed ya fara saukowa yana fadin my man ! Tare da fadada murmushin sa. Rungume juna sukayi kabir kam ajiye game yayi yazo ya kewaye yazeed sau uku sannan ya kalli baban sa yace daddy zan iya zama gidan uncle dinnan Dan inyi kyau? Luku yace kai de da masifar kyau dinka. Indai Abu na da kyau toh kai shikenan kabi ka damu mutane kenan akai.
A mota kuwa tunda zayya ta shiga take ma wa sahir magana amma ko inda take bai kalla ba Dan yasha alwashin koya Mata hankali.
Tace wai me nayi maka ne kawai murmushi yayi Mata yace …….
……
A gidan sabir da bushra ba laifi ana Dan zaman lafiya,yana Dan aikinsa saide me ya lura tunda sukayi auren bushra tayi sanyi dayawa bawai tuban bane kadai akwai matsala hakan yasa yauwa kamar kullum ya tisata a gaba yake tambayar ta matsalar ta. Da Kumar ya samu ta budi Baki zatayi magana ta “ance ana bukatar bone marrow transplant cikin gaggawa da a lissafi na yanzu kwana 20 yayi min saura.”
TO WAI SHIN ME SAHIR ZAICE MA ZAYYA ?
KUNASON KABIR KUWA?
YAYA ZA’A KAYA DA JINYAR BUSHRA ? ZATA MUTU KO ZATA RAYU ?
Takuce KARAMARSU BABBARSU, Jared Ku manta da VOTE, follow And comment .
Miss untichlobanty 💕
RECAP
A gidan sabir da bushra ba laifi ana Dan zaman lafiya,yana Dan aikinsa saide me ya lura tunda sukayi auren bushra tayi sanyi dayawa bawai tuban bane kadai akwai matsala hakan yasa yauwa kamar kullum ya tisata a gaba yake tambayar ta matsalar ta. Da Kumar ya samu ta budi Baki zatayi magana ta “ance ana bukatar bone marrow transplant cikin gaggawa da a lissafi na yanzu kwana 20 yayi min saura.”
CONTINUATION
Salati sabir yayi yace bushra shine kika boye mini baki sanar dani ba ko wani daga gida tace nima a kurarren lokaci na sani shiyasa ma na nemi tuban kowa Dan na fahimci rayuwa ba’a Mata garage sai ta aiko ma Abu alokacin da baka tsammace sa ba.
Riko hannunta yayi tare da zura Mata hijabi sai family house Dina Alhaji mansur domin a fara gwadasu ko za’a samu Wanda yahau daidai a dangi kamin a fita waje wato MRD (matched related donor)
Babu bata lokaci suka nufi asibiti yayinda mom tayi kokarin kiran yazeed amma is not rechargeable Dan haka tabar masa message.
A gidan kuwa su zaiya ne suka iso nan akayi introducing Mata su waye su zaliha. Kabir yaron su luku ne yace la kamar su daya kuma sai ya saka kuka tare da rungume sahla. Cikin damuwa tace menene? Yayinda hankalin kowa yayo kanshi.+
Jan hanci yayi yana goge kwalla cikin kuka da shessheka yace meyasa ba’a cemin na shirya ba? Luku yace big boy ka shirya me? Yace ganin kyau mana ashe hassanan rafi kyau kuka barni nayi garajen zabar Mata. Kama haba yazeed yayi Dan ya rasa abin cewa yadda yake zato zance yayinda minal tace iko sai rabbu zayya kuwa waks ta yanko inda ake cewa “ni bazance komai ba Dan zafi ban shafa ko mai ba”
Shiko kabir cewa yayi AI da nasan akwai Wanda yafi aunty sahla kyau da nace yarta nakeso. Riko hannun zayya yayi Mata fuskar abin tausayi yana Mata wani munafukin Dariya yace aunty zayya ta zaki bani yarki? Sai inyi Mata biyu da yarki Dana aunty sahla Dan bakyau daukar alkwari sannan ba’a cika ba da sai ince na fasa nata. Minal ne ta daki zaliha na wasa tunda a gaban yara suke tace zally ke yanzu duk iyayin naki sanda kika juyewa danki kai kuma kana gani ka barta uncle luku? Kabir ne ya kyalkyale da dariya yace daddy dama sunanka luku? Yace daga yau daddy luku zauna ce maka. Zuwa yayi ya shafa cikin sahla dukda ba’a ganin komai yace uwar gida ta ina miko gaisuwa.
Zayya ne ta kama kwankwaso tace “ummi…” wato minal “ni fa ban gane ba wai wannan yaron me yake nufi ne yake ta zancen wani uwar gidansa?” Tsayawa yayi a gabanta ya gyara Riga tare da ninke hannu yace ni nan da kike ganina babban saurayi, ko cikin turawan nan mr. handsome ake cemin Dan haka…….
Wucewa zayya tayi Dan bata da lokacin sa ta zauna a gefen minal tare da cewa ummi ke nake saurare… zana zahir ma yayi yayinda sahla tayi sauri sauri ta zauna a gefen zayya tace sister albishirinki ai kin kusa zama aunty….. zayya tace tun Bance goro ba? Sannan ta washe baki tace kice Allah? Minal tace wai ku bakuda kunya ne? Zayya bata ma bi ta Jan zancen minal ba ta rage murya kasa kasa tace sis bani sirrin… sahla tace yafi karfinki saide kije kice wa mijinki ya fada miki. Zayya tace an gama Dan itafa tunaninta wani abin za’a sha shiyasa ko ajikinta a inda take zaune ta kalli sahir tace bro wai kasan sirrin ? Toshe Mata baki sahla tayi tare da wucewa daki da ita Dan taga alamun kan da matsala.
Hira sukasha sosai kamin yazeed yace ina wayata mu dauki hoton tarihi. Kabir dake game ya kalla yace big boy je ka Kira mana aunties dinka. Sannan yace wa minal ta dauko wayarsa a daki tace aiko kaga mun manta bamu Kira safina ba. Bata rai yazeed yayi Dan shi already ya sake ta tun sanda ya dawo hankalinsa Dan haka yave kirata dama akwai abinda zan fada Mata sai muyi hotan karshe.
Dauko wayan minal tayi ta kawo masa sannan ta tafi kiran safina aiko tana bude bandaki ta kwalawa yazeed Kira haurowa sama sukayi suna tambayan lafiya hannunta na rawa ta nuna musu bandaki salati suka saka. A bayansu sukaji ance kin kasheta KIN KASHE KIN YAR UWA TA.
A asibiti kuwa an gwada su duka family din wato donors su maman ta da nafisa da auntyn su ana tsammanin result sukaga su yazeed sun shigo da gawar safina wajen su sukaje suna tambayar lafiya wata fiririyar fitsararriya ne tace me kuwa ya faru an kashe mini yar uwa toh wallahi za’ayita. Ran yazeed ne ya baci yadda ta hakikance cewa minal ne ta kashe safina. Mari ya falla Mata yace ke bakida hankali ne kinsan cewa wannan magana ba karama bace? Zance ne ya miki dadi har kike Barbada cewa ita tayi kisa bayan kinsan hukuncin kisa ne ga Wanda ya kashe?
Likita ne ya fito ya tabbatar Musu da cewa tabbas safina ta mutu. Daidai lokacin ma likitan bushra ya fito shima yace babu Wanda yayi matching.
Iyayen safina ne suka fito suma suka iso da yan sanda. Yace wacece ta kashe mini ya fitsararriya nan me suna Billy ta nuna minal kamata yan sanda zasuyi yazeed yayi dariyar manya yace da alamu ku din sabbin jini ne bakisanni ba ko? Toh Wanda be sani ba ya sani Wanda ya sani ya kara sani nine nan retired major gen. yazeed ABDULMAJEED umar.
Kuma duk Wanda ya sake ya taba mini Mata toh lallai ya shirya zaman gidan yari. Anyi bincike ne da za’aje ita ta kashe ta ahalin lamarinnan me sauki ne dakinta akwai CCTV kawai dubawa za’ayi…..
Haka dai yazeed yayi musu wankin bargo kamin aka duba footage din aka ga abinda ya faru nan suka basu hakuri akayi Jana’izanta yayinda aka tambayi su yazeed ko they are willing a duba bone marrow su ko zaiyi matching da na bushra. Koda suka koma gida jikin kowa yayi sanyi na mutuwar safina dukda ko ba wani dasawa sukeyi ba.
Anyi jungum jungum a parlour kowa na kallon kowa, zayya de magana daya ke ci Mata tuwo a kwarya, ganin kamar basu damu ba yasa ta gyara zama. Parlourn yayi tsit Dan haka tayi gyaran murya tare da turo baki tace gaskiya ina magana. Wai ya naga kowa yaki ya fadamin sirrin ne? Abinda ya fito na gaba a bakinta ne yasa kowa yasha jinin jikinsa.
YA SAHIR GASKIYA FA DOLE NIMA KAYI MIN CIKINNAN EHE!
AYI MIN AFUWA KWANA BIYU KUN JINI SHIRU BANYI UPDATE BA BA LAIFINA BANE LAIFIN MAI DAMBU DA TAYI LITTAFI ME DADI.
KARDE KU MATA KU ANTAYO MIN COMMENT TARE DA VOTING SANNAN INA ME BAKIN CIKIN SANAR DAKU CEWA KURUCIYAR MINAL.DINMU YA KUAA YA KARE DOMIN KUWA CAKWAKIYAR ZAYYA DA SAMUN CIKI ZA’AYI SHIKENAN AMMA FA BA SHIKENAN BA DOMIN KUWA SHIMA ZAI BADA KALA SOSAI.
INSHA ALLAH ZAN MUKU UPDATE DA WURI! LOVE YOU ALL💋
miss untichlobanty 💕
2nd June, 2020RECAP
Anyi jungum jungum a parlour kowa na kallon kowa, zayya de magana daya ke ci Mata tuwo a kwarya, ganin kamar basu damu ba yasa ta gyara zama. Parlourn yayi tsit Dan haka tayi gyaran murya tare da turo baki tace gaskiya ina magana. Wai ya naga kowa yaki ya fadamin sirrin ne? Abinda ya fito na gaba a bakinta ne yasa kowa yasha jinin jikinsa.
YA SAHIR GASKIYA FA DOLE NIMA KAYI MIN CIKINNAN EHE!
CONTINUATION
Bata rai yazeed yayi dukda bece komai ba yayin da minal ta dage goshi domin shirme zayya ya fara fita Mata akai. Zaliha ne ta e ke tashi ki bawa mutane waje bamason rashin kunya. Kallon sahir tayi ya kawo agaji amma baice Mata komai ba sai harara daya falla Mata yabar dakin. Tashi tayi a kufule tana bubbuga kafa da yarfa hannu ta tafi dakinta ta fada kan gado kuma ta sake tana fadin to ni me nayi ? Daga cewa inason na haihu shine ya zama rashin kunya? Kowa bayason ya taimaka mini? Toh AI in kunsan wata bakusan wata ba.
Wayarta ta janyo ta rambatsa ma halsey Kira dukda ko tana jin haushin katin ta da zai kare Dan international call kati yake sha kamar me…. ringing wayar ya fara yayinda take gunagunin gara ta Kira halsey Dan yeonsil sai tayi ta tsokanarta kuma bata wani bata shawara arziki ba. Dauka halsey tayi tare da fasa ihu tace besty har nayi missing dinki, nina kings yanzu na iso kasarmu wai shin kinyi magana da yeonsil kuwa? Me yas……+
Zayya ne ta datseta ta hanyar cewa ni duk ba wannan yasa na kiraki ba taimako ko ince shawara nake nema. Gyara tsayuwa halsey tayi Dan a airport ma take tace toooo ina jinki.
Muryan abin tausayi zayya rasa tace kinga ni ina dawowa gida kawai sai na tarar yan biyu na tana da ciki…. halsey tace toooo? Kukam hausawa haihuwar wuri gareki daga aure? AI aurennan ma yayi wuri mukam kinga……..
Zayya tace zaki saurara ko surutu zaki min? Halsey tace toh ina jin ki…. zayya tace toh nima fa so nake na haihu… halsey tace mene? Kee zayya yar yarinya dake kice zaki haihu shekararki sha shida ne fa idan kika fara Yoon fitsari fa? Zayya tace wai ke bakisan zamanin da suma daidai irin shekarunnan suke haihuwa ba? Wasu ma basu kai ba sun mutu ne? Kuma da mutum be kai ya haihu ba ai bazai dau cikin ba nide yanzu shawara nakeson ki bani a garin ya ake samun ciki? Ajiyan zuciya halsey ta sauke tace toh mude a garin mu abinda na sani shine idan mutum yana neman haihuwa bai samu toh sai yaje wajen baita yayi sadaka sannan ya sanar a tayasa addu’a.
Zayya tace toh toh toh na gane… halsey tace ko kuma… zayya tace a ah ya haka ? Kina fatan kar wannan hanyan ta bulle ne da Zaki bani wata? Ki bari na gwada wannan mana. Kashe wayar na tayi tsabar kaguwa bata jira taji sauran zancen ba. Kiran kawarta na tsohuwar makarantar kamin ayi Mata transfer da shike kawar a kano suke.
Tana dauka race Mata ta turo Mata da account number zata tura Mata kudin da za’a ciyar da mutane 20 na kwana uku Allah ya cika Mata burinta.
Kawar Ta ta me suna fati tace ke ko menene wannan buri naki kuma ni ince wa iyayena me? Zayya tace haba fati AI kin fini dabara zakisan abinda zaki fada musu. Kinga kudin da mikewa shi a hannu kenan zan turo miki Dan Allah kiyi min taimakon nan. Fati tace toh shikenan ai. Sannan sukayi sallama.
Shiryawa tayi ta fito har lokacin su minal suna zaune a parlour amma kabir yayi bacci an kaisa daki. Sim sim ta wuce ta dauka basu ganta ba . Ba tare da sun kalleta ba yazeed yace hajiya ina zuwa? Ji tayi kamar ta fashe da kuka Dan bataso sun lura da ita ba. Tsarewa tayi zata fice minal tace kina kara taku daya zan karye miki kafa.
Kukan shagwaba ta fara kamin ta koma dakinta ta fada gado tana kuka. Sahir ne ya shigo fuskar sa a tamke. Rigarsa ya cire ya dale gado baice Mata komai ba. Jin alamun kamar an shigo dakin yasa ta dago kallonsa tayi taga ya kwata ba tare da ya Mata magana ba. Kwafa tayi tace wato kai baka damu ba ma baccin yamma zakayi bayan ni ina nan ina fafatawar yadda zan haihu……
STORY CONTINUES BELOW

Datseta yayi ta hanyar cewa ke ni banason shirme ance miki haka ake haihuwar? Ko ma zaki haihun a wannan haukar zaki haihu? Ihu ta fasa masa harda bori. Dama nasan ba sona kake ba kawai saboda abbana yace ka aureni yasa ka aureni. Toh ta Allah ba taka ba ko dakai ko ba kai sai na haihu….. tana kaiwa nan ta shige ban daki tare face majina.
Sakan baki yayi yana kallon ta. Shi ya dauka da wasa take ashe de batasan me takeyi ba. Dariya ma ta bashi yace toh sannu fagal dole ma sai dani in ba haja ba sunan danki shege. Ihu ta kara kurmawa yace ke ni fito ki kawomin ruwa insha. Tace anki din….
Yazeed ne ya Kira sahir a waya yace kacewa matar ka idan na karajin giunta saina karya Mata kafafu.
Zama tayi a ban dakin tasha kukan ta koda ta fito har yayi bacci. Cire masa safa tayi ta wulla a kayan wanki tana fatan Allah ya karbi wannan aikin ya bata ciki Dan aikin alkhairi baya yawa baya kadan balle na miji😁.
Har tsawon kwana uku kullum sai tayi kokarin fita amma sai an kamata hakan yasa ta Nemo numban malama AMINA (untichlobanty). Tana kira aiko taci sa’a ya shiga, sallama tayi kamin suka gaisa tace dama shawara ce take nema , yaya zatayi ta samu haihuwa? Malama tace maya da fari dai shi haihuwa nufi ne na Allah wato ba’ayi masa dole. Kyautace ya bawa Wanda yaso ya hana Wanda yaso bawai Dan baya sonka ba sai Dan ya gwada imaninka. Wasu sai suyita wahalar nema amma Allah bai basu ba. Wasu kuma basu nema ba sai Allah ya basu da ko wahalar renon ciki basu sha ba. Dan haka ki dage da addu’a sannan kije ke da me gidanki a duba ku domin tabbatar da lafiyar ku. Saide kuma muryanki batayi kama da na babbar Mata ba balle ace kundade babu haihuwa da har zaku fara nema. ku kara hakuri sannan….. kamin malama ta karashe zancenta layin ya tsinke kuma babu wata hujjan Dan ba rashin network bane ashe tabawa tayi da hannunta bata sani ba koda ta dake kira busy ake ce Mata dan haka ta hakura.
Tsalle ta daka tace ashe ashe shine sirrin da aka ki a fada mini wato dai wasu suna Haifa ne wasu kuma Allah ya basu ba tare da sunyi renon cikin ba wato ba tare da sunyi cikin bama. Ita ta dauka haka malama ke nufi batasan malama na nufin ba tare da ansha wahala ba ma Dan a tunanin ta babbar mace ce shiyasa batayi Mata fashin Bali ba.
Shiryawa tayi yauwa kamar kullum ta sansado ta fita aiko Allah ya bata sa’a babu Wanda ya ganta har tabar gidan taxi tahau tace a kaita inda ake samun yara. Shiru yayi sai yayi tunani ko orphanage gidan marayu take nufi . Sai ya kaita can tan saukowa kuwa ranan ana wani celebration Dan haka iyaye da yawa sunzo da yaran su manya da jarirai domin taya marayun murna.
Wata ta gani da ganyen jariri tace la wancan ma ta samu dan haka ta tare ta gaisawa sukayi tace Dan Allah ina kika samu dan nan? Matar tace ban gane ba lafiyar ku kuwa Dana ne.. wuceta tayi tana mamakin yadda shigewarta lafiya lafiya amma kamar tababbiya zayya kam tabe baki tayi tanajin dadi tayi wa yar uwarta wayo ba sai ta wahala ba ma zata samu da.
Haka tayita bin mutane tana musu tambayar mahaukata har aka samu wasu yarabawa suka biyota da gudu sanadiyyar daukan jaririn su da tayi a karkashin bishiya a tunaninta Allah ne ya aiko Mata nata. Har tuntube tayi ta gurde kafa.
A takaice de taci bakar wahala kamin ta dawo gida tayi lubus aiko ta samu anyi cirko cirko ana nemanta. Tana shigowa yazeed da tsumagiyarsa a hannu ya daga kamar zai tsula mata tsurewa tayi ta turo baki tare da kneel down ta fara kuka.
Zama sukayi yazeed yace maza yi bayani, hannu tayi ta fara ABBA Dan Allah kayi hakuri ni wallahi naji jiki na hakura da haihuwar ma tunda naga kowa ba so yake na haihu ba….. tsaro musu labarin tayi tundaga sanda ta dawo ta tarar sahla na da ciki har zuwa yanzu. Hajiyar zuciya yazeed ya sauke yace ba haihuwa bane banason kiyi, munson ki Haifa mana jikoki mana. Irin maganar nan ce ba ayinta gatsau kinji? Kuma wa yace miki tsinto da akeyi ? Ni wannan maganar ba hurumin bace idan kin kara girma zaki fahimta. Bazance nayi nadamar aure dake ba amma gaskiya akwai kura dariyar da sallah ke rikewa ne ya kuce tace ABBA dama kaima ka iya cewa akwai kura? Murmushi yayi yace me zai hanashi kuwa? Ai nima sanda naje matashi sissi kwaro ne ni. Dariya kowa yayi banda zayya da ta tashi sumul sumul ta haura dakinta. Minal ne tayiwa sahir ido alamun ya bita yana haurawa ita da zaliha suka tafa. Yazeed da luku sukace Mata da gulma. Yazeed ne ya kalli mashkur yace tuzuru wai bazakayi aure bane har ka mutu? Shafa gemunshi yayi yace kwantar da hakalinka AI a asibitin nan na kyallo nafeesa kanwar bushra da alamu da ita za’ayi yazeed yace yafi maka.
Jamal ne suka shigo shi da zakiyya sundawo daga koyar tafiya Dan yanzu ta ajiye karfen koyan tafiyan. Jamal yace me akeyi babu mu naga ana raha kamin a amsa mishi wayar yazeed tahau ringing. Mom ce ke kira ya dauka tace Dan albarka kuzo ku yanzunnan kaida daughter mun Kira iyayenta ma akwai magana.
A hanzarce suka shirya zasu fice minal har zata kwankwasawa su zayya yazeed ya hanata janyo hannunta yayi yana Mata wani irin murmushi me kashe jiki . Mannata yayi da kirjinsa tare da shinshina wuyarta. Kunnenta ya Dan ciza sannan ya rada Mata bakyason jika ne? A hankali tace ina..so har tana mamakin yadda muryarta ya sarke lokaci daya. Yazeed yace ana making mana baby shine zaki datsesu? Bige kirjinsa tayi tace kai baka tsufa da wannan abun ne? shekara hamsin fa kake dosa Yar dariya yayi yace ji yadda muryanki ta sauya tsaban mayata amma ni ake cemin bana tsufa ? Handsome dani irin haka? Yanzu dai zo muje daki sai mu gani ko na tsufa…. tace kiran mom din fa? Yace ba matsala zai iya jira kinsan fa ya kamata muyiwa twins dinmu gambo. Dukan kirjinsa tayi a wasa ya dangwali hancinta
Luku ne yayi gyaran murya yace malamai akan tsakiyar beni kuke kuma har a makantar min da yaro. Kallon kabir da zaliha tasawa hannu ta rufewa ido sukayi yayin da yake kyallo ido daya yana gulma. Ganin takura tayi masa yawa yasa yace mummy ni ki barni menene ban gani ba dukda cewa ke da dad kuna fada wani lokacin ina kallonku idan muna parlour sai inyi kamar ina bacci. Ina gani kukeyi K.I.S.S yayi spelling musu. Minal da yazeed ne suka wuce suna fadin this one pass our level yayinda luku ya kalli zaliha yace tabbas na miki godiya da kikasa mukayi masa dakinsa daban tun yana shekaru 3. Dariya yayi yace da anji kunya ko daddy? Shiru lulu yayi kamin yace my boy ka dena itin wannan maganan babu kyau kaji jai karami ne babu kyau kaji? Yace okay daddy.
Bayan su yazeed yaron yabi kamin luku yace dole mu kara kiyayewa da alamu yaronnan yanada wayo. Wani lokutan laifin iyaye ke sawa yaransu su baci. Murmushi tayi taja kamatunsa tace for the first time(a karo na farko) ka fadi magana wacce nayi amanna da ita babu musu.
A dakin su zayya kuwa…….
KU BIYONI A CHAPTER NA GABA KUMA CHAPTER NA KARSHE DOMIN JIN YADDA ZAMU KARE WANNAN LABARI MAI FARIN JININ NAKU WATO KURUCIYAR MINAL. SHIN ZAYYA ZATAYI CIKIN KO YAYA ? ME YASA MOM KE NEMAN SU YAZEED? Ko ciki ne da ita? Cabdi……..8
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU WATO
Miss untichlobanty 💕
4th June, 2020.RECAP
Bayan su yazeed yaron yabi kamin luku yace dole mu kara kiyayewa da alamu yaronnan yanada wayo. Wani lokutan laifin iyaye ke sawa yaransu su baci. Murmushi tayi taja kamatunsa tace for the first time(a karo na farko) ka fadi magana wacce nayi amanna da ita babu musu.
CONTINUATION
A dakin su zayya kuwa sahir yana shiga ya fincikota yace ke wai wace iriyar yarinya ce? Ke bakiga cewa kin girma bane bazakiyi kiyi da sahla ba? Kuka ta fashe dashi tana Jan majina tace toh Dan Allah ni menene laifi na Dan nace inason haihuwa? Ba duk Kaine da lefi banda sanda nace muku haihuwa nakeso amma kujera min fada kaki la taimaka min mu samu da sai kace ni ba matar ka bane.
Dafe kai yayi San yanzu ya gane cewa zayya yarinyace sosai. Dafe kai yayi tare da sauke ajiyan zuciya murmushi ya Mata a hankali ya riko hannunta yayi pecking zaro ido tayi kunya ya rufe ta. Shikam ma dariya ta bashi amma ya rike zaunar da ita yayi anakin gado yace haihuwa kikeso ko? Ta daga kai yace toh zo in baki yana me daurata a cinya.+
Bakin laffayar ta taja ta rufe fuska wai ita jin kunya a hankali tace kunya kikeji ta daga kai kamar doluwa. Kamin tana shan hannu idonta a kasa tace ni idan zayya tana kallon film me irin sumba rude idona nakeyi saboda ba kyau. Lakutar hancinta yayi yace AI ba barsa take kalla ba film ne shiyasa ta fiki wayewa. Rufe idonki yanzuma, rufewa tayi kiri daga nan labari ya canja salonsa……
Su yazeed kuwa suna isa suka tarar da kowa an dallara su ake jira. Bude taro da addu’a akayi sannan Alhaji mansur ya fara magana
Ba komai bane ya tara mu anan wajen sai wani abin mamaki da ya riske mu lokaci daya Wanda zaiyi ma wasu dadi wasu kuma bazaiyi musu ba.
Wato alokacin da aka gwada mu domin bawa bushra bargo munyi mugun mamakin yadda akace babu Wanda nashi ya hau da nata hakan yasa likitan a sirrance yayi mana gwanin DNA yayinda ake gwada na sauran yan uwa dukda ko ba’a tsammace ya hau ba.
Ga mamakin mu sai tahau Dana matar ka ya fadi haka yana kallon yazeed. Shiru kowa yayi yaci gaba da cewa ba abin mamaki bane Dan hakan zai iya faruwa amma anfi tsammanin ya dace Dana yan uwanka na jini.
Lokacin sakamakon DNA ta fito amma likita baima nina mana yayi ba saida yayi na kowa inda ya tabbatar mana babu shakku cewa bushra ba yar mu bace yar malam Yusuf ne mahaifin minal. Zaro ido kowa yayi ana kimanin ya haka ta kasance.
Yaci gaba da cewa na gasta ne duba da kamanceceniya da sukeyi sosai idan ba ka lura ba sai ka kasa banbanta su. Wanda run a fari naji mamaki .
Yanzu Abu daya nake son tabbatarwa kallon minal yayi yace shekarunki nawa tace 36 jinjina kai yayi yace rana da wata fa tace 2nd September. Yace tabbas wannan ranan aka haifi bushra. Babu shakku ku yan biyu ne kuma yadda akayi kuka rabu Allah shine masanin. Fatan mu Allah ya hada kanku.
Baban kowa ne yayi godiya bayan sallama yace toh tunda ta tabbata yata ce amma ku kuka rikota ni bazan harbeta ba na bar muku Abu daya de za’ayi dole abi ka’idar manzon Allah ta canja sunan mahaifi amma nikam na bar muku ita tunda har tayi aure ma ba anfanin na karba.
Godiya Alhaji mansur yayi daga nan aka dan jajanta mutuwar safina kamin kowa ya warware. Inna da tsufa ya fara kamata Dan ta dara shekaru hamsin da biyar tace tace ina kishiyar tawa ne akace hajiya zayya AI gida muka barota tana wani aiki. Tace Allah yasa na arziki ne ba shirme ba. Kallon kallo sukayi sukace ameen.
Bayan watanni sahla ta sambado baby girl dinta amma CS aka Mata. Har ta fara zama zayya ta haifo yan biyunta mace da namiji.
Ranan suna bakin kabir har kunne hoto ake ta dauka shida yaja gefe ya tsaya sanda aka gama mai hoto zai tafi yace mai hoto a dakata. Tsayawa mai hotan yayi yayinda hankalin kowa ya dawo kansa dogon kujera ya zauna yana gyara link dinsa ya zaunar da yar sahla a gefensa sannan ya karbo jinjirar ya daura a cinya.
Yace kai me hoto ka daukeki nida Matana sannan ka yi mana irin rantamemen hotan nan domin acan za’a lika. Ya fadi hakan yana mai NUNI da wani fili a garin parlourn
Daya…biyu… uku aka watsa hotan yana me washe wawulonsa yayinda hular nan tayi coroi a tsakiyar ka.
Yace SHEGE NI ME MATA BIYU kowa ya fashe da dariya 😁😁
NOTE
ALHAMDULILLAH! ANAN NA KAWO KARSHEN WANNAN LITTAFI NAWA MAI FARIN JINI DA ALBARKA DA FATAN AN ILMANTU KUMA AN NISHADAN TU.